luij^lt Ail
iS^J^ ^J) A ^ A J& ^ '.^^ 4JjjJa2 ^L<l^.jJ
^jla ,jd\ ^1^)1 ^ lJU5t Ujl- J-,1 ^JUI -*vJI j*^)\ i^lUJ! v^j J» jlJ-I^ ^)\ j^)\ «a»l ^
. 3j>-Nlj L'jJI <J -up ,jPj>-\ J* «— *l>j 4Jjpj «^1>«^»I j* jli juJ . jU^ ^/-^
^L. JbJ Jl i>-U- J j^JULl ?tw?lj j>-l jUj t^j»- J ^.ajl J Cfr*J-Ji^ 4^i ^Lw f ^^1 01 kj'j Uii jUjj
^ ' * * *~~ * * * * * .
jl£- JS"\ jl **j ^f—J *£j*M **1M p-** jj*uk^i N «a^1 jl kljj ' ^^ Vdj*' <J.j* Jj <*^l>- ta^j J f ^*v'
pjuj ^^1 jT^Jl ^ J> ^1 o^JI iiiJU SyJil & £ IgJ SofUl &UI ^j U>l £JL j^jKi j*JI £11;
jl ^L.>» |iUJ» *Uj <> Cji C^»j >-Sfl £w>j, . JUII Ub Jl a^>JI tf j, i,jVl oi* j ^Ul jU ll f f^ll
U^N *^- *j>-j ±JjlJ *j>- : jj*j>- j vi>l/yi ^ i," 4^j>-JIj Njl LJ» iijf- j ^— ^ aj 4»l «dj;l L. Jp r**-^ ls^ fbu
JJj * \ ^V^ * Ip j ^ Olyiil jc— **" i^-jJ 1^-fl Jl~ ^>l Jj~ dUi *A~j . Iajc^J 5M*aJl J ^OlJll Xp \Ju U ^1
jt^iJ aJ Ixi^j t£jUU ^y* 5 ^j^ ojj-JI <r.,»../aJ ll ^-^Jl Ifp^s^ <%w jl UjU- jlyiJl j^- ^ 5j^- JS~ IJJ jl
i*>-Ju {y£~» Jl*w ^>l jj*« i^>-jJl oJUb jUjj .jj**^' <J jj^-sAflJl jIj^j v_jL—Ij Igi oL—Uilj UbJ^iL ^1 Ol/jlj 3jj*JI
. L-^Al 4iJ Jl jj-'liJI ^jS' t/**^
.oyjJI jTUI iiyJi ^jUU JJ^ JjNl : \sjV& SjuI. I^IT jj^l &X Jo^^ L.UI Jil <*>ylJI oJU jj
S-^ 1 J*" tZ-jW^ 1 vUWIj - <JA=>«^ail obT j l^uij oUKJI Jl*. ^yd Cyli i+>-jA\ oJU ^T j UU?- JliJIj
. 4-^TAJI Oj^^ii A--JL oyjJI j^^l j^j ^j-^l V^ J] [£j\aM ^Lijl V^ t^-' ^j ^^*J ■ c^^^'
e * - ■
l^pLt jlp- iUj Jjl j ^«r*^r' <^*^ X** -^JJ J^~ ^' «Jj*y ^J oly*- *-— J*^>- J J-*^l l-if: l^ 8 -^j
4Jl dUij JtJI j>«JI Jp *ly j* U Jb ^ ISJ : Ifpy j^ JjNl U>-JlJI ^ i*>-JlJI oo* jl L. JT «Jyj. Uij
jj*p oljj U ^>t-^2iJ ijjl { j~-£ : \*)j£i ^j* "^ry. ^*^ t* Cf^ ljl^« ^ ^^ tUa^-Nl Jp /*1^ ^*J>*i <>■ J ^vr*"
4»U i^U Jj i.lp A^%*y\ Ia^ (e>- J*jJI IJla ^-^1 a*j ^ jl^o N SupU* *»ai L^!^ dUi w . <-~* t»
■ ^^ Oi' c>* J^ 1 4^ ^V cf^ «J'j J!^H J^ 1 <^J^ <J' Jj>-^' ci^J 4>V
*N> ji t^l oNl^ jj *^ fcH< aiJ| Jut J i*^-jJI oo* j UIopLj: j^.ii ji ^j^i ^ailj
. \^>^^£ 3 l^rj$\ 3*ly ^ <o ^U ll L-IT iNj Jlj jil ^\L JU^I ili-Nlj ( jSL*>) <UliJI j\> ^ y\ < y>\±jfo\
jjbti j^ji ij^. f u joj . ou&ij oi/yi ju. jp j^-i j*~j ouKu ^^.uji v i^ii >.T j t y 9r3 *u^S/i
**^pl Jp !iU^ la* UUp Oj^oj li-^>- U jikjj e*-L^ H*rJ Call>- 1*^^- IJLa ULp J*^ jl -ail JLJ l^-lj
ja pJp 4»l m\ JJ.JUI £ UljU ijLl J«£j S^Nl^ LjJI j bj^j ( <^iJ\<3-J-) *^ d -^* ti ^ >^j *»' i*^"
.^J-Uailj *IJl^-iJlj ^iJUaJl^ crj^Jl
Gabatarwa
Yabo da godiya su tabbata ga Allah Mai girma, Mai rahama, Mai jin Rai, Ubangijin halittu,
Wanda Ya aiko shugabanmu Muhammad, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da littafinSa
mai bayani domin ya shiryar da mutane da aljannu game da shi. Wanda ya karbi kiransa ya yi aiki da
abin da ya kawo masa, shi ne mai arziki a duniya da Lahira, kuma wanda ya kafirce masa, ga bin son
zuciyarsa, shi ne tababbe.
Bayan haka, lokacin da ya zamana adadin Musulmi na Raruwa kullum a Rasarmu, Afirka Ta
Yamma, Raruwa mai tsananin yawa, kuma mafi yawan Musulminta suna magana da harshen Hausa
ne, kuma ba kowane Musulmi ke iya koyon Larabci ba, saboda halayen da duniya take ciki yanzu,
FCungiyar Rabidatul Alam el-lslaml ta ga ba makawa ga bukatar a yi tarjamar ma'anonin AlRur'ani
mai girma da littafan addini na Larabci, a cikin harshen Hausa, don amfanin ya hada dukan Musulmi,
su koyi addininsu kamar yadda Allah Ya saukar da shi, don su sami babban rabo.
Mun fara tarjamar tun farko da juzu'i na cfaya na Tabaraka da Amma, domin shi ne mafi yawan
mutane ke tsayawa a kai don karatun sallarsu. Da sannu, kuma da yardar Allah, muka kammala
tarjamar AlRur'ani gaba daya, wanda aka wallafa shi cikin 1979.
A kowane farkon sura ana bayar da taRaitaccen bayanin abin da ta kunsa ko take karantarwa
domin mai karatu ya ji sauRin gane ma'anonin ayoyin surar da dangantakarsu.
In Allah Ya so za mu bi bayan wannan da tarjamar littafan tafsirai cikin harshen Hausa.
A wannan wallafar an sami Rarin abubuwa uku : akwai jagora ga mai karatu, inda aka yi bayanin
ina ake tsayawa. Sai kuma Raramin Ramus dauke da kalmomin da ke bukatar fassara. Abu na uku shi
ne fihirisa cikin tsarin abacada.
Kamar yadda aka yi a shiri na farko, a wannan ma an ci gaba da nuna alamar jan sauti a ajamin
boko.
Bayan shekara bakwai na hidimar bugawa ta farko, wannan aiki ya sami karbuwa ga hannun
mutane, kuma sun ba da taimako mai yawa wajen gyara shi zuwa ga wannan matsayi. Akwai wanda
ya karanta da niyyar alheri, kuma akwai wanda ya karanta da niyyar suka, amma su duka sun gamu a
kan abin da ya zama alheri ga Musulmi. Allah Ya saka ma dukansu da alheri.
Akwai mutane da dama da suka taimaka wajen shirya tarjamar nan. Da farko dai muna mika
godiyannu don goyon bayan da muke samu daga Abubakar III (Sokoto). Sai kuma Malam
Ahmad, dan Walin Katsina, Malam Bello, wanda ya taimaka kwarai da karanta abin da ya sawwaRa.
Malam Inuwa Diko, dan Alhaji Adamu B. Diko na Zaria, ya dauki nauyin tsara dukan wannan
aiki a cikin layi kuma ya tsara jagorar karatu, Ramus da fihirisa don taimakon mai karatu ga fahimtar
kalmomi masu wuya da neman ayoyin da suka shafi hukunce-hukunce dabam-dabam a cikin surori
dabam-dabam ta hanya mai sauki. Ya dauki nauyin wannan aiki a cikin shekara biyu. Allah Ya saka
masa da irin sakamakon wadanda suka tsayu ga aiki na gina addinin Allah.
Muna fata Allah Ya karbi aikinmu gaba daya, ya zama sanadin daukakar addinin Musulunci a
wannan Rasa, mu kuma Ya saka mana da alheri, mu da duk wanda ke yin aiki domin Allah. Allah Ya
sa aikinmu ya zama sanadin shigarmu Aljanna, a Lahira, tare da manyan mutanen da Ya yi wa ni'ima,
daga Annabawa da siddiRai da shuhada'u da kuma salihai.
Amin.
Abubakar Mahmud Gumi
^v$%.
V^-^y ^' (J^ JL *^ Oi^A' ***** ci^ f^-^b S^LgflJlj ^OlUJI ^ aJLI juJ-I
r Jijo L«l ... ^jv*^l
f£$\ <ij| c^li^ 4jLjJI J <dJl 4jai>- jybytJl Cj*J*-\ f 3l>- olfOj-jd UL5>*ii
OvJuJb 4-Jbc* jy~J3j* jvJLil l£*^I 0^ OjL£*liU O^JtJ jfr—^J .lp fT***^ ^W^M vA^UJ
diill o^^iJl o^ 1 f ^ £*^ ^^ iL ^ 1 Cj* Jf ^ ^J 1 * 1 " J* **H>
^^L-Vl 1UJI ik,^ oUJt ilSfy 3,^1 oalli vJuyJl cJl>c-JlI ipLUJ Ji«i
oU13l J[ ^1 jTyiil JUc i*^ i^^L-Nl jljdJl J jwjkJI *Up ^Ua5^l J
jjJLAl ^ v^Jb^i ^1 oUUl g* Jl JULI dJUL- c > Jl a^UJJ dUi, i~*-Sll
. aJUI ^ j}3 Jaii JUJ J 4jj^; ^pAs^JJ N ^^
.. A-ftJSS l^LA\ i^Sj, \jyHy .. <^5y.[ j^Ll Ul^ : JU; aJ^L UUIj
^•1 (^JJl 4yL-jAI 4*iJl J} <UU* i^i ±juj£i\ ^Jl>^^S lJUb *JLoi jl UJl*~o
^^J\^\ u J^r\ yi& ^yr 2y£- y^i ci' 7*~*^ *U*-ii 1^^ f^ ^5% ^' 4fei>-
fjip j ^ah^JlI j_£p ^T i^i ju^ iiiJ^i 4JU1 dyu fU aij (-Mr<\v-\r 4 \\)
5^}*>Ul oU*s>c-*aiSl i^^-ty: Ij^>*-j J ^L jl^-I aa>»U- (J i-^ll jiX« v^!J L^jAI i«J
. ^%^l (IUJI i^b l,^ cJ5il,j
cccc
J-s-Jl frl^-. ^JJ ^iU» 4lHj
-£*■
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
Wannan AlCur'ani yana shiryarwa ga abin da yake mafi kyau kuma madaidaici.
Muna farawa da ambaton sunan Allah Mai gamammen jin Rai a nan duniya,
Mai ke&antaccen jin £ai gobe Kiyama.
Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai tsira da aminci su tabbata ga
Shugaban Manzanni Muhammadu, da 'yan 'uwansa muminai.
Bayan haka, akan mu tabbatar da manufar mai kula da masallatai masu alfarma
guda biyu ta kula da Littafin Allah Mai Girma da son sawwaRewar fahimtarsa a
cikin harshe daban-daban don haka aka damRa wannan aiki a hannun masu buga
AlRur'ani Mai Girma a wuri da aka tanada musamman na Sarki Fahad don buga
Kur'ani Mai Girma a Madinatul Munawwara garin Manzo.
Tare da hacfin guiwar Ma'aikatar wuri da aka tanada don buga Alfeir'ani Mai
Girma a Madinatul Munawwara, da kuma Kungiyar hacBn Kan Musulmin Duniya,
sai suka za5o malaman tafsiri dagaRasashenMusulunci daban-daban don su fassara
ma'anonin AlRur'ani Mai Girma cikin harussa daban-daban don abin ya yacht.
Sabo da imani da maganar Allah Madaukaki da ya ce, "Lalle, Muminnai
yan'uwa ne." Kuma sabo da wajabcin taimakon juna a cikin Musulumci, yana
faranta rayukan mu,mu gabatar da wannan AlRur'ani Mai Girma a cikin tarjamar
ma'anoninsa a cikin lugar Hausa, wanda Mai kula da Masallatia biyu masu alfarma
ya yi umarni da bugashi, kuma Mai watsa Littafen Allah Mai Girma, Sarki Fahad
Dan Abdul Azeez Ali Sa'ud, Allah ya tsare shi, wanda Sheikh Abubakar Mahmoud
Gumi, dan majalisar asali ta Rabidatul Alamil lslami, ya fassara a cikin harshen
Hausa. Lalle, wannan aiki, na tarjamar, ya cfauki shekaru bakwai (1391-1399 H).
Kuma da taimakon Allah, Mallam Muhammad Inwa Adamu Dikko, wanda ya
keBanta da sannan lugar Hausa, kuma mataimakin Shugan Labararen Jami'ar
Ahmad Bello, a Nigeria, ya tsayu da gyaran kurakuran masu bugawa. Kuma
Jam'iyyar Rabidatul Alamil lslami (ta duniya) ta yarda da dukan aikin.
Allah ne Mai Shiryarwa zuwa ga tafarki madaidaici.
ALKUR'XNI DA AKA BUGA CIKIN
MADINA GARIN MANZO.
Wannan AlJcur'ani Mai Girma Da Tarjamar Ma'anoninsa kyauta ne daga Mai kula da Masallatai biyu masu alfarma,
Sarki Fahd Dan Abdul Azeez. Ba ya halatta a sayar da shi, domin waRafi ne domin Allah Mai Girma.
Wuri Da Aka Tanada Musamman
Don Buga AlRur'ani Mai Girma Na Mai Kula
Da Masallatai Biyu Masu Tsarki Sarki Fahad.
«■■> .'
I jr,r
^
4 Tit 4*
I *'*
1 — Suratul Fatiha
t^sfe->
Ayoyinta 7 ne. Ana kiran ta Uwar Littafi domin ta tara ilmin
da yake a cikin Alkur'ani a dunkule. Basmala a cikinta take ga
£ira'ar Asim, ruwayar Hafs, amma banda ga kira'ar Warsh.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Da sunan Allah, Mai rahama,
Mai jin kai.
2. Godiya ta tabbata ga Allah,
Ubangijin halittu;
3. Mai rahama, Mai jin kai;
4. Mai nuna Mulkin Ranar
Sakamako.
5. Kai muke bauta wa, kuma
Kai muke neman taimakonKa.
6. Ka shiryar da mu ga hanya
madaidaiciya,
7. Hanyar wadanda Ka yi wa
ni'ima, ba wadanda aka yi wa fushi
ba, kuma ba 6atattu ba (1) .
(1) Da cewa Ubangijin halittu ya tara ilmin tauhidi na Ilahiyya da Rububiyya, Mai
rahama ya tara dukan rahamar duniya da rayarwa da matarwa da ciyarwa da shayarwa da
tufatarwa. Mai jin 2ai ya tara ni'imar duniya mai dogewa zuwa Lahira kamar imani da na
Lahira. Mai mallaka ko Mai nuna mulkin ranar sakamako, ya hacfa dukan wa'azi.Kai
muke bauta wa kuma Kai muke neman taimako, ya tara tauhidin Ilahiyya da ibada
amaliyya ko kauhyya. Hanya madaidaiciya, ta hacfa dukan sharTa da hukunce-hukunce.
Wadanda aka yi wa ni'ima, ya tara dukan tarihin mutanen kirki. Wacfanda aka yi wa fushi,
ya tara dukan tarihin masu tsaurin kai. TSatattu, ya tara tarihin dukan mai aiki da jahilci ko
6ata.
2 — Suratul Balcara
mm-<
Tana karantar da kira zuwa ga addlni da yadda ake ginin
sabuwar al'umma daga mutane daban-daban, na Jahiliyya.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L A. L. M.
2. Wancan ne Littafi, babu
shakka a cikinsa, shiriya ne ga masu
takawa. (1)
3. Wacfanda suke yin imani
game da gaibi, kuma suna tsayar da
salla, kuma daga abin da Muka
arzuta su suna ciyarwa;
4. Kuma wadanda suke yin
imani da abin da aka saukar zuwa
gare ka, da abin da aka saukar daga
gabaninka, kuma game da Lahira
suna yin yaicini.
5. Wadannan suna kan shiriya,
daga Ubangijinsu, kuma wadannan
su ne masu cin nasara.
(1) Ya sifanta Littafi; watau Alloir'ani da kamala ya ce "wancan" maimakon
"wannan" domin masu son su yi aiki da shi, su ne masu talcawa. Talcawa na da sharudxfa
biyu, su ne Imani da aiki da abin da manzancin Annabi Muhammadu ya £unsa. Sa'an nan
mutane a farkon Musulunci ko a inda Musulunci yake sabo, sun kasu kashi hudu. Kashi
na farko su ne masu talcawa wadanda aka facfi sifofinsu a nan.
Suratul Ba£ara
mm-*
6. Lalle ne, wacTanda suka ka-
firta (1) daidai ne a kansu, shin ka yi
musu gargadi ko ba ka yi musu
gargacfi ba, ba za su yi Imani ba.
7. Allah Ya sa hatimi a kan zu-
katansu, da a kan jinsu, kuma a
kan ganin su akwai wata yana;
kuma suna da wata azaba mai
girma.
8. Kuma akwai daga mutane
wanda (2) yake cewa: "Mun yi Imani
da Allah kuma da Yinin Lahira,"
alhali kuwa su ba muminai ba.
9. Suna yaudarayya da Allah da
wadanda suka yi imani, alhali ba su
yaudarar kowa face kansu, kuma
ba su sakankancewa!
10. A cikin zukatansu akwai
wata cuta ; sai Allah Ya kara musu
wata cuta, kuma suna da azaba mai
racfadl saboda abin da suka kasance
suna yi na karya.
11. Kuma idan aka ce musu:
"Kada ku yi barna a cikin kasa,"
sukan ce: "Mu masu kyautatawa
kawai ne"!
12. To, lalle ne su, su ne masu
Barna, kuma amma ba su sansan-
cewa.
13. Kuma idan aka ce musu:
"Ku yi Imani kamar yadda mutane
3 bj&ypjfipr
\- \ y t^i''-'
1 S " yi *>> '\'<> »
El oj> jSolyS UjjiJ^^ J^rt-*3j
(1) Kashi na biyu daga cikin jama'a su ne kafiran da suka doge a kan kafircinsu, babu
wani gisshi kuma Allah Ya san ba za su musulunta ba.
(2) Kashi na uku su ne munafukai da suka bayyana Musulunci da baki amma
zuciyarsu tana a kan kafirci.
2 — Suratul Bakara
Wm~*
^uka yi imani", sukan ce : "Za mu yi
Tmani ne kamar yadda wawaye suka
yilmani?" — To, lalle ne su, su ne
wawaye, kuma amma ba su sani.
14. Kuma idan sun hadu da wa-
rfanda suka yi imani, sukan ce:
"Mun yi Tmani." Kuma idan sun
wofinta zuwa ga shaicfanunsu, (1)
sukan ce: "Lalle ne, muna tare da
ku: Mu masu izgili kawai ne."
15. Allah Yana yin izgili (2) gare
su kuma Yana taimakon su a cikin
Batarsu, suna cfimuwa.
16. Warfannan su ne warfanda
suka sayi Batajla shiriya, sai fatau-
cinsu bai yi riba ba, kuma ba su
kasance masu shiryuwa ba.
17. Misalinsu (3) shi ne kamar
misalin wanda ya hura wuta, to, a
lokacin da ta haskake abin da yake
gefensa (na abin tsoro), Allah Ya
tafi da haskensu, kuma Ya bar su a
cikin duffai, ba su gani.
18. Kurame, bebayen makafi,
saboda haka ba su komowa.
\i£&\ity£\jZ\z#&\jS\l£
'S < • ss
(1) Kashi na hucfu su ne Yahudawa wacfanda suke sun san gaskiyar annabcin
Muhammadu da manzancinsa, amma hasada ta hana su su bi shi, suna kokarin 6ata abin
da ya zo da shi ta hanyar jefa shibhohi a ciki, domin su kange mutane daga shigarsa.
Saboda haka aka ce musu shaicfanu. Duk wanda ya san gaskiya amma kuma ya yi girman
kai daga binta, to, shi ne shaicfan, daga aljannu ko daga mutane.
(2) Allah Yana mayar masu da sakamakon izgilinsu.
(3) Allah Ya bayyana misalin munafuki da misalai biyu, na farko, kamar mutum a
cikin duhu, yana kewaye da abubuwan ban tsoro bai sani ba, sai ya hura wuta, ta yi haske
ya ga abubuwan na ban tsoron sa'an nan wutar ta mutu, ta bar shi a cikin duhu, sai tsdron
ya hauhawu a kansa. Haka munafuki yake a bayan ya yi ikrari da Musulunci,_a kullum
yana cikin tsoron abin da za a ce a kansa. Ana sifanta hasken wuta da hasken imaninsa.
Bayan hasken ya tafi, sai ya zama kurma, bebe makaho, saboda haka ba ya magantuwa.
2 — Suratul Bakara
$ffi$8£-t
19. Ko kuwa kamar girgije mai
zuba (1) daga sama, a cikinsa akwai
duffai da tsawa da walkiya: Suna
sanyawar yatsunsu a cikin kunnu-
wansu daga tsawarwakin, domin
tsoron mutuwa. Kuma Allah Mai
kewayewa ne ga kafirai!
20. Walkiyar tana yin kusa ta
fizge gannansu, ko da yaushe ta
haskaka musu, sai su yi tafiya a
cikinta, kuma idan ta yi duhu a
kansu, sai su yi tsaye. Kuma da
Allah Ya so, sai Ya tafi da jinsu da
gannansu. Lalle ne Allah a kan
dukan kome Mai ikon yi ne.
21. Ya ku mutane! Ku bauta (2)
wa Ubangijinku, Wanda Ya halicce
ku, ku da wadanda suke daga gaba-
ninku, tsammaninku, ku kare
kanku !
22. Wanda Ya sanya muku kasa
shimfkfa, kuma sama gini, kuma Ya
saukar da ruwa daga sama, sa'an
nan Ya fitar da abinci daga 'ya'yan
itace game da shi, saboda ku.
Saboda haka^kada ku sanya wa
Allah wasu kishiyoyi, alhali kuwa
kuna sane.
23. Kuma idan kun kasance a
cikin shakka daga abin da Muka
ifis*' -f\\t\ > >^t^ z *At'<'
^^ s * * * ^ * " ^ *' ' \fs
^^^^1^
(1) Misali na biyu munafukai suna kamar matafa a cikin jeji da dare, ruwa kuma ya
same su a cikin duhu, ba su iya motsawa sai da walkiya, watau ayar da suke so, kuma ga jin
tsoron tsawa ; watau bayanin halayensu a cikin Alkur'ani, ba su son su ji, har suna sanya
kanun yatsunsu suna toshe kunnuwansu, domin kada su ji. Ganin ido da basira da jin
kunne da na hankali duk daya suke, Allah Yana iya karbe su ya bar su a cikin dimuwa.
(2) Bayan ya gama fadin kasusuwan mutane da sifofinsu, sai kuma ya kira su gaba
daya zuwa ga bauta Masa, Shi kadai. Ma'anar bauta Masa Shi kacfai, kowa ya ajiye
al'adarsa, ya koma ga hukuncin Allah kawai; umurni ko hani. Wanda ya bi wani hukunci
na al'adarsa, ya bar abin da Allah Ya ce, to, shi ya sanya wa Allah kishiya ke nan.
2 — Suratul Bakara
i&S&-x
sassaukar ga BawanMu, to, ku zo
da Sura guda daga misalinsa
(Alkur'ani). Kuma ku kirawo shai-
dunku, (1) baicin Allah, idan kun
kasance masu gaskiya.
24. To, idan ba ku aikata (kawo
Sura) ba, to, ba za ku aikata ba.
Saboda haka ku ji tsoron Wuta
wadda makamashinta mutane da
duwatsu ne, an yi tattalinta domin
kafirai.
25. Kumakabayardabisharaga
wacfanda suka yi imani, kuma suka
aikata ayyuka na kwarai, cewa lalle
ne, suna da gidajen Aljanna,
koramu na gudana daga karka-
shinsu. Ko da yaushe aka arzuta su
da abinci daga wasu 'ya'yan itace
daga gare su, (2) sai su ce: "Wannan
shi ne aka arzuta mu da shi daga
gabanin haka." Kuma a je musu da
shi yana mai kama da juna. Kuma
suna da, a cikinsu, matan aure masu
tsarki, kuma su, a cikinsu madaw-
wama ne.
26. Lalle ne, Allah ba Ya jin
kunyar Ya bayyana wani misali,
kowane iri ne, sauro da abin da
yake bisa gare jhi. To, amma
wacfanda suka yi Imani, sai su san
cewa lalle shi ne gaskiya daga
Ubangijinsu, kuma amma wacfanda
suka kafirta, sai su ce: "Mene ne
?• >*■?':•>'•' X"*^'"
(1) Gumakanku su taimake ku kera sura mai kama da Alkur'ani wajen fasaha da tsari
da kawo asirai. An ce wa gumaka shaidu domin suna cewa su ne za su yi musu shaida a
Ranar ICiyama, kuma su cece su, kuma ko da yaushe suna tare da su.
(2) Gonaki ko gidajen Aljanna.
2 — Suratul Baicara
m\m-<
Allah Ya yi nufi da wannan (1) ya
zama misali?" Yana 6atar da wasu
masu yawa da shi, kuma Yana shir-
yar da wasu masu yawa da shi,
kuma ba Ya Batarwa da shi face
fasikai.
27. Wadanda suke warware
alkawarin Allah daga bayan kulla
shi, kuma su yanke abin da Allah
Ya yi umurni da shi a sadar, kuma
suna 6arna a cikin kasa, wadannan
su ne masu hasara.
28. Yaya kuke kafirta da Allah,
alhali kuwa kun kasance matattu
sa'an nan Ya rayar da ku, sa'an nan
kuma Ya matar da ku, sa'an nan
kuma Ya raya ku, sa'an nan kuma
zuwa gare Shi ake mayar da ku?
29. Shi ne Wanda Ya halitta
muku abin da ke a cikin kasa gaba
daya, sa'an nan kuma Ya dai-
daita (2) zuwa sama sa'an nan Ya
aikata su, sammai bakwai. Kuma
Shi ga dukan kome Masani ne.
30. Kuma a lokacin da Ubangi-
jinka Ya ce ga mala'iku: "Lalle ne,
Ni Mai sanya wani halifa ne a cikin
kasa," suka ce: "Ashe, za Ka sanya
a cikinta, wanda zai yi 6arna a
cikinta, kuma ya zubar da jinainai,
alhali kuwa mu, muna yi Maka
tasbihi game da gode Maka,
*ss J . '
**-> ^S-b-VJ i^; 4 ^* *-£id-*&i ^-~*
» < •' r it'*'' > £ ' ' At
W&j~.Ji4ft
(1) Misali da kamar matan Aljanna masu tsarki. Ba mata ba ko da sauro ko abin da
ya fi, ko ya kasa sauro, to, akwai hikima a cikin halittarsa, wadda za ta jawo hankalin mai
hankali ga Tmani da Allah saboda ita.
(2) Ya daidaita, watau Ya yi nufi; "sa'an nan" yana amfanar da jeranta aiki ba
jerantar nufi ba, domin sifofin Allah dukansu, ba fararru ba ne.
2 — Suratul Bakara
W&&-*
kuma (1) muna tsarkakewa gare
Ka" Ya ce: "Lalle ne Ni, Na san
abin da ba ku sani ba."
31. Kuma Ya sanar da Adam
sunaye dukansu, sa'an nan kuma ya
gitta su a kan mala'iku, sa'an nan
Ya ce: "Ku gaya Mini sunayen
wacfannan, idan kun kasance masu
gaskiya."
32. Suka ce: "Tsarki ya tabbata
a gare Ka ! Babu sani a gare mu face
abin da Ka sanar da mu, lalle ne
Kai, Kai ne Masani, Mai hikima."
33. Ya ce : " Ya Adam ! Ka gaya
musu sunayensu." To, a lokacin da
ya gaya musu sunayensu, (Allah)
Ya ce: "Ashe, ban ce muku (2) ba,
lalle Ni, Ina sane da gaibin sammai
da kasa, kuma (Ina sane da) abin da
kuke bayyanawa da abin da kuka
kasance kuna 66yewa?"
34. Kuma a lokacin da Muka ce
ga mala'iku: "Ku yi sujada ga
Adam," sai suka yi sujada, face
Ibifisa ya ki, kuma ya yi girman kai,
kuma ya kasance daga kafirai.
35. Kuma Muka ce : "Ya Adam !
Ka zauna, kai da matarka a Al-
janna, kuma ku ci daga gare ta, bisa
wadata, inda kuke so, kuma kada
ku kusanci wannan itaciya, har ku
kasance daga azzalumai."
^t^f^ V s
t^h< - y *> *c t
(1) Mala'iku sun yi tambaya ne irin ta mai neman ya rinjayi mai jayayya da shi ga
neman haliftaka a kan kasa. Sun san halayen jinn da bunn wacfanda suka fara zama a kan
kasa suka yi Barna da zubar da jini.
(2) Wannan kissa ta nuna cewa shugabanci da ilmi ake yin sa, ba da^awan ibada
wadda mutum yake keftanta da yin ta ba. Domin an nuna wa mala'iku fifitar Adam a
kansu da ilmi, ba da ibada ba. Kuma da wannan sifa zai zama Hallfa, ko da Iblis bai fitar
da shi ba, daga cikin Aljanna, zai fita ta wata hanya domin zartar da hukuncin Allah.
10
2 — Siiratul Bakara
mm-<
36. Sai Shaidan ya talala6antar
da su daga barinta, sai ya fitar da su
daga abin da suka kasance a ci-
kinsa. Kuma Muka ce: "Ku sauka,
sashenku, na makiyi ga sashe, kuma
kuna da, a cikin kasa, matabbata da
jin dadi zuwa ga wani lokaci."
37. Sai Adam ya kar6i wasu kal-
momi daga Ubangijinsa, saboda
haka Ya kar6i tuba a kansa. Lalle
ne Shi, Shi ne Mai karbar tuba, Mai
jin kai.
38. Muka ce: "Ku sauka daga
gare ta gaba tfaya. To, imma lalle
shiriya ta je muku daga gare Ni, to,
wanda ya bi shiriyaTa, to, babu
tsoro a kansu, kuma ba su yin bakin
tiki."
39. "Kuma warfanda suka ka-
firta, kuma suka karyata game da
ayoyinMu, wadannan su ne abokan
Wuta; su a cikinta madawwama
ne."
40. Ya BanTlsra'Tla (1) ! ku tuna
ni'imaTa, wadda Na ni'imta a
kanku, kuma ku cika alkawariNa,
In cika muku da alkawarinku.
Kuma Ni, ku ji tsoroNa.
41. Kuma ku yi Tmani da abin da
Na saukar, yana mai gaskatawa ga
abin da yake tare da ku, kuma kada
ku kasance farkon kafiri game da
4~dt
J^^j^jj^j^^^ ly*^ WSJ
£-"
cei
' '■" ii-iTGs
4£^tf^&)jft*&\>
»< •> .,<!-'• '>
(1) Bayan kiran mutane gaba cfaya zuwa ga addinin Musulunci, sai kuma ya ke6ance
Yahudu da kira zuwa ga addinin, domin sun bambanta da sauran kafirai, saboda ilminsu
ga gaskiyar Musulunci. Ya gabata cewa jama'ar, kashi hudu ce; muminai, da kafiran
Larabawan da ba za su musulunta ba, da munafukai da Yahudu. Ya kira Yahudu da Bani
Isra'ila, domin Ya tunatar da su, cewa ana kiransu ne zuwa ga addini irin na ubansu
Ya'a£ubu bawan Allah.
11
Suratul Baicara
ftSWiS^-r
shi. Kuma kada ku sayi 'yan kucfi
kacfan da ayoyiNa. Kuma ku ji
tsoroNa, NT Kacfai.
42. Kuma kada ku lulluBe gas-
kiya da karya, kuma ku 66ye gas-
kiya, alhali kuwa kuna sane.
43. Kuma ku tsayar da salla;
kuma ku bayar da zakka; kuma ku
yi ruku'i tare da masu yin ruku'i.
44. Shin, kuna umurnin mutane
da alheri, kuma ku manta da kanku
alhali kuwa kuna karatun Littafi?
Shin, ba za ku hankalta ba?
45. Kuma ku nemi taimako da
yin hakuri, da salla : Kuma lalle ne
ita, haklka, mai girma ce face fa a
kan masu tsoron Allah.
46. Wacfanda suka tabbata cewa
lalle ne su masu hacfuwa ne da
Ubangijinsu, kuma lalle ne su zuwa
gare Shi masu komawa ne.
47. Ya Bani Isra'ila! Ku tuna
ni'imaTa, wadda Na ni'imta^a
kanku, kuma lalle ne Ni, Na fifita
ku a kan talikai.
48. Kuma kuji tsoron wani yini,
(a cikinsa) rai ba ya wadatar da
wani rai da kome, kuma ba a karBar
ceto daga gare shi, kuma ba a kama
musanya daga gare shi, kuma ba su
zama ana taimakon su ba.
49. Kuma a lokacin da Muka
tsirar da ku daga mutanen Fir'au-
na, suna taya muku mugunyar aza-
ba, suna yayyanke cfiyanku maza
kuma suna rayar da matanku.
Kuma a cikin wancan akwai jarra-
bawa mai girma daga Ubangijinku.
itAi;
>^ >
'^OJpA*
Out
12
2 — Suratul Ba£ara
«SgHiSS-r
50. Kuma a lokacin da Muka
raba teku saboda ku, sai Muka
tsirar da ku, kuma Muka nutsar da
mutanen Fir'auna, alhali kuwa ku,
kuna kallo.
57. Kuma a lokacin da Muka yi
wa'adi ga Musa, dare arba'in, sa'an
nan kuma kuka riki maraki daga
bayansa, alhali ku, kuna masu za-
lunci (da bauta masa).
52. Sa'an nan kuma Muka yafe
muku daga bayan wancan,
tsammaninku, kuna godewa.
53. Kuma a lokacin da Muka bai
wa Musa Littafi da Rarrabewa,
tsammaninku, kuna shiryuwa.
54. Kuma a lokacin da Musa ya
ce ga mutanensa: "Ya mutanena!
Lalle ne ku, kun zalunci kanku
game da rikonku marakin, sai ku
tuba zuwa ga Mahaliccinku, sai ku
kashe kanku. Wancan ne mafi al-
heri a gare ku a wurin Mahalic-
cinku. Sa'an nan Ya karbi tuba a
kanku. Lalle ne Shi, Shi ne Mai
karbar tuba, Mai jin kai."
55. Kuma a lokacin da Joika ce :
"Ya Musa! Ba za mu yi Tmani ba
dominka, sai mun ga Allah bayy-
ane," saboda haka tsawar nan ta
kama ku, alhali kuwa kuna kallo.
56. Sa'an nan kuma Muka tayar
da ku daga bayan mutuwarku,
tsammaninku, kuna godewa.
57. Kuma Muka sanya girgije ya
yi inuwa a kanku, kuma Muka
saukar da darba da tantabaru a
kanku: "Ku ci daga masu dacfin
abin da Muka arzuta ku." Kuma ba
'\- tit' ' 's\i *■ >\""\' T\ '
set ". *' '{%' ** \ ^ >'~*\z •. x-
^4-O'^V ^ ^ < * *itft*'* Si's
13
2 — Suratul Baicara
SSRigg-f
su zalunce Mu ba, kuma amma
kansu suka kasance suna zalunta.
58. Kuma a lokacin da Muka ce :
"Ku shiga wannan alkarya. Sa'an
nan ku ci daga gare ta, inda kuka so,
bisa wadata, kuma ku shiga kofa
kuna masu tawalu'i, kuma ku ce:
"Kayar da zunubai" Mu gafarta
muku laifukanku, kuma za Mu
kara wa masu kyautatawa.
59. Sai wacfanda suka yi zalunci
suka sake magana watar wannan da
aka ce musu, saboda haka Muka
saukar a kan wacfanda suka yi za-
lunci da azaba daga sama saboda
abin da suka kasance suna yi na
fasikanci.
60. Kuma a lokacin da Musa ya
nemi shayarwa domin mutanensa,
Muka ce: "Ka doki dutsen da san-
darka." Sai marmaro joma sha
biyu suka 6u66uga, hakika, kowa-
cfanne mutane sun san wurin
shansu. "Ku ci kuma ku sha daga
arzikin Ubangijinku, kuma kada ku
yi fasadi, a cikin kasa, kuna masu
6arna."
61. Kuma a lokacin da kuka ce:
"Ya Musa ! Ba za mu yi hakuri ba a
kan abinci guda. Sai ka roka mana
Ubangijinka, Ya fitar mana daga
abin da kasa take tsirarwa daga
ganyenta, da dumanta, da alka-
marta, da wakenta, da albasarta."
Ya ce : "Kuna neman musanya abin
da yake mafi kaskanci da wanda
yake mafi alheri? Ku sauka Masar,
domin lalle ne, kuna da abin da
kuka roka". Kuma Muka doka
musu wulakanci da talauci. Kuma
<P sji&^^yfjhcQ
14
Suratul Ba£ara
mssz-v
suka koma da wani fushi daga Al-
lah. Wancan saboda lalle ne su, sun
kasance suna kafirta game da
ayoyin Allah, kuma suna kashe
annabawa, ba da hakki ba. Wan-
can, saboda sabawarsu ne, kuma
sun kasance suna ketarewar haddi.
62. Lalle ne wadanda suka yi
imani, da wadanda suka tuba (1) , da
Nasara da Makarkata, wanda ya
yi Imani da Allah da kuma Yinin
Lahira, kuma ya aikata aikin
kwarai, to, suna da ijararsu a wurin
Ubangijinsu, kuma babu tsoro a
kansu, kuma ba su zama suna yin
bakin ciki ba.
63. Kuma a lokacin da Muka
riki alkawarinku, kuma Muka
daukaka dutse bisa gare ku: "Ku
kama abin da Muka ba ku da karfi.
Kuma ku ambaci abin da yake a
cikinsa, tsammaninku, ku kare
kanku."
64. Sa'an nan kuma kuka juya
daga bayan wancan, to, ba domin
falalar Allah ba a kanku da raha-
marSa, haklka, da kun kasance
daga masu hasara.
65. Kuma lalle ne, hakika, kun
san wadanda suka ketare haddi
daga gare ku a cikin Asabar, sai
Muka ce musu: "Ku kasance birai
kaskantattu."
^v^jij \^\^<j^\j \JS\*l?j&\Q
/i'f . »-*•
JU3l
jjid \ X3y \ss3jj psJji^u -A>-1 jlj
(1) Wacfanda suka koma; watau Yahudu, daga maganar Musa, "Mun koma gare
Ka" Sura ta 7 aya ta 1 56, kuma Makarkata, jama'a ce daga Larabawa suka karkata daga
addinin ubanninsu zuwa ga bauta wa mala'iku. A farkon Musulunci suna cewa ga wanda
ya musulunta, wai ya yi kama da su.
15
Suratul Ba£ara
w$\m-
66. Muka sanya ta (mas'alar)
azaba, domin abin da yake a gaba
gare ta, da abin da yake a bayanta,
kuma wa'azi ga masu takawa.
67. Kuma a lokacin da Musa ya
ce ga mutanensa: "Lalle ne, Allah
Yana umumin ku da ku yanka wata
saniya." Suka ce : "Shin, kana ri£on
mu ne da izgfli ?" Ya ce : "Ina neman
tsari ga Allah da in kasance daga
jahilai."
68. Suka ce: "Ka ro£a mana
Ubangijinka, Ya bayyana mana,
mece ce ita?" Ya ce: "Lalle ne Shi,
Yana cewa: 'Lalle ne ita saniya ce,
ba tsofuwa ba, kuma ba budurwa
ba, tsattsaki ce a tsakanin wancan,'
sai ku aikata abin da ake umurnin
ku."
69. Suka ce: "Ka ro£a mana
Ubangijinka, Ya bayyana mana
abin da yake launinta." Ya ce:
"Lalle ne, Shi, Yana cewa: 'Ita
wata saniya ce fatsi, mai tsantsan
launinta, tana faranta ran masu
kallo."'
70. Suka ce: "Ka ro£a mana
Ubangijinka, Ya nuna mana abin
da yake ita, lalle ne shanu suna yi
mana kama da juna, kuma mu, idan
Allah Ya so, hakTka, masu shiryuwa
ne."
71. Ya ce: "Lalle ne Shi, Yana
cewa: 'Ita wata saniya ce, ba ho-
rarra ba tana noman £asa, kuma ba
ta shayar da shuka, lafiyayya ce,
babu wani sofane a cikinta.'" Suka
ce: "Yanzu ka zo da gaskiya." Sai
suka yanka ta, kamar ba za su
aikata ba.
^H " -/it - f ~"
\'> S\»- \f ix' T ' » ' -'\"\ \ *~ ' > *.\
, s sss-»* '
M bj-t+J 4i\ *li o^LS^LJ^
16
2 — Suratul Bakara
mm-
72. Kuma a lokacin da kuka yi
kisan kai, kuka dinga tunkucfa wa
jiina laifi a cikinsa (1) , kuma Allah
Mai fitar da abin da kuka kasance
kuna 6dyewa ne.
73. Sai Muka ce: "Ku doke shi
da wani sashenta." Kamar wancan
ne Allah Yake rayar da matattu,
kuma Ya nuna muku ayoyinSa,
tsammaninku, kuna hankalta.
74. Sa'an nan kuma zukatanku,
suka kekashe daga bayan wancan.
Saboda haka suka zama kamar du-
watsu ko mafi tsanani ga
kekashewa. Kuma lalle ne daga
duwatsu, hakllca, akwai abin da
maremari suke 6u66uga daga gare
shi,^kuma lalle ne daga gare su,
haklka, akwai abin da yake tsat-
tsagewa har ruwa ya fita daga gare
shi,^kuma lalle ne daga gare su,
haklka, akwai abin da yake fakfowa
domin tsoron Allah, kuma Allah
bai zama Gafili ba daga barin abin
da kuke aikatawa.
m ojil^li^ JiiL^fUj
(1) Asalin kissar, wani mutum ne mai arziki da yawa daga cikin BanTlsra'ila amma ba
shi da magaji sai dan dan'uwansa. Saboda ya yi gado, sai ya kashe shi da dare, ya kuma
dauke shi, ya aza shi a bakin kofar wani mutum, a cikinsu. Da safiya ta waye, sai suka tashi
domin su yi fada a tsakanin dangin wanda aka kashe da dangin wanda aka same shi a
kofarsu, sa'an nan suka hada ra'ayi ga su kai kara ga Manzon Allah, Musa. Suka isa gare
shi, suka ba shi labarin. Sai ya ce musu : "Lalle ne, Allah Ya ce : 'Ku yanke wata saniya.'"
Da sun yanke kowace inn saniya da sai bukatarsu ta biya musu, amma sai suka yi ta yin
tambayoyi ana ba su amsa, kuma yana kara yi musu wuya, har suka kai ga a sifanta musu
saniyar yaro mai da'a ga uwarsa wadda aka ce, ba za a sayar musu da ita ba sai da zinariya
cike da fatarta ko daidai da nauyinta sau goma. Bayan sun saye ta suka yanka ta sai Musa
ya ce musu, su doki wanda aka kashen nan da wani juzu'i nata. Suka doke shi da kashinta
ko harshenta, sai ya tashi ya ce: "Wane dan dan'uwana, ya kashe ni." Sai suka kama
wanda ya yi kisar suka kashe shi. Tartibin Alkur'ani ya yi ishara da mas'alar tsaurin kan
BanTlsra'ila da hikimar bin umurnin Allah, da Ikon tayar da matattu da gaskiyar wahayin
annabawa, da asiran da Allah Yake sanyawa a cikin wasu abubuwa domin su zama sanadi
ga aukuwar wasu, da yadda Yake arzuta masu yi Masa da'a, da sauransu, duk a cikin kissa
guda, ba da Ya ambaci tsarin asalinta ba. Tsarki ya tabbata ga Allah.
17
Suratul Ba£ara
fig)Ugg-r
75.^ Shin fa, kuna tsammanin za
su yi imani saboda ku, alhali kuwa,
haklka, wata kungiya daga gare su
sun kasance suna jin maganar Al-
lah, sa'an nan kuma su karkatar da
ita daga bayan sun gane ta, alhali
su, suna sane?
76. Kuma idan^ sun harfu da
wadanda^suka yi Tmani sukan ce:
"Mun yi Tmani," kuma idan sash-
ensu ya wofinta zuwa ga sashe,
sukan ce: "Shin, kuna yi musu
magana da abin da Allah Ya buda
muku ne domin su yi muku hujja da
shi a wurin Ubangijinku?"Shin fa,
ba ku hankalta?
77. Shin, kuma ba su sanin cewa
lalle ne Allah Yana sanin abin da
suke 66yewa da abin da suke bayya-
nawa?
78. Kuma daga cikinsu akwai
ummiyyai, ba su da sanin Littafi,
face tatsuniyoyi, kuma su ba kome
suke yi ba face suna yin zato.
79. To, bone ya tabbata ga
wadanda suke rubuta littafi da
hannuwansu, sa'an nan kuma su ce
wannan daga wurin Allah yake,
domin su sayi kucfi kadan da shi,
san nan bone ya tabbata a gare su
daga abin da hannayensu ke rubu-
tawa, kuma bone ya tabbata a gare
su daga abin da suke sana'antawa.
80. Kuma suka ce: "Wuta ba za
ta shafe mu ba, face 'yan kwanuka
kidayayyu." Ka ce: "Ashe kun riki
wani alkawari a wurin Allah, sa'an
nan Allah ba zai sa6a wa alkawa-
rinSa ba, ko kuwa kuna facfin abin
da ba ku sani ba bisa ga Allah?"
5ii»liJ^ii3^^«i\^iSij
>' * * >A\~'\>
•^->XH^ Q-*t *"* ^ 0>*Juo J JjT
© A&Sio
* *^^<*>>
18
Suratul Bakara
*SJISS-f
81. Na'am! Wanda ya yi tsiwur-
wurin mugun abu, kuma laifinsa ya
kewaye shi, to, wadannan su ne
'yan Wuta, su a cikinta madaw-
wama ne.
82. Kuma wadanda suka yi
unani kuma suka aikata ayyukan
kwarai, wadannan 'yan Aljanna
ne, su a cikinta madawwama ne.
83. Kuma a ldkacin da Muka
karBi alkawarin Ban! Isra'Tla (1) :
Kada ku bauta wa kowa face Allah,
kuma ga mahaifa ku kyautata, da
mai zumunta da marayu da mata-
lauta, kuma ku fadi magana mai
kyau zuwa ga mutane, kuma ku
tsayar da salla, kuma ku bayar da
zakka, sa'an nan kuka juya baya,
face kacfan daga gare ku, alhali
kuwa kuna masu bijirewa.
84. Kuma a ldkacin da Muka
ri£i alkawarinku ; ba za ku zubar da
jininku ba, kuma ba za ku fitar da
kanku daga gidajenku ba; sa 9 an
nan kuka tabbatar, alhali kuwa
kuna bayar da shaida (a kanku).
85. Sa'an nan kuma, ga ku, ya
wadannan! Kuna kashe kanku,
kuma kuna fitar da wani bangare
daga gare ku daga gidajensu, kuna
taimakon juna a kansu da zunubi
V^.t ^ -f> -- vf > ~'* > 't''S
, / A-' „. ^ < ^ > »- •
(1) Tunatar da BanTlsra'Ila alkawurra goma da Allah Ya yi da Musa a cikin Attaura
a kansu. Na farko, ba za su bauta wa kowa ba face Allah. Na biyu kyautata wa iyaye da
dangi da marayu da matalauta. Na uku, fadin magana-mai kyau zuwa ga mutane. Na
hudu, tsayar da salla. Na biyar, bayar da zakka. Na shida, ba za a kashe rai babu hakki na
shari'a ba. Na bakwai, ba za a fitar da kowa daga gidansa ba. Na takwas, ba za a taimaki
azzalumi a kan zaluncinsa ba. Na tara, idan abokan gaba sun kama wani daga cikinsu, su
yi fansarsa. Na goma, da'a ga kowane Manzdn Allah wanda bai saba wa Taurata ba ga
aiada.
19
2 — Suratul Bakara
m\m-
da zalunci, kuma idan kamammu
suka je muku, kuna fansarsu, alhali
kuwa shi fitar da su, abin da aka
haramta muku ne. Shin fa, kuna
imani da sashen Littafin ne, kuma
ku kafirta da sashe? To, mene ne
sakamakon wanda ke aikata wan-
can daga gare ku face wulakanci (1)
a cikin rayuwar duniya? Kuma a
Ranar Kiyama ana mayar da su
zuwa ga mafi tsananin azaba.
Kuma Allah bai zama Mai gafala
ba daga barin abin da kuke
aikatawa.
86. Wacfannan su ne wadanda
suka sayi rayuwar duniya da
Lahira, domin haka, ba za a
saukaka azaba ba daga kansu,
kuma su, ba a taimakonsu.
87. Kuma lalle ne, hakika, Mun
bai wa Musa Littafi, kuma Mun
biyar daga bayansa da wasu man-
zanni, kuma Muka bai wa Tsa dan
Maryama hujjoji bayyanannu,
kuma Muka karfafa shi da Ruhi
mai tsarki. (2) Shin fa, ko da yaushe
wani manzo ya je muku tare da abin
da rayukanku ba su so, sai ku kan-
gara, wani 6angare kun karyata,
kuma wani 6angare kuna kashewa?
88. Kuma suka ce: "Zukatanmu
suna cikin rufi." A'a, Allah Ya
la'ane su, domin^kafircinsu kadan
kwarai suke yin imani !
$1Z'> '> ^ » > > '.t ^
<^ <Z* "»>.
01 CJjjy^^^j^X^^^^i^jLa^^h
(1) Aiki da sashen wasu abubuwa na addini da barin wasu kafirci ne mai wajabta
wulakanci a kan Musulmi.
(2) Ruhul Kuds; watau ran tsarki ko rai mai tsarki, shi ne Jibirilu, amincin Allahja
tabbata a gare shi. Ya zauna tare da Tsa inda duk yake suna tare. Ayoyin da aka bai wa Tsa
su ne rayar da matattu da warkar da kutare da makafi da marasa lafiya. Wannan ya sanya
cewa masu da'awar bin sa suka fito da aikin maristan, watau asibiti.
20
2 — Suratul Bakara
W$&-
89. Kuma a lokacin da wani Lit-
tafi daga wurin Allah ya je musu,
mai gaskatawa ga abin da yake tare
da su, alhali kuwa sun kasance daga
gabanin haka suna fatar taimako (1)
da shi a kan wacfanda suka kafirta.
To, a lokacin da abin da suka sani
ya je musu, sai suka kafirta da shi .
Saboda haka la'anar Allah ta tab-
bata a kan kafirai.
90. Tir da abin da suka sayi rayu-
kansu da shi; watau su kafirta da
abin da Allah Ya saukar saboda
zalunci ; (2) kada Allah Ya saukar da
falalarSa a kan wanda Yake so daga
bayinSa. Sai suka komo da fushi
game da wani fushi. Kuma ga kaf-
irai akwai azaba mai wulakan-
tarwa.
91. Kuma idan aka ce musu:
"Ku yi Tmani da abin da Allah Ya
saukar." Sai su ce : "Muna imani da
abin da aka saukar a gare mu,"
kuma suna kafircewa da abin da ke
bayansa, alhali kuwa, shi ne gas-
kiyar (da suka sani) mai gaskatawa
ga abin da yake tare da su (na
Attaura). Ka ce: "To, don me kuke
kashe annabawan Allah gabanin
wannan, idan kun kasance masu
bayar da gaskiya?" (3)
53 ^H^-r^^ C/>Mj s-~^ci°
(1) Suna cewa idan Annabin karshen zamaninsa ya zo, za su yaki kafiran Larabawa
da shi. Suna zaton a cikinsu zai 6ullo. Sai ya fito a cikin Larabawan.
(2) Bisa ga zalunci, watau hasada. Sun yi hasadar Allah Ya saukar da abin da Yake so
na falalarSa a kan wanda Yake so, shi ne Muhammadu, a cikin Larabawa.
(3) Wadannan annabawan da kuka kashe ko kuka karyata a cikinku suke, ku ne aka
saukar wa da abin da aka ba su, saboda haka da'awarku ta cewa kuna Tmani da abin da
aka saukar muku karya ce.
21
2 — Suratul Bakara
*gttiSS-
92. Kuma lalle ne, haklka, Musa
ya zo muku da hujjoji bayyanannu,
sa'an nan kuka riki maraki (1) daga
bayansa, alhali kuwa kuna masu
zalunci.
93. Kuma a lokacin da Muka
riki alkawarinku, kuma Muka
daukaka (2) dutse a bisa gare ku,
(Muka ce:) "Ku riki abin da Muka
kawo muku da karfi, kuma ku ji."
Suka ce: "Mun ji kuma mun ki."
Kuma aka zuba son marakin a cikin
zukatansu saboda kafircinsu. Ka
ce: "Tir da abin dalmaninku yake
umurnin ku da shi, har idan kun
kasance masu Tmani!"
94. Ka ce: "Idan Gidan (3)
Lahira ya kasance saboda ku, a
wurin Allah, keBe ba da sauran
mutane ba, to, ku yi gurin mutuwa,
idan kun kasance masu gaskiya."
95. Kuma ba za su yi gurinta ba
har abada, saboda abin da han-
nayensu, suka gabatar. Kuma Al-
lah Masani ne ga azzalumai.
96. Kuma lalle ne, za ka same su
mafiya kwadayin mutane a kan
rayuwa, kuma su ne mafiya
&*£j u*^ \y 13 \jj
9 l>~
<£lx* \J& tylli f^=0 ££ol $
(1) Riko a nan ma'anarsa bauta wa; watau komawa ga maraki da ibada, ku bar
Allah, ba^an Musa ya nuna muku ayoyin Allah, yana kara karyata maganarku, ta cewa
kuna yin imani da abin da aka saukar muku kawai. Da kuna yin Tmani da abin da aka
saukar muku, da wadannan abubuwa ba su auku ba daga gare ku.
(2) A lokacin da aka ba su Taurata sai suka ki aiki da ita, sai da aka bambari dutse
aka daukaka shi sama a kansu, idan ba su yi aiki da ita ba ya fada a kansu. Sai suka karba,
sa'an nan daga baya kuma suka warware domin haka Ya ce: "Suka ce: 'Mun jiya kuma
mun kiya.'" Hasali dai Yahudu sun ki aiki da Littafinsu, Attaura.
(3) Ya shiga bayanin ruduwar Yahudu, da alfahari da iyaye, ya sanya su har suka gina
ransu, cewa su ne mafifitan mutane a wurin Allah.
22
2 — Suratul Bakara
mm-
kwacfayin rayuwa daga wacfanda
suka yi shirka. T)ayansu yana son
da za a rayar da shi shekara dubu,
kuma ba ya zama mai nisantar da
shi daga azaba domin an rayar da
shi. Kuma Allah, Mai gani ne ga
abin da suke aikatawa.
97. Ka ce: Wanda ya (1) kasance
makiyi ga Jibinlu, to, lalle ne shi ya
saukar da shi a kan zuciyarka da
izinin Allah, yana mai gaskatawa ga
abin da yake gaba gare shi, kuma da
shiriya da bishara ga muminai.
98. Wanda ya kasance makiyi ga
Allah da mala'ikunSa da manzan-
ninSa, da Jibinla da Mika'Ila, to,
lalle ne, Allah Makiyi ne ga kafirai.
99. Kuma lalle ne, haklka, Mun
saukar, zuwa gare ka, ayoyi bay-
yanannu, kuma ba wanda yake ka-
firta da su face fasikai (2) .
100. Shin, kuma a ko da yaushe
suka kulla wani alkawari, sai^wani
6angare daga gare su ya yi jlfa da
shi? A 'a, mafi yawansu ba su yin
Tmani.
101. Kuma a lokacin da wani
manzo (Muhammadu) daga wurin
Allah ya je musu, mai gaskatawa ga
abin da yake tare da su, sai wani
6angare daga watfanda aka bai wa
S^>
(1 ) Mai kin gaskiya kullum yana neman dalTlin da zai kama ya zama wani uzuri a gare
shi wajen kin aiki da gaskiyar. Yahudu suna cewa ba su son Jibirila domin shi ne ake
aikowa da azaba, ya halakar da Adawa da Samudawa da mutanen Ludu, suna nufin su ki
abin da ya kawo wa Annabi na Alkur'ani.
(2) Wannan aya tana umurnin bin Alkur'ani da aiki da shi kamar yadda ayoyin da ke
bin ta suke hana barin aiki da shi domin a koma ga son zuciya kamar sihiri da surkulle
wacfanda yake bin su kafirci ne.
23
Suratul Bakara
~m\m-
Littafi, suka yar da Littafin
(Al£ur'anin) Allah a bayan baya-
nsu, kamar dai su ba su sani ba.
102. Kuma suka bi abin da
Shaidanu (1) ke karantawa a kan
mulkin Sulaimanu, kuma Sulai-
manu bai yi kafirci ba, kuma Shai-
danun, su ne suka yi kafirci, suna
karantar da mutane sihiri. Kuma ba
a saukar da shi ba a kan mala'iku
biyu a Babila, Hariita da Maruta.
Kuma ba su sanar da kowa ba balle
su ce: "Mu fitina kawai ne, saboda
haka kada ka kafirta," balle har su
yi ta neman ilmin abin da suke
rarrabewa tsakanin mutum da ma-
tarsa da shi daga gare su. Kuma su
(masu yin sihirin) ba su zama masu
cutar da kowa da shi ba, face da
iznin Allah. Kuma suna neman il-
min abin da yake cutar da su, kuma
ba ya amfaninsu. Kuma lalle ne,
ha£i£a, sun sani, tabbas, wanda ya
%^j^^^^>
f f Jf'x'X >'~\"
(1) Shaidan shi ne dukan wanda ya san gaskiya kuma ya £i yin aiki da ita, mutum ne
ko aljani. Saboda haka a nan ana nufin miyagun malamai masu dauke mutane daga abin
da Allah Ya saukar musu na addini zuwa ga abin da suke so domin su cuce su. Hanyar
dauke mutane daga addinin gaskiya ita ce a wajen jingina magana ga wani mutum salihi
wanda aka yarda da shi a bayan ya mutu kamar Sulaimanu, ko kuma a jingina ta ga wanda
bazaa iya tambayarsa ba kamar mala'iku. A wannan aya an jingina asalin sihiri ga
Sulaimanu aka ce da sihiri ya kai ga mulkinsa, kuma aka ce asalin sihirin nan ilmi ne daga
Allah Ya saukar da shi ta kan wasu mala'iku biyu wadanda suke a garin da ake ce wa
Babila a kasar Irak, ana kiransu Haruta da Maruta wadanda suke, kafin su gaya wa mai
neman ilmin sihirin daga gare su abin da yake so, sai sun yi masa gargadi da cewa: "Kada
ka yi kafirci," sa'an nan su gaya masa abin da suke iya raba miji da mata da shi na sihiri.
To, Allah Ya farkar da mu cewa Sulaimanu bai yi sihiri ba, domin yin sihiri kafirci ne. Su
malaman masu fadin haka, su ne suka yi kafirci. Haka kuma Allah bai saukar da sihirin ba
a kan wadannan mala'iku da aka ambata a Babila. Kuma ba su karantar da kowa ba, balle
su ce wa mai nema : "Kada ka kafirta". Mai aiki da sihiri bai cutar kowa sai da iznin Allah.
Neman saninsa cuta ne, babu wani amfani. Sa'an nan kuma tanhi ya karyata kissar
saukar da mala'iku a Babila wadda aka yi a bayan Nuhu daT)ufana, alhali su kuwa an
saukar da su a gabanin Nuhu tun zamanin Annabi IdirTsa kamar yadda asalin tatsuniyar ta
fada.
24
2 — Suratul Baicara
m\m-<
saye shi, ba ya da wani rabo a cikin
Lahira. Kuma tir da abin da suka
sayar da rayukansu da shi, da sun
kasance suna sani.
103. Kuma da lalle ne su, sun yi
Tmani, kuma sun yi takawa, haklka,
da sakamako daga wurin Allah shi
ne mafi alheri, da sun kasance suna
sani.
104. Ya ku wacfanda suka yi
Tmani! Kada ku ce: 'Ra'ina\ (1)
kuma ku ce: 'Jinkirta mana \ kuma
ku saurara. Kuma kafirai suna da
azaba mai racfacfi.
105. Wacfanda suka kafirta daga
Ma'abuta Littafi, ba su son a
saukar da wani alheri a kanku daga
Ubangijinku, kuma mushirikai ma
ba su so. Kuma Allah Yana keBan-
cewar wanda Yake so da raha-
marSa. Kuma Allah Ma'abucin
falala mai girma ne.
106. Abin da Muka shafe (2)
daga aya, ko kuwa Muka jinkirtar
da ita, za Mu zo da mafi alheri daga
gare ta ko kuwa misalinta. Ashe, ba
ka sani ba, cewa lallene, Allah a kan
dukkan kome Mai Ikon yi ne?
107. Shin, ba ka sani ba, cewa
lalle ne Allah, ShT ne da mulkin
SD^J »r • ^ aJLio \y \<—r*y % ^ ■■•»**
•f >./tOTl'
E9 j^^\j^2Jij\j^A^\j *i_ia<>*
(1) "Ra'ina" magana ce mai ma'ana iri biyu; ta yabo da ta zagi. Ta farko ita ce a
lokacin da Annabi ke karantar da Sahabbansa, sai su ce 'ra'ina' watau dakata mana har
mu gane wannan; ta biyu ita ce 'ra'ina!' watau ya rubabbe! To, idan Sahabbai sun ce
'ra'ina' suna nufin ma'anar farko, sai Yahudu da mushirikai su juya musu magana da
ma'ana ta biyu.
(2) Wannan aya da abin da yake a bayanta suna korewar shubuhatu watau rikice-
rikicen addini da ma£iyan addini suke sanyawa a cikinsa, domin su sanya Musulmi a cikin
shakka da rikfu.
25
2 — Suratul Baicara
m\m~*
sammai da Rasa, kuma ba ku da,
baicin Allah, wani majibinci, kuma
ba ku da wani mataimaki?
108. K6 kuna nufin ku tambayi
Manzonku, kamar yadda aka tam-
bayi Musa a gabanin haka? Kuma
wanda ya musanya kafirci da imani,
to, lalle ne ya bace tsakar hanya.
109. Masu yawa daga Ma'abuta
Littafi suna gurin da sun mayar da
ku, daga bayan Tmaninku, kafirai,
saboda hasada daga wurin rayu-
kansu, daga bayan gaskiya ta bayy-
ana a gare su. To, ku yafe, kuma ku
kau da kai, sai Allah Ya zo da
umurninSa. Lalle ne Allah, a kan
dukkan kome Mai ikon yi ne.
110. Kuma ku tsayar da salla,
kuma ku bayar da zakka. Kuma
abin da kuka gabatar domin kanku
daga alheri, za ku same shi a wurin
Allah. Lalle ne Allah, ga abin da
kuke aikatawa Mai gani ne.
111. Kuma suka ce: "Babu mai
shiga Aljanna face wadanda suka
zama Yahudu ko Nasara."
Wadancan tatsuniyoyinsu ne. Ka
ce: "Ku kawo dalilinku, idan kun
kasance masu gaskiya."
772. Na'am! Wanda ya sallama
fuskarsa ga Allah, alhali kuwa yana
mai kyautatawa, to, yana da ijarar-
sa, a wurin Ubangijinsa, kuma babu
tsoro a kansu, kuma ba su zama
suna bakin ciki ba.
113. Kuma Yahudawa suka ce:
"Nasara ba su zamana a kan kome
ba," kuma Nasara suka ce: "Yahu-
dawa ba su zamana a kan kome
p-jyG' <-*_$>" Xj *■*& -^£ *•/?•»
26
Suratul Bakara
s^- C
ba," (1) alhali kuwa su, suna karatun
Littafi. Kamar wancan ne wacfanda
ba su sani ba suka facfa, kamar
maganarsu, saboda haka Allah ne
ke yin hukunci a tsakaninsu a
Ranar Kiyama, a cikin abin da suka
kasance suna saBa wa juna a
cikinsa.
114. Kuma wane ne mafi za-
lunci (2) daga wanda ya hana masal-
latan Allah, domin kada a ambaci
sunanSa a cikinsu, sai kuma ya yi
aiki ga rushe su? Wacfannan ba ya
kasancewa a gare su su shige su face
suna masu tsoro. Suna da, a cikin
duniya, wani wulaicanci, kuma suna
da, a cikin Lahira, azaba mai girma.
775. Kuma Allah tfai yake da
gabas da yamma, saboda haka,
inda duk aka juyar da ku, to, a can
yardar Allah take. Lalle ne, Allah
Mawadaci ne, Mai ilmi.
775. Kuma suka ce: "Allah Ya
ri£i (3) da." Tsarki ya tabbata a gare
Shi! A'a, Shi ne da abin da yake a
( 1 ) Mai gaskiya idan marasa gaskiya sun taru suna facfa da shi, to, rashin jituwar
tsakaninsu zai sanya Allah Ya kange shi daga sharrinsu, su duka, kamar husumar da ke
tsakanin Yahudu da Nasara da kuma tsakanin su^ mushirikai, su duka masu yaki da
Musulmi ne kuma masu sa6a wa juna ne wajen akldqjinsu.
(2) Misalin sa6ani tsakaninsu; Nasara suka taimaki Bukht Nassara ga 6ata masal-
lacin Baitil Makdis da jefa mushe da shara a ciki, domin kin Yahudu. Wannan kiyayya ta
bayyana har a cikin takardar alkawari a tsakanin Nasara da Halifa Umar bn Khattab suka
ce kada ya bar Yahudu su shiga Baitil Makdis. Saboda haka idan wasu sun hana ku isa ga
masallacinku ko kuma suka juyar da ku daga Alkibla, to, kada ku ji kome, sun yi irin aikin
danginsu. Gabas da yamma na Allah cfai ne, duk inda aka juyar da ku, to, a can yardar
Allah take. A lokacin Musulmi na dubin baitil Makdis ga salla a bayan hijira daga Makka,
ba su son haka.
(3) Misali na biyu Yahudu na cewa Uzairu cfan Allah, kuma Nasara suna cewa Tsa
dan Allah, Larabawa na cewa mala'iku 'ya'yan Allah. Wannan zai hana su jituwa har
adawarsu ga Musulmi ta yi tasiri.
27
Suratul Bakara
mm-
cikin sammai da Rasa, dukansu, a
gare Shi, masu kankan da kai ne.
117. Mai kyautata halittar sam-
mai da kasa, kuma idan Ya hu-
kunta wani al'amari, sai kawai Ya
ce masa: "Kasance," sai ya yi ta
kasancewa.
118. Kuma wadanda ba su da
sani suka ce: "Don me Allah ba Ya
yi mana magana, ko wata aya ta zo
mana?" (1) Kamar wancan ne
wadanda suke a gabaninsu suka
fada, kamar maganarsu. Zukatansu
sun yi kama da juna. Lalle ne, Mun
bayyana ayoyi ga mutane masu yin
yakini.
119. Lalle ne, Mun aike ka da
gaskiya, kana mai bayar da bishara,
kuma mai gargadi, kuma ba za a
tambaye ka ba, game da abokan
Wuta.
720. Kuma Yahudu ba za su
yarda da kome daga gare ka ba,
kuma Nasaraba za su yarda ba, sai
ka bi irin akTdarsu. Ka ce: "Lalle
ne, shiriyar Allah ita ce shiriya."
Kuma lalle ne, idan ka bi son zuci-
yoyinsu a bayan abin da ya zo maka
na ilmi, ba ka da, daga Allah, wani
majibinci, kuma babu wani matai-
maki.
121. Wadanda Muka bai wa Lit-
tafi suna karatunsa a kan hakkin
karatunsa, wadannan suna imani
da shi (Alkur'ani). Kuma wanda ya
kafirta da shi, to, wadannan su ne
masu hasara.
5^i*
^^.
(1) Misali ne ga irin rikicin mushirikai ga addini kuma da yadda suka yi kama da
Yahudu, wadanda suka ce wa Musa: "Ka nuna mana Allah bayyane."
28
Suratul Bakara
i*2\m-
122. YaBanTlsra'lia!Ku (1) tuna
ni'imaTa wadda Na ni'imtar da ka
a kanku, kuma lalle ne Ni, Na fifita
ku a kan talikai.
123. Ku ji tsoron wani yini, (a
cikinsa) wani rai ba ya tunkude wa
wani rai kome, kuma ba a karbar
musanya daga gare shi, kuma wani
ceto ba ya amfanin sa, kuma ba su
zama ana taimakon su ba.
124. Kuma a lokacin da Ubangi-
jin Ibrahim Ya jarrabe shi da wasu
kalmomi, sai ya cika su. Ya ce:
"Lalle ne Ni, Mai sanya ka shugaba
domin mutane ne." Ya ce: "Kuma
daga zuriyata." Ya ce: "Alka-
wanNa ba zai samu azzalumai
ba."
125. Kuma a lokacin da Muka
sanya T)akin ya zama makoma ga
mutane, da aminci, kuma suka riki
wurin salla daga Makami Ibrahim,
kuma^Muka yi alkawari zuwa ga
Ibrahim, da Isma'ila da cewa:
"Ku tsarkake T)akiNa domin
masu cfawafi da masu lizimta da
masu ruku'i, masu sujada."
126. Kuma a lokacin da Ibrahim
ya ce: "Ya Ubangijiha! Ka sanya
wannan gari amintacce, Ka arzuta
mutanensa,_daga 'ya'yan itacen,
wanda ya yi imani, daga gare su, da
Allah da Ranar Lahira." Allah Ya
ce: "Wanda ya kafirta ma Ina jiyar
E3 CJy^&lQ&ijSj
^Jli^^JjlS^o-UB^t:
( 1 ) K ira na karshe zuwa ga Yahudu domin shiga Musulunci. An biyar da gargadi gare
su da tunatar da su cewa wannan addinin fa, shi ne addinin kakansu Ibrahim, domin kada
su fandare daga addinin ubanninsu na kwarai. Kuma suna da labarin ginin "Dakin Ka'aba
da addu'ar da Ibrahim ya yi a lokacin, wadda ta £unsa zuwan annabi daga cikin zuriyar
Isama'ila a Makka, watau Parana.
29
SuratuJ Bakara
m\m-<
da shi dacfi kadan, sa'an nan kuma
Ina tTlasta shi zuwa ga azabar Wuta.
Kuma makomar, ta munana."
127. Kuma a lokacin da Ibrahim
yake daukaka harsashin gini ga
T)akin, da IsmaTla (suna cewa:)
"Ya Ubangijinmu! Ka karba daga
gare mu, lalle ne Kai, Kai ne Mai ji,
Mai sani.
128. "Ya Ubangijinmu! Ka
sanya mu, mu biyu, wadanda suka
sallama (al'amari) gare Ka, kuma
daga zuriyarmu (Ka sanya)
al'umma mai sallamawa zuwa gare
Ka, kuma Ka nuna mana wuraren
ibadar hajjinmu, kuma Ka karBi
tuba a kanmu. Lalle ne Kai, Kai ne
Mai karbar tuba, Mai rahama.
129. "Ya Ubangijinmu! Ka
aiko, a cikinsu, wani manzo (1) daga
gare su, yana karanta musu ayo-
yinKa, kuma yana karantar da su
Littafin (2) da hikimar, kuma yana
tsarkake su. Lalle ne Kai, Kai ne
Mabuwayi Mai hikima."
130. Kuma wane ne yake gudu
daga akldar Ibrahim, face wanda ya
jahilta ga ransa? Kuma lalle ne,
haklka, Mun zaBe shi, a cikin
duniya, kuma lalle ne shi, a cikin
Lahira, haklka, yana daga salihai.
131. A lokacin da Ubangijinsa
Ya ce masa: "Ka sallama," ya ce:
"Na sallama ga Ubangijin tali-
kai."
0_^^[P^J^I^W^lU
jip\^^\3S\^[\L
* a*> -
(1) Addu'ar, an kar6a, ta aiko Muhammadu, tsTra da aminci su tabbata a gare shi.
(2) Littafin — ya bayyana cewa Al£ur'ani ne, domin babu wani, sai shi. Hikima kuwa
ita ce shari'un da ke a cikinsa. Ya tsarkake su daga daudar shirki idan sun bT shi.
30
2 — Suratul Bakara
SSWSS£-r
132. Kuma Ibrahim ya yi wasi-
yya da ita ga cfiyansa, kuma Ya'
akubu (ya yi wasiyya, suka ce :) "Ya
diyana! Lalle ne, Allah Ya za6a
muku addini, don haka, kada ku
mutu, lalle, face kuna Musulmi."
133. Ko kun (1) kasance halarce a
lokacin da mutuwa ta halarci Ya'a-
£ubu, a lokacin da ya ce wa
cfiyansa: "Mene ne za ku bauta wa
daga bayana?" Suka ce: "Muna
bauta wa Abin bautawarka kuma
Abin bautawar ubanninka Ibrahim
da Isma'Tla da Is'halca, Ubangiji
Guda, kuma mu a gare Shi masu
sallamawa ne."
134. Waccan, wata al'umma ce,
ta riga ta shige, tana da abin da ta
sana'anta, kuma kuna da abin da
kuka sana'anta. Kuma ba za a tam-
baye ku ba daga abin da suka ka-
sance suna aikatawa.
135. Kuma suka ce: "Ku ka-
sance (2) Yahudawa ko Nasara, kwa
shiryu." Ka ce: "A'a, akldar
Ibrahim dai, mai karkata zuwa ga
gaskiya, kuma bai kasance daga
masu shirki ba."
136. Ku (3) ce: "Mun yi Imani da
Allah, da abin da aka saukar zuwa
gare mu, da abin da aka saukar
(1) Lamlrin Yahudawan MadTna ne na zamanin Annabi, wadanda ake kira zuwa ga
Musulunci ana tunatar da su abin da kakansu Isra'ila ya yi wasiyya da shi zuwa ga diyansa,
kafin ya mutu; watau wannan aklda da ake kiran su yanzu zuwa gare ta.
(2) Yahudu suka ce: "Ku kasance Yahudawa ku shiryu," Nasara suka ce: "Ku
kasance Nasara ku shiryu". Allah Ya niina addinin Yahudu da na Nasara ya saBa wa abin
da suke yi, su duka biyu, kuma ya saBa wa na mushirikai.
(3) Musulmi ake yi wa umurni.
31
Suratul Ba£ara
m\m-
zuwa ga Ibrahim da IsmaTla da
Is'ha£a da Ya'a£ubu da Jikoki, da
abin da aka bai wa Musa da Tsa, da
abin da aka bai wa annabawa daga
Ubangijinsu, ba mu rarrabewa a
tsakanin kowa daga gare su, kuma
mu, a gare Shi, masu sallamawa
ne.
137. To, idan sun yilmani (1) da
misalin abin da kuka yi Imani da
shi, to, lalle ne sun shiryu, kuma
idan sun juya baya, to, suna a cikin
sa6ani kawai, saboda haka, Allah
zai isar maka a gare su, kuma Shi ne
Mai ji, Masani.
138. Rinin Allah ! Kuma wane ne
mafi kyau ga rini daga Allah?
Kuma mu, a gare Shi, masu baut-
awa ne.
139. Ka ce : Shin kuna jayayyar
hujja ne da mu a cikin aFamarin
Allah, alhali kuwa Shi ne Ubangi-
jinmu kuma Ubangijinku, kuma
muna da ayyukanmu, kuma kuna
da ayyukanku, kuma mu, a gare
Shi, masu tsarkakewa ne?
14(L Ko kuna^cewa: Lalle ne,
Ibrahim da IsmaTla da Is'ha£a da
Ya'a£ubu da Jikoki, sun kasance
Yahudawa ko kuwa Nasara? Ka
ce : Shin, ku ne kuke mafi sani, ko
Allah? Kuma wane ne ya zama
mafi zalunci daga wanda ya 66ye
shaida a wurinsa daga Allah?
Kuma Allah bai zama Mai gafala
ba daga abin da kuke aikatawa!
< ' 9 1
M
\ bJ^^^Jj^t
S' 9 *
**'.
><JiL
vrv| jLi^J \ U^\y*3 *i
<U*\
>* \\'" ii zf ^ >' t' /I
(1) Tmani irin na Musulmi shi ne rinin Allah watau baptisma.
32
2 — Suratul Bakara
m\m-
141. Waccan, wata arumma ce,
ta riga ta shige, suna da abin da
suka sana'anta, kuma kuna da abin
da kuka sana'anta, kuma ba a tarn-
bayar ku daga abin da suka kas-
ance suna aikatawa.
142. Wawaye daga mutane za su
ce: Mene ne ya juyar da su daga
alkiblarsu wadda suka kasance a
kanta? Ka ce: Allah TDai ne Yake
da gabas da yamma, Yana shiryar
da wanda Yake so zuwa ga hanya
madaidaiciya.
143. Kuma kamar wancan,
Muka sanya ku al'umma matsa-
kaiciya (1) domin ku kasance masu
bayar da shaida a kan mutane.
Kuma Manzo ya kasance mai
shaida a kanku. Kuma ba Mu
sanya Alkibla (2) wadda ka kasance
a kanta ba, face domin Mu san
wanda yake biyar Manzo daga
wanda yake juyawa a kan duga-
dugansa. JCuma lalle ne, ta kas-
ance, haklka, mai girma, sai a kan
wacfanda Allah Ya shiryar. Kuma
ba ^a yiwuwa ga Allah Ya tozartar
da imaninku/ 3) Lalle ne, Allah, ga
mutane, haklka, Mai tausayi ne,
Mai jin Rai.
' ** t '\ "
(1) Adilai, ko matsakaita ga kome, babu zurewa, babu kasawa ga addini da rayuwa
da sauran mu'amaloli duka.
(2) A lokacin da Annabi ya yi hijira zuwa Madina, alhali a cikin mutanenta akwai
Yahudu Allah Ya umurce shi da ya fuskanci Baitil Makdis. Sai Yahudu suka ji dadi. Sai
Manzon Allah ya fuskance ta wata goma sha wani abu kuma Manzon Allah ya kasance
yana son Alkiblar Ibrahim kamar yadda ya gabata ga aya ta 1 15. Kuma ya kasance yana
addu'a yana dubi zuwa ga sama, har Allah Ya saukar da hukuncin juyawa zuwa gare ta.
(3) Tmaninku watau sallarku da kuka yi wajen Baitil Makdis, domin kun yi ta ne a
kan umurnin Allah da imani da Shi.
33
2 — Suratul Bakara
seiuss-f
144. Lalle ne, Muna ganin jujju-
yawar fuskarka a cikin sama. To,
lalle ne, Mu juyar da kai ga Alkibla
wadda kake yarda da ita. Sai ka
juyar da fuskarka wajen Masallaci
Tsararre, kuma inda duk kuka kas-
ance, to, ku juyar da fuskokinku
jiharsa. Kuma lalle ne wacfanda
aka bai wa Littafi, hakika, su, suna
sanin lalle ne, shl ne gaskiya daga
Ubangijinka. Kuma Allah bai
zama Mai gafala ba daga abin da
suke aikatawa.
145. Kuma hakika, idan ka je
wa wacfanda aka bai wa Littafi da
dukan aya, ba za su bi Alkiblarka
ba, kuma kai ba ka zama mai bin
Alkiblarsu ba, kuma sashensu ba
mai bin Alkiblar (1) sashe ba ne.
Kuma hakika, idan ka bi son zuci-
yoyinsu daga bayan abin da ya zo
maka daga ilmi, lalle ne kai, sa'an
nan, hakika, azzalumi kake.
146. Wacfanda Muka ba su Lit-
tafi, suna saninsa kamar yadda
suke sanin diyansu. Kuma lalle ne
wani 6angare daga gare su, hakika,
suna 66yewar gaskiya alhali kuwa
su, suna sane.
>*~
*JW[
(1) Al£iblar Yahudu ita ce falalen diitsen da ke Bai til Makdis. Kuma ita ce Alkiblar
Nasara a zamanin Tsa. A bayansa Alkiblarsu ta koma^ga mafitar rana, da kagensu saboda
St. Paul ko Bubs el Kissi, ya ce musu bayan an cfauke Tsa cewa : "Na hadu da Tsa ya ce mini
lalle ne rana tauraro ne wanda yake ina son sa. Yana kai gaisuwata a cikin kowane yini
saboda haka ka umurci mutanena, su fuskanta zuwa gare ta." Da haka ya karkatar da su
daga al£iblarsu. Kuma ina zaton haka abin yake ga girmamawar Lahadi maimakon
Asabar domin Rumawa, rana suke bauta wa a ranar Lahadi, wannan kuwa shi ne ma'anar
"Sunday" da Turancin, watau 'yinin rana.'
34
Suratul Bakara
wm-
147. Gaskiya daga Ubangi-
jinka (1) take, saboda haka; lalle
kada ka kasance daga masu shakka.
148. Kuma kowane Bangare
yana da alkibla wadda yake shi mai
fuskantar ta ne. Sai ku yi tsere
zuwa ga ayyukan alheri, inda kuka
kasance duka, Allah zai zo da ku
gaba cfaya. Lalle ne Allah, a kan
kome, Mai Tkon yi ne.
149. Kuma daga inda ka fita, to,
sai ka juyar da fuskarka a wajen
Masallaci Tsararre, kuma lalle,
tabbas, shi ne gaskiya daga
Ubangijinka. Kuma Allah bai
zama Mai gafala ba daga abin da
kuke aikatawa.
150. Kuma daga inda ka fita, to,
ka juyar da fuskarka a wajen Ma-
sallaci Tsararre, kuma inda kuke
duka, to, ku juyar da fuskokinku a
wajensa, domin kada wata hujja ta
kasance ga mutane a kanku, face
wadanda suka yi zalunci daga gare
su. Saboda haka kada ku ji tsor-
onsu, kuma ku ji tsoroNa, kuma
domin In cika ni'imaTa a kanku,
kuma tsammaninku za ku shiryu.
151. Kamar (2) yaddaMukaaika
Manzo a cikinku, daga gare ku,
*&*'>'>*'
(1) Juyawar alkibla abu ne na gaskiya daga Allah domin rarrashin wanda Allah bai yi
nufi da tsirarsa ba ya kare. Bayan rarrashi sai yankewa, wannan shi ne matakin farko da
Musulmi suka fara tsiraita da shi daga makiyansu bayyane. Yanzu kuma Musulmi sun
zama dabam.
(2) Juyar da alkibla da yankewa daga dukan kafirai da hani daga tsoronsu, kuma
Allah Ya farkar da Musulmi ga ni'imomin da Ya yi musu game da aiko Annabi daga gare
su, zuwa gare su, a cikinsu, domin ya tsarkake su, bayyane da 66ye, daga dukan Rurar
kafirci. Wannan ya nuna cewa sai an yi rarrashin mutane wajen kira zuwa ga addini da
kowace hanya mai yiwuwa. Bayan haka a yanke wa wanda ya ki bin gaskiya bayyane,
kuma kada a ji tsoronsa. Kuma aka umurce su da fuskanta zuwa ga Allah kawai da tunawa
gare Shi da godiya, da nisantar kafirci.
35
Suratul Bakara
*SRSSg-f
yana karanta ayoyinMu a gare ku
kuma yana tsarkake ku, kuma
yana sanar da ku Littafi da hikima,
kuma yana sanar da ku abin da ba
ku kasance kuna sani ba.
152. Saboda haka ku tuna Ni, In
tuna ku, kuma ku yi godiya gare
Ni, kuma kada ku butulce Mini.
153. Ya ku wacfanda (1) suka yi
imani! Ku nemi taimako da hakuri
game da salla. Lalle ne, Allah na
tare da masu hakuri.
154. Kada ku ce ga wadanda (2)
ake kashewa a cikin hanyar Allah:
"Matattu ne." A'a, rayayyu ne,
kuma amma ba ku sansancewa.
755. Kuma lalle ne, Muna jar-
rabar ku da wani abu daga tsoro da
yunwa da nakasa daga dukiya da
rayuka da 'ya'yan itace. Kuma ka
yi bishara ga masu hakuri.
156. Wacfanda suke idan wata
maslfa ta same su, sai su ce: "Lalle
ne mu ga Allah muke, kuma lalle ne
mu, zuwa gare Shi, masu komawa
ne .
157. Wadannan akwai albarku a
kansu daga Ubangijinsu da wata
rahama. Kuma wadannan su ne
shiryayyu.
158. Lalle ne Safa da Marwa (3)
U.J&\£46\%
iS >
(1) Magana kuma ta fuskanta zuwa ga muminai kawai domin a shirya zamansu.
(2) Wanda ya tsiraita da kansa, to, makiyinsa ba zai bar shi ba, saboda haka an fara
kulla zukatan muminai ga tarbon wahalar tsiraita da dogara ga kai, bayan Allah.
(3) Al'umma ba ta hacfuwa sai an wanke ta daga al'adun Jahiliyya, har dai wacfanda
suka hadu da ibada, saboda haka aka fara da Safa da Marwa, domin a ije cewa dawafi a
tsakaninsu aikin Jahiliyya ne, su suna cikin ayyukan ibada da Allah Ya shar'anta, kuma
dawafin mutane da sa'ayi a kansu da tsakaninsu duka daidai suke, Bakuraishe da Balarabe
da Ajama duka daidai suke.
36
2 — SQratul Bakara
m\m-
suna daga wuraren ibadar Allah,
to, wanda ya yi hajin "Daki ko
kuwa ya yi Umra, to, babu laifi a
kansa ga ya yi dawafi gare su, su
biyu. Kuma wanda ya £ara yin
wani aikin alheri, to, lalle ne Allah
Mai godiya ne, Masani.
159. Lalle ne wadanda suke
Boyewar abin da Allah Ya saukar
da ga hujjoji bayyanannu, da shir-
iya, daga bayan Mun bayyana shi
ga mutane, a cikin Littafi
(Alkur'ani), wadannan Allah Yana
la'anar su, kuma masu la'ana suna
la'anar su.
160. Sai wadanda suka tuba,
kuma suka gyara, kuma suka bayy-
ana, to wadannantaa karBar tuba
a kansu, kuma Ni ne Mai kar6ar
tuba, Mai jin kai.
161. Lalle ne, wadanda suka ka-
firta, kuma suka mutu, alhali kuwa
suna kaflrai, wadannan akwai, a
kansu, la'anar Allah da mala'iku
da mutane gaba daya.
162. Suna madawwama a ci-
kinta, ba a saukaka azaba daga
barinsu, kuma ba su zama ana jin-
kirta musu ba.
163. Kuma Ubangijinku Uban-
giji (1) Guda ne. Babu wani Uban-
giji face Shi, Mai rahama, Mai jin
kai.
164. Lalle ne, a cikin halittar
sammai da kasa, da sa6awar dare
>^J*^ljJ\ j^^i*^ \^ifj&
^ >£>.
(1) Ubangiji Shi ne Mai rayarwa da matarwa, Mai umurni da hani kuma Mai
halattawa da haramtawa. Avar da ke bin wannan, tana nuna dalTlan samuwarSa da
kadaitarSa.
37
Suratul Ba£ara
m\m-
da yini, da jirage wacfanda suke
gudana a cikin teku (dauke) da
yake amfanin mutane, da abin
da Allah Ya saukar daga sama
daga ruwa, sai Ya rayar da kasa da
shi a bayan mutuwarta, kuma Ya
watsa, a cikinta, daga dukan
dabba, kuma da juyawar iskoki da
girgije horarre a tsakanin sama da
kasa; hakika, akwai ayoyi ga mu-
tane masu yin hankali.
165. Kuma akwai daga mutane
wanda yake rikon kinaye, baicin
Allah, suna son su, kamar son Al-
lah, kuma wacfanda suka yi Tmani
ne mafiya tsananin so (1> ga Allah.
Kuma da wadanda (2> suka yi za-
lunci, suna ganin lokacin da za su
ga azaba, da cewa lalle ne karfi ga
Allah yake duka, da cewa lalle ne
Allah Mai tsananin azaba ne.
166. A lokacin da wadanda aka
bi suka barranta daga wadanda
suka bi, kuma suka ga azaba, kuma
sabubba suka yanke da su.
167. Kuma wadanda suka bi,
suka ce: "Da lalle ne muna da
wata komawa (duniya) sai mu bar-
ranta daga gare su kamar yadda
suka barranta daga gare mu (da ba
su ri£i kinayen ba)." Kamar wan-
can ne Allah ke nuna musu ayyu-
< ** *> i
(1) So mai kai ga kar6ar umumi daga abin son, wanda ba Allah ba, shi ne shirki da
kafirci. Amma so saboda ihsanin abin son, ko domin zamansa salihi domin a yi koyi da
aikinsa na cikin haddodin shari'a, ba shirki ba ne, domin bai kai yadda muminai ke son
Allah ba.
(2) Ayoyi na 165 da 166 da 167 duka dinke suke ga ma'anoninsu. Aya ta 166 zarafi ce
gataJ65, sa'annanta 167anhadarabintagaayata 166. Sa'an nan sauran aya 167tazama
ta'a£ibi da bayani gare su duka.
38
Suratul Bakara
i$$m-
kansu, suna da nadamomi a kansu,
kuma ba su zama masu fita daga
Wutar ba.
168. Ya ku mutane (1) ! Ku ci
daga abin da yake a cikin kasa,
wanda yake halal, mai dacfi. Kuma
kada ku bi zambiyoyin (2) Shaidan.
Lalle ne shi, a gare ku, makiyi ne
bayyananne.
169. Yana umurnin ku ne kawai
da mugun aiki da alfasha, kuma da
ku facfi abin da ba ku sani ba ga
Allah.
170. Kuma idan aka ce musu:
"Ku bi abin da Allah Ya saukar,"
sai su ce: A'a, muna bin abin da
muka iske ubanninmu a kansa."
Shin, kuma ko da ubanninsu ba su
hankaltar kome, kuma ba su
shiryuwa?
171. Kuma misalin (mai kiran)
wadanda suka kafirta, kamar mis-
alin wanda ke yin me! me! ga abin
da ba ya ji ne, face kira da kara,
kurame, bebaye, makafi, saboda
haka ba su hankalta.
172. Ya ku wadanda suka yi
Tmani! Ku ci ku sha daga masu
dacfin abin da Muka arzuta ku.
Kuma ku gode wa Allah, idan kun
kasance Shi kuke bauta wa.
*Lxx • \^ x \Zs i.^'/>*
(1) Ya kira mutane a kan, bai ce muminai ba, domin ba dukan Musulmi yake mumini
ba, sai wanda ya tsTra daga ayoyin da ke tafe. A cikinsu akwai abin da zai mai da Musulmi
kafiri ko mai bidi'a.
(2) Hanyoyin Shaidan ga halattar da abin da Allah Ya haramta ko haramtar da abin
da Allah Ya halatta domin kaga hukuncin da bai zo daga Allah ba, shirki ne tare da Allah.
Ya ce zambiyoyin Shaidan, domin Shaidan ba ya da hanya mikakkiya.
39
2 — Suratul Baicara
m\m~*
173. Kawai abin da Ya haramta
a kanku, mushe da jini da naman
alade da abin da aka kururuta
game da shi ga wanin Allah. To,
wanda aka matsa, wanin dan
tawaye, kuma banda mai zalunci,
to, babu laifi a kansa. Lalle ne Al-
lah Mai gafara ne, Mai jin kai.
174. Lalle ne wadannan da suke
Boye abin da Allah Ya saukar daga
Littafi, kuma suna sayen kudi
kadan da shi; wadannan ba su cin
kome a cikin cikkunansu face
Wuta, kuma Allah ba zai yi musu
magana ba a Ranar Kiyama, kuma
ba zai tsarkake su ba, kuma suna
da azaba mai radacfi.
175. Wadannan su ne warfanda
suka sayi Bata da shiriya, kuma
azaba da gafara. To, me ya yi
hakurinsu a kan Wuta!
176. Wancan domin lalle ne, Al-
lah ya saukar da Littafi da gaskiya,
kuma lalle ne wadanda suka saBa a
cikin Littafin,Jiakika, suna a cikin
saBani mai nlsa.
177. Bai zama addini (1) ba
domin kun juyar da fuskokinku
wajen gabas da yamma, kuma
amma addini shi ne ga wanda ya yi
Tmani da Allah da Ranar Lahira da
mala'iku da littattafan sama da
annabawa, kuma ya bayar da
dukiya, a kan yana son ta, ga mai
zumunta da marayu da matalauta
da dan hanya da masu roko, kuma
'""'w:*
^
>>>
<*""+'' , 5.
p^Jj ^ j3 t j l^-ZJ \ Zg=ssc&^\JL\
&ffio 9 J& & hy^^^L^ * Q
Csl$\ %&&\ iJXii cyj^jl
o]j^tvli^\jj^5tSLiB:i
(1) Bayanin cewa Musulunci ba yin salla cfai ba ne. A'aha! Musulunci tsarewar
rayuwa ne kamar yadda Allah Ya ce a tsare ta.
40
2 — Suratul Bakara
wm?-
a cikin fansar wuya, kuma ya
tsayar da salla, kuma ya bayar da
zakka, da masu cika alkawari idan
sun kulla alkawarin da masu
hakuri a cikin tsanani da cuta da
lokacin yaki. Wadannan su ne suka
yi gaskiya. Kuma warfannan su ne
masu takawa.
178. Ya ku wadanda suka yi
Tmani! An wajabta, a kanku, yin
kisasi (1) a cikin kasassu; da da da,
kuma bawa da bawa, kuma mace
da mace, to, wanda aka yi rang-
wamen wani abu gare shi daga
cfan'uwansa, to, a bi da alheri, da
biya zuwa gare shi da kyautatawa.
Wancan saukakewa ne daga
Ubangijinku, kuma rahama ce. To,
wanda ya yi zalunci a bayan wan-
can, to, yana da azaba mai radacfi.
179. Kuma kuna da rayuwa a
cikin kisasi, ya ma'abuta hankula;
tsammaninku, za ku yi takawa.
180. Kuma an wajabta (2) , a kan-
ku, idan mutuwa ta halarci
dayanku, idan ya bar wata dukiya,
wasiyya domin mahaifa da dangi
bisa ga abin da aka sani; wajabce a
kan masu takawa.
181. To, wanda ya musanya
masa a bayan ya jT shi, to, kawai
laifinsa yana a kan wadanda suke
musanya shi. Lalle ne, Allah Mai ji
ne, Masani.
>\)
<y *'< <.
©£J*
ydVU^^U-^J^JJ
M OjilJ> JpU>-^j?/^J^
(1) Bayanin hukuncin kisasi : Ana kashe namiji saboda ya kashe mace, ba a kashe cfa
da Musulmi saboda kashin bawa da kafiri sai idan ya zama kisan gila ne ko kwace. Gila shi
ne kashe mutum domin dukiyarsa ko matarsa.
(2) Bayanin hukuncin wasiyya : Sunna ta bayyana cewa babu wasiyya ga wanda zai yi
gado, kuma wasiyya ba za ta shige sulusin dukiyar tarika ba.
41
Suratul Baicara
wm-i
182. To, wanda ya ji tsoron kar-
kata ko kuwa wani zunubi daga
mai wasiyyar, sai ya yi sulhi a
tsakaninsu, to, babu laifi a kansa.
Lalle ne Allah Mai gafara ne, Mai
jin kai.
183. Ya ku wadanda suka yi
Imani! An wajabta (1) azumi a kan-
ku kamar yadda aka wajabta shi a
kan wadanda suke daga gaba-
ninku, tsammaninku, za ku yi ta-
kawa,
184. Kwanuka kidayayyu. To,
wanda ya kasance daga gare ku
majinyaci ko kuwa yana a kan
tafiya, sai (ya biya) adadi daga
wasu kwanuka na dabam. Kuma a
kan wadanda suke yin sa da wahala
akwai fansa; ciyar da matalauci, sai
dai wanda ya kara alheri, to, shi ne
mafi alheri a gare shi. Kuma ku yi
azumi (da wahalar) ne mafi alheri a
gare ku, idan kun kasance kuna
sani.
185. Watan Ramalana ne wanda
aka saukar da Alkur'ani a cikinsa
yana shiriya ga mutane da hujjoji
bayyanannu daga shiriya da rarra-
bewa. To, wanda ya halarta daga
gare ku a watan, sai ya azumce shi,
kuma wanda ya kasance majinyaci
ko kuwa a kan tafiya, sai ya biya
adadi daga wasu kwanuka na
dabam. Allah Yana nufin sauki
gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani
gare ku, kuma domin ku cika
adadin, kuma domin ku girmama
oy*^
'< *L S >
4»»- >* * A si^Ja \ /^-^ JL^J» < yoJ QLsyu \j
(1) Bayanin hukuncin azumi da darajar watan Ramalana wanda aka saukar da
Aliair'ani a cikinsa.
42
Suratul Bakara
wm-
Allah a kan Ya shiryar da ku,
kuma tsammaninku, za ku gode.
186. Kuma idan bayiNa suka
tambaye ka daga gare Ni, to, lalle
Ni Makusanci ne. Ina kar6a kiran
mai kira idan ya kira Ni (1) . Saboda
haka su nemi karbawaTa, kuma su
yi Tmani da Ni: tsammaninsu, su
shiryu.
187. An halatta a gare ku, a
daren azumi, yin jima'i (2) zuwa ga
matanku, su tufa ne a gare ku,
kuma ku tufa ne a gare su, Allah
Ya sani, lalle ne ku, kun kasance
kuna yaudarar kanku. Saboda
haka Ya karbi tubarku, kuma Ya
yafe muku. To, yanzu ku rungume
su, kuma ku nemi abin da Allah ya
rubuta muku. Kuma ku ci kuma ku
sha har slllli fari ya bayyana a gare
ku daga sTlTli baki daga alfijiri,
sa'an nan kuma ku cika azumi
zuwa ga dare. Kuma kada ku run-
gume su alhali kuna masu itikafi a
cikin masallatai. Wadancan iyako-
kin Allah ne: don haka kada ku
kusance su, kamar haka ne Allah
Yake bayyana ayoyinSa ga
mutane: tsammaninsu, za su yi
takawa.
> -^>
(1) Bayanin yin addu'a: Ana son addu'a a cikin Ramalana, yadda neman kar6ar
addu'a da aikin cfa'a yake bayan Tmani. Aikin kwarai shT ne godiyar addu'a.
(2) Abubuwan^da aka hana, a cikin azumi, da rana, an halatta su da dare har zuwa
fltar alfijiri wato sTlTli fari na hasken safiya da sTlTli baki na duhun dare. Ba a yin jima'i ko
da dare a halin itikafi, kuma ba a yin itikafi sai a cikin masallaci.
43
Suratul Ba£ara
*sns^-f
188. Kada ku ci dukiyoyinku (1)
a tsakaninku da karya, kuma ku
sadu da ita zuwa ga mahukunta
domin ku ci wani yanki daga
dukiyoyin mutane da zunubi, alhali
kuwa ku, kuna sani.
189. Kuma suna tambayar ka (2)
daga jirajiran wata. Ka ce: "Su 16k-
atai ne domin mutane da haji,
kuma ba addini ba ne ku je wa
gidaje daga bayansu: kuma amma
abin da yake addini shi ne wanda
ya yi takawa. Kuma ku je wa gidaje
daga kofofinsu, kuma ku bi Allah
da takawa: tsammaninku, ku ci
nasara.
190. Kuma ku yaki wacfanda (3)
suke yakinku, a cikin hanyar Allah,
kuma kada ku yi tsokana, lalle ne
Allah ba Ya son masu tsokana.
191. Kuma ku yake su inda
kuka same su, kuma ku fitar da su
daga inda suka fitar da ku. Kuma
fitina ita ce mafi tsanani daga kisa.
Kuma kada ku yake su a wurin
Masallaci Tsararre (Hurumin
Makka) face fa idan sun yake ku a
cikinsa. To, idan sun yake ku, sai
ku yake su. Kamar wancan ne
sakamakon kafirai yake.
m ^x^j\ -4-^v 4*\^L>i\j
> ,^ ,„ > >
~> »Zt^
^$^s» S ^*-» "i" ^ 's'^ »z- 9 '' £*>^< , x
(1) Haramun cin dukiyar mutane da zalunci. An hada wannan aya da ta gabaninta,
ta azumi, domin hadin hana ci da ya gama su. Saduwa da mahukunta da dukiya, shi ne
rashawa, Allah Ya la'ani mai bayar da ita da mai karftarta.
(2) Shiga Musulunci yarda ne da barin al'adu da hukunce-hukuncen Jahiliyya,
saboda haka ake samun tambayoyi da yawa daga sabon Musulmi kafin ya kammala da
canza tsofaffin al'adunsa da sababbi. Allah Ya yi tarbiyar Sahabban Annabi a cikin
rayuwar Annabi, bayan saukar wahayi.
(3) An umurci Musulmi da tsare kansu da yaki ga duk wanda ya yake su, a ko'ina
yake. Sai dai an hana su tsokanar wasu, kuma an hana su su yi yaki a cikin Hurumin
Makka sai fa idan an fada su da yaki a cikinsa.
44
2 — Suratul Bakara
mm-
192. Sa'an nan idan sun harm,
to, lalle Allah Mai gafara ne, Mai
jin £ai.
193. Kuma ku ya£e (1) su har ya
zama wata fitina ba za ta kasance
ba, kuma addini ya zama na Allah.
Sa'an nan idan sun hanu, to, babu
tsokana face a kan azzalumai.
194. Watan alfarma da wani
watan alfarma — alf armomi masu
dukar juna ne. Saboda haka wanda
ya yi tsokana a kanku, sai ku yi
tsokana a kansa, da misalin abin
da ya yi tsokana a kanku. Kuma
ku bi Allah da takawa. Kuma ku
sani cewa lalle ne, Allah Yana tare
da masu takawa.
195. Kuma ku ciyar (2) a cikin
hanyar Allah. Kuma kada ku jefa
kanku da hannayenku, zuwa ga
halaka. Kuma ku kyautata; lalle
ne, Allah Yana son masu kyauta-
tawa.
196. Kuma ku cika (3> hajji da
umra domin Allah. To, idan an
kange ku, to, ku bayar da abin da
ya saukaka na hadaya. Kuma kada
ku aske kanunku, sai hadaya ta kai
wurinta. To, wanda ya kasance
(1) An umurci Musulmi da tsokana ga kafiran da suke nuna musu £iyayya bayyane,
domin su nana su yin addininsu da kyau, kamar yadda Allah Ya umurce su, suna fitinar su
da wahaloli. Kuma kada ku bar su, su labe da wani watan alfarma ko hurumi, duk yadda
hali ya yi, a yi haka nan, alfarmomi na da kisasi.
(2) Ba a iya ya£i sai da abinci, kuma ba kowa ke iya zuwa ya£i ba, kamar yadda yake
ba kowa yake da abinci ba. Saboda haka sai a ciyar da dukiya, a tara ta domin daukaka
kalmar Allah. Rashin bayar da ita, to, halaka kai ne.
(3) Hukunce-hukuncen hajji a cikin fitina ko a cikin rashin lafiya, idan sun auku a
bayan harama, da hukuncin wanda ya ji dadi da umra sa'an nan ya yi hajji, ko kuma ya
hada su a cikin harama guda, watau kirani, hukuncinsu daya.
45
2 - Suratul Ba£ara
£-r
majinyaci daga cikinku, ko kuwa
akwai wata cuta daga kansa (ya yi
aski) sai fansa (fidiya) daga azumi
ko kuwa sadaka ko kuwa yanka.
To, idan kuna cikin aminci, to,
wanda ya ji dacfi da umra zuwa
haji, sai ya biya abin da ya saukaka
daga hadaya, sa'an nan wanda bai
samu ba, sai azumin yini uku a
cikin haji da bakwai idan kun
koma, wadancan goma ne cikakku.
Wancan yana ga wanda iyalinsa ba
su kasance mazaunan Masallaci
Tsararre ba. Kuma ku bi Allah da
takawa. Kuma ku sani cewa Allah
Mai tsananin ukuba ne.
197. Hajji watanni ne sanannu.
To, wanda ya yi niyyar hajji (1) a
cikinsu, to, babu jima'i, kuma babu
fasikanci, kuma babu jayayya a
cikin hajji. Kuma abin da kuka
aikata daga alheri, Allah Ya san
shi. Kuma ku yi guzuri. To, mafi
alherin guzuri yin takawa. Kuma
ku bi Ni da takawa, ya ma'abuta
hankula.
198. Babu laifi a kanku ga ku
nemi falala daga Ubangijinku.
Sa'an nan idan kun malalo daga
Arafat, sai ku yi ta ambatar Allah a
wurin Mash'aril Harami, kuma ku
tuna Shi kamar shiriyar da Ya yi
muku, kuma lalle ne kun kasance, a
gabaninsa, haklka, daga 6atattu.
199. Sa'an nan kuma ku malalo
daga inda mutane suke malalowa.
Kuma ku nemi gafara ga Allah.
Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin
kai.
"i '<*■ " A'^»>\\^'
J^ijL^aUjj^:
(1) Bayanin abubuwan da aka hana a cikin hajji da wadanda ake son a yi.
46
2 — Suratul Bakara
m\$m-
200. To, idan kun kare ayyukan
hajji, sai ku ambaci Allah kamar
ambatarku ga ubanninku, ko kuwa
mafi tsanani ga ambato. To, daga
cikin mutane akwai wanda yake
cewa: "Ya Ubangjinmu! Ka ba mu
a cikin duniya!" Kuma ba ya da
wani rabo a cikin Lahira.
201. Kuma daga gare su akwai
wanda yake cewa: "Ya Ubangi-
jinmu! Ka ba mu mai kyau a cikin
duniya da mai kyau a cikin Lahira,
kuma Ka tsare mana azabar Wuta !"
202. Wadannan suna da rabo
daga abin da suka sana'anta; kuma
Allah Mai gaggawar sakamako da
yawa ne.
203. Kuma ku ambaci Allah a
cikin kwanuka £idayayyu. (1) To,
wanda ya yi gaggawa a cikin kwana
biyu, to, babu laifl a kansa, kuma
wanda ya jinkirta, to, babu laifi a
kansa, ga wanda ya yi takawa.
Kuma ku bi Allah da takawa,
kuma ku sani cewa lalle ne ku,
zuwa gare Shi ake tara ku.
204. Kuma akwai daga mu-
tane (2) wanda maganarsa tana ba
ka sha'awa a cikin rayuwar duniya,
alhali yana shaidar da Allah a kan
abin da yake cikin zuciyarsa, kuma
shi mai tsananin husuma ne.
' ' '\' ' I
•^ • «^-^ s<
(1) Bayanin kabbarori, bayan sallolin farillai goma sha biyar, ana farawa da sallar
azahar ta ranar salla a £are da sallar asuba ta raha ta hutfu daga ranar salla. Kwanukan
Mina uku ne daga ranar salla, sai ga wanda ya yi gaggawa ya fita daga Mina bayan fitar
ranar nan kuma gabanin faduwar rana.
(2) Bayanin munafuki da halayensa, a cikin jama'a, a san shi, domin kada a dogara a
kansa. Haka mutumin kirki shi ma ana son a san shi domin a dogara da shi kamar yadda
ya yi bayaninsa.
47
Suratul Bakara
m\m-
205. Kuma idan yajuya sai yayi
gaggawa a cikin kasa domin ya yi
barna a cikinta, kuma ya halaka
shuka da 'ya'yan dabbobi. Kuma
Allah ba Ya son barna.
206. Kuma idan an ce masa:
"Ka ji tsoron Allah," sai girman
kai da yin zunubi ya cfauke shi. To
abin da yake mai jsarsa Jahannama
ce. Kuma haklka, shimfkfa ta
munana.
207. Kuma akwai daga mu-
tane (1) wanda yake sayar da ransa,
domin neman yardar Allah : Kuma
Allah Mai tausayi ga bayi ne.
208. Ya ku wadanda suka yi
Tmani! Ku shiga cikin Musulunci
gaba daya ; kuma kada kubi zambi-
yoyin Shaidan ; lalle ne shTa gare ku
makiyi ne, bayyananne.
209. To, idan kun karkace daga
bayan hujjoji bayyanannu sun zo
muku, to, ku sani cewa lalle ne
Allah, Mabuwayi ne, Mai hikima.
210. Shin, suna jira, face dai Al-
lah Ya je musu a cikin wasu inuwoyi
na girgije, da mala'iku, kuma an
hukunta aFamarin? Kuma zuwa ga
Allah aFamurra ake mayar da su.
211. Ka tambayi Ban! Isra'ila,
da yawa Muka ba su daga ayoyi
bayyanannu. Kuma wanda ya mu-
sanya ni'imar Allah daga bayan ta
je masa, to, lalle ne Allah Mai tsana-
nin ukuba ne.
^ »>» **??
\^j^xljzSi ^£Z £y \>\j
■< <<ts ' ■-
£l_*^ <C^LJl> <£s-Za j* o^ui IO£ J
(\S'Nl /it ^a a lr: ^*--=a i.A \l
£3 c->UJ\jbJL^
(1) Bayanin mumini sosai a cikin Musulmi da halayensa, a san shi domin a dogara a
kansa.
48
2 — Suratul Bakara
m\m-
212. An kawata rayuwar duniya
ga wacfanda suka kafirta, kuma
suna izgili daga wacfanda suka yi
Tmani, alhali wadanda suka yi ta£a-
wa suna bisa gare su, a Ranar Kiya-
ma. Kuma Allah Yana arzuta wan-
da Yake so, ba da lissafi ba.
213. Mutane sun kasance al'um-
ma guda. Sai Allah Ya aiki an-
nabawa suna masu bayar da bish-
ara kuma masu gargadi; kuma Ya
saukar da Littafi da gaskiya tare da
su domin (Littafin) ya yi hukunci a
tsakanin mutanen, a cikin abin da
suka sa6a wa juna a cikinsa; kuma
babu wanda ya sa6a, a cikinsa,
face wadanda aka bai wa shi daga
bayan hujjqji bayyanannu sun je
musu, domin zalunci a tsakaninsu.
Sai Allah Ya shiyar da wadanda
suka yi imani ga abin da suka sa6a
a cikinsa daga gaskiya da izninSa.
Kuma Allah Yana shiryar da
wanda Yake so, zuwa ga hanya
madaidaiciya.
214. Ko kuna zaton ku shiga
Aljanna, kuma tun misalin wadan-
da suka shige daga gabaninku bai zo
muku ba? Wahaloli da cuta sun
shafe su, kuma aka tsoratar da su
har manzonsu da wadanda suka yi
Tmani tare da shi su ce: "Yaushe
taimakon Allah zai zo?" To! Lalle
ne, taimakon Allah yana kusa!
215. Suna tambayar ka mene ne
za su ciyar. Ka ce: Abin da kuka
ciyar daga alheri sai ga mahaifa (1)
(1) Ciyar da mahaifa matalauta wajibi ne haka cfiya da 'ya'ya kanana wacfanda ba su
da dukiya har yaro ya balaga a kuma aurar da yarinya ta tare a gidan mijinta. Amma
49
2 — Suratul Bakara
m\m-<
da mafi kusantar dangantaka da
marayu da matalauta da dan hanya.
Kuma abin da kuka aikata daga
alheri, to, lalle ne, Allah gare shi
Masani ne.
216. An wajabta (2) yaki a kanku,
alhali kuwa shi abin ki ne a gare ku,
akwai fatar cewa ku ki wani abu,
alhali shi ne mafi alheri a gare ku,
kuma akwai fatar cewa kuna son
wani abu alhali kuwa shi ne mafi
sharri a gare ku. Kuma Allah ne
Yake sani, kuma ku ba ku sani ba.
217. Suna tambayar ka game da
Watan Alfarma: yin yaki a cikinsa.
Ka ce: "Yin yaki a cikinsa babban
zunubi ne, kuma hani ne daga ha-
nyar Allah, kuma kafirci da Shi ne
kuma da Masallaci Tsararre.
Kuma fitar da mutanensa daga
gare shi, shi ne mafi girman zunubi
a wurin Allah." Kuma fitina ita ce
mafi girma daga kisa. Kuma ba su
gushewa suna yakinku har su
mayar da ku daga barin addininku
idan za su iya. Kuma wanda ya yi
ridda daga gare ku ga barin addi-
ninsa har ya mutu alhali kuwa
yana kafiri, to, wadannan ayyu-
kansu sun Baci a cikin duniya da
Lahira. Kuma wadannan abokan
Wuta ne, su a cikinta madawwama
ne.
m>U
'\'*'
«£
^ji\^J^=9\ 4J^JUi\j Alii JC^^O \4J^
•>*' 9 '
matar aure da bawan mutum ciyar da su wajibi ne ko da suna da dukiya. Liyafa ga bako
har kwana uku gwargwadon bukata wajibi ne, sauran ciyarwa mustahabbi ce bayan an
fitar da zakka idan ta wajaba.
(2) Bayanin hukuncin yaki da wuri da lokacin da aka hana yinsa, da dalilin yinsa.
50
Suratul Bakara
m\m-<
218. Lalle ne wacfanda suka yi
Tmani, da wacfanda suka yi hijira
kuma suka yi jihadi a cikin hanyar
Allah, wacfannan suna fatar (sa-
mun) rahamar Allah, kuma Allah
Mai gafara ne, Mai jin kai.
219. Suna tambayar ka game da
giya da caca (1) . Ka ce: "A cikinsu
akwai zunubi mai girma da wasu
amfanoni ga mutane, kuma zunu-
binsu ne mafl girma daga amfanin-
su." Kuma suna tambayar ka mene
ne za su ciyar; ka ce: "Abin da ya
rage." (2) Kamar wancan ne Allah
Yake bayyanawar ayoyi a gare ku:
tsammaninku, kuna tunani.
220. A cikin duniya da Lahira.
Kuma suna tambayar ka game da
marayu. (3) Ka ce: "Kyautatawa
gare su ne mafi allien, kuma idan
kun hacfa da su (wajen abinci), to,
'ya'uwanku ne; kuma Allah Yana
sanin mai Batawa daga mai kyauta-
tawa. Kuma da Allah Ya so, da Ya
tsananta muku. Lalle ne Allah Ma-
buwayi ne, Mai hikima.
221. Kuma kada ku auri mata (4)
mushirikai sai sun yi Tmani : Kuma
lalle ne baiwa mumina ita ce mafi
W'sh&^JStp&il
(1) Bayanin hukuncin caca da giya da ciyarwa ta alheri. Caca da giya haramun ne
domin cutarsu ta fi amfaninsu yawa, ana hukunci da abin da ya rinjaya. Ayoyin wata sura
sun bayyana haramcin.
(2) Abin da ya rage daga larurarku da ta iyalanku da wanda ciyar da shi yake wajibi a
kanku, saura shi ne afwu. Daga afwu ake sadakar tacfamfi.
(3) Bayanin gama abinci da yara marayu masu dukiyar kansu.
(4) Bayanin irin maza da matan wani addini da ba za a aure su ba sai sun musulunta,
watau mushirikai, banda matan Mutanen Littafi, su kam ana auren 'ya'yansu tare da
kafircinsu. Ba a auren wanda ya yi ridda daga addinin Musulunci.
51
2 — Suratul Bakara
m\m-<
alheri daga diya kafira, kuma ko da
ta ba ku sha'awa. Kuma kada ku
aurar wa maza mushirikai, sai sun
yi imani, kuma lalle ne bawa mumi-
ni shi ne mafi alheri daga cfa mushi-
riki, kuma ko da ya ba ku sha'awa,
wadannan suna kira ne zuwa ga
Wuta, kuma Allah Yana kira zuwa
ga Aljanna da gafara da izninSa.
Kuma Yana bayyana ayoyinSa ga
mutane : tsammaninsu suna
tunawa.
222. Kuma suna tambayar ka
game da haila (1) . Ka ce : Shi cuta ne.
Saboda haka ku nlsanci mata a
cikin wurin haila, kuma kada ku
kusance su sai sun yi tsarki. To, idan
sun yi wanka sai ku je musu daga
inda Allah Ya umurce ku. Lalle ne,
Allah Yana son masu tuba, kuma
Yana son masu tsarkakewa.
223. Matanku gonaki ne a gare
ku, saboda haka ku je wa gona-
kinku yadda kuka so. Kuma ku
gabatar (2) (da alheri) saboda kan-
ku, ku bi Allah da ta£awa. Kuma
ku sani cewa lalle ne ku masu harfu-
wa da Shi ne. Kuma ka bayar da
bishara ga muminai.
f^H y^, 'CAMS'
»>• ^t &*!•' \lA< 2*%*? *' <'.
\jJ*aj 4*\ \y>->\j *f^oi yJaj
(1) Bayanin hukuncin saduwa da matan aure a lokacin hailarsu; watau jima'i ya
haramta a cikin haila ko bayan haila gabanin ta yi wanka. Ko da ta yi taimama ta yi salla
duk da haka dai sai ta yi wanka sannan farjinta yake halatta ga mijinta. Amma ana iya
mubashara da rungumayya ko a cikin haila bayan ta daura gyauto, ta riife cTbiya zuwa
gwiwa.
(2) Mutum na iya saduwa da matarsa yadda yake so kuma yadda ya saukaka a gare
shi, daga gaba ko daga baya^ amma ga farji banda ga dubura. Ma'anar ku gabatar da
alheri domin rayukanku, shT ne ku yi basmala ku nemi tsari daga Shaidan saboda
'ya'yanku. Ba a jima'i da mace alhali tana barci, ana son gabatar da wasa.
52
2 - Sural uJ Ba£ara
mm-
224. Kuma kada ku sanya (1) Al-
lah kambu ga rantsuwoyinku do-
min kada ku yi wani alheri, kuma
ku yi takawa, kuma ku yi wani
gyaratsakanin mutane, kuma Allah
Mai ji ne, Masani.
225. Allah ba Ya kama ku da
laifi saboda yasasshiya a cikin
rantsuwoyinku. Kuma amma Yana
kama ku saboda abin da zukatan-
ku C2) suka sana'anta. Kuma Allah
Mai gafara ne, Mai hakuri.
226. Ga wadanda suke yin rant-
suwa (3) daga matansu akwai jinki-
rin wata hucfu. To, idan sun koma,
to, lalle ne Allah Mai gafara ne, Mai
jin £ai.
227. Kuma idan sun yi niyyar
saki, to, lalle ne, Allah Mai ji ne,
Masani.
228. Kuma mata wadanda (4)
aka saki aurensu, suna jinkiri da
kansu tsarki uku. Kuma ba ya ha-
latta a gare su, su Boye abin da
ZSy>^3ffi&&
(1) Bayanin rantsuwa da hukunce-hukuncenta. Kada ku sanya rantsuwa da Allah
sababin rashin aikata wani alheri, ko wani aikin da'a, ko kuma sanya sulhu a tsakanin
mutane, kamar a ro£e shi ga wani abu daga cikinsu, sal ya yi rantsuwa ya ce: "Wallahi ba
zan yi ba 9 ' domin tsare kansa daga aikata war abin da aka nema gare shi. Yin inn wannan
rantsuwa makariihi ne ko haram, gwargwadon nauyin abin da aka yi ta saboda rashin yin
sa. Kambu shi ne wurin gwada harbi.
(2) Yasasshiyar rantsuwa ita ce, a wurin Malik, rantsuwa a kan abin da mutum ke
ganin sa tabbatacce ne, sai ya bayyana daga baya akasin tunaninsa. Kamar ya ce Wallahi
ba ni da kudi, ga saninsa kuwa haka ne ba ya da su, bai sani ba ashe wani ya mutu, ya yi
gado. A Shafl'i ita ce: a'aha Wallahi, i, Wallahi, a cikin magana ba da nufi ba.
(3) Hukuncin Tla'i, watau rantsuwa a kan barin takin matarsa domin ya wahalar da
ita, a jira shi wata hucfu, idan ya £i komawa a sake ta daga gare shi.
(4) Bayanin iddar saki da hukunce-hukuncen da suka ratayu da ita iddar tsarki uku
ga matar aure diya, baiwa tsarki biyu. Kwarkawara tsarki guda. lstibra'in zina ko kuskure
kamar idda yake.
53
2 — Suratul Bakara
g*$m-t
Allah Ya halitta a cikin mahai-
funsu, idan sun kasance suna yin
Tmani da Allah da Ranar Lahira.
Kuma mazan aurensu su ne mafiya
hakki ga mayar da su a cikin wan-
can, idan sun yi nufin gyarawa.
Kuma su matan suna da kamar
abin da yake a kansu, yadda aka
sani. Kuma maza suna da wata
daraja a kansu (su matan). Kuma
Allah Mabuwayi ne, Mai hikima.
229. Saki sau biyu (1) yake, sai a
rika da alheri, ko kuwa a sallama
bisa kyautatawa. Kuma ba ya ha-
latta a gare ku (maza) ku kar6e
wani abu daga abin da kuka ba su,
face fa idan su (ma'auran) na tsoron
ba za su tsayar da iyakokin Allah
ba. Idan kun (danginsu) ji tsoron ba
za su tsayar da iyakokin Allah ba,
to, babu laifi a kansu a cikin abin da
ta yi fansa da shi. Wacfancan iyako-
kin Allah ne, saboda haka kada ku
ketare su. Kuma wanda ya ketare
iyakokin Allah, to wadannan su ne
azzalumai.
230. Sa'an nan idan ya sake ta
(na uku), to, ba ta halatta a gare shi,
daga baya, sai ta yi jima'i da wani
miji, waninsa. Sa'an nan idan (sa-
bon mijin, watau na biyu) ya sake
ta, to, babu laifi a kansu ga su koma
wa (auren) juna, idan sun (mijin
farko da ma tar) yi zaton cewa za su
tsayar da iyakokin Allah, kuma
(1) Sakin aure da hukunce-hukuncen da suka ratayu da shi. Wanda ya saki matarsa
sau daya ko sau biyu, yana iya mayar da ita ko da ba ta so ba matukar ba ta £are idda ba.
Wanda ya yi saki uku, ba ya iya koma aurenta, sai ta yi jima'i da wani sabon miji a cikin
aure sahihi. Sakin bawa biyu ne.
54
Suratul Bakara
mm-
wacfancan dokokin Allah ne, Yana
bayyana su ga mutane wacfanda
suke sani.
231. Kuma idan kun saki mata,
sa'an nan suka isa ga ajalinsu (id-
darsu), sai ku ri£e su da alheri ko ku
sallame su da alheri, kuma kada ku
rike su a kan cutarwa domin ta
tsawaita idda. Kuma wanda ya aik-
ta wancan, to, haJaka, ya zalunci
kansa. Kuma kada ku riki ayoyin
Allah da izgili. Kuma ku tuna
ni'imar Allah da abin da Ya saukar
a kanku na Littafi da hikima. Yana
yi muku wa'azi da shi. Kuma ku bi
Allah da takawa, kuma ku sani
cewa lalle ne Allah ga dukan kome
Masani ne.
232. Kuma idan kuka saki mata,
har suka isa ga ajalinsu (iddarsu),
to, kada ku (waliyyansu) hana su,
su auri mazansu (da suka sake su)
idan sun yarda da juna a tsakaninsu
(tsohon miji da tsohuwar mata) da
alheri. Wancan ana yin wa'azi da
shi ga wanda ya kasance daga gare
ku yana Tmani da Allah da Ranar
Lahira. Wancan ne mafi mutunci a
gare ku,kuma mafi tsarki. Kuma
Allah Yana sani, kuma ku ba ku
sani ba.
233. Kuma masu haifuwa (sa-
kakku) (1) suna shayar da abin
haifuwarsu shekara biyu cikakku
ga wanda ya yi nufin ya cika sha-
yarwa. Kuma ciyar da su da tufatar
>'"< Six. '-' au< \'Z' "K't'^'sSv'
&i$&i3x&&
z*£: >\ \i$W""Z'x'i\\<.y \'\S\"\
(1) Bayanin shayar da mama ga jinjirin da ubansa ya saki uwarsa a lokacin shayarwa
ko kuma ta haife shi bayan sakin ya auku.
55
2 — Suratul Bakara
m\m-<
da su yana a kan wanda aka haifar
masa, da alheri. Ba a kallafa wa rai
face iyawarsa. Ba a cutar da uwa
game da cfanta, kuma ba a cutar da
uba game da cfansa, kuma a kan
magaji akwai misalin wancan. To,
idan suka yi nufin yaye, a kan
yardatayya daga gare su, da sha-
wartar juna, to, babu laifi a kansu.
Kuma idan kun yi nufin ku bayar
da cfiyanku shayarwa, to, babu laifi
a kanku, idan kun mlka abin da
kuka zo da shi bisa al'ada. Kuma ku
bi Allah da takawa. Kuma ku sani
cewa lalle ne Allah, ga abin da kuke
aikatawa, Mai gani ne.
234. Kuma wacfanda suke mutu-
wa (1) daga gare ku suna barin ma-
tan aure, matan suna jinkiri da
kansu wata hurfu da kwana goma.
To, idan sun isa ga ajalinsu, to,
babu laifi a kanku a cikin abin da
suka aikata game da kansu ga
al'ada. Kuma Allah ga abin da kuke
aikatawa Masani ne.
235. Kuma babu laifi a kanku a
cikin abin da kuka gitta (2) da shi
daga neman auren mata ko kuwa
kuka Boye a cikin zukatanku. Allah
Ya san cewa lalle ne ku, za ku
ambata musu (shi). Kuma amma
kada ku yi wa juna alkawari da shi a
Boye, face dai ku facfi magana
sananniya. Kuma kada ku kulla
(1) Bayanin iddar mutuwar maza; mace cfiya za ta zauna wata hucfu da kwana goma.
Baiwa matar aure tana a kan rabi. Wadda ke shakkar ciki sai ta zauna sai shakka ta debe.
Ana takaba watau mai iddar mutuwa ta nisanci kawa kowace iri ce, sai ta kare idda.
(2) Bayanin hukuncin neman auren mace a cikin iddarta. An hana sai dai da bananci,
kamar ya ce mata, "Ina zan sami kamarki?"
56
2 — Suratul Bakara
mm»-<
niyyar daurin auren sai littafm
(idda) ya kai ga ajalinsa. Kuma ku
sani cewa lalle ne, Allah Yana sanin
abin da yake cikin zukatanku, sabo-
da haka ku ji tsoronSa. Kuma ku
sani cewa Allah Mai gafara ne, Mai
hakuri.
236. Kumababu laifi (1) akanku
idan kun saki mata, matukar ba ku
shafe su ba, kuma ba ku yanka
musu sadaki ba. Kuma ku ba su
kyautar dacfacfawa, a kan mawada-
ci gwargwadonsa, kuma a kan ma-
kuntaci gwargwadonsa; domin
dadadarwa, da alheri, wajibi ne a
kan masu kyautatawa.
237. Kuma idan kuka sake su
daga gabanin ku shafe su, alhali
kuwa (2) kun yanka musu sadaki, to,
rabin abin da kuka yanka face idan
sun yafe, ko wanda daurin auren
yake ga hannunsa ya yafe. Kuma ku
yafe din ne mafi kusa da takawa.
Kuma kada ku manta da falala a
tsakaninku. Lalle ne Allah ga abin
da kuke aikatawa Mai gani ne.
238. Ku tsare (3) lokatai a kan
salloli da salla mafificiya. Kuma ku
tsayu kuna masu kankan da kai ga
Allah.
Xjk^^Jt^x^ \>WSj**j J&julJ \ ( JF'_3*j -to
^ " 9 >\\'\'
(1) Bayanin sadakin wadda aka saki gabanin shafa da yanka sadaki, watau mijin ya
saki tun bai sadu da ita ba kuma bai yanka sadaki ba. Babu sadaki gare ta sai kyautar
dacfacfawa kawai.
(2) Bayanin sadakin wadda aka yanka wa sadaki amma kuma aka sake ta gabanin
shafa, to, ita tana da rabin sadakinta, sai idan ta zauna a cfakinsa shekara guda cikakkiya,
to, sai a biya ta dukan sadakinta.
(3) Bayanin hukuncin tsare lokatan salla a cikin kowane hali: aminci ko tsoro, da
bayar da salla yadda hali ya bayar duka; tsaye ko da tafiya ko gudane. Hikimar sanya
wannan hukunci a tsakanin hukunce-hukuncen aure, domin farkarwa a kan muhimman-
cin salla, domin kada mu'amala ta shagaltar da Musulmi daga gare ta.
57
Suratul Bakara
wm^-
239. To, idan kun ji tsoro, to (ku
dai yi salla gwargwadon hali) da
tafiya icasa ko kuwa a kan dabbobi.
Sa'an nan idan kun amince, sai ku
ambaci Allah, kamar yadda Ya
nuna muku abin da ba ku kasance
kuna sani ba.
240. Kuma wadanda suke mutu-
wa (1) daga gare ku, alhali suna
barin matan aure, wasiyya ga ma-
tan aurensu da dadadawa zuwa ga
shekara guda babu fitarwa, to, idan
sun fita, to, babu laifi a kanku a
cikin abin da suka aikata game da
kansu daga abin da aka sani, kuma
Allah Mabuwayi ne, Mai hikima.
241. Kuma wadanda aka saki
suna da dadadawa gwargwadon
hali, wajabce a kan masu ta£awa (2) .
242. Kamar wancan ne Allah
Yake bayyana muku ayoyinSa:
tsammaninku, kuna hankalta.
243. Shin, ba ka gani ba, zuwa ga
wadanda suka fita (3) daga gidajen-
su, alhali kuwa su dubbai ne, domin
4$
(1) Al'ada idan ba ta saba wa rukunin sharT'a ba, ba a hana ta, sai dai babu tilastawa
ga yinta. A zamanin Jahiliyya mata suna iddar mutuwar mazansu shekara guda. Wanda ya
yi wasiyyar kada matarsa ta fita daga cfakinta har shekara, ana karbar masa, sai dai babu
tllas a gare ta da ta zauna, domin an shafe hukuncin iddar shekara ta al'adar Jahiliyya.
(2) Bayanin hukuncin dacfacfawa ga matan da aka saki bayan an yi zaman aure da su.
Tamattu'i gare su wajibi ne a kan mazansu, gwargwadon hali.
(3) Wasu mutane ne daga cikin Bani Isra'ila, annoba ta auku a kansu, sai suka fita
daga gidajensu domin gudun mutuwa, su dubu hudu ko takwas ko wanin wannan adadi,
sai Allah Ya ce musu; "Ku mutu," sai suka mutu kwana takwas ko hiyaka. Sa'an nan
kuma Allah Ya tayar da su domin Ya nuna musu cewa gudun mutuwa, ba ya hana ta, sai
abin da Ya so, shTke aukuwa. Wannan kissa tana amfanar da karfafa rayuka domin jihadi,
saboda haka umurni da yaki ya bi ta; watau ita shimficfa ce ga umurnin jihadi da fita zuwa
yaki. Kuma surar na karantar da tattalin arziki daga nan zuwa karshenta. Watau kafa gari
wajibi ne ga tattalin arziki.
58
2 — Suratul Bakara
Mlli^-
tsoron mutuwa? Sai Allah Ya ce
musu: "Ku mutu." Sa'an nan kuma
Ya rayar da su, lalle ne Allah, hakT-
ka, Ma'abucin falala a kan mutane
ne, kuma amma mafi yawan muta-
ne ba su godewa.
244. Kuma ku yi yaki a cikin
hanyar Allah, kuma^ku sani cewa
lalle ne, Allah Mai jT ne, Masani.
245. Wane ne wanda (1) zai bai
wa Allah ranee, ranee mai kyau,
domin Ya riBanya masa, riBanyawa
mai yawa? Kuma Allah Shi ne ke
damkewa, kuma yana shimficfawa,
kuma zuwa a gare Shi ake mayar da
ku.
246. Shin, ba ka gani ba zuwa ga
wasu mashawarta (2) daga Bani Is-
ra'Tla daga bayan Musa, a lokacin
da suka ce ga wani annabi nasu:
"Nacfa mana sarki, mu yi yaki a
cikin hanyar Allah." Ya ce: "Ashe,
akwai tsammaninku, idan an wa-
jabta yaki a kanku cewa ba za ku yi
yakin ba?" Suka ce: "Kuma mene
ne a gare mu, ba za mu yi yaki ba, a
cikin hanyar Allah, alhali kuwa,
haklka, an fitar da mu daga gidajen-
mu da cfiyanmu?" To, a lokacin da
aka wajabta yakin a kansu, suka
juya, sai kacfan daga gare su. Kuma
Allah Masani ne ga azzalumai.
»
CJS Ills \Lj[jL)j "S^s o* L-^p-»
(1) Bayani ga cewa jihadi ba ya yiwuwa sai mutane kowa ya bayar da taimakonsa na
dukiya ko na ma'ana. Kuma duk wanda ya bayar da taimako, to, ranee ne ya bai wa Allah,
wanda yake Shi ne Ya bayar da asalin dukiyar, da yawa ko kadan, kuma Mai sakamako ga
wanda ya yi aiki da umurninSa da babban sakamako, bayan an koma zuwa gare Shi.
Jihadi wajibi ne ga tattalin arziki domin tsaro.
(2)^Wannan kissa tana nuna cewa ba a iya yin yaki sai da Sarki, shugaba. Kuma ta
fadi dalilin da ke sanya jama'a su yi yaki; watau domin tsaron addini da rayuka da nasaba
da mutunci da dukiya.
59
2 — Suratul Bakara
m\m-
247. Kuma annabinsu (1) ya ce
musu: "Lalle ne, Allah ya nacfa
muku T)aluta (2) ya zama sarki."
Suka ce: "Yaya ne sarauta za ta
kasance a gare shi, a kanmu, alhali
kuwa mu ne mafi cancanta da sa-
rauta daga gare shi, kuma ba a ba
shi wata wadata ba daga dukiya?"
Ya ce: "Lalle ne, Allah Ya za6e shi
a kanku, kuma Ya kara masa yalwa
a cikin ilmi da jiki. Kuma Allah
Yana bayar da mulkinSa ga wanda
Yake so, kuma Allah Mawadaci ne,
Masani.
248. Kuma annabinsu ya ce
musu: "Lalle ne, alamar mulkinSa
ita ce akwatin (3) nan ya zo muku, a
cikinsa akwai natsuwa daga
Ubangijinku da sauran kaya daga
abin da Gidan Musa da Gidan Ha-
runa suka ban, mala'iku suna dau-
karsa. Lalle ne a cikin wancan ak-
wai alama a gare ku (ta nadin T)a-
luta daga Allah ne) idan kun ka-
sance masu imani."
clXMA
. *2 -X-A £
^ft^K?
(1) Sunan annabinsu Shamwilu daga Sibt Lawaya. A bayan Musa, Yaush'u bin Nun,
sa'an nan Kalib, sa'an nan Hizkfl, sa'an nan Ilyas sa'an nan Alyasa'u, daga nan Bani
Isra'ila suka rasa mai jan su har Amalika cfiyan Amine bn Ad, wadanda ke zaune a FalastTn
suka rinjayi Bani Isra'ila, suka karkashe su suka kore su daga gidajensu suka kama
'ya'yansu, har a lokacin da wata mace daga Sibt Lawaya ta haifi Shamwilu Annabi. Ya
nacfa musu sarki T>aluta.
(2) T>aluta yana a cikin gidan Binyaminu dan Ya'akubu talakawa ne suna dogara a
kan sana'a. Zuriyyar Yahuza, su ne sarakuna domin haka sunansu ya rinjaya a kan Bani
Isra'ila. Zuriyyar Lawaya su ne annabawa da malamai.
(3) 'Akwatin Natsuwa' an saukar da shi tare da Adam, a cikinsa akwai surorin
annabawa, da gadon rikonsa ya kai ga Musa yana sanya Attaura a ciki, saboda haka aka
sami karyayyun allunan Attaura a ciki da rawnin Haruna da wani abu daga Mannu da
Salwa. A lokacin da Amalika suka rinjaye su, sai suka karbe wannan akwati, suka ajiye shi
inda bai dace da shi ba, har a lokacin da mala'iku suka dauke shi zuwa ga T>aluta.
60
Suratul Bakara
M$\m-
249. A lokacin da T)aluta ya
fita (1) da rundunonin, ya ce: "Lalle
ne Allah Mai jarrabarku ne da wani
kogi. To, wanda ya sha daga gare
shi, to, ba shi daga gare ni, kuma
wanda bai cfancfane shi ba, to, lalle
ne shi, yana daga gare ni, face wan-
da ya kamfata, kamfata guda da
hannunsa." Sai suka sha daga gare
shi, face kacfan daga gare su. To, a
lokacin da (T)aluta) ya ketare shi,
shi da wacfanda suka yi Tmani tare
da shi, (sai wacfanda suka sha)
suka ce: "Babu Tko a gare mu yau
game da Jaluta da rundunoninsa."
Wacfanda suka tabbata cewa lalle
su masu gamuwa ne da Allah, suka
ce: "Da yawa kungiya kacfan ta
rinjayi wata kungiya mai yawa da
iznin Allah, kuma Allah Yana tare
da masu hakuri."
250. Kuma a lokacin da suka (2)
bayyana ga Jaluta da runduno-
ninsa, suka ce: "Ya Ubangijinmu!
Ka zuba hakuri a kanmu, kuma Ka
tabbatar da sawayenmu, kuma Ka
taimake mu a kan mutanen nan
kafirai."
251. Sai suka karya su da iznin
Allah. Kuma Dawudu ya kashe
Jaluta, kuma Allah Ya ba shi mulki
da hikima, kuma Ya sanar da shi
daga abin da Yake so. Kuma ba
\<">* \'
Jj^^\sjA\Jc>\
(1) Soja na bukatar tarbiya, su saba da wahala da kishirwa da magana mai shiryarwa.
Kogin kuwa shi ne kogin Urdun tsakanin Urdun da Falastin.
(2) Dawudu dan Aisha ya gaji annabcin Shamwilu da mulkin T)aluta, shi ne ya fara
hacfa su a cikin Bani Isra'ila bayansa sai cfansa Sulaiman ya gaje shi haka nan. Yawan
mutanen T)aluta da suka yi yaki kamar adadin mutanen Badar ne wacfanda suka yi yaki tare
da Annabi, tsira da aminci su tabbata a gare shi.
61
2 — Suratul Bakara
l£IIS3£-r
domin tunkudewar Allah ga muta-
ne sashensu da sashe ba, lalle ne, da
Rasa ta 6aci; kuma amma Allah
Ma'abucin falala ne a kan talikai.
252. Wadancan ayoy in Allah ne :
Muna karanta su a kanka da gas-
kiya: Kuma lalle ne kai, hakika,
kana daga manzanni.
253. ^Wadancan manzanni n ( 1 >
Mun fifita sashensu a kan sashe:
daga cikinsu akwai wanda Allah Ya
yi masa magana ; kuma Ya daukaka
sashensu^da darajoji; kuma Muka
bai wa Tsa dan Maryama hujjoji
bayyanannu, kuma Muka karfafS
shi da Ruhi mai tsarki. Kuma da
Allah Ya so da wadanda suke daga
bayansu, ba za su yi yaki ba, daga
bayan hujjoji bayyanannu sun je
musu. Kuma amma sun sa6a wa
juna, saboda haka daga cikinsu
akwai wanda ya yi Tmani, kuma
daga cikinsu akwai wanda ya kafir-
ta. Kuma da Allah Ya so, da ba za
su yaki juna ba, kuma amma Allah
yana aikata abin da Yake nufi.
254. Ya ku wadanda (2) suka yi
Tmani ! Ku ciyar daga abin da Muka
arzuta ku daga gabanin wani yini ya
^^J i>^-> * UU Jul) &* *Jb Juo &•
(1) Allah Yana tunkucfe 6araa a cikin kasa da wasicfar karantar da masu alheri,
domin su yaki masu sharri. Ya saukar da ilminSa da wasidar manzanninSa wadanda Ya
tabbatar da cewa Muhammadu, tsira da amincinSa su tabbata a gare shi, yana cikinsu
kuma shi ne ya fi daukaka daga cikinsu. Daga wannan aya zuwa karshen Sura duka, karin
bayani ne da shiryarwa ga hukunce-hukuncen da suka gabata da kuma yadda za a zartar
da aiki da su, kamar yadda tsarin magana zai nuna in Allah Ya so.
(2) Bayan tabbatar da manzancin Annabi Muhammadu, tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi, sa'an nan ya sabunta fuskanta da kira zuwa ga wadanda suka yi imani
da Annabi, kuma ya farkar da su game da zuwan babbar rana ta FCiyama. Sa'an nan ya
fadi sunanSa Ta'ala, Allah Mai sifofin da ke cikin aya ta 255.
62
Suratul Bakara
lOxIii^-r
zo, babu ciniki a cikinsa, kuma
babu abuta, kuma babu ceto, kuma
kafirai su ne azzalumai.
255. Allah, babu wani Ubangiji
face Shi, Rayayye, Mai tsayuwa da
kome, gyangyadj ba ya kama Shi,
kuma barci ba ya kama Shi, Shi ne
da abin da yake a cikin sammai da
abin da yake a cikin kasa. Wane ne
wanda yake yin ceto a wurinSa, face
da izninSa? Yana sanin abin da
yake a gaba gare su da abin da yake
a bayansu. Kuma ba su kewayewa
da kome daga ilminSa, face da abin
da Ya so. KursiyyunSa ya yalwaci
sammai da kasa. Kuma tsare su ba
ya nauyayarSa. Kuma Shi ne
Macfaukaki, Mai girma.
256. Babu tllastawa (1) a cikin
addini, haklka, shiriya ta bayyana
daga 6ata: Saboda haka wanda ya
kafirta da T)aguta kuma ya yi imani
da Allah, to, haklka, ya yi riko ga
igiya amintacciya, babu yankewa a
gare ta. Kuma Allah Mai ji ne,
Masani.
257. Allah Shi ne Masoyin wa-
cfanda suka yiTmani: Yana fitar da
su daga dufFai zuwa ga haske, kuma
<^v
StJiI^N^i^Xci
(1) Abubuwan bautawa, iri biyu ne; Ubangijin da Ya aiko Muhammadu da wannan
gaskiya da shiriya Shi ne Allah, da sauran iyayengiji masu dokokin kai da na son zukata
kamar nafsu da Shaicfan, na aljannu da mutane, masu kaga abin da suke so, su kira mutane
a kansa ana ce musu TDagutu. Ya yi bayanin sakamakon mabiyin kowane irin bautawar.
Sa'an nan ya biyar da kissoshi^uku domin bayanin abin da wannan magana ta kunsa; ta
farko Namaruzu tare da Ibrahim, tana nuna cewa mai mulki ana umurtar sa da bin Allah
da takawa, idan ya bi son zuciyarsa, to, ya zama T)agutu. Allah zai halakar da shi. Ta biyu
kissar Uzairu, tana nuna cewa babu abin da yake da wuya ga Allah. Ta uku kissar Ibrahim
da yadda Allah ke rayar da matattu, tana nuna cewa babu laifi ka roki Allah Ya ganar da
kai dukan abin da ya shige maka duhu domin ka kara Imani.
63
2 — Suratul Ba£ara
W®&-
wacfanda suka kafirta, masoyansu
T)agutu ne: suna fitar da su daga
haske zuwa ga duffai. Wacfannan
abokan Wuta ne, su a cikinta ma-
dawwama ne.
258. Shin, ba ka gani (1) ba zuwa
ga wanda ya yi hujjatayya da Ibra-
him a cikin (al'amarin) Ubangi-
jinsa, domin AllahYa ba shi mulki,
a lokacin da Ibrahim ya ce: "Uban-
gijina Shi ne Wanda Yake rayawa
kuma Yana matarwa." Ya ce: "Ni
ina rayarwa kuma ina matarwa."
Ibrahim ya ce: "To, lalle ne Allah
Yana zuwa da rana daga gabas : to,
ka zo da ita daga yamma." Sai aka
cfimautar da wanda ya kafirta.
Kuma Allah ba Ya shiryar da muta-
ne azzalumai.
259. K6 kuwa (2) wanda ya shude
a kan wata alkarya, alhali kuwa
tana wofintacciya a kan gadajen
resunanta. Ya ce: "Yaya Allah zai
rayar da wannan a bayan
mutuwarta." Sai Allah Ya matar da
shi, shekara dari; sa'an nan kuma
ya tayar da shi. Ya ce: "Nawa ka
zauna?" Ya ce: "Na zauna yini
daya ko kuwa rabin yini." Ya ce:
"A 'a, ka zauna shekara dari." To,
ka duba zuwa ga abincinka, da abin
shanka, (kowanensu) bai sake ba,
kuma ka duba zuwa ga jakinka,
kuma domin Mu sanya ka wata aya
ga mutane. Kuma ka duba zuwa ga
(1) Kissar farko ta Ibrahim da Namaruzu.
(2) Kissa ta biyu Uzairu da alfiarya matacciya, da jakinsa, da abincinsa bayan
shekara dari.
64
Suratul Ba£ara
W$&&-
Rasusuwa yadda Muke motsar da
su, sa'an nan kuma Mu tufatar da
su da nama." To, a lokacin da (abin)
ya bayyana a gare shi, ya ce: "Ina
sanin cewa lalle Allah a kan dukan
kome Mai Ikon yi ne."
260. Kuma a lokacin da Ibrahim
ya ce: "Ya Ubangijina! Ka nuna
mini yadda Kake rayar da
matattu." Ya ce : "Shin, kuma ba ka
yi Tmani ba?" Ya ce: "Na'am!
Kuma amma domin zuciyata, ta
natsu." Ya ce: "To, ka riici hutfu
daga tsuntsaye, ka karkatar da su
zuwa gare ka, ka yanka su, sa'an
nan kuma ka sanya juzu'i daga gare
su a kan kowane dutse, sa'an nan
kuma ka kira su, za su zo maka
gudane. Kuma ka sani cewa lalle
Allah Mabuwayi ne, Masani."
261. Sifarwadandasuke ciyar da
dukiyoyinsu a cikin hanyar Allah,
kamar sifar kwaya ne wadda ta
tsirar da zangarniya bakwai, a cikin
kowace zangarniya akwai kwaya
dari. Kuma Allah Yana ri6inyawa
ga wanda Ya so. Kuma Allah Ma-
wadaci ne, Masani.
262. Wadanda suke ciyar da
dukiyoyinsu a cikin hanyar Allah,
sa'an nan kuma ba su biyar wa abin
da suka ciyar din da gori, ko cuta,
suna da sakamakonsu a wurin
Ubangijinsu, kuma babu tsoro a
kansu, kuma ba su zama suna bakin
tiki ba.
263. Magana mai kyau da gafar-
tawa su ne mafi alheri daga sadaka
wadda wata cutarwa take biyar ta.
Kuma Allah Wadatacce ne, Mai hakuri.
» CT *' * * *{' "' s i4\ ><'*'* ii-Xf
9 ^^A^K^pWG^
^** > " "
>><i J Lj~>
i»l jl pMj L-**-*» ^H4 o*^^ ' *
WgA£
65
Suratul Ba£ara
m\m-
264. Ya ku wacfanda suka yi
Tmani! Kada ku Bata sadakokinku
da gori da cutarwa, kamar wanda
yake ciyar da dukiyarsa domin
nuna wa mutane, kuma ba ya yin
Tmani da Allah da Ranar Lahira.
To, abin da yake misalinsa, kamar
falalen dutse ne, a kansa akwai
turBaya, sai wabilin hadari (1) ya
same shi, sai ya bar shi Rankara. Ba
su iya amfani da kome daga abin da
suka sana'anta. Kuma Allah ba Ya
shiryar da mutane kafirai.
265. Kuma sifar wadanda suke
ciyar da dukiyarsu domin neman
yardqjin Allah, kuma da tabbatar-
wa daga kansu, kamar misalin 1am-
bu ne a jigawa wadda wabilin hada-
ri ya samu, sai ta bayar da amfanin-
ta ninki biyu. To, idan wabili bai
same ta ba, sai yayyafi (ya ishe ta).
Kuma Allah ga abin da kuke aika-
tawa Mai gani ne.
266. Shin dayanku na son cewa
wani lambu ya kasance a gare shi
daga dablnai da inabobi, maremari
suna gudana daga Rarkashinsa,
yana da, a cikinsa, daga kowane
'ya'yan itace, kuma tsufa ya same
shi, alhali kuwa yana da zuriyya
masu rauni — sai guguwa wadda
take a cikinta akwai wuta, ta same
shi, har ta Rone? Kamar wancan ne
Allah Yana bayyanawar ayoyi a gare
ku; tsammaninku kuna tunani.
267. Ya ku warfanda suka yi
Tmani! Ku ciyar daga mai kyaun
."" -,<'
/'^m > \ 9 *\* ?"**•? \st "'
^a* \j*-a>\ G^'^^HH^
(1) 'Wabilin hadari' watau ruwan sama kamar da bakin £warya.
66
2 — Suratul Bakara
m\m-<
abin da kuka sana'anta, kuma daga
abin da Muka fitar saboda ku
daga kasa, kuma kada ku yi nufin
mummuna ya zama daga gare shi ne
kuke ciyarwa, alhali kuwa ba ku
zama masu karBarsa ba face kun
runtse ido a cikinsa. Kuma ku sani
cewa lalle ne, Allah Mawadaci ne,
Godadde.
268. Shaicfan yana yi muku alka-
warin talauci, kuma yana umur-
nin ku da alfasha, (1) kuma Allah
Yana yi muku alkawarin gafara
daga gare shi da kari, kuma Allah
Mawadaci ne, Masani.
269. Yana bayar da hikima (ga
fahimtar gaskiyar abubuwa) ga
wanda Yake so. Kuma wanda aka
bai wa hikima, to, lalle ne, an ba shi
alheri mai yawa. Kuma babu mai
tunani face ma'abuta hankula.
270. Kuma abin da kuka ciyar
daga ciyarwa, ko kuka cika alwashi
daga wani bakance, to, lalle ne,
Allah Yana sanin sa. Kuma az-
zalumai ba su da wasu mataimaka.
277. Idan kun nuna sadakoki to,
yana da kyau kwarai kuma idan
kuka 66ye su kuma kuka je da su ga
matalauta, to, shi ne mafi alheri a
gare ku, kuma Yana karkarewa,
daga barinku, daga miyagun ayyu-
kanku. Kuma Allah ga abin da
kuke aikatawa Masani ne.
ISL^C
•V? - >.•<<.
>£*^&&zc*\£&
(1) Alfasha ita ce ayyukan zunubi kamar zina da shan giya, alhali ftatar da dukiya a
nan, ya fi tsanani, kuma babu wani badali don sakamako, saboda haka kin ciyarwa domin
gudun talauci da umurninku da alfasha sun sa6a wa juna, ga abin da shi Shaidan yake gaya
muku; watau kada ku ciyar, domin gudun talauci, amma ku sha giya, ku yi zina!
67
Suratul Bakara
m\m~i
272. Shiryar da su ba ya a kanka,
kuma amma Allah Shi ne Yake
shiryar da wanda Yake so, kuma
abin da kuka ciyar daga alheri, to,
domin kanku ne, kuma ba ku ciyar-
wa, face domin neman yardar Al-
lah, kuma abin da kuke ciyarwa
daga alheri za a cika ladarsa zuwa
gare ku, alhali kuwa ku ba a zalun-
tar ku.
273. (Ciyarwar a yT ta) ga mata-
lautan (1) nan wadanda aka tsare a
cikin hanyar Allah, ba su iya tafiyar
fatauci a cikin fcasa, jahilin halinsu
yana zaton su wadatattu saboda
kamun kai, kana sanin su da ala-
marsu, ba su ro£on mutane da na-
cewa. Kuma abin da kuka ciyar
daga alheri, to, lalle Allah gare shi
Masani ne.
274. Wadanda suke ciyar da
dukiyoyinsu, a dare da yini, 66ye da
bayyane, to suna da sakamakonsu a
wurin Ubangijinsu. Kuma babu
tsoro a kansu, kuma ba su zama
suna bafcin ciki ba.
275. Wadanda suke cin riba (2) ,
ba su tashi, face kamar yadda wan-
<j^J&\^£^jjJ&£^s\&S$ $
»< • \i ..t.ssyt/L'
*?* .<
* "^ <*L~
.*+ ^* +* "*'*■ ji»
(1) Matalautan nan 'muhajiruna' ne wacfanda suka bar dukiyarsu da iyalansu domin
hijira. Kuma ba su sami wata mataka ba a Madina, sai aka yi musu rumfuna, suna kwana a
ciki, suka tsare kansu domin jihadi da yaki da karatun Alkur'ani da ibada kamar matsayin
sqja a yanzu. Su wajen cfari hucfu ne, shugabansu, shi ne Abdur Rahman bn Sakhar, Abu
Huraira el Dibsy.
(2) Riba ita ce kari ga adadi ko ga lokaci. Amma karin adadi shi ne kari a cikin
mu'amala da zinari da azurfa, da abubuwan ci ga rayuwa. Yana haramta ga jinsi guda
kawai, kuma ana sharcfantawa ga abinci ya zama abinci ko abin gyaransa, kuma ana iya
aijiye shi, ban da 'ya'yan itacen marmari da duma da ruwa. Amma ga jinkiri an hana riba
mudlakan ko da ga 'ya'yan itacen marmari. Takardun kudi kamar sil'o'i suke domin haka
kimarsu tana hawa kuma tana sauka. Har yanzu malamai ba su yanke hukunci a kansu ba
sosai. Annabi, tsTra da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : "Ka bar abin da yake
sanya maka shakka zuwa ga wanda ba ya sanya maka shakka."
68
Suratul Ba£ara
m\m-
da Shaicfan yake cfimautarwa daga
shafa yake tashi. Wancan, domin
lalle ne sun ce: "Ciniki kamar riba
yake." Kuma Allah Ya halatta cini-
ki kuma Ya haramta riba. To, wan-
da wa'azi daga Ubangijinsa ya je
masa, sa'an nan ya hanu, to yana da
abin da ya shige, kuma al'amarinsa
(ana wakkala shi) zuwa ga Allah.
Kuma wanda ya koma, to, wacfan-
nan su ne abokan Wuta, su a cikinta
madawwama ne.
276. Allah Yana shafe albarkar
riba, kuma Yana kara sadakoki.
Kuma Allah ba Ya son dukan mai
yawan kafirci, mai zunubi.
277. Lalle ne, wacfanda suka yi
Tmani, kuma suka aikata ayyukan
kwarai, kuma suka tsayar da salla,
kuma suka bayar da zakka, suna
da sakamakonsu a wurin Ubangi-
jinsu, kuma babu tsoro a kansu,
kuma ba su zama suna yin bakin
ciki ba.
278. Ya ku wacfanda suka yi
Tmani! Ku bi Allah da takawa,
kuma ku bar abin da ya rage daga
riba, idan kun kasance masu Tmani.
279. To, idan ba ku aikata ba, to,
ku sani fa da akwai yaki daga Allah
da ManzonSa. Kuma idan kun
tuba, to, kuna da asalin duki-
yoyinku, ba ku zalunta, kuma ba a
zaluntar ku.
280. Kuma idan ma'abucin wa-
hala ya kasance (mabacci) to, jinkir-
tawa ake yi zuwa ga saukin al'ama-
rinsa, kuma da kun yi sadaka, shi ne
mafi alheri a gare ku, idan kun
kasance kuna sani.
.^> *
69
Suratul Ba£ara
fSM»5TW.
- r
281. Kuma ku ji tsoron wani
yini wanda ake mayar da ku a cikin-
sa zuwa ga Allah, sa'an nan kuma a
cika wa kowane rai abin da ya
sana'anta, kuma su ba a zaluntar
su.
282. Ya ku wacfanda suka yi
Tmani! Idan kun yi mu'amalar
bayar da bashi zuwa ga wani ajali
ambatacce, sai ku rubuta shi. Kuma
wani marubuci ya yi rubutu a tsaka-
ninku da adalci. Kuma kada maru-
buci ya ki rubutawa, kamar yadda
Allah Ya sanar da shi, sai ya rubuta.
Kuma wanda bashin yake a kansa
sai ya yi shibta, kuma ya ji tsoron
Allah, Ubangijinsa, da takawa,
kuma kada ya rage wani abu daga
gare shi. To, idan wanda bashin
yake a kansa ya kasance wawa ne
ko kuwa rarrauna, ko kuwa shi ba
ya iya shibta, to, sai waliyyinsa ya yi
shibtar da adalci. Kuma ku shaidar
da shaidu biyu daga mazanku, to,
idan ba su zama maza biyu ba, to,
namiji guda da mata biyu, daga
wacfanda kuke yarda da su daga
shaidun, domin mantuwar cfa-
yansu, sai gudarsu ta mazakutar (1)
da cfayar. Kuma kada shaidun su ki,
idan an kira su. Kuma kada ku kosa
ga rubuta shi, karami ya kasanci ko
babba, zuwa ajalinsa. Wancan ne
mafi adalci a wurin Allah, kuma
mafi tsayuwa ga shaida, kuma mafi
kusa ga rashin shakkarku. Sai idan
ya kasance fatauci ne halartacce
^si^r
oWp^WJi^
*K
? > \- 9 \^\ 9 S\\ >l\" \ y'A'-'* 1" > "\
*?' '% '
£ *A
(1) Watau mata biyu su zama kamar namiji guda ga bayar da shaida. Kuma ana
fassara shi da "ta tunatar da dayar"
70
2 — Suratul Bakara
m\m-
wanda kuke gewayarwa da shi han-
nu da hannu a tsakaninku, to babu
laifi a kanku, ya zama ba ku rubuta
shi ba. Kuma ku shaidar idan kun yi
sayayya. Kuma kada a wahalar da
marubuci, kuma kada a wahalar da
shaidu, kuma idan kun aikata, to,
lalle ne, shi fasikanci ne game da ku.
Kuma ku bi Allah da takawa, kuma
Allah Ya sanar da ku. Kuma Allah
ga dukan kome Masani ne.
283. Kuma idan kun kasance a
kan tafiya, kuma ba ku sami maru-
buci ba, to, a bayar da jingina
kar6a66iya (ga hannu). To, idan
sashenku ya amince wa sashe, to,
wanda aka amince wan nan sai ya
bayar da amanarsa, kuma ya bi
Allah, Ubangijinsa, da takawa.
Kuma kada ku 66ye shaida, kuma
wanda ya 66ye ta, to, shi mai zunu-
bin zuciyarsa ne. Kuma Allah ga
abin da kuke aikatawa Masani ne.
284. Allah ne, da abin da yake a
cikin sammai da abin da yake a
cikin kasa, kuma idan kun bayyana
abin da yake a cikin zukatanku (na
shaida), ko kuka 66ye shi, Allah zai
bincike ku da shi, sa'an nan Ya yi
gafara ga wanda Yake so, kuma Ya
azabta wanda Yake so. Kuma Al-
lah a kan dukan kome Mai Ikon yi
ne.
(i)
' * tr*
A
(1) Wannan aya ita ce karshen bayani a kan bayar da shaida. A kan shaidar da
mutum ya bayyana ko ya boye a cikin rai, Allah Yake yi masa bincike domin hakkin wani
da ya rataya a kan wannan bayyanawar ko boyewar. Ita ayar da biyu na bayanta sun
£unsa ilmin Bakara dukanta.
71
Suratul Bakara
I*M&-
285. Manzon Allah ya yi imani
da abin da aka saukar zuwa gare shi
daga Ubangijinsa, da muminai.
Kowanensu ya yi Imani da Allah, da
mala'ikunSa, da littattafanSa, da
manzanninSa. Ba mu rarrabewa a
tsakanin cfaya daga manzanninSa.
Kuma (muminai) suka ce, "Mun ji
kuma mun yi cfa'a: (muna neman)
gafararKa, ya Ubangijinmu, kuma
zuwa a gare Ka makoma take (1) "
286. Allah ba Ya kallafa wa rai
face ikon yinsa, yana da ladar abin
da ya tsirfanta, kuma a kansa akwai
zunubin abin da ya yi ta aikatawa :
"Ya Ubangijinmu! Kada Ka kama
mu, idan mun yi mantuwa, ko kuma
mun yi kuskure. Ya Ubangijinmu !
Kuma kada Ka aza nauyi a kanmu,
kamar yadda Ka aza shi a kan
wacfanda suke a gabaninmu. Ya
Ubangijinmu! KadaJCa sanya mu
cfaukar abin da babuTko gare mu da
shi. Kuma Ka yafe daga gare mu,
kuma Ka gafarta mana, kuma Ka yi
jin kai gare mu. Kai ne MajiBin-
cinmu, saboda haka Ka taimake mu
a kan mutanen nan kafirai."
(1) Aya ta 285 da ta 286 sun kunsa aikin Annabi da wacfanda suka bi shi daga akTda
da magana da aiki da kyautatawa da mayar da al'amari ga Allah, da addu'ar tsari da
nema daga Ubangijinsu. Aya ta 286 ita ce mafl kyaun addu'a. Kuma ta nuna Musulmi sun
sa6a wa Yahudawa masu cewa 'Mun ji, mun lei!'
72
3 — Suratu Al 'Imrana
£MfcJli&-r
Tana karantar da cewa Allah Yana kar6a addu'ar wanda ya
kira Shi da gaskiyar niyya, kuma Yana keta al'adu da wannan kira.
Babu abin da yake da wuya ga Allah idan an kacfaita Shi da
tsarkakewa daga shirki da abin da ya yi kama da shirki.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. A. L. M.
2. Allah, babu wani abin bauta-
wa face Shi, Rayayye Mai tsayuwa
da kome.
3. Ya sassaukar da Littafi a gare
ka da gaskiya, yana mai gaskatawa
ga abin da ke gaba gare shi, kuma
Allah Ya saukar da Attaura da
LinjTla.
4. A gabani, suna shiryar da mu-
tane, kuma Ya saukar da littattafai
masu rarrabewa. Lalle ne wacfanda
suka kafirta da ayoyin Allah, suna
da azaba mai tsanani. Kuma Allah
Mabuwayi ne, Ma'abucin azabar
ramuwa.
5. Lalle ne, Allah babu wani abin
da ke Boyuwa gare Shi a cikin kasa,
kuma babu a cikin sama.
33 i»
fti*ffitfti\'A&£1
73
3 — Suratu Al 'Imrana
t«j&-r
6. Shi ne Wanda Yake suranta
ku a cikin mahaifu yadda Yake so.
Babu abin bautawa face Shi, Mabu-
wayi, Mai hikima.
7. Shi ne Wanda ya saukar da
Littafi a gare ka, daga cikinsa akwai
ayoyi bayyanannu, su ne mafi ya-
wan Littafin, da wasu masu kama
da juna. To, amma wacfanda yake a
cikin zukatansu akwai karkata, sai
suna bin abin da yake da kama da
juna daga gare shi, domin neman
yin fitina da tawTlinsa. Kuma babu
wanda ya san tawilinsa face Allah.
Kuma matabbata a cikin ilmi suna
cewa : "Mun yilmani da shi ; dukan-
sa daga wurin Ubangijinmu yake."
Kuma babu mai tunani face
ma'abuta hankula.
S. Ya Ubangijinmu! Kada Ka
karkatar da zukatanmu bayan har
Ka shiryar da mu, kuma Ka ba mu
rahama daga gunKa. Lalle ne, Kai,
Kai ne Mai yawan kyauta.
9. "Ya Ubangijimu ! Lalle ne Kai,
Mai tara mutane ne domin wani
yini wanda babu shakka a gare shi.
Lalle ne Allah ba Ya sabawar loka-
cin alkawari."
10. Lalle ne wacfanda suka kafir-
ta, dukiyoyinsu ba su tunkude
musu kome daga Allah, kuma
'ya'yansu ba su tunkudewa, kuma
wacfannan, su ne makamashin wuta.
77. Kamar cfabi'ar mutanen Fi-
r'auna da wacfanda ke a gabaninsu,
sun icaryata ayoyinMu, sai Allah
Ya kama su saboda zunubansu,
kuma Allah Mai tsananin ulcuba ne.
^•J ov^ v-JbjboiJUb Aju>L>1§ ££*ib^
c
•>f>^
's ^ ,^ » # • I y s
74
Suratu Al 'lmrana
$my$&-r
12. Ka ce wa wacfanda suka ka-
firta : "Za a rinjaye ku, kuma a tara
ku zuwa Jahannama, kuma shimfi-
cfar ta munana!
13. "Lalle ne wata aya ta ka-
sance a gare ku a cikin kungiyoyi
biyu da suka hadu; kungiya guda
tana yaki a cikin hanyar Allah, da
wata kafira, suna ganin su ninki
biyu nasu, a ganin ido. Kuma Allah
Yana karfafa wanda Yake so da
taimakonSa. Lalle ne a cikin wan-
nan, haklka, ^akwai abin kula ga
ma'abuta baslra."
14. An kawata wa mutane son
sha'awoyi daga mata da cfiya da
dukiyoyi abubuwan tarawa daga
zinariya da azurfa, da dawaki kiwa-
tattu da dabbobin ci da hatsi. Wan-
nan shi ne dacfin rayuwar duniya.
Kuma Allah a wurinSa kya-
kkyawar makoma take.
75. Ka ce: Shin kuma, in gaya
muku mafi alheri daga wannan?
Akwai gidajen Aljanna a wurin
Ubangiji saboda wadanda suka bi
Shi da takawa, koguna suna gudana
daga karkashinsu, suna madaw-
wama a cikinsu, da matan aure
tsarkakakku, da yarda daga Allah.
Kuma Allah Mai gani ne ga ba-
yinSa.
16. Wadanda suke cewa: "Ya
Ubangijinmu ! Lalle ne mu, mun yi
Tmani, sai Ka gafarta mana zunu-
banmu kuma Ka tsare mu daga
azabar wuta."
17. Masu hakuri, da masu gas-
kiya, da masu kankan da kai, da
75
3 — Suratu Al 'Imrana
3Mj&-r
masu ciyarwa, da masu istingifari a
lokutan asuba.
18. Allah Ya shaida cewa : Lalle
ne babu abin bautawa face Shi,
kuma mala'iku da ma'abuta ilmi
sun shaida, Yana tsaye da adalci,
babu abin bautawa face Shi, Mabu-
wayi, Mai hikima.
19. Lalle ne, addini a wurin Al-
lah, shi ne Musulunci. Kuma wa-
danda aka bai wa Littafi ba su sa6a
ba, face a bayan ilmi ya je musu,
bisa zalunci a tsakaninsu. Kuma
wanda ya kaflrta da ayoyin Allah,
to, lalle ne Allah Mai gaugawar
sakamako ne.
20. To, idan sun yi musu da kai,
sai ka ce, "Na sallama fuskata ga
Allah, kuma wanda ya bi ni
(haka)." Kuma ka ce wa wadanda
aka bai wa littafi da Ummiyyai: (1)
"Shin, kun sallama?" To, idan sun
sallama, haklka, sun shiryu, kuma
idan sun juya, to, kawai abin da ke
kanka, shi ne iyarwa. Kuma Allah
Mai gani ne ga bayinSa.
21. Lalle ne wadanda suke kaflr-
ta da ayoyin Allah, kuma suna
kashe annabawa, ba da wani hakki
ba, kuma suna kashe wadanda ke
umurni da yin adalci daga mutane,
to, ka yi musu bushara da azaba
mai radacfi.
#P&^&$fi&ffi
'•:\'H\''><\:
VCSsQj&ti
*■'"+' ss ** ^ *'>-' *%"*"' ' s %~s * '
4 T ^
?" > \<
"J
^ 'tf -<" \* *" -' 9< '**\\
(1) Ummiyyi shi ne wanda bai iya karatu da rubutu ba. A cikin Alkur'ani ana nufin
Larabawa da wannan sunan, domin ba su da wani littafin sama da suke da shi a lokacin
nan. Amma ba ana nufin ba su da rubutu ba. Haruffan rubutun Alkur'ani tun a zamanin
Isma'ila dan Ibrahima aka san su. Kuma a cikin Larabawa da yawa sun san su, har suna
rubuta kasidu masu kyau, suna ratayewa a cikin Ka'aba. Jahiliyya ita ce lokacin da ba a
aiki da wani littafi na sama kamar yadda mafi yawan mutane suke a yanzu, karnin ishirin.
Shi ma karnin wata Jahiliyya ne.
76
3 — Suratu Al 'Imrana
$mYi&-r
22. Wacfannan ne wacfanda
ayyukansu suka Baci a cikin duniya
da Lahira, kuma ba su da wasu
mataimaka.
23. Shin, ba ka ga wacfanda aka
bai wa rabo daga littafi ba ana kiran
su zuwa ga Littafin Allah domin ya
yi hukunci a tsakaninsu sa'an nan
wata kungiya daga cikinsu ta juya
baya, kuma suna masu bijirewa?
24. Wannan kuwa, domin lalle
ne su, sun ce: "Wuta ba za ta shafe
mu ba, face a 'yan kwanaki
kidayayyu." Kuma abin da suka
kasance suna kirkirawa na karya
ya rude su a cikin addininsu.
25. To, yaya idan Mun tara su a
yini wanda babu shakka a cikinsa,
kuma aka cika wa kowane rai
sakamakon abin da ya tsirfanta,
alhali kuwa, su ba za a zalunce su
ba?
26. Ka ce : (1) "Ya Allah Mamal-
lakin mulki, Kana bayar da mulki
ga wanda Kake so, Kana zare mulki
daga wanda Kake so, kuma Kana
buwayar da wanda Kake so, kuma
Kana kaskantar da wanda Kake so,
ga hannunKa alheri yake. Lalle ne
Kai, a kan kowane abu, Mai ikon yi
ne.
27. "Kana shigar da dare a cikin
yini, kuma Kana shigar da yini a
cikin dare, kuma Kana fitar da mai
\> \' \< • It's ** s f<*s
>££&
^syft$£4*\Q*SjZti4$$&
(1) Wato ka mayar da Ikon kome ga Allah, Yana yin sa yanda Yake so, babu mai iya
hanawa, sa'an nan kuma ka ce wa muminai, kada su yi wata mu'amala da kafirai, su bar
yan'uwansu muminai, sai dai a kan lalura kawai. Wanda ya riki kafirai ya bar muminai, to,
ba shi tare da Allah a cikin kome.
77
3 — Siiratu Al 'Imrana
3MJ&-r
rai daga mamaci, kuma Kana fitar
da mamaci daga mai rai, kuma
Kana arzuta wanda Kake so ba da
lissafi ba."
28. Kada muminai su riki kafirai
masoya, baicin muminai. Kuma
wanda ya yi wannan, to, bai zama a
cikin kome ba daga Allah, face fa
domin ku yi tsaro daga gare su da
'yar kariya. Kuma Allah Yana tso-
ratar da ku Kansa. Kuma zuwa ga
Allah makoma take.
29. Ka ce: "Idan kun 66ye abin
da ke a cikin kirazanku, ko kuwa
kun bayyana shi, Allah Yana sanin
sa. Kuma Yana sanin abin da ke a
cikin sammai da kasa. Kuma Allah
a kan kowane abu Mai Ikon yi ne."
30. A ranar da kowane rai yake
samun abin da ya aikata daga alhe-
ri, a halarce, da kuma abin da ya
aikata daga sharri, alhali yana gu-
rin, da dai lalle a ce akwai fage mai
nlsa a tsakaninsa da abin da ya
aikata na sharrin! Kuma Allah
yana tsoratar da ku Kansa. Kuma
Allah Mai tausayi ne ga bayinSa.
31. Ka ce: "Idan kun kasance
kuna son Allah, to, ku bl ni, Allah
Ya so ku, kuma Ya gafarta muku
zunubanku. Kuma Allah Mai gafa-
ra ne, Mai jin kai."
32. Ka ce: "Ku yi cfa'a ga Allah
da Manzo". To, amma idan sun
juya baya, to, lalle ne Allah ba Ya
son kafirai.
33. Lalle ne Allah Ya zaBi Ada-
ma da Nuhu da Gidan IbrahTma da
Gidan Imrana a kan talikai.
G3 K^\^^j^XJ^b^
r >. 9 * .'£
ftp C^uilJ\J^o>^J\^j
78
3 — Suratu Al 'Imrana
$tmm-r
34. Zuriyya ce sashensu (1) daga
sashe, kuma Allah Mai ji ne,
Masani.
35. A lokacin da matar Imra-
na (2) ta ce: "Ya Ubangijina! Lalle
ni, jia yi bakancen abin da ke cikin
cikma gare Ka; ya zama 'yantacce,
sai Ka karba daga gare ni. Lalle ne
Kai, Kai ne Mai ji, Masani".
36. To, a lokacin da ta haife ta,
sai ta ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne
ni, na haife ta mace!" Kuma Allah
ne Mafi sanin abin da ta haifa.
"Kuma namiji bai zama kamar
mace ba. Kuma m, na yi mata suna
Maryamu (3) , kuma lalle ne ni, ina
nema mata tsari gare Ka, ita da
zuriyarta daga Shaicfan jefaffe."
37. Sai Ubangijinta Ya karbe ta
karba mai kyau. Kuma Ya
yabanyartar da ita yabanyartarwa
mai kyau, kuma Ya sanya renonta
ga Zakariyya. Ko da yaushe
Zakariyya ya shiga masallaci, a gare
ta, sai ya sami abinci a wurinta. (Sai
kuwa) ya ce: "Ya Maryamu! Daga
ina wannan yake gare ki?" (Sai) ta
ce "Daga wurin Allah yake. Lalle
<?« <^f
r ro T
\*z£\&J^ f V&\
/*» ••>
y&fi&}$b \^^j^\C>j v^BtJS^jUJi
* < <.+s
<5*^1*2H«
M,
lL*«^bui \^Cj>\j ^y~~*- <J>?A? WfL> ^ 4^- tV'*
•y jf '
Epc- >L— *^-j^t JlZ&o*
(1) Su duka daidai suke ga mai da al'amari ga Allah.
(2) Matar Imrana sunanta Hannatu diyar Fa£uza, ba ta haifuwa, sai wata rana ta ga
tsuntsuwa tana ciyar da tsakonta, sai ta yi sha'awar samun da, saboda haka ta roki Allah
Ya ba ta cfa. Da mijinta Imrana ya take ta sai ta sami ciki, domin murna sai ta yi alkwarin
'yanta shi da bakance ga Masallacin Baitil Mukaddas domin ya ri£a yi masa hidima. To, a
lokacin da ta haihu sai ta sami diya mace. Ga shari'arsu ba a 'yanta mace ga irin wannan
aiki na hidimar masallaci, domin haka ta nemi uzuri da cewa, ta haife ta mace, mace ba
kamar namiji take ba. Har ta yi rucfii ta juya, ta ce, namijin ba kamar mace ba, domin
namiji ne a cikin zuciyarta.
(3) Maryam, ma'anarta mai ibada. Abinci da ake kai mata a cikin Masallaci shT ne
'ya'yan itace, irin na dari, a lokacin bazara, kuma irin na bazara a lokacin dari. Wannan
kuma ya motsar da begen Zakariyya ga samun da, bayan shi da matarsa sun tsufa ba su
haifu ba. Sai ya roki Allah kuma Ya karba masa, Ya ba shi Yahaya Annabi.
79
3 — Suratu Al 'Imrana
Offli&-r
ne, Allah Yana arzuta wanda Ya so,
ba da lissafi ba."
38. A can ne Zakariyya ya roki
Ubangijinsa, ya ce, "Ya Ubangijina!
Ka ba ni zuriyya mai kyau daga
gunKa. Lalle ne Kai Mai jin addu'a
Kake".
39. Sai mala'iku suka kiraye shi,
alhali kuwa shT yana tsaye yana
salla a cikin masallaci. (Suka ce),
"Lalle ne, Allah Yana ba ka busha-
ra da Yahaya, alhali yana mai
gaskatawar wata kalma daga Allah,
kuma shugaba, kuma tsarkakke,
kuma annabi daga salihai."
40. Ya ce: "Ya Ubangijina!
Yaya yaro zai samu a gare ni, alhali
kuwa, lalle tsufa ya same ni, kuma
matata bakarariya ce?" Allah ya
ce, "Kamar hakan ne, Allah Yana
aikata abin da Yake so."
41. Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka
sanya mini wata alama!" (Allah)
Ya ce "Alamarka ita ce ba za ka iya
yi wa mutane magana ba har yini
uku face da ishara. Sai ka ambaci
Ubangijinka da yawa. Kuma ka yi
tasblhi da marece da safe."
42. Kuma a lokacin da mala'iku
suka ce: "Ya Maryamu! Lalle ne,
Allah Ya zaBe ki, kuma Ya tsarkake
ki, kuma Ya zaBe ki a kan matan
talikai.
43. "Ya Maryamu! Ki yi kankan
da kai ga Ubangijinki, kuma ki yi
sujada, kuma ki yi ruku'i tare (1) da
masu ruku'i."
:&&&
\ 9 ' *''vr**'r
■r-
&
^^iJb JL3J (%^(4 o^j^lyj Jt3
(1) Wannan ya nuna muhimmancin salla tare da jama'a a masallaci, ko da ga mata.
Sai dai hali ya nuna an fi son mace ta yi salla a dakinta.
80
3 — Siiratu Al 'Imrana
3Wi&-r
44. Wannan yana daga laba-
run (1) gaibi, Muna yin wahayinsa
zuwa gare ka (Muhammadu). Ba ka
kasance ba a wurinsu, a Iokacin da
suke jefa alkalumansu (domin ku-
ri'a) wane ne zai yi renon Maryam.
Kuma ba ka kasance a wurinsu ba a
Iokacin da suke ta yin husuma (2) .
45. A Iokacin da mala'iku suka
ce"Ya Maryamu! Lalle ne Allah
Yana ba ki bushara da watajcalma
daga gare Shi; sunansa MasThuTsa
cfan Maryama, yana mai daraja a
duniya da Lahira kuma daga
Makusanta.
46. "Kuma yana yi wa mutane
magana a cikin shimfidar jariri, da
kuma Iokacin da yana dattijo,
kuma yana daga salihai."
47. Ta ce: "Ya Ubangijina!
Yaya yaro zai kasance a gare ni,
alhali kuwa wani mutum bai shafe
ni ba?" (Allah) Ya ce: "Kamar
wannan ne, Allah Yana halittar
abin da Yake so. Idan Ya hukunta
wani al'amari, sai ya ce masa, c Ka
kasance!' Sai yana kasancewa."
p ^S^^OJJ**^*
±2
»1'
(1) Wannan yana daga cikin dalTlan annabcin Annabi Muhammad, tsira da aminci su
tabbata a gare shi, wajen fadar labarin abin da bai halarta ba.
(2) Uwar Maryamu ta dauke ta, ta kai ta ga Bani Kahin dan Haruna dan'uwan Musa,
a Iokacin nan, su ne suke tsaron Baitil Mukaddas, ta mlka musu ita, ta ce: "Ku karba. Na
'yantar da ita, kuma mace mai haila ba ta shiga masallaci, kuma ba zan mayar da ita a
gidana ba." Sai suka ce: "Wannan diyar Limaminmu ce kuma Shugaban Kurbaninmu."
Zakariyya ya ce: "Ku ba ni ita domin innarta tana tare da ni." Su ka ce: "Rayukanmu ba
su iya barin ta ga wani." Sai suka yi kurTa da alkalumansu da suke rubutun Attaura da su.
Sai Zakariyya ya rinjaya. An ce sun tafi kogin Urdun ne suka jefa alkaluman nasu, a kan
cewa wanda alkalaminsa bai bi ruwa ba, ya tsaya, shi ne ya rinjaya. Sai Zakariyya ya
rinjaya, ga shi kuma shine shugabansu, kuma malaminsu, kuma annabinsu, sai ya sanya ta
a cikin bene, a cikin masallacinsa.
81
3 — Suratu Al 'Imrana
$mm>-r
48. Kuma Ya sanar da shi rubu-
tu da hikima da Taurata da InjTla.
49. Kuma (Ya sanya shi) manzo
zuwa ga Bani Isra'ila £da sako,
cewa), "Lalle ne, ni hakika, na zo
muku da wata aya daga Ubangi-
jinku. Lalle ne, ni, ina halitta muku
daga laka, kamar siffar tsuntsu,
sa'an nan in hura a cikinsa, sai ya
kasance tsuntsu, da izinin Allah.
Kuma ina warkar da wanda aka
haifa makaho, da kuturu, kuma ina
rayar da matattu, da izinin Allah.
Kuma ina gaya muku abin da kuke
ci da abin da kuke ajiyewa a cikin
gidajenku. Lalle ne, a cikin wannan
akwai aya a gare ku, idan kun ka-
sance masu yin Tmani.
50. "Kuma ina mai gaskatawa ga
abin da yake a gabanina daga Tau-
rata. Kuma (na zo) domin in halatta
muku sashen abin da aka haramta
muku. Kuma na tafo muku da wata
aya daga Ubangijinku. Sai ku bi
Allah da takawa, kuma ku yi mini
da'a.
51. "Lalle Allah Shi ne Ubangi-
jina, kuma Ubangijinku, sai ku bau-
ta Masa. Wannan ce hanya madai-
daiciya."
52. To, a lokacin da Tsa ya gane
kafirci daga gare su, sai ya ce: "Su
wane ne mataimakana zuwa ga
Allah?" Hawariyawa suka ce: "Mu
ne mataimakan Allah. Mun yi Tma-
ni da Allah. Kuma ka shaida cewa,
lalle ne mu, masu sallamawa ne.
*s -< •
£?' srfx&'s'*'
^j^^^/^4^^y^^
*j^, _f K " + >
> <* +%'
ti'J&y
>*<
$&+
&£&£^y&x*j&&
82
3 — Suratu Al 'Imrana
$iMm-r
53. "Ya Ubangijinmu! Mun yi
Tmani da abin da Ka saukar, kuma
mun bi ManzonKa, sai Ka rubuta
mu tare da masu shaida. (1) "
54. Kuma (Kafirai) suka yi ma-
kirci, Allah kuma Ya yi musu (saka-
makon) makircin, kuma Allah ne
Mafi alherin masu saka wa makirci.
55.^ A lokacin da Ubangiji Ya ce :
"Ya Tsa ! Lalle NlMai karbar ranka
ne, kuma Mai dauke ka ne zuwa
gare Ni, kuma Mai tsarkake ka
daga wadanda suka kafirta, Jcuma
Mai sanya wadanda suka bi ka a
bisa wadanda suka kafirta, har Ra-
nar Kiyama. Sa'an nan kuma zuwa
gare Ni makomarku take, sa'an nan
In yi hukunci a tsakaninku, a cikin
abin da kuka kasance kuna sa6a wa
juna.
56. "To, amma wadanda suka ka-
firta, sai In azabta su da azaba mai
tsanani, a cikin duniya da Lahira,
kuma ba su da wasu masu taimako.
57. Kuma amma wadanda suka
yi Tmani, kuma suka aikata ayyu-
kan kwarai, sai (Allah) Ya cika
musu ijarorinsu. Kuma Allah ba Ya
son azzalumai.
58. ' ' Wannan Muna karanta shi a
gare ka (Muhammad) daga ayoyi,
da Tunatarwa mai hikima
(Alkur'ani)."
^+s\so J.s<ys 4* Ci
C*>J
<*£$*, ^^ Z*
(1) Masu shaida su ne Musulmi domin a cikin Attaura sunansu masu shaida, mabiya
Annabi Ummiyyi.
83
3 — Suratu Al 'Imrana
®Mf&-r
59. Lalle, ne misalin Tsa a wurin
Allah kamar misalin Adama ne,
(Allah) Ya halitta shi daga tur6aya,
sa'an nan kuma Ya ce masa: "Ka
kasance." Sai yana kasancewa.
60. Gaskiya daga Ubangijinka
take, saboda haka kada ka kasance
daga masu shakka.
61. To, wanda ya yi musu (1) da
kai a cikinsa, a bayan abin da ya zo
maka daga ilmi, to ka ce: "Ku zo
mu kirayi 'ya'yanmu da 'ya'yanku
da matanmu da matanku da kanmu
da kanku, sa'an nan kuma mu kan-
kantar da kai, sa'an nan kuma mu
sanya la'anar Allah a kan makar-
yata."
62. Lalle ne wannan, hakTka, shi
ne labari tabbatacce, kuma babu
wani abin bautawa face Allah,
kuma lalle ne, Allah, hakTka, Shi ne
Mabuwayi Mai hikima.
63. To, idan sun juya baya, to,
lalle Allah Masani ne ga ma-
6annata.
64. Ka ce: "Ya ku Mutanen
Littafi! (2) Ku tafo zuwa ga kalma
Jo^fSCjj^^ia^^^
(|p d/CS JT^J &'s$x~>\jo*
L^J/yALJbwi-»>o*^Sdlj >/w§. la*
(1) Wanda ya yi hujjacewa da Annabi a kan sha'anin Tsa; kamar Nasaran Najran,
sun tafi domin su yi jayayya da Annabi. Ya kira su zuwa ga mubahala, suka ce, sai sun yi
shawara, suka ce wa junansu: "Kun san gaskiya mutumin nan Annabi ne. Ku bar
ra'ayinku na mubahala, domin wani Annabi bai taba yin ta tare da wasu mutane ba, face
sun halaka." Bayan haka suka iske Annabi ya fito,jshi da Hasan da Husaini da Fatima da
Ali, kuma ya ce musu: "Idan na yi addu'a ku ce, 'Amin"\ Sai suka ki mubahalar, suka yi
sulhu a kan jizya.
(2) Mutanen Littafi su ne Yahudujla Nasara ko da yake an kare magana ne a kan
Tsa, domin kira zuwa ga addini mai akida sahThiya ya hada kowanensu.
84
Suratu Al 'Imrana
$mm-r
mai daidaitawa (1) a tsakaninmu da
ku; kada mu bauta wa kowa face
Allah. Kuma kada mu hacfa kome
da Shi, kuma kada sashenmu ya riki
sashe Ubangiji, baicin Allah." To,
idan sun juya baya sai ku ce: "Ku
yi shaida cewa, lalle ne mu masu
sallamawa ne."
65. Ya Mutanen Littafi ! Don me
kukejiujjacewa a cikin sha'anin
Ibrahlma, alhali kuwa ba a saukar
da Attaura da Injila ba face daga
bayansa? Shin ba ku hankalta?
66. Gaku ya wadannan! Kunyi
hujjacewa a cikin abin da yake kuna
da wani ilmi game da shi, to, don me
kuma kuke yin hujjacewa a cikin
abin da ba ku da wani ilmi game da
shi? Allah Yana sani, kuma ku, ba
ku sani ba!
67. Ibrahlma bai kasance Baya-
hude ba, kuma bai kasance Bana-
sare ba, amma ya kasance mai kar-
kata zuwa ga gaskiya, mai salla-
mawa, kuma bai kasance daga
masu shirki ba.
\i\fj\ LyMJ U^UO J^fcXj J J \£yJZ*-A->
^^^j^^i^cJ^l^
t •5.-*
>^<>
*%&<-* S*i ^HJ d^3 Oj^Uo ^f%
(1) Kalma mai daidaitawa ita ce kalmar shahada, domin ta tabbatar da cewa babu
abin bautawa face Allah. Bauta ita ce bin wani ga hukunce-hukunce na wajabtawa ko
haramtawa ko halattawa ko sanya wasu sharudda wadanda shan'a ba ta zo da su ba.
Wannan aya ba ta tsaya ga Yahudu da Nasara wadanda suka dauki Ahbar da Ruhban da
masu kirkira wasu hukunce-hukunce ba. A 'a ta kai har ga Musulmi masu raunin hankali
da Tmani, wadanda suke zaton waliyyai suna iya cutarwa, ko suna iya amfanin wani da
zatinsu, kuma suna iya halattawar abin da Allah Ya haramta, kuma suna iya haramtawar
abin da Ya halatta, tare da haka kuma suna kaga bidi'o'Tmasu girma wadanda Allah bai
saukar da wani dalTli a kansu ba, suna sanya wadannan bidi'o'T su zama danku ga
wadannan waliyyan. Suna riya cewa su ne masu ceton mutum, ko da suke suna saba wa
shari'a, suna zaton cewa suna kan wani abu. To, su ne makaryata, Shaidan ya rinjaye su
har ya mantar da su daga tuna Allah. Wadannan su ne kungiyar Shaidan. (Dubi Sawi).
85
3 — Suratu Al 'Imrana
$imm-r
68. Lalle ne mafi hakkin mutane
da IbrahTma, hakTka, su ne wacfan-
da suka bi shi a (zamaninsa) da
wannan Annabi (Muhammadu) da
wacfanda suka yi Tmani. Kuma Al-
lah ne Maji6incin muminai.
69. Wata kungiya daga Mutanen
Littafi sun yi gurin su 6atar da ku,
to, ba su Batar da kowa ba face
kansu, kuma ba su sansancewa!
70. Ya Mutanen Littafi ! Don me
kuka kafirta da ayoyin Allah, alhali
kuwa ku, kuna shaida (cewa su
gaskiya ne)?
71. Ya Mutanen Littafi ! Don me
kuke lulluBe gaskiya da karya,
kuma kuke 66ye gaskiya, alhali
kuwa kuna sane?
72. Kuma wata kungiya jiaga
Mutanen Littafi ta ce : "Ku yi Tmani
da abin da aka saukar a kan wadan-
da suka yi Tmani (da Muhammadu)
a farkon yini, kuma ku kafirta a
karshensa; tsammaninsu, za su
komo.
73. "Kada ku yi Tmani face (1 } da
wanda ya bi addininku". Ka ce:
"Lalle ne, shiriya ita ce shiriyar
Allah. (Kuma kada ku yi imani)
cewa an bai wa wani irin abin da
aka ba ku, ko kuwa su yi musu da
ku a wurin Ubangijinku." Ka ce:
"Lalle ne falala ga hannun Allah
take, Yana bayar da ita ga wanda
Yake so, kuma Allah Mawadaci ne,
Masani."
Qy>J m
(1) Maganganu sun shiga juna domin a yi raddin kowace guntuwar magana da
jawabin da ya dace da ita tare da ita. A lura da kyau.
86
Suratu Al 'Imrana
<m$ij&-r
74. Yana ke6ance wanda Ya so
da rahamarSa, kuma Allah
Ma'abucin falala ne, Mai girma.
75. Kuma daga Mutanen Littafi
akwai wanda yake idan ka ba shi
amanar kindari (1) , zai bayar da shi
gare ka, kuma daga gare su akwai
wanda idan ka ba shi amanar dlna-
ri, ba zai bayar da shi gare ka ba,
face idan ka dawwama a kansa
kana tsaye. Wannan kuwa, domin
lalle ne su, sun ce, "Babu laifi a
kanmu a cikin Ummiyyai (2) ." Suna
fadar Icarya ga Allah, alhali kuwa
suna sane.
76. Na'am! Wanda ya cika
alkawarinsa, kuma ya yi takawa, to,
lalle ne Allah Yana son masu
takawa.
77. Lalle ne wadanda suke sayen
'yan tamani kadan da alkawarin
Allah da rantsuwoyinsu, wadannan
babu wani rabo a gare su a Lahira,
kuma Allah ba Ya yin magana da
su, kuma ba Ya dubi zuwa gare su, a
Ranar Kiyama, kuma ba Ya tsar-
kake su, kuma suna da azaba mai
radadi.
78. Kuma lalle ne, daga gare su
akwai wata kungiya suna karkatar
da harsunansu da Littafi, domin ku
yi zaton sa daga Littafin, alhali
kuwa ba shi daga Littafin. Kuma
suna cewa, "Shi daga wurin Allah
X ^' " S" ^
ifj&j\sl^
'> / \>-
(1) Kincfar shi ne ukiyya dubu goma sha biyu, kuma Miyya cfaya tana daidai da
dirhami dubu biyu da cfari biyar ko dlnari dubu.
(2) Babu laifi idan mun ci dukiyarsu : watau Bayahude yana ganin cin dukiyar wanda
ba Bayahude ba irinsa halal ne a gare shi.
87
3 — Suratu Al 'Imrana
$lM$&-r
yake." Alhali kuwa shi, ba daga
wurin Allah yake ba. Suna facfar
karya ga Allah, alhali kuwa suna
sane.
79. Ba ya yiwuwa ga wani mu-
tum, Allah Ya ba shi Littafi da
hukunci da annabci, sa'an nan
kuma ya ce wa mutane : "Ku kasan-
ce bayi gare ni, baicin Allah."
Amma (zai ce): "Ku kasance masu
aikin ibada da abin da kuka kasan-
ce kuna karantar da Littafin, kuma
da abin da kuka kasance kuna
karantawa (1) ."
80. Kuma ba ya umurnin ku da
ku riki mala'iku da annabawa
Iyayengiji. Shin, zai umurce ku da
kafirci ne a bayan kun riga kun
zama masu sallamawa (Musulmi)?
81. Kuma a lokacin da Allah Ya
riki alkawarin annabawa: "Lalle ne
ban ba ku wani abu ba daga Littafi
da hikima, sa'an nan kuma wani
manzo ya je muku, mai gaskatawa
ga abin da yake tare da ku; lalle ne
za ku gaskata shi, kuma lalle ne za
ku taimake shi." Ya ce: "Shin, kun
tabbatar, kuma kun riki alka-
wanNa a kan wannan a gare ku?"
Suka ce, "Mun tabbatar/' Ya ce:
"To, ku yi shaida, kuma Nla tare da
ku Ina daga masu shaida."
82. To, wacfanda kuma suka
juya baya a bayan wannan, to, wa-
cfannan su ne fasikai.
^ >' 9> s X' ***-'? ' W
•"^IS
fi&$j$d$>lZ&y£
(1) Wannan ya nuna karatun Alkur'ani kawai ba da sanin ma'anarsa ba, domin a yi
aiki da shi, ba ya isar mutum. Amman wanda ya koyi ibada sosai, sa'an nan ya karanta
Alkur'ani, to, za a ba shi lada ko da ba ya fahimtar ma'anarsa.
88
3 — Suratu Al 'Imrana
tSJ&-r
83. Shin wanin Addinin Allah
suke nema, alhali kuwa a gare Shi
ne wadanda ke cikin sama da kasa
suka sallama Wa, a kan so da ki,
kuma zuwa gare Shi ake mayar da
su?
84. Ka ce: "Mun yi Tmani da
Allah kuma da abin da aka saukar
mana^ da abin da aka saukar wa
Ibrahima da Isma'Tla da Is'haka da
Yakuba da Jlkoki, da abin da aka
bai wa Musa da Tsa da annabawa
daga Ubangijinsu, ba mu bamban-
tawa a tsakanin kowa daga gare su.
Kuma mu, zuwa gare Shi masu
sallamawa ne."
85. Kuma wanda ya nemi wanin
Musulunci ya zama addini, to, ba za
a karba daga gare shi ba. Kuma shi
a Lahira yana daga cikin masu
hasara.
86. Yaya Allah zai shiryar da
mutane wadanda suka kafirta a
bayan Tmaninsu, kuma sun yi shai-
dar cewa, lalle Manzo gaskiya ne,
kuma hujjoji bayyanannu sun je
musu? Allah ba Ya shiryar da mu-
tane azzalumai.
87. Wadannan, sakamakonsu
shi ne, lalle a kansu akwai la'anar
Allah da mala'iku da mutane gaba
cfaya.
88. Suna masu dawwama a ci-
kinta, ba a saukaka azabar gare su,
kuma ba su zama ana yi musu jinki-
ri ba.
89. Face wadanda suka tuba
daga bayan wannan, kuma suka yi
89
3 — Suratu Al 'Imrana
fc»i&-r
gyara, to, lalle ne Allah Mai gafara
ne Mai jin kai.
90. Lalle ne wacfanda suka kafir-
ta a bayan Imaninsu, sa'an nan
kuma suka kara kafirci, ba za a
karbi tubarsu ba. Kuma wacfannan
su ne batattu.
91. Lalle ne wacfanda suka kafir-
ta, kuma suka mutu alhali kuwa
suna kafirai, to, ba za a karbi cike
da kasa na zinari daga cfayansu ba,
ko da ya yi fansa da shi. Wacfannan
suna da azaba mai racfacfi, kuma ba
su da wasu mataimaka.
92. Ba za ku sami kyautatawa
ba, sai kun ciyar daga abin da kuke
so. Kuma abin da kuka ciyar, ko
mene ne, to, lalle ne Allah, gare shi,
Masani ne.
93. Dukan abinci ya kasance ha-
lal ne ga Bani Isra'Tla, face abin da
Isra'ila ya haramta wa kansa daga
gabanin saukar da Attaura. Ka ce :
"To, ku zo da Attaura, sa'an nan
ku karanta ta, idan kun kasance
masu gaskiya ne.
94. "To, wanda ya kirkira karya
ga Allah daga bayan wannan, to,
wacfannan su ne azzalumai."
95. Ka ce: "Allah Y a yi gaskiya,
saboda haka ku bi akldar IbrahTma,
mai karkata zuwa ga gaskiya ; kuma
bai kasance daga masu shirki ba."
96. Kuma lalle ne, TDaki na far-
ko (1) da aka aza domin mutane,
fix'*' 9 >'\ '\~*?\ * ^ "?t y \'
DjU* 4>i c^jJJ (jAjl&fu^j C-Jb Jjl ol
(1) TDakunan Allah a cikin kasa domin mutane su yi ibada zuwa gare su biyu ne;
Ka'aba a Makka da Baittt Mukaddas. An gina Ka'aba a gabaninsa da shekara arba'in.
T)akin Bakka kuwa IbrahTma ne ya gina shi, alhali Yahudu da Nasara suna cewa a kan
addininsa suke. Da suna fadar gaskiya da sun koma a gare shi gaba daya.
90
Suratu Al 'Imrana
$mm-r
haklka, shi ne wanda ke Bakka (1) ,
mai albarka kuma shiriya ga talikai.
97. A cikinsa akwai ayoyi bayya-
nannu; (ga misali) matsayin Ibrahl-
ma. Kuma wanda ya shige shi ya
kasance mai amincewa. Kuma ak-
wai hajjin T)akin domin Allah akan
mutane, ga wanda ya sami Tkon
zuwa gare shi, kuma wanda ya ka-
firta, to, lalle Allah Mawadaci ne
daga barin talikai.
98. Ka ce: "Ya ku Mutanen Lit-
tafi ! Don me kuke kafirta da ayoyin
Allah, alhali kuwa Allah Mai shai-
da ne a kan abin da kuke aikata-
wa?"
99. Ka ce: "Ya ku Mutanen Lit-
tafi! Don me kuke taushe wanda ya
yi Tmani, daga hanyar Allah, kuma
kuna neman ta zama karkatacciya,
alhali kuwa kuna masu shaida?
Kuma Allah bai gushe daga abin da
kuke aikatawa ba Yana Masani."
100. Ya ku wadanda suka yi
imani! Idan kun yi da'a ga wani
6angare daga wadanda aka bai wa
Littafi,jza su mayar da ku kafirai a
bayan Tmaninku !
101. Kuma yaya kuke kafircewa
alhali kuwa ana karanta ayoyin
Allah a gare ku, kuma a cikinku
akwai manzonSa? Kuma wanda ya
nemi tsari da Allah, to, an shiryar
da shi zuwa ga hanya mikakkiya.
102. Ya ku wadanda suka yi
Tmani! Ku bi Allah da takawa, a
kan hakkin binSa da takawa, kuma
J$£JL>\1> bj '
S ^**S'*'£ y *>
Raj OjL^U^J^aWj
fas>A
L^JJb JU3 4ttU pf^o* J^y^j f^^-tZ 3
(1) Ana ce wa Makka Bakka.
91
3 — Suratu Al 'Imrana
$lM%&-r
kada ku mutu face kuna masu salla-
mawa (Musulmi).
103. Kuma ku yi daidami da
igiyar Allah gaba cfaya, kuma kada
ku rarraba. Kuma ku tuna ni'imar
Allah a kanku, a lokacin da kuka
kasance makiya, sai Ya sanya
soyayya a tsakanin zukatanku, sa-
boda haka kuka wayi gari, da
ni'imarSa, 'yan'uwa. Kuma kun
kasance a kan ga6ar rami na wuta,
sai Ya tsamar da ku daga gare ta.
Kamar wannan ne Allah Yake
bayyana muku ayoyinSa, tsamma-
ninku, za ku shiryu.
104. Kuma wata jama'a daga
cikinku, su kasance suna kira zuwa
ga alheri, kuma suna umurni da
alheri, kuma suna hani daga abin da
ake ki. Kuma wacfannan, su ne
masu cin nasara.
105. Kuma kada ku kasance ka-
mar wacfanda suka rarrabu, kuma
suka sa6a wa juna, bayan hujjoji
bayyanannu sun je musu, kuma
wacfannan suna da azaba mai
girma.
106. A ranar da wasu fuskoki
suke yin fari kuma wasu fuskoki
suke yin baki, (za a ce wa wacfanda
fuskokinsu suke yin^bakin): "Shin,
kun kafirta a bayan imaninku? Don
haka sai ku cfancfani azaba saboda
abin da kuka kasance kuna yi na
kafirci."
707. Kuma amma wacfanda
fuskokinsu suka yi fari, to su, suna
cikin rahamar Allah, kuma su, a
cikinta, madawwama ne.
>J i IkAA'*'? >Y\ ":•'•" . Arff
» \.'*\<'»>
!^^Jxp<
. ^ >>><- > £
S'**o > >."
3 OjyiXj 'AaLj eJ JuJ Wj>j is
92
3 — Suratu Al 'Imrana
t3MJ&-r
108. Wacfannan ayoyin Allah ne,
muna karanta su a gare ka da gas-
kiya, kuma Allah ba Ya nufin wani
zalunci ga talikai.
109. Kuma abin da ke cikin sam-
mai da abin da ke cikin kasa, na
Allah ne, kuma zuwa gare Shi ake
mayar da al'amurra.
110. Kun kasance mafi alherin
al'umma wadda aka fitar ga muta-
ne, kuna umurni da alheri, kuma
kuna hani daga abin da ake ki,
kuma kuna imani da Allah. Kuma
da Mutanen Littafi sun yi Imani,
lalle ne, da (haka) ya kasance mafi
alheri a gare su. Daga cikinsu akwai
muminai, kuma mafi yawansu fasi-
kai ne.
111. Ba za su cuce ku ba, face dai
tsangwama. Kuma idan sun yake
ku za su juya muku baya, sa'an nan
kuma ba za a taimake su ba.
112. An doka kaskanci a kansu a
inda duk aka same su, face da wani
alkawari daga Allah da alkawari
daga mutane. Kuma sun koma da
fushi daga Allah, kuma aka doka
talauci a kansu. Wannan kuwa do-
min su, lalle sun kasance suna kafir-
ta da ayoyin Allah, kuma suna
kashe annabawa, ba da wani hakki
ba. Wannan kuwa domin sabawar
da suka yi ne, kuma sun kasance
suna yin ta'adi.
113. Ba su zama daidai ba; daga
Mutanen Littafi akwai wata al'um-
ma wadda take tsaye, suna karatun
ayoyin Allah a cikin sa'o'in dare,
alhali kuwa suna yin sujada.
93
3 — Suratu Al 'Imrana
®MJ&-r
114. Suna Tmani da Allah da Yi-
nin Lahira, kuma suna umurni da
abin da aka sani kuma suna hani
daga abin da ba a sani ba, kuma
suna gaugawa a cikin alherai.
Kuma wadannan suna cikin salihai.
115. Kuma abin da suka aikata
daga alheri, to, ba za a yi musu
musunsa ba. Kuma Allah Masani
ne ga masu takawa.
116. Lalle ne wadanda suka ka-
firta, dukiyoyinsu ko cfiyansu ba za
su wadatar musu da kome ba daga
Allah kuma wacfannan abokan
Wuta ne, su, a cikinta, madawwama
ne.
117. Misalin abin da suke ciyar-
wa, a cikin wannan rayuwar du-
niya, kamar misalin iska ce ( wadda)
a cikinta akwai tsananin sanyi, ta
sami shukar wasu mutane wadanda
suka zalunci kansu, sai ta halakar
da ita. Allah bai zalunce su ba,
amma kansu suka kasance suna
zalunta.
118. Ya ku wadanda suka yi
Tmani! Kada ku riki abokan asiri
daga waninku, ba su takaita muku
Barna. Kuma sun yi gurin abin da
za ku cutu da shi. Hakika, kiyayya
ta bayyana daga bakunansu, kuma
abin da zukatansu ke Boyewa ne
mafi girma. Kuma lalle ne, Mun
bayyana muku ayoyi, idan kun ka-
sance kuna hankalta.
119. Ga ku y a wacfannan ! Kuna
son su, ba su son ku, kuma kuna
Tmani da Littafi dukansa. Kuma
idan sun hacfu da ku sukan ce "Mun
*+£
\\
/"< *t' + **'\A*m'
^^y y * l y\ y ' 5*
*< ' »y -'xy*\£ X S. '*''
S^v y > *y*> ^
3J 0j&*>i>£ <l4
|>>AJ
* y '* s '. y .'Zs.y^KS £* y^l ' y *)> y^**
94
3 — Suratu Al 'lmrana
®fflj&-r
yi Tmani". Kuma idan sun kacfaita
sai su ciji yatsu a kanku don takaici.
Ka ce, "Ku mutu da takaicinku.
Lalle ne, Allah Masani ne ga abin
da ke cikin kiraza."
120. Idan wani alheri ya shafe ku
sai ya bakanta musu rai, kuma idan
wata cuta ta shafe ku sai su yi
farin ciki da ita. Kuma idan kun yi
hakuri kuma kuka yi takawa, kullin-
su ba ya cutar ku da kome. Lalle ne,
Allah ga abin da suke aikatawa Mai
kewayewa ne.
121. Kuma a 16kacin (1) da ka yi
sauko daga iyalanka kana zaunar
da muminai a wuraren zama domin
yaki, kuma Allah Mai ji ne, Masani.
722. A lokacin da kungiyoyi (2)
biyu daga gare ku suka yi niyyar su
karye, kuma Allah ne MajiBincinsu,
don haka, ga Allah muminai sai su
dogara.
123. Kuma lalle ne, haklka, Al-
lah Ya taimake ku a Badar, alhali
(1) Misali ne ga cewa idan kun yi imani, kuma yun yi takawa, to, kullinsu ba ya cutar
da ku da kome, domin abin da ya auku a Yakin Uhdu ya isa misali ga cewa, sai kun karka-
ce daga hanya sa'an nan wani abu zai same ku. Asalin maganar shT ne, Annabi ya fita Uhdu
da mutum cfari tara da hamsin, kuma kafirai suna dubu uku. Annabi ya sauka a Uhdu ranar
Asabat, bakwai ga Shawwal, shekara ta uku ga Hijira, ya sanya bayansa wajen dutsen
Uhdu, ya gyara safufuwan mayaka, kuma ya zaunar da wata runduna ta maharba a gefen
dutsen da shugabancin Abdullahi dan Zubair. Sa'an nan ya ce musu : "Ku kare mu da harbi,
kada su zo mana daga baya, kada ku daga daga nan, mun rinjaya ko an rinjaye mu." Sai
suka saba wa umurnin, don haka masTfar Uhdu ta auku.
(2) Banu Salmah da Banu Harisa sun tashi komawa gida, su bar yaki, a lokacin da
Ubayyi bn Salul ya koma da jama'arsa, j\llah Ya tsare musu Tmaninsu, ba su koma ba.
Watau yana cewa idan wani abu na masifa ya same ku, to, kun saba wa Allah ne kamar
yadda ya auku a Uhdu, suka sanya Annabi ya fito daga MadTna kuma maharba suka bar
wurin da aka ayyana musu. Amma kuma ai Allah Ya Taimake ku, a Badar a lokacin da
karfinku bai kai haka ba, saboda rashin sa6awarku ga umurninSa.
95
3 — Suratu Al 'Imrana
$&m-r
kuwa kuna mafiya rauni, saboda
haka ku bi Allah da takawa
tsammaninku, kuna godewa.
124. A lokacin da kake cewa ga
muminai, "Shin, bai ishe ku ba,
Ubangijinku Ya taimake ku da
dubu uku daga mala'iku saukakku?
125. "Na'am! Idan kuka yi ha-
kuri, kuma kuka yi takawa, kuma
suka zo muku da gaugawarsu, irin
wannan, Ubangijinku zai kare ku
da dubu biyar daga mala'iku masu
alama."
126. Kuma Allah bai sany a shi ( 1 }
ba, face domin bushara a gare ku,
kuma domin zukatanku su natsu da
shi. Taimako bai kasance ba face
daga wurin Allah, Mabuwayi, Mai
hikima.
727. Domin Ya katse wani gefe
daga wadanda suka kafirta, ko
kuma Ya kaskanta su, har su juya,
suna masu rubushi.
128. Babu kome a gare ka game
da al'amarin (shiryar da su banda
iyar da manzanci). Ko Allah Ya
karbi tubarsu, ko kuwa Ya yi musu
azaba, to lalle ne su, masu zalunci
ne.
129. Allah ne da mulkin abin da
yake a cikin sammai da abin da
yake a cikin kasa, Yana gafarta wa
wanda Yake so, kuma Yana azabta
wanda Yake so, kuma Allah Mai
gafara ne, Mai jin kai.
' st'isK
^§r *v£ - 7 *^
(1) Taimako da mala'iku.
96
Suratu Al 'Imrana
®m&-r
130. Ya ku wacfanda suka yi
imani ! Kada ku ci riba ninki ninki,
riBanye, kuma ku bi Allah da taka-
wa, tsammaninku za ku ci nasara.
131. Kuma ku ji tsdron wuta
wadda aka yi tattali domin kafirai.
132. Kuma ku yi cfa'a ga Allah
da ManzonSa, tsammaninku a yi
muku rahama.
133. Kuma ku yi gaugawa zuwa
ga neman gafara daga Ubangijinku
da wata Aljanna wadda fadinta
(daidai da) sammai da kasa ne, an yi
tattalinta domin masu takawa.
134. Wacfanda suke ciyarwa a
cikin sauki da tsanani, kuma suke
masu hadiyewar fushi, kuma masu
yafe wa mutane laifi. Kuma Allah
Yana son masu kyautatawa.
135. Kuma wadanda suke idan
suka aikata wata alfasha ko suka
zalunci kansu sai su tuna da Allah,
saboda su nemi gafarar zunubansu
ga Allah. Kuma wane ne ke gafara
gazunubai, face Allah? Kuma ba su
doge a kan abin da suka aikata ba,
alhali kuwa suna sane.
136. Wadannan sakamakonsu
gafara ce daga Ubangijinsu, daga
Gidajen Aljanna (wacfanda) koramu
na gudana daga karkashinsu, suna
madawwama a cikinsu. Kuma ma-
dalla da ijarar masu aiki.
137. Lalle ne, misalai sun shude a
gabaninku, sai ku yi tafiya a cikin
kasa, sa'an nan ku duba, yaya aki-
bar masu karyatawa ta kasance.
^ i< \\f l~t\\ • ' ^ ^ m?
» <i
97
Suratu Al 'lmrana
$mm-r
138. Wannan bayani ne ga mu-
tane, kuma shiryuwa ce da wa'azi
ga masu takawa.
139. Kuma kada ku yi rauni,
kuma kada ku yi bakin ciki, alhali
kuwa ku ne mafiya^cfaukaka, idan
kun kasance masu imani.
140. Idan wani miki ya shafe ku,
to, lalle ne, wani miki kamarsa ya
shafi mutanen, kuma wacfancan
kwanaki Muna sarrafa su a tsaka-
nin mutane, domin Allah Ya san
wacfanda suka yi Imani kuma Ya
sami masu shahada daga gare ku.
Kuma Allah ba Ya son azzalumai.
141. Kuma domin Allah Ya cfau-
raye wacfanda suka yi Tmani, kuma
Ya koke kafirai.
142. Ko kun yi zaton ku shiga
Aljanna alhali kuwa Allah bai wada
sanin wacfanda suka yi jihadi daga
gare ku ba, kuma Ya san masu
hakuri?
143. Kuma lalle ne, haklka, kun
kasance kuna gurin mutuwa tun a
gabanin ku hacfu da ita, to, lalle ne,
kun gan ta, (1) alhali kuwa kuna
kallo.
144. Kuma Muhammadu bai
zama ba face manzo, lalle ne man-
zanni sun shucfe a gabaninsa. Ashe
idan ya mutu ko kuwa aka kashe
shi, za ku juya a kan dugaduganku?
To wanda ya juya a kan dugadu-
gansa, ba zai cuci Allah da kome ba.
Kuma Allah zai saka wa masu
godiya.
p* Sg&XtU$8&fi&
JJJ3 DjAJb o» J^u^^** » 0^-> AS JUUJ
(1) Mutuwa watau, kuna gurin wani ya£i a bayan na Badar ya zo.
98
3 — Suratu Al 'Imrana
$m]m-r
145. Kuma ba ya yiwuwa ga
wani rai ya mutu face da iznin
Allah, wa'adi ne mai kayyadadden
ajali. Kuma wanda yake nufin saka-
makon duniya Muna ba shi daga
gare ta. Kuma wanda ke nufin
samakon Lahira Muna ba shi daga
gare ta. Kuma za Mu saka wa masu
godiya.
146. Kuma da yawa wani annabi
wanda ya yi yaki, akwai jama'a
masu yawa tare da shi, sa'an nan ba
su yi laushi ba ga abin da ya same su
a cikin hanyar Allah, kuma ba su yi
rauni ba kuma ba su sad da kai ba.
Kuma Allah Yana son masu
hakuri.
147. Kuma babu abin da ya ka-
sance maganarsu face fadarsu
cewa : "Ya Ubangijinmu ! Ka gafar-
ta mana zunubanmu da 6arnarmu a
cikin aFamarinmu, kuma Ka tabba-
tar da dugaduganmu, kuma Ka
taimake mu a kan mutanen nan
kafirai."
148. Allah Ya saka musu da
sakamakon duniya da kuma
kyakkyawan sakamakon Lahira.
Kuma Allah Yana son masu kyau-
tatawa.
149. Ya ku wadanda suka yi
Tmani ! Idan kun yi tfa'a ga wadanda
suka kafirta za su mayar da ku a
kan dugaduganku, har ku juya
kuna masu hasara.
150. A^a, Allah ne Maji6incinku,
kuma ShT ne Mafi alherin matai-
maka.
^<s ">^ "'•" \ >
99
3 — Suratu Al 'Imrana
tSJ&-r
151. Za Mu jefa tsdro a cikin
zukatan wacfanda suka kafirta, sa-
boda shirkin da suka yi da Allah
game da abin da bai saukar da wani
dalili ba game da shi. Kuma mako-
marsu Wuta ce, kuma tir da maza-
unin azzalumai!
152. Kuma lalle ne, hakika, Al-
lah Ya yi muku gaskiya ga wa'a-
dinSa, a lokacin da kuke kashe su
da izninSa, har zuwa lokacin da
kuka kasa (1) , kuma kuka yi jayayya
a cikin aFamarin, kuma kuka saba,
a bayan (Allah) Ya nuna muku abin
da kuke so. Daga cikinku akwai
wanda yake nufin duniya kuma
daga cikinku akwai wanda ke nufin
Lahira. Sa'an nan kuma Ya juyar
da ku daga gare su, domin Ya jarra-
be ku. Kuma lalle ne, hakTka, Ya
yafe muku laifinku. Kuma Allah
Ma'abucin falala ne ga muminai.
153. A lokacin da kuke hawan
dutse, gudane. Kuma ba ku karkata
a kan kowa ba, alhali kuwa Man-
zon Allah na kiran ku a cikin na
karshenku (2) . Sa'an nan (Allah) Ya
saka muku da bakin ciki a tare da
wani bakin ciki. Domin kada ku yi
•>s <\< V y \' 'X* < 9 <<?i"> t
(1) A lokacin da aka fara Yakin Uhdu, Musulmi suka fara kora suna kisa, suna
kamu. Sai wasu maharba suka ce: "Kada a kame gamma a bar mu". Shugabansu
Abdullahi bn Zubair ya ce musu "Ku tuna da maganar Manzon Allah da ya ce kada mu
bar wurinmu sai idan shi ne ya kiraye mu." Sai suka ki ^auraran maganarsa suka tafi
kamun ganima. Sai Allah Ya biyo musu da Khalid bn WalTd ta baya, ya kashe Abdullahi
da sauran wacfanda suka rage. Sa'an nan kuma sai yakin Musulmi ya karye, suka gudu
suka hau dutse, sai mutum goma sha cfaya ko sha biyu kawai aka bari tare da Annabi, yana
kiran su suna gudu.
(2) Bayan da hankalinsu ya koma gare su sai suka ga sakamakon saba wa umurnin
Allah, ya zama karyewar yaki da rashin ganima.
100
3 — Suratu Al 'Imrana
$mm-r
bakin ciki a kan abin da ya ku6uce
muku, kuma kada ku yi bakin cikin
a kan abin da ya same ku. Kuma
Allah Masani ne ga abin da kuke
aikatawa.
154. Sa'an nan kuma (Allah) Ya
saukar da wani aminci a gare ku
daga bayan bakin cikin; gyangyacfi
yana rufe wata kungiya daga gare
ku, kuma wata kungiya, lalle ne,
rayukansu sun shagaltar da su, suna
zaton abin da ba shi ne gaskiya ba, a
game da Allah, irin zaton jahiliyya,
suna cewa: "Ko akwai wani abu a
gare mu dai daga aFamarin?" Ka
ce, "Lalle ne al'amari dukansa na
Allah ne." Suna 66yewa, a cikin
zukatansu, abin da ba su bayyana
shi a gare ka. Suna cewa : "Da muna
da wani abu daga aFamarin da ba a
kashe mu ba a nan." Ka ce : "Ko da
kun kasance a cikin gidajenku, da
warfanda aka rubuta musu kisa sun
fita zuwa ga wuraren kwanciyarsu;"
kuma (wannan abu ya auku ne)
domin Allah Ya jarrabi abin da ke
cikin kirazanku. Kuma domin Ya
tsarkake abin da ke cikin zuka-
tanku. Allah Masani ne ga abin da
ke cikin kiraza.
755. Lalle ne, warfanda suka
juya daga gare ku a ranar harfuwar
jama'a biyu, Shairfan kawai ne ya
talala6antar da su, saboda sashen
abin da suka tsirfanta. Kuma lalle
ne haklka, Allah Ya yafe laifi daga
gare su. Lalle Allah ne Mai gafara
Mai hakuri.
101
3 — Suratu Al 'Imrana
3Mi&-r
156. Ya ku wacfanda suka yi
Tmani! Kada ku kasance kamar
wacfanda suka kafirta, kuma suka ce
wa 'yan'uwansu idan sun yi tafiya a
cikin kasa ko kuwa suka kasance a
wurin yaki: "Da sun kasance a
wurinmu, da ba su mutun ba, kuma
da ba a kashe su ba." (Wannan
kuwa) Domin Allah Ya sanya wac-
can magana ta zama nadama a cikin
zukatansu. Kuma Allah ne Yake
rayarwa kuma Yake matarwa.
Kuma Allah, ga abin da kuke aika-
tawa, Mai gani ne.
157. Kuma lalle ne, idan aka
kashe, ku a cikin hanyar Allah, ko
kuwa kuka mutu, haklka, gafara
daga Allah da rahama ne mafi alhe-
ri daga abin da suke tarawa.
158. Kuma lalle ne idan kun
mutu ko kuwa aka kashe ku, haki-
ka, zuwa ga Allah ake tara ku.
159. Saboda wata rahama ce
daga Allah ka yi sanyin hali a gare
su. Kuma da ka kasance mai hushi,
mai kaurin zuciya, da sun watse
daga gefenka. Sai ka yafe musu
laifinsu, kuma ka nema musu gafa-
ra, kuma ka yi shawara (1) da su a
cikin aFamarin. Sa'an nan kuma
idan ka yi niyyar zartarwa, to, ka
dogara ga Allah, lalle ne, Allah
Yana son masu tawakkali.
J^U^os^^ji^J <S4^o£J^j£-£
; y <*s *s**
(1) Annabi shi ne makomar aFamurra ga dukan kome, amma Allah Ya lizimta masa
saukin hali zuwa ga Sahabbansa, da yin ma'amala da su, ma'amala mai kyau, da yi musu
addu'a a kowane hali, kuma a wurin yaki ko abin da ya shafi yaki, Ya lizimta masa ya yi
shawara da su, kuma Ya ba shi damar yin ijtihadi a nan, sa'an nan Ya umarce shi da ya
dogara ga Allah wajen zartaswa, a kan ra'ayin da ya gani daga gare su.
102
3 — Suratu Al 'Imrana
tffiflj&-r
160. Idan Allah Ya taimake ku,
to, babu marinjayi a gare ku. Kuma
idan Ya yar6e ku, to, wane ne wan-
da yake taimakon ku bayanSa?
Kuma ga Allah sai muminai su
dogara.
161. Kuma ba ya yiwuwa ga
wani annabi ya ci gululu. (1) Wanda
ya ci gululu zai je da abin da ya ci na
gululun, a Ranar Kiyama. Sa'an
nan a cika wa kowane rai saka-
makon abin da ya tsirfanta. Kuma
su, ba za a zalunce su ba.
162. Shin fa, wanda ya bibiyi
yardar Allah, yana zama kamar
wanda ya koma da fushi daga Al-
lah, kuma makomarsa Jahannama
ce? Kuma tir da makoma ita!
163. Su, darajoji (2) ne a wurin
Allah, kuma Allah Mai gani ne ga
abin da suke aikatawa.
164. Lalle ne, hakllta, Allah Ya
yi babbar falala (3) a kan muminai,
domin Ya aika, a cikinsu, Manzo
daga ainihinsu yana karanta ayo-
yinSa a gare su, kuma yana tsar-
kake su, kuma yana karantar da su
Littafi da hikima, kuma lalle, sun
kasance daga gabani, hakika suna
cikin 6ata bayyananniya.
pJ M. aU f^ C&^^fc^A
\s ~t 9 ' " ****>
<£$*> 'Xi'i '!&" \'\"
(1) Gululu shT ne satar wani abu daga ganlmar yaki a gabanin raba ta a tsakanin
mayaka. Allah Ya ce, "Yin gululu haram ne a kan kowane annabi ko da wacfanda ba a
halatta wa cin ganima ba, balle ga wanda aka halatta wa. Kamar yadda gululu yake haram
a kan annabawa haka yake haram a kan mabiyansu."
(2) Muminai masu darajoji ne a wurin Allah gwargwadon Tmaninsu da takawarsu da
kuma falalar da Allah Ya yi musu. Haka su kuma kaflrai suna da magangara zuwa kasa
gwargwadon mugun aikinsu.
(3) Allah Ya nuna falalar da Ya bai wa Annabi Muhammadu, tsTra da aminci su
tabbata a gare shi, da yake har Yana yi wa muminai gori da kyautar da Ya yi musu ta
hanyar aiko musu shi.
103
3 — Suratu Al 'Imrana
$!M$&-r
165. Shin, kuma a 16kacin (1) da
wata maslfa, haklka, ta same ku,
alhali kuwa kun samar da biyunta,
kun ce: "Daga ina wannan yake?"
Ka ce: "Daga wurin rayukanku (2)
yake." Lallene, Allah, a kan dukan
kome, Mai Ikon yi ne.
166. Kuma abin da ya same ku a
ranar hacfuwar jama'a biyu, to, da
izinin Allah ne, kuma domin (Al-
lah) Ya san muminai (na gaskiya).
167. Kuma domin Ya san wa-
cfanda suka yi munafunci, kuma an
ce musu: "Ku zo ku yi yaki a cikin
hanyar Allah, ko kuwa ku
tunkucfe." (3) Suka ce: "Da mun san
(yadda ake) yaki da mun bi ku." Su,
zuwa ga kafirci a ranar nan,jsun fi
kusa daga gare su zuwa ga imani.
Suna cewa da bakunansu abin da ba
shi ne a cikin zukatansu ba. Allah ne
Mafi sani ga abin da suke Boyewa.
168. Wacfanda suka ce wa
'ya'uwansu kuma suka zauna abin-
su: "Da sun yi mana cfa'a, da ba a
kashe su ba." Ka ce: "To, ku tun-
kude mutuwa daga rayukanku,
idan kun kasance masu gaskiya."
169. Kada ka yi zaton wacfanda
aka kashe a cikin hanyar Allah
matattu ne. A'a, rayayyu ne su, a
"£ -» * y s 9y ,~* s""'*s9s %*»
ISP oji*>J ^ ^JLaJ J
Cw;
( 1 ) Duk masTfar da ta same ku, to, ku ne kuka jawo wa kanku ita da wani laifi na saba
wa umurnin Allah. Kuma kamin maslfa guda ta same ku, to, alheri biyu sun same ku.
(2) Kowace irin maslfa ta sami mutum, to, shi ne ya yi sababinta a kansa. Kuma ya
kamata ya yi bincike ya gane sababin, a inda ya jahilce shi. Kuma duk da haka kamin
maslfa guda ta same shi, ya sami ni'ima biyu ko fiye da haka.
(3) Ku tunkucfe mana makiya da duhunku, ko da ba ku yi yaki ba.
104
3 — Suratu Al 'Imrana
$sS!Ij&-r
wurin Ubangijinsu. (1) Ana ciyar da
su.
1 70. Suna masu farin ciki saboda
abin da Allah Ya ba su daga falalar-
Sa, kuma suna yin bushara ga wa-
danda ba su risku da su ba, daga
bayansu; "Babu tsoro a kansu
kuma ba su zama suna yin bakin
ciki ba."
171. Suna yin bushara saboda
wata ni'ima daga Allah da wata
falala. Kuma lalle ne, Allah ba Ya
tozartar da ijarar muminai.
172. Wacfanda suka kar6a (2)
kira zuwa ga Allah da ManzonSa,
daga bayan mTki ya same su. Akwai
wata lada mai girma ga wadanda
suka kyautata (3) yi daga gare su,
kuma suka yi takawa.
173. Wadanda mutane (4) suka
ce musu : "Lalle ne, mutane sun tara
(1) A cikin Hadisi an ruwaito cewa, Annabi ya ce Allah Yana sanya ruhinsu a cikin
cikkunan tsuntsaye masu koren launi, suna tafiya da su a cikin Aljanna suna ci daga
'ya'yan itacenta da rana, sa'an nan su koma zuwa ga wasu fitillu wacfanda aka rataye a
cikin inuwar Al'arshi.
(2) Bayan komawar Musulmi daga Uhdu da miyakun da suka same su, sai Annabi ya
umurce su da fita a bayan kafirai, domin kada su yi tunanin komawa. Sai suka fita
bayansu, aka dace kuwa Abu Sufyana ya umurci mutanensa da komawa Madina domin su
tumbuke Musulmi. An yi Uhdu ta farko ran Asabat, sa'an nan suka fita a bayansu a ranar
Lahadi, suka riske su a Hamra'al Asad. Sai aka yi tawafuki (yarjejeniya) tsakanin Annabi
da Abu Sufyana a kan a bar yaki a lokacin, sai shekara mai zuwa, a hacfu a Badar. Allah
Ya yabi Musulmi, da suka karba wannan kira, a cikin miyaku. Haka duka mai karbawa
irinsu, ya shiga a cikin irin wannan yabo har ya zuwa tashin Kiyama.
(3) Kyautata yi shi ne tsarkake aiki domin Allah watau ihsani ko ihlasi.
(4) Yakin Badar na Uku, a cikin shekara ta hucfu yake, a watan Sha'aban. Badar
kasuwa ce babba ga kabllun Larabawa a kowace shekara. A bayan Uhdu an yi alkawari da
Abu Sufyana, a kan a hadu a Badr shekara mai zuwa. Saboda haka sai Abu Sufyana ya fita
daga Makka har ya sauka Marriz Zahran, sai Allah Ya sanya masa tsoro a cikin zuciyarsa,
sai ya gamu da Nu'aima bn Mas'ud el Ashja'iy, ya ce masa: "Ni na yi alkawari da
Muhammadu a kan mu hacfu a Kasuwar Badar. Wannan kuwa shekar fari ce. Ina son
105
3 — Suratu Al 'Imrana
iSIj^-r
(rundunoni) saboda ku, don haka
ku ji tsoronsu. Sai (wannan maga-
na) ta kara musu Imani, kuma suka
ce: "Mai isarmu Allah ne, kuma
madalla da Wakili Shi"
1 74. Sa'an nan suka juya da wata
ni'ima daga Allah da wata falala,
wata cuta ba ta shafe su ba, kuma
suka bi yardar Allah. Kuma Allah
ne Ma'abucin falala Mai girma.
175. Wancan, Shaicfan ne kawai
yake tsoratar da ku masoyansa. To,
kada ku ji tsoronsu, ku ji^ tsoroNa,
idan kun kasance masu Imani.
176. Kuma wacfannan da suke
gaugawa a cikin kafirci kada su
Bata maka rai. Lalle ne su, ba za su
cuci Allah da kome ba. Allah Yana
nufin cewa, ba zai sanya musu wani
rabo ba a cikin Lahira, kuma suna
da wata azaba mai girma.
1 77. Lalle ne, wadanda suka sayi
kafirci da Imani, ba za su cuci Allah
da kome ba. Kuma suna da azaba
mai radacfi.
178. Kuma kada wadanda suka
kafirta su yi zaton cewa, lalle ne,
jinkirin da Muke yi musu alheri ne
ga rayukansu. Muna yi musu jin-
kirin ne domin su kara laifi kawai,
kuma suna da azaba mai wula-
kantarwa.
i^\ \ ' i 9 ' ^ >"\' "{' ' 9 f >^^i^
l5P &&& ^tilQJ^J
** *•£*** VZ z t '
\Z$4>&{$j&£'&
?->/
^^^J^^^^i^^i^T^X
sa6awar alkawarin ta zama daga gare shi, ba daga gare ni ba. Ka tafiMadlna ka yi £6£arin
hana su fitowa, zan ba ka ra£uma goma." Sai Nu'aimu ya tafi Madma ya iske Annabi da
Sahabbansa suna shirin fita. Sai ya ce musu: "Me kuke nufi?" Suka ce; "Alkawarin Abu
Sufyana." Sai ya ce: "Ba za ku iya ba, domin kuwa sun tara rundunoni saboda ku." Sai
Annabi ya ce: "Zan fita ko da ni kacfai ne." Sai Annabi ya fita da mutum dubu da cfari
biyar, suka tafi Badar babu Abu Sufyana. Suka ci kasuwa suka komo.
106
3 — Suratu Al 'Imrana
$S&flJ&-r
779. Allah bai kasance Yana ba-
rin muminai a kan abin da kuke
kansa ba, sai (1) Ya rarrabe mu-
mmuna daga mai kyau. Kuma Al-
lah bai kasance Yana sanar da ku
gaibi ba. (2) Kuma amma Allah
Yana za6en wanda Ya so daga
manzanninSa. (3) Saboda haka ku yi
Tmani da Allah da manzanninSa.
Kuma idan kun yi Tmani kuma kuka
yi takawa, to, kuna da lada mai
girma.
180. Kuma kada wacfannan da
suke yin rowa da abin da Allah Ya
ba su daga falalarSa su yi zaton shT
ne mafi alheri a gare su. A'a, shT
mafi sharri ne a gare su. Za a yi
musu sakandami da abin da suka yi
rowa da shi a Ranar Kiyama.
Kuma ga Allah gadon sammai da
kasa yake, kuma Allah, ga abin da
kuke aikatawa, Masani ne.
181. Lallene, haklka, Allah Yaji
maganar wacfanda suka ce: "Lalle
ne, Allah faklri ne, mu ne wada-
tattu." Za mu rubuta abin da suka
facfa, da kisan da suka yi wa anna-
bawa ba da wani hakki ba. Kuma
Mu ce: "Ku cfancfani azabar gob-
ara!
,< x f-£ >* 4 £<' i^ *< t> fir?
(1) Watau Allah ba zai bar mutane su ce, 'Mun yi imam/ da baki kawai ba, sai Ya
jarraba su Ya fltar da muminan kwarai daga munafukai. Saboda haka Ya sanya ranaiku
kamar ranar Uhdu wadda Allah Ya jarrabi muminai da ita har hakurinsu da cfa'arsu su-
ka bayyana, kuma munafukai suka bayyana.
(2) Allah bai sanar da gaibi ga jiutane wadanda ba annabawa ba, saboda haka, ba ku
iya sanin imanin mutum ko rashin imaninsa, sai^da alama ta wani aiki ko magana wadda
take da ita za a iya yin hukunci da kafirci ko imani ga mutum.
(3) Allah Ya zabi wanda Ya so daga manzanninSa, watau Ya zabi Annabi Muham-
madu da karin daraja a kan sauran annabawa da falalarSa. Wannan ne maflficin yabo a
gare shi.
107
3 — Suratu Al 'Imrana
f3Mj&-r
182. "Wannan (azabar) kuwa sa-
boda abin da hannuwanku suka
gabatar ne. Kuma lalle ne Allah bai
zama mai zalunci ga bayinSa ba."
183. Wacfanda suka ce : "Lalle ne
Allah Ya yi^alkawari zuwa gare mu,
kada mu yi Tmani saboda wani man-
zo sai ya zo mana da Baiko wadda
wuta za ta ci." Ka ce: "Lalle ne
wasu manzanni sun je muku, a ga-
banlna, da hujjoji bayyanannu,
kuma da abin da kuka facfa, to, don
me kuka kashe su, idan kun kasance
masu gaskiya?"
184. To, idan sun karyata ka, to
lalle ne, an karyata wasu manzanni
a gabaninka, sun je musu da hujjoji
bayyanannu da littattafai, da kuma
Littafi mai haske.
185. Kowane rai mai cfancfanar
mutuwa ne. Kuma ana cika muku
ijarorinku kawai ne a Ranar Kiya-
ma. To, wanda aka msantar daga
barin wuta, kuma aka shigar da shi
Aljanna, to, lalle ne ya tsira. Kuma
rayuwar duniya ba ta zama ba face
jin dacfin rucfi.
186. Lalle ne za a jarraba (1 ) ku a
cikin dukiyarku da rayukanku,
kuma lalle ne kuna jin cutarwa mai
yawa daga wacfanda aka bai wa
Littafi a gabaninku da kuma wa-
cfanda suka yi shirki. Kuma idan
kun yi hakuri, kuma kuka yi taka-
wa, to lalle ne, wannan yana daga
manyan al'amurra.
^h ' - S* ** &" . »> »7"- "• < 9>9 t-
A ?4 "
\&l\
(1 ) Duk wanda ya tsayu da gaskiya ko umurni da alheri, ko hani daga abin da ba a so,
to lalle ne sai an cutar da shi, kuma ba shi da magani sai ha£uri, domin Allah, da neman
taimako daga Allah, da komawa zuwa ga Allah.
108
3 — Suratu Al 'Imrana
$!Mm-r
187. Kuma a lokacin da Allah
Ya ri£i alkawarin wacfanda aka bai
wa (1) Littafi, "Lalle ne kuna bayya-
na shi ga mutane, kuma ba za ku
66ye shi ba." Sai suka jefar da shi a
bayan bayansu, kuma suka sayi
'yan kucfi kacfan da shi. To, tir da
abin da suke saye!
188. Kada lalle ka yi zaton wa-
cfanda suke yin farin ciki da abin da
suka bayar, kuma suna son a yabe
su da abin da ba su aikata ba. To,
kada lalle ka yi zaton su da tsira
daga azaba. Kuma suna da azaba
mai racfacfi.
189. Kuma ga Allah mulkin
sammai da Rasa yake. Kuma Allah,
a kan kome, Mai ikon yi ne.
190. Lalle ne, a cikin halittar
sammai da Rasa da sa6awar dare da
yini akwai ayoyi ga ma'abuta
hankali.
191. Wacfanda suke ambatar Al-
lah a tsaye da zaune da a kan sasan-
ninsu, kuma suna tunani a kan
halittar sammai da Rasa: "Ya
Ubangijinmu! Ba Ka halitta wan-
nan a kan banza ba. TsarkinKa!
Saboda haka Ka tsare mu daga
azabar wuta.
"»»• > \
E9 ^jjlZAa
*> <" K S >Z'*S '-,Si' &\" \\\
(1) A cikin wannan akwai gargacfi ga malaman Musulmi, kada su shiga hanyar
Yahudu ta boye ilmin gaskiya, ko kuwa abin da ya same su, su ma ya same su, kuma ya
shiga da su mashigarsu. Wajibi ne a kan malamai su bayar da abin da ke hannuwansu na
ilmi mai amfani, mai mini a kan aikin kwarai, kada su boye kome daga gare shi. Idan sun
boye, to, la'anar Allah da mala'iku da ta mutane za ta tabbata a kansu, kamar yadda ta
tabbata a kan malaman Yahudu.
109
3 — Suratu Al 'Imrana
$mm-r
192. "Ya Ubangijinmu! Lalle ne
Kai, wanda Ka shigar a cikin wuta,
to, hakika, Ka tozarta shi, kuma
babu wasu mataimaka ga azzalu-
mai.
193. "Ya Ubangijinmu! Lalle ne
mu L mun ji Mai kira yana kira zuwa
ga Tmani cewa, 'Ku yi Tmani da
Ubangijinku.' Sai muka yi Trnani.
Ya Ubangijinmu! Saboda haka Ka
gafarta mana zunubanmu, kuma
Ka kankare miyagun ayyukanmu
daga gare mu. Kuma Ka karBi
rayukanmu tare da mutanen kirki.
194. "Ya Ubangijinmu! Ka ba
mu abin da Ka yi mana wa'adi
(alkawari) a kan manzanninKa,
kuma kada Ka tozarta mu a Ranar
Kiyama. Lalle ne Kai, ba Ka saBa-
war alkawari."
195. Saboda haka Ubangijinsu
Ya karBa musu cewa, "Lalle ne Ni,
ba zan tozartar da aikin wani mai
aiki ba daga gare ku, namiji ne ko
kuwa mace, sashenku daga sashe.
To, wadanda suka yi hijira kuma
aka fitar da su daga gidajensu,
kuma aka cutar da su a cikin hanya-
Ta, kuma suka yi yaki, kuma aka
kashe su, lalle ne zan kankare musu
miyagun ayyukansu, kuma lalle ne
zan shigar da su gidajen Aljanna
(wadanda) koramu ke gudana daga
karkashinsu, a kan sakamako daga
wurin Allah. Kuma a wurinSa ak-
wai kyakkyawan sakamako.
196. Kada jujjuyawar wadanda
suka kafirta a cikin garuruwa ta
rude ka.
\a^&j>-\ JLA3 j \JJ \ cf^-k O* ^ D^.J
^ Kit \'*\ X \' > \'' 9 '<"*(?**
>*z
t"" ■•.«■*
^^ J^ ^o\ y <3)p4ijp& v^UJL—b
CfJb \3 o^O.ot p>^<**> &*j\j >CJif^l
*, m 4*
f|p jjjLjT^ ijjLST^j \ vilis ic^jo V
110
3 — Suratu Al 'lmrana
ea85M»-r
797. Jin dadi ne kadan, sa'an nan
makdmarsu Jahannama ce, kuma
tir da shimfida ita!
198. Amma wadanda suka bi
Ubangijinsu da takawa, suna da
Gidajen Aljanna (wacfanda) kora-
mu ke gudana a karkashinsu, suna
madawwama a cikinsu, a kan liyafa
daga wurin Allah, kuma abin da ke
wurin Allah ne mafi alheri ga bar-
rantattu.
199. Kuma lalle ne daga Muta-
nen Littafi a> , haklka, akwai wanda
yake yin Tmani da Allah da abin da
aka saukar zuwa gare ka, da abin da
aka saukar zuwa gare su, suna masu
tawalu'i ga Allah, ba su sayen tama-
ni kacfan da ayoyin Allah. Wadan-
nan suna da ijararsu a wurin
Ubangijinsu. Lalle ne Allah Mai
gaugawar sakamako da yawa ne.
200. Ya ku wadanda suka yi
imani! Ku yi hakuri kuma ku yi
dauriya, kuma ku yi zaman dako,
kuma ku yi takawa, tsammaninku
za ku ci nasara. (2)
*-» s*
(1) A cikin Mutanen Littafi akwai mutanen kwarai, na kirki wadanda hasada ba ta
hana su bin gaskiya ba. Sun sifantu da sifofin kamala; watau ba dukkansu ne miyagu ba.
Akwai na kwarai a cikinsu kamar yadda hali yake a kowane taron mutane.
(2) Hakuri a kan ibada da daukar wahalolin shan'a gaba daya gwargwadon Ikon yi.
Dauriya a kan abokan gaba; watau kada makiya su fi muminai hakuri wajen yaki da
daukar wahalolinsa. Zaman dako ga taushewar hanyoyin abokan gaba daga barin shiga
kasar Musulmi. Babu bambanci ga makiyi bayyananne da makiyi boyayye. Makiyi
boyayye ya fi aibi domin kasasshensa, zai shiga wuta, amma kasasshen makiyi bayya-
nanne, zai shiga Aljanna. Takawa ita ce bin umurnin Allah da kangewa daga barin haninSa
kamar yadda Ya fada. Wannan shine kan ibada duka bayan Tmani, domin haka ya ce ko za
ku ci nasara, idan kun rike wadannan abubuwa da kyawo.
111
4 — Suratun Nisa'
a2»4-£
Tana karantar da hanyoyin tsare hakkokin jama 'a, da
alakokin da suke a tsakanin arummar Musulmi kanta, ko kuma a
tsakaninta da tsakanin wata al'umma.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
L Ya ku mutane ! Kq bi Ubangi-
jinku da takawa, Wanda Ya halitta
ku daga rai guda, kuma Ya halitta,
daga gare shi, ma'auransa, kuma
Ya watsa daga gare su maza masu
yawa da mata. Kuma ku bi Allah da
takawa, Wanda kuke rokon juna da
(sunan) Shi, da kuma zumunta (1) .
Lalle ne Allah Ya kasance, a kanku,
Mai tsaro ne.
2. Kuma ku bai wa marayu duki-
yoyinsu, kuma kada ku musanya
mummuna da mai kyau. Kuma
kada ku ci dukiyoyinsu zuwa ga
dukiyoyinku. Lalle shi, ya kasance
zunubi ne mai girma.
&<&
(1) Bin Allah wanda Ya halitta ku, kira ga tabbatar da tauhidin Uluhiyya da
Rububiyya. Fitar mutane daga asali guda, wanda babu wani surki a cikinsa, yana wajabtar
da girman jinsin mutum, kowane iri ne, kowane launi, kuma kowace halitta yake dauke da
ita. Tsoron Allah da tsaronSa a kan mutane yana wajabtar da tsayawa a cikin haddodin
shan'arsa. Tsoron zumunta ko rantsuwa da ita yana wajabtar da tausayi da rahama a kan
halittar Allah na kusa da na nesa. Hadisi ya nuna ba a yin rantsuwa da wanin Allah,
saboda haka ma'anar ayar ita ce, 'Ku ji tsoron Allah ku tsare mahaifa da zumunta!'
112
4 — Suratun Nisa'
wm&-t
3. Kuma idan kunjitsoron baza
ku yi adalci ba a cikin marayu (1) ,
to, (akwai yadda za a yi) ku auri
abin da ya yi muku dacfi daga mata ;
biyu-biyu, da uku-uku, da hutfu-
hudu. Sa'an nan idan kun ji tsoron
ba za ku yi adalci ba, to, (ku auri)
guda ko kuwa abin da hannayenku
na dama suka mallaka. Wannan shi
ne mafi kusantar zama ba ku wuce
haddi ba.
4. Kuma ku bai wa mata sada-
kokinsu da saukin bayarwa. Sa'an
nan idan suka yafe muku wani abu
daga gare shi, da dacfin rai, to, ku ci
shi da jin dacfi da saukin hacfiya.
5. Kada ku bai wa wawaye (2)
dukiyarku, wadda Allah Ya sanya
ta a gare ku, kuna masu tsayuwa (ga
gyaranta). Kuma ku ciyar da su a
cikinta, kuma ku tufatar da su,
kuma ku gaya musu magana sanan-
niya ta alheri.
6. Kuma ku jarraba marayu, har
a lokacin da suka isa aure. To, idan
kun lura da shiriya daga gare su, to,
ku mika musu dukiyoyinsu. Kada
ku cTta da Barna, kuma da gaggawa
kafin su girma. Kuma wanda yake
*> a
31*5^I^a«
(1) Asalin maraya shi ne yaron da bai balaga ba, kuma ubansa ya mutu. Amma a
cikin aya-Allah Ya sani-ana nufin dukkan mai rauni a cikin al'umma, wanda yake neman a
tsare haickinsa da Allah Ya cfora wa Musulmi su tsare^ Saboda haka Ya shafe jawabin
sharadin, kuma Ya fara da hukunce-hukunce, a kan tafsTlin yadda za a tsare masu rauni a
cikin al'umma. Ya fara da mata a wajen aure, adadinsu daga daya zuwa hucfu, gwarg-
wadon karfin mutum da iyawarsa ga tsai da adalci a gare su, ko a tsakaninsu. Adalci na
kwana da ciyarwa da tufatarwa.
(2) Sa'an nan yadda ake rikon dukiyar wawa wanda bai san yadda ake rikon dukiya
ba, ko da shi baligi ne, ya yi aure, kuma ko da shi ne yake neman dukiyarsa da kansa;
kamar da ijara. Wannan wata hanya ce ta tsaron hakkin masu rauni.
113
4 — Suratun Nisa'
assail -i
wadatacce, to, ya kama kansa,
kuma wanda yake faklri, to, ya ci,
gwargwadon yadda ya kamata. To,
idan kun mika musu dukiyoyinsu,
sai ku shaidar a kansu. Kuma Allah
Ya isa Ya zama Mai bincike.
7. Maza suna da rabo (1) daga
abin da iyaye biyu da mafi kusantar
dangi suka ban, kuma mata suna da
rabo daga abin da iyaye biyu da
mafi kusantar dangi suka ban, daga
abin da ya karanta daga gare shi ko
kuwa ya yi yawa, rabo yankakke.
8. Kuma idan ma'abuta zumun-
ta da marayu da matalauta suka
halarci rabon, to, ku azurta su daga
gare shi, kuma ku facfa musu maga-
na sananniya ta alheri.
P. Kuma wacfanda suke, da sun
bar (2) zuriyya masu rauni a bayan-
su, za su ji tsoro a kansu, su yi
sauna, sa'an nan su bi Allah da
ta£awa, kuma su facfi magana
madaidaiciya.
10. Lalle ne, wacfanda suke cin
dukiyar marayu da zalunci, to,
wuta kawai suke ci a cikin cikku-
nansu, kuma za su shiga cikin wata
wuta mai tsanani.
11. Allah Yana yi muku wasiyya
a cikin 'ya'yanku; namiji yana da
rabon mata biyu. Idan sun kasance
T^lil'
(1) Hukunce-hukuncen rabon gado, hanya ce ta tsaron hakkin masu rauni.
(2) Watau yadda mutum mai kananan 'ya'ya yake tsoron ya mutu ya bar su babu
wata dukiya da za ta taimake su, haka kuma su Musulmi wacfanda aka sanya aikin rabon
gado a hannunsu, su yi tunani, da su ne suka mutu suka bar 'ya'yansu haka. Saboda haka
wannan zai karya zuciyar mai son ya yi zalunci daga dukiyar marayu.
114
4 — Suratun Nisa'
IKtftKtfA
iS^-i
mata ne fiye da biyu kuwa, to, suna
da biyu daga kashi uku cfin abin da
ya bad, kuma idan ta zama guda ce
(kawai), to, tana da rabi. Kuma
iyayensa biyu kowane cfaya daga
cikinsu yana da cfaya daga kashi
shida cfin abin da ya bari idan wani
reshe ya kasance gare shi, to, idan
reshe bai kasance gare shi ba, kuma
iyayensa ne (kawai) suka gaje shi,
to, uwa tana da sulusi (cfaya daga
cikin kashi uku). Sa'an nan idan
'yan'uwa sun kasance gare shi, to,
uwarsa tana da sudusi (cfaya daga
cikin kashi shida) daga bayan wa-
siyya wadda ya yi ko kuwa bashi.
Ubanninku da 'ya'yanku, ba ku
sani ba, wannensu ne mafi kusantar
amfani a gare ku. Yankawa daga
Allah. Lalle ne, Allah Ya kasance
Masani Mai hikima.
12. Kuma kuna da rabin abin da
matanku na aure suka bari idan
reshe bai kasance gare su ba. Sa'an
nan idan reshe ya kasance gare su,
to, kuna da rubu'i (cfaya daga cikin
kashi hudu) daga abin da suka ba-
rin, daga bayan wasiyya wadda
suka yi ko kuma bashi. (Su) kuma
suna da rubu'i daga abin da kuka
bari idan reshe bai kasance ba gare
ku, idan kuwa reshe ya kasance gare
ku, to, suna da sumuni (cfaya daga
cikin kashi takwas) daga abin da
kuka bari, daga bayan wasiyya
wadda kuka yi ko kuwa bashi. Idan
wani namiji ya kasance ana gadon
sa bisa kalala, ko kuwa wata mace,
alhali kuwa yana da cfan'uwa ko
03 lA-5siU^lc
»\' < >< s K /^
-Aj 64* ol^^o^j<£^l^^6|
+-*&&
JJU-<
*J>
> 1i^\^ ir c >> 4,fi^ >-•>
115
Suratun Nisa'
t£<A
-i
'yar'uwa (1) to, kowane daya daga
cikinsu yana da sudusi (daya daga
cikin kashi shida), sai idan sun ka-
sance mafi yawa daga wannan, to,
su abokan tarayya ne a cikin sulusi
(daya bisa uku), daga bayan wa-
siyya wadda aka yi ko kuma bashi.
Ba da yana mai cutarwa ba, ga
wasiyya, daga Allah. Kuma Allah
Masani ne Mai hakuri.
13. Wadancan iyakokin Allah
ne. Wanda ya yi da'a ga Allah da
Manzonsa, (Allah) zai shigar da shi
gidajen Aljanna (wadanda) koramu
suna gudana daga karkashinsu,
suna madawwama a cikinsu, kuma
wannan shi ne rabo babba.
14. Kuma wanda ya sa6a wa
Allah da ManzonSa, kuma ya keta-
re iyakokinSa, zai shigar da shi
Wuta, yana madawwami a cikinta,
kuma yana da wata azaba mai wala-
kantarwa.
15. Kuma wadanda suka je wa
alfasha daga matanku, to, ku nemi
shaidar mutane hudu daga gare ku
a kansu. To, idan sun yi shaida, sai
ku tsare su a cikin gidaje har mutu-
wa ta kar6i rayukansu, ko kuwa
Allah Ya sanya wata hanya a gare
su.< 2 >
p %J&-%J& 4tt\j 40^ *C-^->
( 1 ) *Dan'uwa ko 'yar'uwa, a nan, ana nufin ITummi ko lfummiya, kowane dayansu
yana da sudusi; idan suna da yawa, watau sun kai biyu ko abin da ya fi biyu, to, suna da
sulusi. Babu bambanci tsakanin namiji da mace gare su, domin jihar gadonsu mace ce,
watau uwar mamacin.
(2) Ayoyi na 15 da 16 an shafe hukuncinsu wajen haddi da ayar Suratun Nur ta biyu
da Hadisin Rajami ga zawari da zawara wadanda suka yi zina, kuma da bulala dari da
korar babane namiji, da kuma bulala dari ga budurwa. Kuma ana jefe mai liwacfi da wanda
ake yi a kansa idan sun balaga, ko da su banawa ne. Ana ladabi ga mai liwadl da matarsa,
amma ba a kashe shi. Liwadi da wata mace kamar zina yake ga namijin.
116
4 — Suratun Nisa'
7tf. Kuma wacfanda (maza biyu)
suka je mata (1) daga gare ku, to, ku
cutar da su, sa'an nan idan sun tuba
kuma suka kyautata halayensu, sai
ku kau da kai da ga barinsu. Lalle
ne, Allah Ya kasance Mai kar6ar
tuba ne, Mai jin kai.
17. Abar da take tuba kawai ga
Allah, ita ce ga wacfanda suke aika-
tawar mugun aiki da jahilci sa'an
nan su tuba nan kusa (2) . To,
wadannan Allah Yana kar6ar tu-
barsu. Kuma Allah Ya kasance Ma-
sani ne, Mai hikima.
18. Ba tuba ba ce ga wadanda
suke aikatawar munanan ayyuka
har idan mutuwa ta halarci dayansu
ya ce: "Lalle ne ni, na tuba yanzu."
Kuma ba tuba ba ce ga wadanda
suke mutuwa alhali kuwa suna kafi-
rai. Wadannan Mun yi musu tatta-
lin wata azaba mai radacfi.
19. Ya ku wadanda suka yi Tma-
ni ! Ba ya halatta a gare ku, ku gaji
mata a kan tllas. Kuma kada ku
hana su aure domin ku tafi da sas-
hen abin da kuka ba su, face idan
suka zo da wata alfasha (3) bayya-
nanniya. Kuma ku yi zamantakewa
da su da alheri. Sa'an nan idan kun
kT su, to, akwai tsammanin ku ki
l^Zbj ills ^=^4 WvLo C^\ JO \ j
l^^ll^l^^^f
<? . > ^<.
(1) Maza biyu masu je wa alfasha su ne masu yin liwacfi da junansu.
(2) Nan kusa, watau a gabanin mutuwa.
(3) Mugun halin da shari'a ba ta yarda da shi ba kamar iciyo ko yawon banza, a nan
babu laifi ku hana su aure sai sun yi muku hul'i, kuma Allah Ya hana gadon mata kamar
dukiya. Sun kasance suna yin haka, ba da sake bayar da sadaki ba, domin dogara da
wanda ubansa ya bayar, sai su aurar da ita a kan haka ga wani dan'uwan mamacin, ko
kuma wanda suke so ya aure ta.
117
Suratun Nisa'
rai^-i
wani abu alhali kuwa Allah Ya
sanya wani alheri mai yawa a
cikinsa.
20. Kuma idan kun yi nufin mu-
sanya mata a matsayin wata mata,
alhali kuwa kun bai wa cfayarsu
kincfari (1) , to, kada ku karbi kome
daga gare shi. Shin, za ku karBe shi
da karya da zunubi bayyananne?
21. Kuma yaya za ku karbe shi
alhali kuwa, hakTka, sashenku ya
sadu zuwa ga sashe, kuma sun riki
alkawari (2) mai kauri daga gare ku?
22. Kuma kada ku auri abin da
ubanninku suka aura daga mata,
face abin da ya shige. Lalle ne shi, ya
kasance alfasha da abin kyama.
Kuma ya munana ya zama hanya.
23. An haramta muku uwa-
yenku, da 'ya'yanku, da 'yan'-
uwanku mata, da goggoninku, da
innoninku, da 'ya'yan cfan'uwa, da
'ya'yan 'yar'uwa, da uwayenku wa-
cfanan da suka shayar da ku mama,
da 'yan'uwanku mata na shan
mama, da uwayen matanku, da
agololinku wacfanda suke cikin
cfakunanku daga matanku wa-
cfanda kuka yi duhuli da su, kuma
idan ba ku yi duhuli da su ba, to,
babu laifi (3) a kanku, da matan
'ya'yanku wacfanda suke daga
tsatsonku, kuma kada ku hacfa tsa-
, ., ' *< 'w'*- -i>*. \ 9 \'
M Lxu-4 ui^j UTL^J -»4j>j x>\z\ UZl«*
fM y^j^ui ^Xlujj \sji*j aJl^S
(1) Kincfari, shi ne dukiya mai yawa; ukiya dubu goma sha biyu, na azurfa.
(2) Alkawarin rikonsu da alheri ko kuma sallamarsu da kyautatawa. Bakara Aya ta
231.
(3) T)aurin aure a kan cfiya yana haramta uwarta, amma cfaurin aure a kan uwa, ba ya
haramta cfiyar sai in an yi duhuli da ita, ko kuma an yi tamattu'i da ita.
118
4 — Suratun Nisa'
-i
kanin 'yan'uwa biyu mata, face
abin da ya shige. Lalle ne, Allah Ya
kasance Mai gafara ne Mai jin Icai.
24, Da tsararrun auren (1) wasu
maza, face dai abin da hannuwanku
suka mallaka. (Ku tsare) Littafin
Allah a kanku. Kuma an halatta
muku abin da yake bayan wancan.
Ku nema da dukiyoyinku, kuna
masu yin aure, ba masu yin zina ba.
Sa'an nan abin da kuka ji dadi da
shi daga gare su, to, ku ba su ijaro-
rinsu bisa farillar sadaki. Babu laifi
a gare ku ga abin da kuka yi yarda-
tayya (2) da shi a bayan farillar sada-
ki. Lalle ne Allah Ya kasance Masa-
ni ne, Mai hikima.
25. Kumawanda (3) baisamiwa-
data ba daga cikinku bisa ga ya auri
'ya'ya muminai, to, (ya aura) daga
abin da hannuwanku na dama suka
mallaka, daga kuyanginku mumi-
nai. Kuma Allah ne Mafi sani ga
Tmaninku, sashenku daga (4) sashe.
Sai ku aure su da izinin mutanensu.
Kuma ku ba su ijarorinsu bisa ga
abin da aka sani, suna masu kamun
^io^Ak^Ui^ &
*s<.
A»/ <\**< <&JZi s^ \~<\*
EEJ L-. ??j by*-^ jo '4&\<^)C*L
C^T^ r^S-V". ly^^O' (*==*}> *bj ^
• x » - - I
9 ^^\< < ' J>ff ' ' 9> Y\
(1) An haramta muku matan auren wasu maza, matukar mazansu ba su sake su ba,
Musulmi ne ko kuwa Kitabawa, sai fa idan kun kamo su ne daga kasar da take ta abokan
gaba, a nan kuna iya takinsu haka, domin kamu ya warware aurensu. Idan kun yi tamattu'i
da wasu mata a kan kuskure, ba da aure ba, sai ku biya su sadaki a kan haka. An hana
auren tamattu'i, watau yin aure zuwa ga ajali. Abdullahi bn Abbas ya ce yin sa ya fi zina.
(2) Bayan sadakin da aka yanka babu laifi Tdan kun yi yardatayya da kara wani abu a
kan farilla, kuma babu laifi idan ita matar ta yarda da kayar da karin ko kuwa shi mijin ya
yarda da biyan karin.
(3) Hukunce-hukuncen auren kuyanga ga wanda bai sami Tkon auren 'ya ba. Aibin
auren kuyangi shi ne bautar da zuriya, domin bauta daga uwa take. Saboda haka ba ya
halatta ga Musulmi ya auri baiwar kafiri, kome larurar da take ciki, sai dai ya saye ta daga
gare shi.
(4) Ku duka daidai kuke wajen Tmani da Musulunci. Dubi kuma Al 'Imrana 195.
119
Suratun Nisa'
mmm^-i
kai, ba masu zina ba, kuma ba masu
rikon abokai ba. To, idan aka aure
su, sai kuma suka zo da wata al-
fasha, to, akwai a kansu rabin abin
da ke a kan 'ya'ya daga azaba.
Wancan (auren kuyanga) ga wanda
ya ji tsoron wahala ne daga gare ku.
Kuma ku yi hakuri shi ne mafi
alheri a gare ku. Kuma Allah Mai
gafara ne Mai jin kai.
26. Allah Yana nufin Ya bay-
yana muku, kuma Ya shiryar da ku
hanyoyin wacfanda suke a gaba-
ninku kuma Ya karBi tubarku.
Kuma Allah Masani ne Mai
hikima.
27. Kuma Allah Yana nufin Ya
karBi tubarku. Kuma wacfanda
suke bin sha'awoyi suna nufin ku
karkata, karkata mai girma.
28. Allah Yana nufin Ya yi
muku sauki, kuma an halitta mu-
tum yana mai rauni.
29. Ya ku wacfanda suka yi Ima-
ni! Kada ku ci dukiyoyinku a tsa-
kaninku da yaudara, (1) face idan ya
kasance daga fatauci ne, bisa yarda-
tayya daga gare ku. Kuma kada ku
kashe kanku. Lalle ne Allah Ya
kasance, game da ku, Mai jin kai ne.
30. Wanda ya aikata wancan
bisa ta'adi da zalunci, to, za Mu
kone shi da Wuta. Kuma wannan
ya kasance ga Allah (abu ne) mai
sauki.
%1&L&
y, 4'> >'9>, <' ' */ *\> t^i'
>^< 'jt*~<* >
' > x l^
i\0z>
•'Si
p£— Jut \^CJui j ^xll Jp\j J&
' 9 * 'm'
'>— ^
(1) Hukuncin cin dukiyar mutane da Jcarya ko yaudara, haramun ne, domin yana kai
ga mutane su kashe kansu.
120
4 — Suratun Nisa'
- t
31. Idan kuka nlsanci manyan
abubuwan da ake hana ku aika-
tawa, to, za Mu kankare munanan
ayyukanku daga gare ku, kuma Mu
shigar da ku mashiga ta karimci.
32. Kuma kada ku yi gurin abin
da Allah Ya fifita sashenku da shi a
kan sashe; maza suna da rabo daga
abin da suka tsirfanta, kuma mata
suna da rabo daga abin da suka
tsirfanta. Ku roici Allah daga fala-
larSa. Lalle ne, Allah Ya kasance,
ga dukkan kome, Masani.
33. Kuma ga kowa, Mun sanya
magada daga abin da mahaifa da
mafiya kusancin zumunta suka
bari. Kuma wacfanda rantsu-
woyinku suka kulla (1) ku ba su
rabonsu. Lalle ne, Allah Ya kasan-
ce, a kan dukkan kome, Mahalarci.
34. Maza masu tsayuwa ne (2) a
kan mata, saboda abin da Allah Ya
fifita sashensu da shi a kan sashe,
kuma saboda abin da suka ciyar
daga dukiyoyinsu. To, salihan mata
masu cfa'a ne, masu tsarewa ga gaibi
saboda abin da Allah Ya tsare.
Kuma wacfanda kuke tsoron bijire-
warsu, to, ku yi musu gargacfi,
^" s *' 4"*" * y ^ y y * y s yy y ^
'%—
< *ts ^y y •Z'*'* A *^
y K ^** y.yy. y
y^ 9 > y *s
' *' >* y >.'C
^£^j^o^^\y^\^i^\lj
(1) A zamanin Jahiliyya ana kullin amana a tsakanin kabilu ko a tsakanin mutum da
wani mutum. Wannan kullin amanar yakan hacfa har da sudusin dukiyar wanda ya mutu
daga cikinsu. Wasu Musulmi sun shiga Musulunci a bayan sun kulla irin wannan amanar,
saboda haka Allah Ya yi umurni da cika wannan alkawarin, kuma Ya kashe al'adar, Ya
musanya ta da hukunce-hukuncen Musulunci. Kuma ana fassara masu kullin rantsuwa da
masu gudanar da aikin rabon dukiyar gado. Ana biyan su ijarar wahalarsu daga kawunan
magada kamar yadda ya kamata.
(2) Allah Ya sanya shugabancin gida da gudanar da tasarrufinsa a hannuwan maza,
domin ginar jikinsu, da hankalinsu da kuma dukiyarsu da suke ciyarwa ga sadaki da kuma
nafakar (ciyarwar) gidan. Kuma Allah Ya aza wa mata da 'a ga maza da kuma tsare
farjojinsu domin kada su kawo wani bakon da ba dan gida ba, a cikin gidan.
121
Suratun Nisa'
imw&-i
kuma ku kaurace musu a cikin wu-
raren kwanciya, kuma ku doke su.
Sa'an nan kuma, idan sun yi muku
cfa'a, to, kada ku nemi wata hanya a
kansu. Lalle ne Allah Ya kasance
Madaukaki, Mai girma.
35. Kuma idan kun ji tsoron sa-
6awar tsakaninsu, to, ku aika da
wani mai sulhu daga mutanensa da
wani mai sulhu daga mutanenta. (1)
Idan sun yi nufin gyarawa, Allah zai
daidaita tsakaninsu (ma'auran).
Lalle ne Allah Ya kasance Masani,
Mai jarrabawa.
36. Kuma ku bautawa (2) Allah,
kuma kada ku hacfa wani da Shi,
kuma ga mahaifa ku yi kyautatawa,
kuma ga ma'abucin zumunta da
marayu da matalauta, da makwabci
ma'abucin kusanta, da makwabci
manlsanci, da aboki a gefe da dan
hanya, da abin da hannuwanku na
dama suka mallaka. Lalle ne Allah
ba Ya son wanda ya kasance mai
takama, mai yawan alfahari.
37. Wadanda suke yin rowa,
kuma suna umurnin mutane da yin
rowa, kuma suna boyewar abin da
Allah Ya ba su na falalarSa. Kuma
Mun yi tattali, saboda kafirai, aza-
ba mai walakantarwa.
\/'\\ • *> >> 9 \' ^ * n- <
\<\\'. >•!
(1) Hakamani ko masu sulhu biyu, su tafi su yi binciken abin da ya hana auren kyau,
su tsawaci maras gaskiya daga cikin ma'auran, ko kuma su hukunta rabuwa da hul'i, ko ba
da hul'i ba. Abin da suka hukunta alkali ya zartar da shi.
(2) Bauta wa Allah shi ne a bi umurninSa, a bar haninSa a kome. Sa'an nan ya biyar
da nau'ukan mutane wacfanda mutum zai yi ihsani zuwa gare su gwargwadon darajarsu
kuma da halinsa. Sa'an nan zargi a kan marowaci da sakamakonsa, da mai ciyarwa amma
ba a bisa hanyar bauta wa Allah ba.
122
4 — Suratun Nisa'
l$&-l
38. Kuma wacfanda suke ciyar
da dukiyoyinsu domin nuna wa
mutane, kuma ba su yin Tmani da
Allah, kuma ba su yin Tmani da
Ranar Lahira, kuma wanda Shai-
cfan ya kasance abokin hacfi a gare
shi, to, ya munana ga abokin hacfi.
39. Kuma mene ne a kansu, idan
sun yi Tmani da Allah, kuma da
Ranar Lahira, kuma sun ciyar da
abin da Allah Ya azurta su, kuma
Allah Ya kasance, gare su, Masani?
40. Lalle ne, Allah ba Ya za-
luncin gwargwadon nauyin zarra,
idan ta kasance alheri ce, zai ri6a-
nya ta, kuma Ya kawo daga gunSa
ijara mai girma.
41. To, yaya, idan Mun zo da
shaidu daga dukan al'umma, kuma
Muka zo da kai a kan wacfannan,
kana mai shaida!
42. A ranar nan, wacfanda suka
kafirta kuma suka sa6a wa Manzo,
suna gurin da an baje kasa da su,
kuma ba su 66ye wa Allah wani
labari.
43. Ya ku wacfanda suka yi Tma-
ni! Kada ku kusanci salla alhali
kuwa kuna masu maye (1) , sai kun
san abin da kuke facfa, kuma haka
idan kuna masu janaba, face mai
ketare hanya, har ku yi wanka.
'4 ->^
(1) A lokacin ba a hana shan giya ba. Sa'an nan aka hana ta da ayar Suratul Ma'idah
ta 90. Mai janaba kuma ba ya yin salla kuma ba ya shiga masallaci sai ya yi wanka ko
taimama, sai dai yana iya shiga da niyyar wucewa daga kofa zuwa ga wata, ko kuwa ya
shiga ya cfebo ruwa ya fita. Ana yin taimama saboda rashin ruwa hakikatan, ko ma'anan,
kamar mai rashin lafiya. Shafar mace na karya alwala, amma ba ya sabbaba wanka idan an
yi shafar da niyyar jin dacfi ko kuma an sami jin dacfin ba da nufi ba. Mai shafar da wanda
aka shafa duka cfaya suke.
123
4 — Suratun Nisa'
as2ira&-i
Kuma idan kun kasance majinyata,
ko kuwa a kan tafiya ko kuwa wani
daga cikinku, idan ya zo daga gaya-
cfi, ko kuwa kun shafi mata, ba ku
sami ruwa ba, to, ku nufl fuskar
kasa mai kyau, ku yi shafa ga fusko-
kinku da hannuwanku (1) . Lalle ne,
Allah Ya kasance Mai yafewa Mai
gafara.
44. Shin, ba ka gani ba, zuwa ga
wadanda aka bai wa rabo daga
Littafi, suna sayen bata, kuma suna
neman ku bace daga hanya?
45. Kuma Allah ne Mafi sani ga
makiyanku, kuma Allah Ya isa Ya
zama Majibinci, kuma Ya isa Ya
zama Mataimaki.
46. Daga wadanda suka tuba
(Yahudu), akwai wasu suna karka-
tar da magana daga wurarenta,
suna cewa: "Munjiya (2) kumamun
kiya, kuma ka jiya a wanin wurin
jiyawa, kuma ra'ina (da ma'anar
"rubabbe"), ka tsare mu," domin
karkatarwa da harsunansu, kuma
domin suka a cikin addini. Kuma
JojDj J& C^}$^^\ f& 4$j
(1) Watau ku yi taimama saboda rashin ruwa.
(2) Yahudu, ana kiran su da maganar Musa da ya ce wa Ubangiji, 'Mun tuba zuwa
gare Ka, ya Allah,' (A'araf, aya ta 155) domin izgili da suke yi na kin bin haddodin Allah.
Suna karkatar da magana da asalin ma'anarta zuwa ga wata ma'ana ta izgili, suna cewa
'Mun ji' amma aikinsu yana nuna cewa, 'Sun ki' suke nufi. Kuma 'Ka jiya a wanin wurin
jiyawa' addu'a ce mai cfaukar ma'anar alheri da ma'anar sharri, su kuwa suna nufin ta
sharrin. Haka kalmar 'ra'ina' tana da ma'anar 'tsare mu' ko 'saurara mana', kuma tana da
ma'anar 'Ya ru6a66e'. Suna nufin ma'anar karshen.
Wannan bayani shi ma taimako ne ga Musulmi masu raunin hankali domin a tsare
musu addininsu kamar yadda ake tsaron dukiyarsu. An cusa irin wannan makirci a wata
addu'a da suke cewa 'Jauharatul Kamali' inda suka sifanta wanda suke yi wa salati da
"askam" mafi cuta. Wannan ta yi daidai da kalmar ra'ina, ko ma ta fi muni, domin ra'ina
tana da wata ma'ana ta yabo, amma askam ba ta da wata ma'ana sai ta zagi kawai. Allah
Ya tsare mu daga sharrin makiyan addini.
124
4 — Suratun Nisa'
Ml*£4-t
da lalle su, sun ce: "Mun jiya kuma
mun yi cfa'a, kuma ka saurara kuma
ka dakata mana," haklka, da ya
kasance mafi alheri a gare su, kuma
mafi daidaita; amma Allah Ya
la'ane su, saboda kafircinsu don
haka ba za su yiTmani ba, sai kadan.
47. Ya ku wacfanda aka bai wa
Littafi! Ku yi Tmani da abin da
Muka saukar, yana mai gaskatawa
ga abin da yake tare da ku, tun
gabanin Mu shafe wasu fuskoki,
sa'an nan Mu mayar da su a kan
bayayyakinsu, ko Mu la'ane su ka-
mar yadda Muka la'ani masu Asa-
bar. Kuma umurnin Allah ya ka-
sance abin aikatawa.
48. Lalle ne, Allah ba Ya gafarta
a yi shirki game da Shi, kuma Yana
gafarta abin da yake bayan wannan
ga wanda Yake so, kuma wanda ya
yi shirki da Allah, to, lalle ne ya
kirkiri zunubi mai girma.
49. Shin, ba ka gani ba, zuwa ga
wadanda suke tsarkake kansu? A'a,
Allah ne Yake tsarkake wanda
Yake so. Kuma ba za a zalunce su
da zaren gurtsun dabino ba.
50. Ka duba yadda suke kirkira
karya ga Allah ! Kuma shi ya isa ga
zama zunubi bayyananne.
51. Shin, ba ka gani ba zuwa ga
wadanda aka bai wa rabo da ga
Littafi, sunalmani da gunki da Shai-
dan (1) , kuma suna cewa ga wadan-
$^%£J&&^J£1 fy^i ^
%^k^\
?>* \
\i < . " «.
(1) Jibti sunan kowane gunki ne. T)agutu sunan Shaicfan ne mai kirkira karya ya
jingina ta ga Allah, shecfanin da yake zama tare da gumaka ko waninsu, mutum ne ko
aljani, domin ya 6atar da masu raunin hankali, a cikin Yahudu ko a cikin Musulmi.
125
Suratun Nisa'
IRtftKGA
-I
da suka kafirta: "Wacfannan ne
mafiya shiriya daga wacfanda suka
yi Tmani ga hanya"?
52. Wacfannan ne wacfanda Al-
lah Ya la'ane su, kuma wanda Allah
Ya la'ana, to, ba za ka sami matai-
maki a gare shi ba.
53. Ko suna da rabo ne daga
mulki? To, a sa'an nan ba za su iya
bai wa mutane hancin gurtsun dabi-
no ba.
54. Ko suna hasadar mutane (1)
ne a kan abin da Allah Ya ba su
daga falalarSa? To, lalle ne, Mun
bai wa gidan Ibrahim Littafi da
hikima kuma Mun ba su mulki mai
girma.
55. To^dagacikinsuakwai wan-
da ya yi imani da shi, kuma daga
cikinsu akwai wanda ya kange daga
gare shi. Kuma ya isa Jahannama ta
huru da shi.
56. Lalle ne wacfanda suka kafir-
ta da ayoyinMu za Mu kone su da
Wuta, ko da yaushe fatunsu suka
nuna, sai Mu musanya musu wasu
fatun, domin su cfancfani azaba.
Lalle ne Allah Ya kasance Mabu-
wayi, Mai hikima.
57. Kuma wacfanda suka yi Tma-
ni, kuma suka aikata ayyuka na
kwarai, za Mu shigar da su gidajen
Aljanna, (wacfanda) koramu suna
gudana daga karkashinsu, suna
dawwamammu a cikinsu har aba-
C5V
* S s^S'
f**>
•>- A
(1) Annabi Muhammadu, tsTra da amincin Allah sun tabbata a gare shi. An ce masa
dan gidan Ibrahim domin Yahudu su san shi ba kasasshe ba ne ga dangantaka, daga gare
su. Kum bai fita ba daga tsarin cewa Annabawa masu Littafi a bayan Ibrahim, daga
zuriyarsa za su fito. Kuma sun san wannan a cikin littafinsu, watau Attaura.
126
4 — Suratun Nisa'
wm&-i
da, suna da, a cikinsu, matan aure
masu tsarki. Kuma Muna shigar da
su a wata inuwa matabbaciyar
lumshi.
58. Lalle ne Allah Yana umur-
nin ku ku bayar da amanoni zuwa
ga masu su. (1) Kuma idan kun yi
hukunci a tsakanin mutane, ku yi
hukunci da adalci. Lalle ne, Allah
madalla da abin da Yake yi muku
wa'azi da shi. Lalle ne Allah Ya
kasance Mai ji ne, Mai gani.
59. Yaku wacfandasukayiTma-
ni! Ku yi da'a ga Allah, kuma ku yi
da'a ga ManzonSa, da ma'abuta
al'amari daga cikinku. (2) Idan kun
yi jayayya a cikin wani abu, to ku
mayar da shi zuwa ga Allah da
ManzonSa, idan kun kasance kuna
Tmani da Allah da Ranar Lahira.
Wannan ne mafi alheri, kuma mafi
kyau ga fassara.
60. Shin, ba ka gani ba, zuwa ga
wadanda suke riyawar cewa suna
Tmani da abin da aka saukar zuwa
gare ka da abin da aka saukar daga
gabaninka, suna nufin su kai kara
zuwa gaT)agutu (3) alhali kuwa, lal-
(1) Talakawa mutane ne masu rauni a cikin hannuwan shugabanninsu. Su da
dukiyarsu amanoni ne na Allah a cikin hannuwan shugabanni, saboda haka tsaronsu da
dukiyarsu, gwargwadon shari'a, da yin hukunci a tsakaninsu da adalci, bayar da amana ne
ga masu ita. Wanda ya bi son zuciyarsa duka ga dayan wadannan abubuwa, to, ya yi
yaudara ga Allah ke nan. Allah kuma zai kama shi da hukuncin mayaudari.
(2) Haka su kuma mutane talakawa, amana ce a kansu su yarda da hukuncin Allah da
ManzonSa, a kome na aFamurransu da mu'amalolinsu. Kuma wajibi ne a kansu su yarda
da abin da aka hukunta a kansu daidai da shari'ar Allah. Sai kuma idan sun saba, to, sun
yaudari amanar Allah ke nan.
(3) T)agutu shi ne dukan mai yin dokoki wadanda ba dokokin Allah ba. Dukan
wanda ya bi doka wadda ba ta Allah ba a cikin ibada, ko wadda ta saba wa haddin Allah a
cikin mu'amaloli na hakkoki ko na laifuka, to, ya shiga cikin wannan tarkon.
127
Suratun Nisa'
w$m-L
le ne, an umurce su da su kafirta da
shi, kuma Shaicfan yana neman ya
6atar da su, 6atarwa mai nisa.
61. Kuma idan aka ce musu:
"Ku zo zuwa ga abin da Allah Ya
saukar, kuma zuwa ga Manzo" za
ka ga munafukai (1) suna kange mu-
tane daga gare ka, kangewa.
62. To, yaya, idan wata maslfa ta
same su, saboda abin da hannu-
wansu suka gabatar sa'an nan
kuma su je maka suna rantsuwa da
Allah cewa, "Ba mu yi nufin kome
ba sai kyautatawa da daidaitawa."?
63. Wacfannan ne wadanda Al-
lah Ya san abin da ke cikin zuka-
tansu. Saboda haka ka kau da kai
daga gare su, kuma ka yi musu
gargadi, kuma ka gaya musu, a
cikin sha'anin kansu, magana mai
nauyi da fasaha.
64. Kuma ba Mu aiki wani Man-
zo ba face domin a yi masa da'a da
izinin Allah. Kuma da dai lalle su, a
lokacin da suka zalunci kansu, (2)
sun zo maka, sa'an nan suka nemi
gafarar Allah kuma Manzo ya
nema musu gafara, hakika, da sun
sami Allah Mai karBar tuba, Mai
jin kai.
-^ . <
**$r ->• -^ \" 5- "
{5y \j±^j\L>\j 4JA1 \yJ+*y
(1) Miyagun shugabanni masu karkatar da muminai daga hukuncin Allah da hujjar
wai suna nufin su daidaita domin a hada Musulmi da kaflrai ga hukunci; ta haka har
kaflri ya kasance mai yin hukunci a kan Musulmi. Su wacfannan masu yin haka, ba
Musulmi ba ne, munafukan Musulmi ne. Musuluncinsu na baki ne kawai, da ya kai ga
zuciya da ba su yi ko tunanin yarda da haka ba. Allah Ya tsare mu daga sharrin Shaicfan.
(2) Wanda ya £i hukuncin Allah, ya yi laifi biyu, domin sa6a wa Allah da ManzonSa.
Kuma wannan ya nuna rashin Tmaninsa da Allah da ManzonSa. Saboda haka ne aya mai
bin wannan ta ce Musulmi ba su da imani sai sun yarda da hukuncin Allah ga kome daga
aFamurransu, kuma su yarda da hukuncinSa, ba da jin wani kunci a cikin zukatansu ba.
128
4 — Suratun Nisa'
^SIKS5i-t
65. To, a'aha! Ina rantsuwa da
Ubangijinka, ba za su yi imani ba,
sai sun yarda da hukuncinka ga
abin da ya saba a tsakaninsu, sa'an
nan kuma ba su sami wani kunci a
cikin zukatansu ba, daga abin da
ka hukunta, kuma su sallama sal-
lamawa.
66. Kuma da dai lalle Mu, Mun
wajabta musu cewa, "Ku kashe
kanku, ko kuwa ku fita daga gi-
dajenku", da ba su aikata shi ba,
face karfan daga gare su. Kuma da
dai lalle su sun aikata abin da ake
yi musu gargadi da shi, hakTka, da
ya kasance mafi alheri daga gare
su, kuma mafi tsanani ga tabba-
tarwa.
67. Kuma a sa'an nan, hakTka,
da Mun ba su, lada mai girma,
daga gunMu.
68. Kuma lalle ne, da Mun shi-
ryar da su hanya madaidaiciya.
69. Kuma wadannan da suka yi
da'a ga Allah da ManzonSa, to,
wadannan suna tare da wadanda
Allah Ya yi ni'ima a kansu, daga
annabawa da masu yawan gaska-
tawa, da masu shahada ci) , da sali-
hai. Kuma wadannan sun kyautatu
ga zama abokan tafiya.
^^//?^
%
^bx-A^-L^»\j
0t^5JKJa£#3f<fc
- ^Vky^^To^i
(1) Darajar cfaukaka ga addini shi ne zama Annabi sa'an nan SiddTk, watau manyan
sahabban kowane Annabi. Wadannan darajoji biyu yanzu an rufe su daga kowa, domin
babu sauran annabci wanda yake tare da siddikanci. Ta uku ita ce shahada watau a kashe
mutum a wurin ya£i domin cfaukaka kalmar Allah da tsare ha££o£in Musulmi. Wannan
ita ce makasudin abin fada a nan, domin abin da surar ke karantarwa, kuma domin ya
zama shimfidar magana a kan darajar jihadi da amfanoninsa. Ta hucfu zama salihi mai son
abin da Allah Yake so kuma mai £in abin da Allah Yake £i.
129
Suratun Nisa'
8231184-1
70. Waccan falalar daga Allah
take, kuma Allah Ya isa zama Ma-
sani.
71. Ya ku wacfanda suka yi Ima-
ni! Ku riki shirinku (1> , sa'an nan
ku fitar da hari jama'a jama'a, ko
ku fitar da yaki gaba daya.
72. Kuma lalle ne daga cikinku
akwai mai fasarwa (2> . To, idan
wata maslfa ta same ku, sai ya ce:
"Lalle ne, Allah Ya yi mini ni'ima,
domin ban kasance mahalarci tare
da su ba."
73. Kuma lalle ne, idan wata
falala daga Allah ta same ku, ha-
klka, tabbas, yana cewa, kamar
wata soyayya ba ta kasance a tsa-
kaninku da shi ba: "Ya kaitona!
Da na zama tare da su dai, domin
in rabonta da rabo mai girma!"
74. Sai wacfanda suke sayar da
rayuwar duniya su karBi ta Lahira
su yi yaki, a cikin hanyar Allah.
Kuma wanda ya yi yaki a cikin
hanyar Allah, to, a kashe shi ko
kuwa ya rinjaya, sa'an nan za Mu
je masa da ijara mai girma.
75. Kuma mene ne ya same ku,
ba ku yin yaki a cikin hanyar Allah,
da wacfanda aka raunanar daga
maza da mata da yara, suna cewa:
"Ya Ubangijinmu! Ka fitar da mu
daga wannan alkarya wadda muta-
nenta suke da zalunci, kuma Ka
&&$kL>zb-*&M
(!) Ba ya halatta Musulmi su zauna babu tattalin yaki da fitar da yaki ko hari a kan
makiyansu, saboda abin da ke cikin wannan ayar ta 71.
(2) Sifar munafuki ita ce ya £i fita zuwa yaki, kuma ya fasar da waninsa, ya yi muraar
hasarar Musulmi, kuma ya yi bakin cikin nasararsu, ya so a raba gamma da shi.
130
Suratun Nisa'
assise -t
sanya mana majibinci daga gunKa,
kuma Ka sanya mana mataimaki
daga gunKa"?
76. Wadanda suka yi imani,
suna yaki a cikin hanyar Allah,
kuma wadanda suka kafirta suna
yaki a cikin hanyar T)agutu (Shai-
dan). To, ku yaki majibintan Shai-
dan. Lalle ne kaidin Shaidan ya
kasance mai rauni.
77. Shin, ba ka gani ba zuwa ga
wadanda aka ce musu : "Ku kange
hannuwanku, kuma ku tsayar da
salla, kuma ku bayar da zakka."?
To, a lokacin da aka wajabta musu
yaki sai ga wani bangare daga ci-
kinsu suna tsoron mutane kamar
tsoron Allah, ko kuwa mafi tsanani
ga tsoron, kuma suka ce: "Ya
Ubangijinmu! Don me Ka wajabta
yaki a kanmu? Me ya hana Ka
jinkirta mana zuwa ga wani ajali na
kusa?" Ka ce: "Jin dacfin duniya
kacfan ne, kuma Lahira ce mafi
alheri ga wanda ya yi takawa.
Kuma ba a zaluntar ku da slfilin
hancin gurtsun dabino!
78. "Inda duk kuka kasance,
mutuwa za ta riske ku, kuma ko da
kun kasance ne a cikin ganuwoyi
ingatattu!" Kuma idan wani alheri
ya same su sai su ce: "Wannan
daga wurin Allah ne," kuma idan
wata cuta ta same su, sai su ce,
"Wannan daga gare ka ne". Ka ce:
"Dukkansu daga Allah ne." To,
me ya sami wadannan mutane, ba
su kusantar fahimtar magana?
79. Abin da ya same ka daga
alheri, to, daga Allah yake, kuma
f >
fe£f.&^yj^y^c^J**t \?p^ u^3
\>* >'t
'-'Zli
£jz(j+*o£* 'jjyu 41 ■ ,. ^ p 4 ; ^ Ojj* Jill*
4^'a*&&^
131
4 — Suratun Nisa'
abin da ya same ka daga sharri, to,
daga kanka yake, kuma Mun aike
ka zuwa ga mutane, (kana) Manzo,
kuma Allah Ya isa ga zama Shaida.
80. Wanda ya yi da'a ga Manzo,
to, hakTka, ya yi da'a ga Allah.
Kuma wanda ya juya baya, to, ba
Mu aike ka ba don ka zama mai
tsaro a kansu.
81. Kuma suna cewa, "Da'a,"
sa'an nan idan sun fita daga wu-
rinka, sai wata kungiya daga cikin-
su ta kwana da niyyar wanin abin
da take fatfa, alhali kuwa Allah na
rubuta abin da suke kwana da
niyyarsa. Saboda haka ka kau da
kai daga gare su, kuma ku dogara
ga Allah, kuma Allah Ya isa ya
zama Walali.
82. Shin, ba su kula da Alkur'-
ani, kuma da ya kasance daga wu-
rin wanin Allah, hakTka, da sun
samu, a cikinsa, sa6a wa juna mai
yawa?
83. Kuma idan wani aFamari (1)
daga aminci ko tsoro ya je musu,
sai su watsa shi. Da sun mayar da
shi zuwa ga Manzo da ma'abuta
aramari daga gare su, lalle ne, wa-
cfanda suke yin bincikensa, daga
gare su, za su san shi. Kuma ba
domin falalar Allah ba a kanku da
rahamarSa, hakika, da kun bi Shai-
cfan face kacfan.
m
'"'A .. * i-f^i^iK ^ AA>"
<j^^^^\^\/S^)
(1) Umurnin al'umma da cewa idan sun ga wani al'amari da ba su san kansa ba, ko
kuwa idan wani abu na ban tsoro ya auku, to, haram ne su yi ta barararsa domin su firgitar
da mutane. Abin da yake wajibi a kansu sa'an nan, shi ne su kai rahotonsa ga shugabanni
masu sanyawa a bincika a san yadda abin yake, da kuma yadda za a yi maganinsa.
132
4 — Suratun Nisa'
84. Saboda haka, ka (1) yi yaki a
cikin hanyar Allah, ba a kallafa
maka ba, face a kanka, kuma ka
kwacfaitar da muminai. Akwai
tsammanin Allah Ya kange gafin
wacfanda suka kafirta, kuma Allah
ne Mafi tsananin gafi, kuma Mafi
tsananin azabtawa.
85. Wanda ya yi (2) ceto, ceto
mai kyau, zai sami rabo daga gare
shi, kuma wanda ya yi ceto, ceto
mummuna, zai sami ma'auni daga
gare shi, Kuma Allah Ya kasance,
a kan dukkan kome, Mai kayyade
lokaci.
86. Kuma idan an gaishe (3) ku
da wata gaisuwa, to, ku yi gaisuwa
da abin da yake mafi kyau daga
gare ta, ko kuwa ku mayar da ita.
Kuma Allah Ya kasance a kan
dukkan kome Mai lissafi.
87. Allah, babu abin bautawa
face Shi. Lalle ne, hakika, Yana
tara (4) ku har zuwa ga Yinin Kiya-
^t ^ *^"l "A'\ s\'l 'A&i'
t 4<,'s
\^ v a^'>^)^o
Ml^^j^^^oS
^f^iijxli^^i^i^l
(1) Umurni zuwa ga Annabi, tsTra da aminci su tabbata a gare shi.
(2) Ma'anar ceto : watau wani ya yi wa wani hanya a kan biyan bukatarsa ta kowace
iri, saboda darajar mai yin ceton. Ya kamata ya yi ceton domin Allah Wanda Ya ba shi
darajar, ba da ya bai wa Allah kome ba. Idan kuma sayar da ceton yake yi, Allah zai karbe
darajar daga gare shi. Ci da ceto haramun ne. Sakamakonsa shi ne Allah Ya karbe darajar
ceton daga gare shi.
(3) A gaisuwa idan an ce muku : "Assalamu alaikum" ku mayar da cewa, "Wa'alaiku-
mus salamu wa rahamatul Lahi wa barakatuH." Ko ku mayar kamar yadda aka yi muku.
Watau kada ku naicasa 'yan'uwanku ko da ga gaisuwa ne. Facfakarwa: Fara sallama
mustahabbi ne, mayarwa kuma farilla ne, amma wanda ya fara, ya fl lada. Haka yin tsarki
a gabanin lokaci mustahabbi ne, amma a bayan shigar lokaci ya zama wajibi. Wanda ya yi
mustahabbi a nan ya fl lada. Haka jinkirtar da biyan bashi ga matsattse wajibine, amma
barrantar da shi mustahabbi ne. Yin mustahabbi a nan ya fi lada.
(4) Idan kun tsare hukunce-hukunce da Allah, Wanda babu abin bautawa sai Shi, Ya
umurce ku da su, to zai hacfa kalmarku ta tabbata guda har ya zuwa Ranar Kiyama.
133
Suratun Nisa'
;lg&-t
ma, babu shakka a cikinsa. Kuma
wane ne mafi gaskiya daga Allah ga
labari?
88. To, mene ne ya same (1) ku a
cikin munafukai, kun zama kun-
giya biyu, alhali kuwa Allah ne Ya
mayar da su saboda abin da suka
tsirfanta? Shin, kuna nufin ku shir-
yar da wanda Allah Ya Batar ne?
Kuma wanda Allah Ya Batar, to,
ba za ka sami wata hanya ba zuwa
gare shi.
89. Suna gurin ku kafirta kamar
yadda suka kafirta, domin ku ka-
sance daidai. Saboda haka kada ku
riki wasu masoya daga cikinsu, sai
sun yo hijira a cikin hanyar Allah.
Sa'an nan idan sun juya, to, ku
kama su, kuma ku kashe su inda
duk kuka same su. Kuma kada ku
riki wani masoyi daga gare su ko
wani mataimaki.
90. Face dai wacfanda suke sa-
duwa zuwa ga wasu mutane, wa-
cfanda a tsakaninku da su akwai
alkawari, ko kuwa wacfanda suke
sun je muku (domin) kirazansu sun
yi kunci ga su yake ku, ko su yaki
mutanensu. Kuma da j\llah Ya so,
lalle ne, da Ya^ba su iko a kanku,
sa'an nan, haklka, su yake ku. To,
idan sun nlsance ku, sa'an nan ba
su yake ku ba, kuma suka jefa
sulhu zuwa gare ku, to, Allah bai
sanya wata hanya ba, a gare ku, a
kansu.
. '>Xi • ^
Cu>- j^Jb^JLSB ij pAj JoO Vyy o te
(1) Hani ne kada muminai su rarraba kansu domin jayayya a cikin sha'anin kafirai.
Sai su bi abin da Allah Ya ce a yi da su, kamar yadda bayaninsa yake tafe a cikin wannan
aya da ayoyin da suke a bayanta. Ya yi bayani da tafsili daki-daki.
134
4 — Suratun Nisa'
91. Za ku sami wasu (1) suna nu-
fin su amintar da ku, kuma su
amintar da mutanensu, ko da yaus-
he aka mayar da su ga fitina, sai a
dulmuya su a cikinta. To, idan ba
su nlsance ku ba, kuma sun jefa
sulhu zuwa gare ku, kuma sun kan-
ge hannuwansu, to, ku kama su,
kuma ku kashe su inda duk kuka
kama su, kuma jvadannan, Mun
sanya muku dallli bayyananne a
kansu.
92. Kuma ba ya kasancewa (2) ga
mumini ya kashe wani mumini,
face bisa ga kuskure. Kuma wanda
ya kashe mumini bisa ga kuskure,
sai 'yantawar wuya mumina da
diyya abar mifcawa ga mutanensa,
face idan sun bari sadaka. Sa'an
nan idan (wanda aka kashe) ya
kasance daga wasu mutane maiciya
a gare ku, kuma shi mumini ne, sai
'yantawar wuya mumina. Kuma
idan ya kasance daga wasu mutane
ne (wadanda) a tsakaninku da tsa-
kaninsu akwai alkawari, sai diyya
abar mlicawa zuwa ga mutanensa,
da 'yantawar wuya mumina. To,
wanda bai sami (wuyan ba) sai
-^ ~S- -> '\'>
i.A
u£k&v&£i
y<
(1) Sun bayyana imaninsu gare ku domin ku amince musu, kuma sun bayyana kafirci
a wurin mutanensu kafirai domin su amince musu, watau suna ido ruwa ido tudu. Su kam
kafirai ne, ku ya£e su, sai fa idan sun musulunta, ko kuma sun bayyana sulhunsu sosai a
gare ku.
(2) Kisan kuskure babu iasasi a cikinsa, sai dai biyan diyya da kuma kaffara. Amma
biyan diyya yana kan dukkan dangin mai kisan, gwargwadon icarfinsu, shi cfaya ne daga
cikinsu. Idan danginsa ba su isa ba, ko kuwa babu su, to, sai baitulmali na Musulmi ya
biya. Ana biyan diyya a cikin shekaru hucfu. Ana bayar da ita ga magadan wanda aka
kashe. Amma kaffara, ita kam a kan mai kisan kawai take a kan tartibinta. Wanda ya
kashe bawa bisa kuskure zai biya £imarsa ga mai shi, kuma ana son ya yi kaffara.
135
Suratun Nisa'
rai^-i
azumin watanni biyu jere, domin
tuba daga Allah. Kuma Allah Ya
kasance Masani, Mai hikima.
93. Kuma wanda ya kashe wani
mumini da ganganci, (1) to, saka-
makonsa Jahannama, yana
madawwami a cikinta, kuma Allah
Ya yi fushi a kansa, kuma Ya
la'ane shi, kuma Ya yi masa tatta-
lin azaba mai girma.
94. Ya ku wacfanda suka yi Tma-
ni ! Idan kun yi tafiya (a cikin kasa),
domin jihadi, to, ku nemi bayani. (2)
Kuma kada ku ce wa wanda ya jefa
sallama zuwa gare ku: "Ba Musul-
mi kake ba." Kuna neman hajar
rayuwar duniya, to, a wurin Allah
akwai ganimomi masu yawa. Ka-
mar wannan ne kuka kasance a
gabanin ku musulunta, sa'an nan
Allah Ya yi muku falala. Saboda
haka ku zan neman bayani. Lalle
ne Allah Ya kasance, ga abin da
kuke aikatawa, Masani.
95. Masu zama (3) daga barin
yaki daga muminai, wasun
ma'abuta larura, da masu jihadi a
cikin hanyar Allah da dukiyoyinsu
da rayukansu, ba su zama daidai.
<> J&f ^ . < '\S • iA y< > f S'
* K <' *\4'\s >'"\'
^^&^^
^^lJo tL s^> D^\>^^r^Lj4
(1) Wanda ya kashe muminai da ganganci, kuma yana kudurcin halaccin kashe shi
din, to, shi kafiri ne. Amma idan yana kudurcin haramcin kisa, amma duk da haka ya
kashe shi domin wata fa'ida ta duniya, ko domin adawa, to yana nan mumini, hukuncinsa
kisasi. Surar Bakara, aya ta 179.
(2) Bayanin cewa ana daukar wanda aka ji ya yi kalmar shahada mumini, sai fa idan
an ga ya yi wani aiki, ko aka ji ^a yi wata magana wadda take warware ma'anar kalmar
shahadar, babu kuma wani tawili ko jahilcin da yake iya zama uzuri ga mai shi.
(3) Falalar masu jihadi a kan wadanda ba su jihadi daga cikin muminai. Fadar falalar
tana karfafa zukata ga yin jihadi domin tsaron addini da rayukan masu rauni da
dukiyarsu.
136
Suratun Nisa'
mmm-i
Allah Ya fifTta masu jihadi da duki-
yoyinsu da rayukansu a kan masu
zama, ga daraja. Kuma dukansu
Allah Ya yi musu alkawari da jibu
mai kyau (1) . Kuma Allah ya fifita
masu jihadi a kan masu zama da
lada mai girma.
96. Darajoji daga gare Shi da
gafara da rahama. Kuma Allah Ya
kasance Mai gafara ne, Mai jin kai.
97. Lalle ne, wadanda ma-
la'iku (2) suka kar6i rayukansu, (al-
hali) suna masu zaluntar kansu,
sun ce (musu): "A cikin me kuka
kasance?" (Su kuma) suka ce:
"Mun kasance wadanda aka rau-
nana a cikin kasa." Suka ce: "Ashe
kasar Allah ba ta kasance mayal-
waciya ba, domin ku yi hijira a
cikinta?" To, wadannan mako-
marsu Jahannama ce. Kuma ta mu-
nana ta zama makoma.
98. Face wadanda aka raunana
daga maza da mata da yara wadan-
da ba su iya yin wata dabara, kuma
ba su shiryuwa ga hanya.
99. To, wadannan akwai tsa-
mmanin Allah Ya yafe laifi daga
gare su, kuma Allah Ya kasance
Mai yafewa ne, Mai gafara.
100. Kuma wanda ya yi hijira a
cikin hanyar (3) Allah, zai samu, a
&J
x f Xt' T>" 4 '
' **X5i
i0^\ * S s >' *s 'sK.' ' > \' 9 ' +Ct
(1) Aljanna.
(2) Hukuncin rashin hijira zuwa wurin yardar Allah domin tsayar da hakkokin Allah.
Hukuncin mai dogewa ne, idan an sami dalTlin yin hijirar, kuma babu abin da ya hana ta na
uzurori.
(3) Allah Yana kwadaitar da muminai ga yin hijira zuwa wurin neman yardarSa.
Hukuncin hijira yana nan a ko da yaushe hali ya hukunta da a yi ta.
137
4 — Suratun Nisa'
iMwm-i
cikin kasa, wuraren juyawa masu
yawa da yalwa. Kuma wanda ya
fita daga gidansa yana mai hijira
zuwa ga Allah da ManzonSa, sa'an
nan kuma mutuwa ta riske shi, to,
lalle ne, ladarsa ta auku ga Allah.
Kuma Allah Ya kasance, a gare ku,
Mai gafara, Mai jin kai.
101. Kuma idan kun yi tafiya a
cikin kasa, to, babu laifi a kanku
ku rage (1) daga salla idan kun ji
tsoron wadanda suka kafirta su
fitine ku. Lalle ne kafirai sun ka-
sance, a gare ku, makiyi bayya-
nanne.
102. Kuma idan ka kasance a
cikinsu, sai ka tsayar musu da salla,
to, wata kungiya daga gare su ta
tsaya tare da kai, kuma sai su rike
makamansu. Sa'an nan idan sun yi
salla, to, sai su kasance daga
bayanku. Kuma wata kungiya ta
dabam (ta) wadanda ba su yi sallar
ba, ta zo, sa'an nan su yi sallar tare
da kai. Kuma su riki shirinsu da
makamansu. Wadanda suka kafir-
ta sun yi gurin da dai kuna shagala
daga makamanku da kayanku do-
min su karkata a kanku, karkata
guda. Kuma babu laifi a kanku
idan wata cuta daga ruwan sama ta
kasance a gare ku, ko kuwa kun
kasance masu jinya ga ku ajiye
***
b^p^>xLm»i »j J^-LJ j <JJLx* jt^5 <L-ju Up
\ >1'f >\<t' »>" K *\' »>"' X t'Vt'
^ + st y.
(1) Rage salla a nan ba ana nufin sallar kasaru ta tafiya ba, wanda take ta tabbata da
Sunna. Wannan rage salla, shi ne sallar tsoro wadda ake yi gwargwadon halin da ake ciki
na tsoro. Idan yana yiwuwa a yi ta da lTmami, sai ya kasa jama'a kashi biyu, to, sai a yi
kamar yadda aya ta tafe za ta yi bayani, idan kuwa ba zai yiwu ba, sai a yi yadda hali ya
saukaka duka, kamar a aya ta 239 daga Suratul Bakara.
138
Suratun Nisa'
mm&-i
makamanku. Kuma dai ku riki shi-
rinku. Lalle ne, Allah Ya yi tattali,
ga kafirai, azaba mai walakan-
tarwa.
103. Sa'an nan idan kun kare
salla, to ku ambaci Allah tsaye da
zaune da a kan sasanninku. Sa'an
nan idan kun natsu, to, ku tsayar da
salla. Lalle ne, salla ta kasance a
kan muminai farilla mai kayya-
daddun lokuta.
104. Kuma kada ku sassauta a
cikin neman mutanen, idan kun
kasance kuna jin zogi, to, lalle su
ma, suna jin zogi kamar yadda
kuke jin zogi. Kuma kuna tsam-
mani, daga Allah, abin da ba su
tsammani. Kuma Allah Ya kasance
Masani Mai hikima.
105. Lalle ne, Mu, Mun sau-
kar (1) , zuwa gare ka, Littafi da
gaskiya, domin ka yi hukunci a
tsakanin mutane da abin da Allah
Ya nuna maka, kuma kada ka ka-
sance mai husuma domin masu
yaudara.
&^\S ZSx<' ' . £*"T» *^f *?^ t ^ *
>* <"S >£'
^t \-C * "1/ 'V^' i*Y\ 11
(1) Gudanar da hukunci a cikin mahakama, kada mai shari'a ya taimaki kowane
sashe, duk yadda^suke a gare shi, sai ya cfauke su daidai a gabansa, kamar yadda ya auku a
gaban Annabi, tsira da aminci su tabbata a gare shi. Wani mutum Musulmi ana ce masa
Mat'ama bn Ubairak ya yi satar sulke ya 66ye shi a wurin wani Bayahude. A lokacin da
aka gane sulken a wurin Bayahuden, sai Mat'ama ya yi masa Razafi da satarsa, shi kuma ya
yi rantsuwa cewa ba shi ne ya sata ba. Kuma mutanensa suka ro£i Annabi, tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi, domin ya yi musu jayayya ya kubutar da Mat'ama, Annabi
kuwa bai yarda ba. Kamar yadda ayoyin nan suka bayyana, domin ya zama abin koyi.
Wannan kuma ya nuna cewa, ga gudanar da shari'a Annabi yana yin ijtihadi
gwargwadon abin da ya bayyana daga hujjoji ya yi hukunci, kamar wajen shawara a wurin
yaJci. Ya zama abin koyi.
139
4 — Suratun Nisa'
mztiite-i
106. Kuma ka nemi Allah gafa-
ra. Lalle ne Allah Ya kasance Mai
gafara, Mai jin kai.
107. Kuma kada ka yi jayayya
domin tunkude wa wadanda suka
yaudari kansu. Lalle ne Allah ba
Ya son wanda ya kasance mai ya-
wan ha'inci mai yawan zunubi.
108. Suna neman 66yewa daga
mutane kuma ba su neman 66yewa
daga Allah, alhali kuwa Shi Yana
tare da su a lokacin da suke kwana
da niyyar yin abin da ba Ya yarda
da shi daga maganar. Kuma Allah
Ya kasance ga abin da suke aika-
tawa Mai kewayewa.
109. Ga ku, ya wadannan (1) !
Kun yi jidali, domin tunkude musu
(kunya) a cikin rayuwar duniya, to,
wane ne zai yi jidali domin tunkude
musu a Ranar Kiyama? Ko kuwa
wane ne zai kasance wakili a
kansu?
110. Kuma wanda ya aikata
cuta ko kuwa ya zalunci kansa,
sa'an nan kuma ya nemi Allah ga-
fara, zai sami Allah Mai gafara,
Mai jin Rai.
111. Kuma wanda ya yi tsirfar
zunubi, to yana tsirfarsa ne a kan
kansa kawai. Kuma Allah Ya ka-
sance Masani, Mai hikima.
3f H^3 \jyLC>ob4)lS ^^l4$\jAJ*l^t\j
9 s '*~Ss'
(S3 [*^j\jjL&A&\j^>tJ4tt\
(1) Wannan yana nuna aikin lauya (Lawyer) domin ya taimaki marasa gaskiya
saboda ya ku6uta haramun ne, har dai idan za a mayar da laifi ga wani barrantacce, ko
kuwa za a kar6e hakkin mai hakki a bai wa wanda bai cancanta da shi ba. Amma wakilin
sharT'a yana halatta idan bai zama domin 66ye gaskiya ba. WakTlai irin na zamanin nan
masu sana'a da wannan, su ne karnukan duniya na farautar haram domin su sha jini.
140
4 — Suratun Nisa'
112211*34-1
112. Kuma wanda ya yi tsiwir-
wirin kuskure ko kuwa zunubi,
sa'an nan kuma ya jefi wani
barrantacce da shi, to, lalle ne ya
tattali kirkiren karya da zunubi
bayyananne.
113. Kuma ba domin falalar Al-
lah ^ba, a kanka, da rahamarSa,
haklka, da wata kungiya daga gare
su ta himmatu ga su 6atar da kai.
Kuma ba su Batarwa face kansu,
kuma ba su cutar ka daga kome.
Kuma Allah Ya saukar da Littafi
da hikima gare ka, kuma Ya sanar
da kai abin da ba ka kasance ka
sani ba. Kuma falalar Allah ta ka-
sance mai girma a gare ka.
114. Babu wani alheri a cikin
masu yawa daga ganawarsu (1) , face
wanda ya yi umurni da wata sada-
ka ko kuwa wani alheri ko kuwa
gyara a tsakanin mutane. Wanda
ya aikata haka domin neman
yardodin Allah, to, za Mu ba shi
lada mai girma.
115. Kuma wanda yasaba wa (2)
Manzo daga bayan shiriya ta
bayyana a gare shi, kuma ya bi
wanin hanyar muminai, za Mu
J*
XL
c-> \^9^ *^*2*J >JJy* cP^ <J* J
(1) Hukuncin ganawa da Annabi ko wani shugaban jama'a mai tsayuwa matsayin
Annabi ga gyaran sha'aninsu, ba ya halatta sai idan akwai wani alheri a ciki, wanda
amfaninsa zai shaft jama'a duka.
(2) Hana fassarar Alkur'ani ko Sunnar Annabi, ba a kan hanyar da Annabi ko
Sahabbansa da wadanda suka bi hanyarsu suka fassara Jsa. Da mutum ya yi tawilin
Alkur'ani, gara ya ce bai sani ba. Tawilin Alkur'ani ko Hadlsi da hankali yana kai ga bude
£6far kafirci boyayye da yin hukunci da abin da Allah bai saukar ba. Na'am ba a hana
ijtihadi ga abin da ba a sami nassi a kansa ba, ko kuma aka sami nassi wanda ba
bayyananne ba. Jingina ijtihadi ga ra'ayi ya fi tawilin abin da bai bayyana ba daga
Alkur'ani ko Hadlsi, domin ra'ayi ba ya batar da wasu, amma tawlli yana batarwa.
141
Suratun Nisa'
USSIH^-i
jiBintar masa abin da ya jiBinta,
kuma Mu kone shi da Jahannama.
Kuma ta munana ta zama
makoma.
116. Lalle ne, Allah ba Ya ga-
farta a yi shirki da Shi, kuma Yana
gafarta abin da yake bayan wan-
nan, ga wanda Yake so. Kuma
wanda ya yi shirki da Allah, to,
lalle ne ya Bace Bata mai riTsa. (1)
117. Ba su kiran kowa, baicin
Shi, face mata, kuma ba su kiran
kowa face Shaicfan, mai tsaurin kai.
118. Allah Ya la'ane shi. Kuma
ya ce: "Lalle ne, za ni riki rabo
yankakke (2) , daga bayinKa.
119. "Kuma lalle ne ina Batar da
su, kuma lalle ne ina sanya musu
guri, kuma lalle ne ina umurnin
su domin su katse (3) kunnuwan
dabbobi, kuma lalle ne ina umurnin
su domin su canza halittar Allah."
Kuma wanda ya riki Shaicfan maji-
Binci, baicin Allah, to, hakTka ya yi
hasara, hasara bayyananniya.
120. Yana yi musu alkawari,
kuma yana sanya musu guri, alhali
Shaidan ba ya yi musu wani
wa'adin kome face rucfi.
* ' 9 T^""!
lA-^* O *L*j *\ 4^jk-+a> J
(1) Bayanin shirki da hukunce-hukuncensa da abin da yake ratayuwa da shi. Sanin
ma'anar shirki wajibi ne, domin a kan tauhTdi ne aka gina shikashikan Musulunci.
(2) Rabon Shaidan daga kowane dubu, shi ne dari tare da cas'in da tara, kamar yadda
aka ruwaito a cikin Hacfisi.
(3) Suna katse kunnuwan dabbobi domin su nuna cewa na gumakansu ne. Sunan
mata shi ne ga duk abin da ba ya da rai, kamar wata, itatuwa duka mata ne. Canza halitta
kamar tsagen fuska da fake hakora da karkarar gemu domin neman kyau, duka umurnin
Shaidan ne.
142
4 — Suratun Nisa'
3SSHIS&-1
121. Wacfannan matattararsu
Jahannama ce, kuma ba su samun
makarkata daga gare ta.
722. Kuma wadanda suka yi
imani, kuma suka aikata ayyukan
kwarai, za mu shigar da su gidajen
Aljanna (wadanda) koramu suna
gudana a karkashinsu, suna masu
dawwama a cikinsu har abada bisa
ga wa'adin Allah tabbatacce. Wane
ne mafi gaskiya daga Allah ga
magana?
123. (ATamari) bai zama gura-
ce-guracenku ba, kuma (1) ba
gurace-guracen Mutanen Littafi ba
ne. Wanda ya aikata mummunan
aiki za a saka masa da shi, kuma ba
zai sami wani masoyi ba, baicin
Allah, kuma ba zai sami mataimaki
ba.
124. Kuma wanda ya yi aiki
daga ayyukan kwarai, namiji ne ko
kuwa mace, alhali kuwa yana
mumini, to, warfannan suna shiga
Aljanna kuma ba za a zalunce su da
gwargwadon hancin gurtsun dabl-
no ba.
125. Kuma wane ne ya fi kyau
ga addini daga wanda ya sallama
fuskarsa ga Allah, alhali kuwa
yana mai kyautatawa kuma ya bi
akidar Ibralimi, yana mai karkata
zuwa ga gaskiya? Allah Ya riki
Ibrahim badadayi (2) .
■i J* C*£%kja&\{jA JUlS^J'* J
t^ XX' **•'<< \*
'4. <
\< ' ' '••'If "<X'* »>'>'
(1) Addini ba tatsuniyar baki ba ne, aiki ne, ko mutum ya yi mugu ya shiga Wuta, ko
kuma ya yi na kwarai ya shiga Aljanna.
(2) Akwai kwacfaitarwa ga cewa, wanda yake son Allah Ya so shi, to sai ya bi akida
da aiki irin na Ibralnma, sai Allah Ya so shi.
143
4 — Suratun Nisa'
3231^ -i
126. Kuma Allah ke da (1) (ma-
llakar) abin da ke cikin sammai da
kuma abin da ke cikin kasa, kuma
Allah Ya kasance, ga dukan kome,
Mai kewayewa.
127. Suna yi maka fatawa a ci-
kin sha'anin mata. Ka ce: Allah
Yana bayyana fatawarku a cikin
sha'aninsu, da abin da ake karan-
tawa a kanku a cikin Littafi, a cikin
sha'anin marayun mata wadanda
ba ku ba su abin da aka rubuta
musu (2) (na gado) ba, kuma kuna
kwadayin ku aure su, da sha'anin
wadanda aka raunana daga yara,
da sha'anin tsayuwarku ga marayu
da adalci. Kuma abin da kuka ai-
kata daga alheri, to, lalle ne, Allah
Ya kasance Masani a gare shi.
128. Kuma idan wata mace ta ji
tsoron kiyo daga mijinta ko kuwa
bijirewa, to, babu laifi a kansu, su
yi sulhu a tsakaninsu, sulhu (mai
kyau). Kuma yin sulhu ne mafi
alheri. Kuma an halartar wa rayu-
ka yin rowa. Kuma idan kun kyau-
tata, kuma kuka yi takawa, to, lalle
ne, Allah Ya kasance, ga abin da
kuke aikatawa, Masani.
(1) Ko da yake Allah Ya riki Ibrahlma "KhalTl" watau masoyi, amma bai hana
Ibrahlma ya zama a cikin bayin Allah kuma mulkinSa ba, domin yana daga cikin abin da
sama da kasa suka kunsa a cikinsu.
(2) A cikin Jahiliyya ba su bai wa yara da mata gado. Musulunci ya soke wannan
al'ada da ayar gado, aya ta 1 1. Kuma idan akwai wata marainiya ga hannun wani tana da
dukiya, sai ya jefa mata mayafinsa domin ya hana ta auren wani namiji. Shi kuma ko ya
aure ta ko kuma ya bar ta babu aure har ta mutu, su yi gadonta.
144
Suratun Nisa'
asaras-i
129. Kuma ba za ku iya yin
adalci ba a tsakanin (1) mata, ko da
kun yi kwadayin yi. Saboda haka
kada ku karkata, dukan karkata,
har ku bar ta kamar wadda aka
rataye. Kuma idan kun yi sulhu,
kuma kuka yi takawa, to, lalle ne
Allah Ya kasance Mai gafara, Mai
jin kai.
130. Kuma idan sun rabu, Allah
zai wadatar da kowanne daga yal-
warSa. Kuma Allah Ya kasance
Mayalwaci, Mai hikima.
13 L Kuma Allah ne da mulkin
abin da ke cikin sammai da abin da
ke cikin kasa. Kuma lalle ne, hakT-
ka, Mun yi wasiyya ga wacfanda
aka bai wa Littafi a gabaninku, da
ku, cewa ku bi Allah da takawa,
kuma idan kun kafirta, to, lalle ne,
Allah Yana da abin da yake cikin
sammai da abin da yake cikin kasa.
Kuma Allah Ya kasance Wada-
tacce, Godadde.
132. Kuma Allah ne da mulkin
abin da yake cikin sammai da abin
da yake cikin kasa^ kuma Allah Ya
isa Ya zama Wakili.
133. Idan Ya so, za Ya tafi da
ku, ya ku mutane ! kuma Ya zo da
wasu. Allah Ya kasance a kan
haka, Mai Tkon yi ne.
^9 \+~&0 'jjA-^OO 4W»Cj^>i3
-A*.
*'<<* A <. »*
&3J?K\&'3^ ( £^ <£)£> AS
mm
'SI"
(1) Wajen so, ba za a iya daidaita su ba, sai a daidaita ga kwana da ciyarwa da wurin
kwana da tufafi gwargwadon halin kowace.
145
Suratun Nisa'
Mfci-t
134. Wanda ya kasance (1) yana
nufin sakamakon duniya, to, a wu-
rin Allah sakamakon duniya da
Lahira yake. Kuma Allah Ya ka-
sance Mai ji, Mai gani.
135. Ya ku wacfanda suka yi
Tmani! Ku kasance masu tsayuwa
da adalci, masu shaida (2) saboda
Allah, kuma ko da a kanku ne ko
kuwa mahaifa da mafi kusantar
zumunta, ko (wanda ake yi wa
shaida ko a kansa) ya kasance
mawadaci ko matalauci, to, Allah
ne Mafi cancanta da al'amarinsu,
saboda haka kada ku blbiyi son
zuciya, har ku karkata. Kuma idan
kuka karkatar da magana, ko
kuwa kuka kau da kai, to, lalle ne,
Allah Ya kasance Masani ga abin
da kuke aikatawa.
136. Ya ku wacfanda suka yi
Tmani ! Ku yi Tmani (3) da Allah da
ManzonSa, da Littafin da Ya
sassaukar ga ManzonSa da Littafin
nan wanda Ya saukar daga gabani.
To, wanda ya kafirta da Allah da
mala'ikunSa, da LittattafanSa, da
(1) Wannan shi ne karshen wasiyya ga Yahudu da Nasara da kuma Musulmi, kuma
ma'anar wasiyya ita ce Allah Ya yi umurni da ku yi Masa da 'a, amma ba domin Yana
neman wani abu daga gare ku ba, domin ba za ku kara Masa mulki ba, domin Shi ne da
sammai da kasa da abin da ke tsakaninsu, ku kuma kuna cikinsu. Saboda haka neman
da'ar nan domin amfanin kanku ne.
(2) Bayar da shaida da hukunce-hukuncen da suka ratayu da shi. Bayar da shaida
amana ce ta Allah daidai da tsaron dukiyar amana, ko ma ta fi tsanani, domin takan kai ga
rai. Karkatar da magana, watau a fade ta ba yadda take ba. Bijirewa ita ce a ki bayar da
shaida.
(3) Tmani da dukan rukunnan Tmani shida yana cikin tsaron amana. Rukunnan Tmani
su ne, Tmani da Allah da ManzanninSa, da mala'iku da LittattafanSa da Ranar Lahira da
kaddara.
146
Suratun Nisa'
ManzanninSa, da Ranar Lahira,
to, lalle ne Ya 6ace, 6ata mai nTsa.
137. Lalle ne wacfanda suka yi
Tmani, sa'an nan kuma sukajcafir-
ta, sa'an nan kuma suka yi Tmani,
sa'an nan kuma suka kafirta, sa'an
nan kuma suka kara kafirci, Allah
bai kasance Yana gafarta musu ba,
kuma ba zai shiryar da su ga hanya
ba.
138. Ka yi wa munafukai bus-
hara da cewa lalle ne suna da azaba
mai racfacfi.
139. Wacfanda suke rikon kafi-
rai masoya, baicin muminai. Shin
suna neman izza ne a wurinsu? To,
lalle ne izza ga Allah take gaba
cfaya.
140. Kuma lalle ne, Ya sassau-
kar (1) muku a cikin Littafi cewa
idan kun ji ayoyin Allah, ana kafir-
ta da su, kuma ana izgili da su, to,
kada ku zauna tare da su, sai sun
shiga cikin wani labari. Lalle ne ku,
a lokacin nan misalinsu kuke. Lalle
ne, Allah Mai tara munafukai da
kafirai ne a cikin Jahannama gaba
cfaya.
141. Wacfanda suke jiran dako
game da ku ; har idan wata nasara
daga Allah ta kasance a gare ku, sai
su ce: "Ashe, ba mu kasance tare
da ku ba?" Kuma idan wani rabo
ya samu ga kafirai sai su ce, "Ashe
ba mu rinjaye ku ba, kuma muka
tsare ku daga muminai?" To, Allah
*jA\ify >yA\f>Jcj> ^jkXxJ C>C-j2l
** * ' \<\ 9 \ '{'It v 9 *s 9 Y if' *''
(1) A cikin Al£ur'ani, Suratul An'am, aya ta 68.
147
4 — Suratun Nisa'
U22)li^-i
ne Yake yin hukunci a tsakaninku
a Ranar Kiyama, kuma Allah ba
zai sanya hanya ba ga kafirai a kan
muminai.
142. Lalle ne munafukai suna
yaudarewa da Allah, alhali kuwa
Shi ne mai yaudararsu; kuma idan
sun tashi zuwa ga salla, sai su tashi
suna masu kasala. Suna nuna wa
mutane, kuma ba su ambatar Allah
sai kacfan.
143. Masu kai-kawo ne a tsa-
kanin wancan; ba zuwa ga wacfan-
nan ba, kuma ba zuwa ga wacfan-
nan ba. Kuma wanda Allah Ya
Batar, to, ba za ka samar masa
wata hanya ba.
144. Ya ku wacfanda suka yi
Tmani! Kada ku riki kafirai ma-
soya, baicin muminai. Shin, kuna
nufin ku sanya wa Allah dafili
bayyananne a kanku?
145. Lalle ne, munafukai suna a
magangara mafi kaskanci daga
wuta. Kuma ba za ka sama musu
mataimaki ba.
146. Sai wadianda suka tuba,
kuma suka gyara, kuma suka nemi
fakuwa ga Allah, kuma suka tsar-
kake addininsu domin Allah, to,
wadannan suna tare da muminai,
kuma Allah zai bai wa muminai
lada mai girma.
147. Mene ne Allah zai amfana
da yi muku azaba idan kun gode,
kuma kun yi Tmani? Allah Ya ka-
sance Mai godiya Masani.
^\^Xzft\tf$£JXj
148
Suratun Nisa'
-i
148. Allah ba Ya son bayya-
nawa da munana daga magana (1)
face ga wanda aka zalunta. Kuma
Allah Ya kasance Mai ji, Masani.
149. Idan kun bayyana alheri,
ko kuwa kuka Boye shi, ko kuwa
kuka yafe laifi daga ciita, to, lalle
ne Allah Ya kasance Mai yafewa,
Mai ikon yi.
150. Lalle ne, wadanda suke ka-
firta da Allah da ManzonSa kuma
suna nufin su rarrabe (2) a tsakanin
Allah da manzanninSa, kuma suna
cewa: "Muna Tmani da sashe,
kuma muna kafirta da sashe".
Kuma suna nufin su riki hanya a
tsakanin wannan.
151. Wadannan su ne kafirai so-
sai, kuma Mun yi tattali, domin
kafirai, azaba mai walakantarwa.
152. Kuma wadanda suka yi
Tmani da Allah da manzanninSa,
kuma ba su rarrabe a tsakanin
kowa ba daga gare su, wadannan
za Mu ba su ijarorinsu, kuma Allah
Ya kasance Mai gafara, Mai jin
kai.
153. Mutanen Littafi suna tarn-
bayar ka ka saukar da wani littafi
daga sama, a kansu, to, lalle ne sun
zj^o&^j^y *y&~y la^'j-w* o\
(1) Magana mummuna. Allah ba Ya son bayyana mugunyar magana, sai dai wanda
akazalunta, yana iya kai kara, kuma yana iya yin addu'a a kan wanda ya zalunce shi. Sa'an
nan ya shiga bayyanawar abin da ake nufi da miyagun maganganu a cikin ayoyin da suke
bin wannan.
(2) Rarrabewa tsakanin Allah da manzanninSa, shi ne mutum ya ce ga misali, "Na
yarda Allah gaskiya ne, zan yi duka abin da yake mai kyau saboda Shi, amma babu ruwana
da wani annabi ko wani manzo", ko kuma ya ce ai duk addinai cfaya ne, ana nufin Allah da
su, sai mutum ya bi abin da ya ga dama. Duka irin wadannan maganganu ba su da kyau,
kafirci ne.
149
4 — Suratun Nisa'
assail - 1
tambayi Musa mafi girma daga
wannan, suka ce: "Ka nuna mana
Allah bayyane." Sai tsawa ta kama
su saboda zaluncinsu, sa'an nan
kuma suka riki maraki (abin bau-
tawa) bayan hujjoji bayyanannu
sun je musu. Sa'an nan Muka yafe
laifi daga wancan. Kuma Mun bai
wa Musa dalTli bayyananne.
154. Kuma Muka daukaka dut-
se sama da su, saboda alkawarinsu,
kuma Muka ce musu: "Ku shiga
kofar kuna masu tawali'u," kuma
Muka ce musu: "Kada ku ketare
haddi a cikin Asabat," kuma Muka
riki alkawari mai kauri daga gare
su.
755. To, saboda warwarewarsu
ga alkawarinsu, da kafirtarsu da
ayoyin Allah, da kisansu ga anna-
bawa, ba da hakki ba, da maganar-
su; "Zukatanmu suna cikin rufi."
A'a, Allah ne Ya yunke a kansu
saboda kafircinsu, saboda haka ba
za su yi imani ba face kadan.
156. Kuma saboda kafircinsu da
fadarsu, a kan Maryama, kiren ka-
rya mai girma.
157. Da fadarsu (1) j "Lalle ne
mu, mun kashe MasThu Tsa dan
>^i^l>^OjJ^*b^J^(^^
\S9S./S S..S S ,'
bis U j dUb £> byL*i c£Q I
ptLk^^
v°x
*> SS "S <'
^j^J^j
(1) Fadarsu ta izgili watau suna cewa: "Mun kashe Tsa dan Maryama wanda yake
da'awar shi Manzon Allah ne." Asalin maganar Yahudu suka karkatar da Dawuda Sarkin
Dimashka, da cewa ga wani mutum nan yana 6ata kasa da akTdar mutane^a Baitil Makdis.
Saboda haka ya bayar da oda ga hakimansa a Baitil Makdis da a kashe Tsa. Sai suka tafi
suka tsare shi a cikin gida shi da sahabbansa, watau Hawariyawa. Tsa ya roki waninsu da
yarda da kisa a kan sakamon Aljanna. Sai karaminsu ya yarda, Allah Ya sanya masa
sifar Tsa, a bayan haka Ya dauke Tsa. Shi kuma aka kashe shi matsayin Tsa. Daga nan,
Yahudu suna zaton sun kashe shi, kuma wadanda suka halarci kissar, suka saba wa juna
wajen sifar Tsa da cewa shi ne Allah, ko cfan Allah, ko cfayan uku, ko manzon Allah, kamar
yadda ya gabata a cikin Bakara.
150
Suratun Nisa'
mmm-i
Maryama Manzon Allah," alhali
kuwa ba su kashe shi ba, kuma ba
su kere shi ba, kuma amma an
kamanta shi ne a gare su. Lalle ne
wacfanda suka saBa wa juna a cikin
sha'aninsa, lalle ne, suna shakka
daga gare shi, ba su da wani ilmi
face bin zato, kuma ba su kashe shi
ba bisa ga yaklni.
158 A 'a, Allah Ya cfauke shi
zuwa gare Shi, kuma Allah Ya ka-
sance Mabuwayi, Mai hikima.
159. Kuma babu kowa daga
Mutanen Littafi (1) , face lalle yana
Imani da shi a gabanin mutuwarsa,
kuma a Ranar Kiyama yana kasan-
cewa mai shaida, a kansu.
160. To, saboda zalunci daga
wacfanda suka tuba (Yahudu)
Muka haramta musu abubuwa
masu dacfi, wacfanda aka halatta su
a gare su, kuma saboda taushe-
warsu daga hanyar Allah da yawa.
161. Da karBarsu ga riba, alhali
kuwa an hana su daga gare ta, da
cin su ga dukiyar mutane da karya.
Kuma Muka yi tattali, domin kafi-
rai, azaba mai racfacfi.
162. Amma tabbatattu (2) a cikin
ilmi daga gare su, da muminai,
suna Tmani da abin da aka saukar
zuwa gare ka, da abin da aka sau-
T 9 \ S ft » * s < •> s* 9 * ' ,\\
^ ^ . * j'
s^^lr^\Jj>- \j*\* sJ^fto^-A**?
-t 4
(1) An ce Mutanen Littafi na zamanin Annabi Isa lalle suna imani da shi gabanin
mutuwarsa cewa shi ba Allah ne ba, kuma ba dan Allah ne ba; kowannensu kamin ya
mutu yana imani da cewa Isa Manzon Allah ne, a lokacin da imanin ba ya amfanin sa Bisa
ga wannan fassara Isa ba zai komo ba. Allah Ya fi sani.
(2) Kabila mai asali tana lalacewa saboda rashin bin addini, har ta zama mafi sharrin
halittar Allah, kamar Yahudu. Kuma a cikin haka wanda ya koma wa gaskiya sai ya koma
ga tsohon asalin, ya £ara cfaukaka da shi, kamar wacfanda suka musulunta daga cikinsu.
151
Suratun Nisa'
wm±-i
kar daga gabaninka, madalla da
masu tsai da salla, da masu bayar
da zakka, da masu Tmani da Allah
da Ranar Lahira. Wacfannan za
Mu ba su lada mai girma.
163. Lalle ne Mu, Mun (1) yi wa-
hayi zuwa gare ka, kamar yadda
Muka yi wahayi zuwa ga Nuhu da
annabawa daga bayansa. Kuma
Mun yi wahayi zuwa ga Ibrahlma
da Isma'Tla da Is'haka da Yakubu
da Jikoki da Tsa da Ayuba da Yu-
nusa da Haruna da Sulaiman.
Kuma Mun bai wa Dawuda
Zabura.
164. Da wasu manzanni, hakl-
ica, Mun ba da labarinsu a gare ka
daga gabani, da wasu manzanni
wacfanda ba Mu ba da labarinsu ba
a gare ka, kuma Allah Ya yi maga-
na da Musa, magana sosai.
165. Manzanni masu bayar da
bushara kuma masu gargacfi domin
kada wata hujja ta kasance ga mu-
tane a kan Allah bayan manzannin.
Kuma Allah ya kasance Mabu-
wayi, Mai hikima.
166. Amma Allah Yana shaida
da abin da Ya saukar zuwa gare ka.
Ya saukar da shi da saninSa. Kuma
mala'iku suna shaida. Kuma Allah
Ya isa Ya zama Shaida.
^3\^y^j^^J^j
J^^j oir*j o-^jij ^y}3 fe^&j
(1) Muhammadu ba shi ne farkon manzanni ba, kuma ba shi ne aka fara yi wa wahayi
ba, ba shi ne aka fara bai wa Littafi ba. Sai dai shi ne karshensu ga dukkan wadannan
abubuwa, kamar yadda bushararsu ta bayyana tun a gabaninsa. Kuma yawan annabawa
da manzanni babu wanda ya san shi sai Allah. Wahayi shi ne ishara ko yanda Allah ke aiko
mala'iki da manzanci zuwa ga wani annabi ko manzonSa.
152
Suratun Nisa'
wMm-t
167. Lalle ne wacfanda suka ka-
firta kuma suka kange (wasu muta-
ne) daga hanyar Allah, haklka, sun
Bace, Bata mai nTsa.
168. Lalle ne wacfanda suka ka-
firta, kuma suka yi zalunci, Allah
bai kasance Yana yi musu gafara
ba, kuma ba Ya shiryar da su ga
hanya.
169. Face hanyar Jahannama,
suna masu dawwama a cikinta har
abada, kuma wannan ya kasance,
ga Allah, mai sauki.
170. Ya ku mutane! Hakika,
Manzo ya je muku da gaskiya daga
Ubangijinku. Saboda haka ku yi
Tmani ya fi zama alheri a gare ku.
Kuma idan kun kafirta, to, Allah
Yana da abin da ke cikin sammai da
kasa. Kuma Allah Ya kasance
Masani, Mai hikima.
171. Ya Mutanen Littafi! Kada
ku zurfafa a cikin addininku. Kuma
kada ku facfa, ga Allah, face gas-
kiya. Abin da aka sani kawai, MasT-
huTsa dan Maryama Manzon Allah
ne, kuma kalmarSa, ya jefa ta zuwa
ga Maryama, kuma ruhi ne^daga
gare Shi. Saboda haka, ku yi Tmani
da Allah da manzanninSa, kuma
kada ku ce, "Uku". Ku hanu (daga
facfin haka) ya fi zama alheri a gare
ku. Abin da aka sani kawai, Allah
Ubangiji ne Guda. TsarkinSa ya
tabbata daga wani abin haifuwa ya
kasance a gare Shi ! Shi ne da abin
da ke cikin sammai da abin da ke
cikin kasa,_kuma Allah Ya isa Ya
zama Wakili.
fnvJL
^4=J^^y^^^J
153
4 — Suratun Nisa'
asaiusi-t
172. Maslhu ba ya kyamar ya
kasance bawa ga Allah, kuma haka
mala'ikun nan makusanta. Kuma
wanda ya yi kyamar bautarSa kuma
yi yi girman kai, to, zai tara su
zuwa gare Shi gaba cfaya.
173. To, amma wacfanda suka yi
imani, kuma suka aikata ayyukan
kwarai, to, za Ya cika musu ijaro-
rinsu, kuma Yana kara musu daga
falalarSa. Kuma amma wadanda
suka yi kyama, kuma suka yi gir-
man kai, to, za Ya yi musu azaba,
azaba mai radacfi, kuma ba su sa-
mun wani masoyi domin kansu,
baicin Allah, kuma ba su samun
mataimaki.
174. Ya ku mutane! HakTka,
wani dalili daga Ubangijinku ya je
muku, kuma Mun saukar da wani
haske bayyananne zuwa gare ku.
175. To, amma wadanda suka yi
Imani da Allah, kuma suka faku a
gare Shi, to, zai shigar da su cikin
wata rahama daga gare Shi da wata
falala, kuma Ya shiryar da su zuwa
gare Shi ga tafarki madaidaici.
176. Suna yi maka fatawa (1) . Ka
ce: "Allah Yana bayyana muku
>>±
,^<*?M -?>.,
4 .^> *^<^' 9 S
} jy
m$x&
'</>** „'
-c- .->
(1) Bayan dogon bayani a kan tauhTdin Allah, da korewar shubhohin Yahudu da
Nasara a cikin addini, domin sai zuciya ta yarda da kadaita Allah sa'an nan za ta ji karfin
riko da karfin cfauka ga hukunce-hukuncen da Allah Yake aza mata. To, ya koma ne ga
abin karantawar surar na tsaron dukiya, ya rufe ta da shi. Ya yi magana a kan mas'alar
'Kalala', watau mutum ya mutu bai bar reshensa ba, ko wani asali sai fukafukai kawai,
watau 'yan'uwa, maza ko mata wadanda ba li'ummai ba. Magana a kan li'ummai kuwa ta
gabata a farkon sura. Ana gabatar da shakTki a kan li'abi, kuma ana gabatar da na kusa a
kan na nesa, mafi kusantar zumunta. Ana kiyasin bai wa 'ya'ya mata biyu, biyu daga uku
na dukiya a kan 'yan'uwa mata, domin su ba a ce fiye da biyu ba. T)iyar tsatso ta ft
'yar'uwa karfin zumunta, kuma ta fi kusanci.
154
4 — Suratun Nisa'
rai^-i
fatawa a cikin 'Kalala', idan mutum
ya halaka, ba shi da reshe kuma
yana da 'yar'uwa, to, tana da rabin
abin da ya bari, kuma shi yana
gadon ta, idan wani reshe bai kasan-
ce ba a gare ta. Sa'an nan idan
('yan'uwa mata) suka kasance biyu,
to, suna da kashi biyu daga kashi
uku din abin da ya bari. Kuma idan
sun kasance, 'yan'uwa, maza da
mata, to, namiji yana da misalin
rabon mata biyu. Allah Yana
bayyanawa a gare ku, domin kada
ku 6ace. Kuma Allah ne, Masani ga
dukan kome.
Tana karantar da cikawar alkawurra da abin da ya rataya da su
wajen rarrabewa a tsakanin halat da haram, da kyautata aicida da
aiki.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L Ya ku warfanda suka yilmani !
Ku cika alkawurra. An halatta
muku dabbobin jin dacfi, face abin
da ake karantawa a kanku, ba kuna
masu halattar da farauta ba alhali
kuwa kuna masu harama. Lalle ne,
Allah Yana hukunta abin da Yake
nufi.
oL-1 ^5-*J yyjl Xy^-^jJ^ \ W^
155
5 — Suratul Ma'ida
?mm-<
2. Ya ku wacfanda suka yi Tmani !
Kada ku halattar da ayyukan iba-
dar Allah game da hajji, kuma da
Wata Mai alfarma, kuma da ha-
daya, kuma da ratayar rakumar
hadaya, kuma da masu nufin TDaki
Mai alfarma, suna neman falala
daga Ubangijinsu da yarda. Kuma
idan kun kwance harama, to, ku yi
farauta. Kuma kada kiyayya da
wasu mutane ta cfauke ku, domin
sun kange ku daga Masallaci Mai
alfarma, ga ku yi zalunci. Kuma ku
taimaki juna a kan aikin kwarai da
takawa. Kuma kada ku taimaki
juna a kan zunubi da zalunci, kuma
ku bi Allah da takawa. Lalle ne
Allah Mai tsananin ukuba ne.
3. An haramta muku mushe da
jini da naman alade da abin da aka
ambaci sunan wanin Allah a gare
shi, da makararriya da jefaffiya da
mai gangarowa da sokakkiya, da
abin da masu dagi suka ci, face abin
da kuka yanka, da abin da aka
yanka a kan gunki (shi ma an ha-
ramta). Kuma kada ku yi rabo da
kibau na caca, wannan fasikanci ne.
A yau wacfanda suka kaflrta sun
yanke kauna daga addininku. Sa-
boda haka kada ku ji tsoronsu,
kuma ku ji tsoroNa. A yau Na
kammala muku addininku, kuma
Na cika ni'imaTa a kanku, kuma
Na yarda da Musulunci ya zama
addini a gare ku. To, wanda aka
sanya wa lalura a cikin yunwa mai
tsanani, ba yana mai karkata zuwa
ga wani zunubi ba, to, lalle ne Allah
Mai gafara ne, Mai jin kai.
y ^^ *o £4*^^- s 9%"**^ » ** ys o % y yy y S
^3j'J^ p+J f-»b -ajlZ-j \ ^Cio C^J>-
><:l~<'\\'><: / ***** *' ~, \ \
s s -" * l* y ^— ^ w -"
' > *^*CT ^ y > "£ i* ' ' ' "* )> s y } l^y
"sit*- 9 < Ti' ~> *<*- " V?-^
y * 9 ^<y > *S5i' t^y *£"T > ?^>*?
r% * *
156
Suratul Ma'ida
KlSUM-
4. Suna tambayar ka cewa mene
ne aka halatta musu? Ka ce: "An
halatta muku abubuwa masu dacfi,
da abin da kukajanar (farauta)
daga masu yin mlki, kuna masu
sakinsu daga hannuwanku, kuna
sanar da su daga abin da Allah Ya
sanar da ku. To, ku ci daga abin da
suka kama saboda ku, kuma ku
ambaci sunan Allah a kansa, kuma
ku bi Allah da takawa. Lalle ne
Allah Mai gaugawar sakamako da
yawa ne.
5. A yau an halatta muku abu-
buwa masu dacfi, kuma abincin wa-
danda aka bai wa Littafi (1) halal ne
a gare ku, kuma abincinku halal ne
a gare su, da mata masu kamun kai
daga muminai da mata 'ya'ya daga
wadanda aka bai wa Littafi a gaba-
ninku, idan kun je musu da sada-
kokinsu, kuna masu yin aure, ba
masu yin zina ba, kuma ba masu
rikon abokai ba. Kuma wanda ya
kafirta dalmani, to, lalle ne aikinsa
ya 6aci, kuma shl, a cikin Lahira,
yana daga masu hasara.
6. Ya ku wadanda suka yi imani !
Idan kun tashi (1) zuwa ga salla, to,
ku wanke fuskokinku da hannu-
\or„
Hl^-
>k
p\ffij^'JZ&J&&<&
-<s S4
^t£^~ O^J^T o^*'*- 1 * *l(*^*ot
s>" fit" \' '
* / >, > »> y «_•>
(1) Watau Yahudawa da Kiristawa.
(2) Abin da ake halatta salla da shi ruwa mai tsarki domin cfauke hadasi karami da
alwala, da hadasi babba da wanka. Idan babu ruwa a yi taimama da wurijia fuskar kasa
wanda bai sake ba da wata sana'ar mutum. Bauli da wadiyyi da gayadi da rihi da shafar jin
dacfi na namiji ga mace ko mace ga namiji, da shafar zakarin kansa, duka suna wajabtar da
alwalla. Fitar maniyyi da haila suna wajabtar da wanka. Maziyyi na wajabtar da wanke
dukkan zakari sa'an nan a yi alwalla. Yankan hannun 6arawo ya nuna iyaka inda ake
shafar farilla na taimama, da sunna, kamar yadda ake yin sauran ayyuka duka a kan
kiyasinsu bisa ga wasu.
157
5 - Suratul Ma'ida
*m$&-o
wanku zuwa ga magincirori, kuma
ku yi shafa ga kanunku, kuma ku
(wanke) kafafunku zuwa idanun
sawu biyu. Kuma idan kun kasance
masu janaba, to, ku yi tsarki, kuma
idan kun kasance majinyata, ko
kuwa a kan tafiya, ko kuwa daya
daga gare ku ya zo daga gayacfi, ko
kuka yi shafayyar juna da mata,
sa'an nan ba ku sami ruwa ba, to,
ku yi nufin wuri (1) mai kyau, sa'an
nan ku yi shafa ga fuskokinku da
hannuwanku daga gare shi. Allah
ba Ya nufi domin Ya sanya wani
kunci a kanku, kuma amma Yana
nufi domin Ya cika ni'imarSa a kan-
ku, tsammaninku kuna godewa.
7. Kuma ku tuna ni'imar Allah a
kanku, da alkawarinku wanda Ya
daure ku da shi, a lokacin da kuka
ce: "Mun ji kuma mun yi da'a."
Kuma ku bi Allah da takawa. Lalle
ne Allah Masani ne ga abin da ke a
cikin zukata.
8. Ya ku wadanda suka yi Tma-
ni! Ku kasance masu tsayin daka
domin Allah, masu shaida da adal-
ci. Kuma kada kiyayya da wasu
mutane ta dauke ku a kan ba za ku
yi adalci ba. Ku yi adalci. ShT ne
mafi kusa ga takawa. Kuma ku bi
Allah da takawa. Lalle Allah Masa-
ni ne ga abin da kuke aikatawa.
9. AllahYa yi wa'adi ga wadan-
da suka yilmani, kuma suka aikata
ayyukan kwarai. Suna da wata ga-
fara da lada mai girma.
$& * dlf^ $J f^*JrJ IjL-ili
>Z < ' *C^<'
> *
5,-zff ><>''
3 jjJL-vaJl ^\J>JL^&\d\^\\j&\j
^. ?'A*/C\>.'
^ ^l^tff^ / y '\>'K'< ?\\>"X<"
(1) Watau ku yi taimama.
158
5 - Suratul Ma'ida
*m$&-o
10. Kuma wadanda suka kafirta,
kuma suka karyata, game da ayo-
yinMu, wadannan su ne abokan
wuta.
11. Ya ku wadanda suka yi una-
ni! Ku tuna ni'imar Allah a kanku,
a lokacin da wasu mutane suka yi
niyyar su shimflda hannuwansu
zuwa gare ku (1) sai Ya kange han-
nuwansu daga gare ku, kuma ku bi
Allah da takawa. Kuma sai mumi-
nai su dogara ga Allah kawai.
12. Kuma lalle Allah Ya riki
alkawarin Bam IsraTla, kuma
Muka ayyana wakilai goma sha
biyu (2) daga gare^su kuma Allah
Ya ce: "Lalle ne NT, Ina tare da ku,
haklka, idan kun tsayar da salla,
kuma kun bayar da zakka, kuma
kun yi Tmani da manzanniNa, kuma
kuka taimake su, kuma kuka bai wa
Allah ranee mai kyau, haklka, Ina
kankare laifukanku daga gare ku,
kuma hakTka, Ina shigar da ku
gidajen Aljanna (wadanda) koramu
suna gudana a karkashinsu, sa'an
nan wanda ya kafirta a bayan wan-
nan daga gare ku, to, lalle ne, ya
6ace daga tsakar hanya.
^Ci^i^fcJJjS l^Sfe^i tj
>-ti'*\r ' ~ >
4W\ J L-3J ^-rf^/^L^ ' -*A* J £ : *-Z**J
SJ^x-jJ\
(1) Wannan kiyayewa ya auku a wurare da yawa tun Musulmi suna da rauni kuma
kafirai suna da £arfi, kuma suna son su kashe Musulmi da Musulunci. Allah Ya tsare su.
Saboda haka yanzu da Musulmi suka yi £arfi da Rarfin Allah, ya wajaba a kansu su gode
wa Allah da takawa. Watau su ri£e alkawarin Allah, su yi abin da Ya aza musu
gwargwadon hali.
(2) An ayyana wakilai goma sha biyu daga £abTlun Bani Isra'Tla goma sha biyu domin
su daukar musu alkawari daga wurin, kuma su tsare^mutanensu ga ganin ba a saba wa
alkawarin ba. An gina addinin Bani Isra'Tla a kan £abTlanci. Saboda haka addininsu ba ya
fita daga da'irarsu.
159
5 - Suratul Ma'ida
%mm-^
13. To, saboda warwarewarsu ga
alkawarinsu Muka la'ane su, kuma
Muka sanya zukatansu Icelcasassu,
suna karkatar da magana daga
wurarenta, kuma suka manta da
wani yanki daga abin da aka tuna-
tar da su da shi, kuma ba za ka
gushe ba kana tsinkayar yaudara
daga gare su face kacfan daga gare
su. To, ka yafe laifi daga gare su,
kuma ka kau da kai. Lalle ne, Allah
Yana son masu kyautatawa.
14. Kuma daga wadanda suka
ce: "Lalle ne mu, Nasara ne," Mun
rilci alkawarinsu, sai suka manta da
wani yanki daga abin da aka tuna-
tar da su da shi, sai Muka shyshuta
adawa da £eta a tsakaninsu har ya
zuwa ga Ranar Kiyama. Kuma Al-
lah zai ba su labari da abin da suka
kasance suna sana'antawa.
75. Ya Mutanen Littafi! Lalle
ne, ManzonMu ya je muku, yana
bayyana muku abu mai yawa daga
abin da kuka kasance kuna 66yewa
daga Littafi, kuma yana rangwame
daga abu mai yawa. Hala£a, wani
haske da wani Littafi mai bayya-
nawa ya je muku daga Allah.
16. Da shi, Allah Yana shiryar da
wanda ya bi yardarSa zuwa ga
hanyoyin aminci, kuma Yana fitar
da su daga duffai zuwa ga haske da
izninSa, kuma Yana shiryar da su
zuwa ga hanya madaidaiciya.
17. Lalle haiailca^ wadanda suka
ce : "Lalle Allah, Shi ne Maslhu dan
Maryama", sun kafirta. Ka ce:
"To, wane ne ke iya mallakar wani
abu daga Allah, idan Ya nufi Ya
•>>*^i »*:m *
£S£\z^\lffi^M^
**i\£
Qp ^- <a. — ^ ^yecil^itl+iJ
160
5 - Suratul Ma'ida
*mm-^
halakar da MasSiu dan Maryama
da uwarsa da wanda yake a cikin
kasa gaba daya?" Kuma Allah ne
da mallakar sammai da kasa da
abin da ke a tsakaninsu, Yana halit-
ta abin da Yake so. Kuma Allah, a
kan dukkan kdme, Mai Ikon yi ne.
18. Kuma Yahudu da Nasara
sun ce: "Mu ne diyan Allah, kuma
masoyanSa." Ka ce: "To, don me
Yake yi muku azaba da zunu-
banku? A'a ku mutane ne daga
wadanda Ya halitta, Yana gafar-
tawa ga wanda Yake so, kuma
Yana azabta wanda Yake so. Kuma
Allah ne da mulkin sammai da kasa
da abin da ke tsakaninsu, kuma
zuwa gare Shi makoma take."
19. Ya Mutanen Littafi! Lalle
ManzonMu ya je muku yana
bayyana muku, a kan lokacin fatara
daga manzanni, domin kada ku ce:
"Wani mai bayar da bushara bai zo
mana ba, kuma haka wani mai
gargadi bai zo ba." To, haklka, mai
bayar da bushara da mai gargadi
sun je muku. Kuma Allah ne, a kan
dukkan kdme, Mai ikon yi.
20. Kuma a lokacin da Musa ya
ce wa mutanensa: "Ya ku mu-
tanena! Ku tuna ni'imar Allah a
kanku; domin Ya sanya annabawa
a cikinku, kuma Ya sanya ku sara-
kuna, kuma Ya ba ku abin da bai
bai wa kowa ba daga talikai.
21. "YamutanenaIKu shiga £a-
sar nan, abar tsarkakewa, wadda
Allah Ya rubuta saboda ku, kuma
kada ku koma da baya, har ku juya
kuna masu hasara."
c^Vl^^J^^s^t
> .r>
4*\j ill* U $£.„ U4^L» J Of S* 'J
"vf?^ .. "S\\ *vi*
pj/v-^rf &\j ££?£ J
&**' 'i'li' »<*'$ ~>Ji\t ^'i.^^i^"i«
%< * y"^ 'k.'" S* *+s fit* ^ *•- **• » »<* *** ^
161
Suratul Ma'ida
*mm~o
22. Suka ce: "Ya Musa! Lalle
ne, a cikinta akwai wasu mutane
masu Jcarfi, kuma lalle ne ba za mu
shige ta ba sai sun flee daga gare ta,
to, idan sun flee daga gare ta, to,
lalle ne mu, masu shiga ne."
23. Wasu mazabiyu (1) daga wa-
danda suke tsoron Allah, Allah Ya
yi ni'ima a kansu, suka ce: "Ku
shiga gare su, daga kofar, domin
idan kuka shige shi, to, lalle ne ku,
masu rinjaya ne, kuma ga Allah sai
ku dogara idan kun kasance
muminai."
24. Suka ce : "Ya Musa ! Lalle ne
mu, ba za mu shige ta ba har abada
matukar sun dawwama a cikinta,
sai ka tafi kai da Ubangijinka do-
min ku yi yaki. Lalle ne mu, muna a
nan zaune."
25. Ya ce: "Ya Ubangijina! Lal-
le ne ni, ba ni mallakar kowa face
kaina da dan'uwana, sai Ka rarrabe
a tsakaninmu da tsakanin mutane
fasikai."
26. (Allah) Ya ce: "To, lalle ne
ita abar haramtawa ce a gare su,
shekara arba'in, suna yin dimuwa a
> .•
^
• ^<: ^>
*i^u- <jiyojl -^2b Aaj-£- L^Jl» J V*
(1) Maza biyu su ne Yusha'u da Kalib daga Nu£aba'u, watau wakilai goma sha biyu
wacfanda Annabi Musa ya aike su domin su yiwo binciken halayen mutanen da suke zaune
a cikin Kudus. Yadda ya faru shi ne, bayan da Allah Ya halaka Fir'auna sai Bani Isra'ila
suka koma Masar, daga nan sai Allah Ya rubuta musu cewa su tashi, su koma Ariha'a a
cikin kasar Sham alhali mazaunanta kuwa Kan'aniyyawa ne. Sai Musa ya gaya musu
cewa, ga Rasar da Allah Ya ba su, su fitar da wacfanda ke a ciki su zauna. Musa ya aika da
mutum goma sha biyu domin su yiwo le£en asiri su zo masa da labari, kada su gaya wa
mutane abin da suka gani domin kada su firgita. Bayan da suka komo, sai suka warware
alkawarin : sai mutum biyu daga cikinsu, Yusha'u da Kalib.
162
Suratul Ma'ida
%$£&%& - o
cikin kasa. (1) Saboda haka kada ka
yi bakin ciki a kan mutane fasikai."
27. Kumakarantamusu (2) laba-
rin diya biyu (3) na Adamu, da gas-
kiya, a lokacin da suka bayar da
baiko, sai aka karba daga dayansu
kuma ba a karba daga dayan ba, ya
ce: "Lalle ne, zan kashe ka."
(TDayan kuma) ya ce: "Abin sani
dai, Allah Yana karba daga masu
takawa ne."
28. "Lalle ne, idan ka shimfufa
hannunka zuwa gare ni domin ka
kashe ni, ban zama mai shimficfa
hannuna zuwa gare ka ba domin in
kashe ka. Lalle ne m, ina tsoron
Allah Ubangijin talikai.
29. "Lalle ne ni, ina nufin ka
koma da zunubina game da zunu-
binka, har ka kasance daga abokan
wuta. Kuma wannan shi ne saka-
makon azzalumai."
30. Sai ransa ya kawatar masa
kashewar cfan'uwansa, sai kuwa ya
kashe shi, sa'an nan ya wayi gari
daga masu hasara.
~*Jl
J*-
<'>*'+ < < '
(1) Wannan shi ne sakamakon sa6awar alkawari, da aka ce wa magewaya kada su
fadi abin da suka gani, saboda da akibar abin, kusan duka sai da suka mutu a cikin halin
dimuwar.
(2) Kuraishawa ko kuwa aPummarka.
(3)^T)iyan Adamu biyu,Kab!la da Habila. Asalin maganar kamar yadda aka ruwaito,
matar Adamu, Hauwa'u, tana haifuwar namiji da mace a kowane ciki, wajen aure sai^ a
shirbata domin babu wasu mutane sai su. Sai Kabila ya ki yarda^a bai wa Habila
'yar'uwarsa, har Adam ya sanya su yin baiko da abin sana'arsu. Kabila manomi ne, ya
bayar da munana daga kayan nomansa, shi kuma Habila ya bayar da rago mai kyau domin
sana'arsa kiwo ne. Sai wuta ta sauko ta cfauki ragon Habila, alamar karba. Wannan kuwa
ya cfauki Kabila ga tunanin kashe shi. Laifi guda yana sabbaba wasa laifuka masu yawa.
163
Suratul Ma'ida
*mm~*
31. Sai Allah Ya aiki wani
hankaka, yana tono a cikin kasa
domin ya nuna masa yadda zai
turbude gawar dan'uwansa. Ya ce:
"Kaitona! Na kasa in kasance ka-
mar wannan hankaka domin in tur-
bude gawar dan'uwana?" Sai ya
wayi gari daga masu nadama.
32. Daga sababin wannan, (1)
Muka rubuta a kan BanT Isra'Tla
cewa, lalle ne wanda ya kashe rai ba
da wani rai ba, ko 6arna a cikin
kasa, to kamar ya kashe mutane
duka ne, kuma wanda ya raya rai,
to, kamar ya rayar da mutane ne
gaba daya. Kuma lalle ne, haklka,
ManzanninMu sun je musu da huj-
joji bayyanannu, sa'an nan kuma
lalle ne, masu yawa daga gare su, a
bayan wannan, haklka, masu 6arna
ne a cikin kasa.
33. Abin sani kawai, saka-
makon (2) wadanda suke yakin Al-
lah da ManzonSa, kuma suna aiki a
cikin kasa domin 6arna, a kashe su,
ko kuwa a kere su, ko kuwa a
kakkatse hannuwansu da kafa-
funsu daga saBani, ko kuwa a kore
su daga kasa. Wannan gare su wula-
kanci ne a cikin rayuwar duniya,
kuma a Lahira suna da wata azaba
mai girma.
>^ <\ A»v • >^ ~* set ^ i ' "<
afS* \ c|^v— 3j\ ^-Ju jjjo L~*jb JLSb ,>•
sdy>jj -oil ojj>jl^o;all »3;>^u^
(1) Aikata Raramin laifi yana sabbaba babban laifi har barna mai yawa ta watsu a
cikin Rasa.
(2) Muharib shi ne dan fashi mai tare hanya da makamai. Ana yi masa dayan abin da
aka ga ya dace da shi. Wanda aka yi wa "Salbu" sai kuma a kashe shi. Amfanin Salbu shi ne
a gan shi, domin hankalin mutane ya natsu. Korewa yanzu sai ta koma ga tfauri har ya
mutu ko ya tuba.
164
Suratul Ma'ida
*mm->
34. Face fa wacfanda suka tuba
tun a gabanin ku sami iko a kansu,
to, ku sani cewa lalle ne, Allah Mai
gafara ne, Mai jin kai.
35. Ya ku wacfanda suka yi ima-
ni ! Ku bi Allah da takawa, kuma ku
nemi tsari zuwa gare Shi, kuma ku
yi jihadi (1) a cikin hanyarSa,
tsammaninku, za ku ci nasara.
36. Lalle ne wacfanda suka kafir-
ta, lalle da suna da abin da ke a cikin
kasa gaba cfaya da misalinsa tare da
shi, domin su yi fansa da shi daga
azabar Ranar Kiyama, ba a kar6ar-
sa daga gare su, kuma suna da
azaba mai racfadi.
37. Suna nufin su fita ne daga
wuta, kuma ba su zama masu fita
daga gare ta ba, kuma suna da
azaba zaunanniya.
38. Kuma 6arawo da 6arauniya
sai ku yanke hannuwansu, bisa
sakamako ga abin da suka tsirfanta,
a kan azaba daga Allah. Kuma
Allah Mabuwayi ne, Mai hikima.
39. To, wanda ya tuba a bayan
zaluncinsa, kuma ya gyara (halin-
sa), to, lalle ne Allah Yana kar6ar
tubarsa. Lalle Allah Mai gafara ne,
Mai jin kai.
*Li*'*\
f \ > >z
w^>£r^\j**&^&*<^&
fi <>» >< S*i
nj *f*jjy&*& b\£& >~>y>t
(1) Wasila ita ce dukkan aikin ibada wanda zai kusantar da mutum zuwa ga
Ubangijinsa, amma da sharadin an gina shi a kan takawa. Kuma takawa ita ce bin Allah
kamar yadda Ya yi umurni a bi Shi, ta hanyar manzonSa kawai. Jihadi yana cikin takawa
amma Ya koma ambatonsa ne domin muhimmancinsa. Shi kuma iri biyu ne: karami,
watau yakin abokan gaba na bayyane, da babba , shi ne yakin abokan gaba na boye , watau
rai da Shaicfan. Wanda makiyinsa na bayyane ya kashe shi ya mutu ShahTdi, wanda
makiyinsa na 6oye ya kashe shi ya mutu fasiki ko kafiri watau shakiyyi.
165
Suratul Ma'ida
&&&%&-<>
40. Shin, ba ka sani ba cewa lalle
ne, Allah Shi ne da mulkin sammai
da kasa, Yana azabtar da wanda
Yake so, kuma Yana yin gafara ga
wanda yake so, kuma Allah, a duk-
kan kome, Mai Tkon yi ne?
41. Ya kai Manzo! Kada wa-
danda suke tseren gaugawa a cikin
kafirci su Bata maka rai,^daga wa-
danda suka ce: "Mun yiTmani" da
bakunansu, alhali zukatansu ba su
yi Tmanin ba, kuma daga wadanda
suka tuba (watau Yahudu) masu
yawan saurare ga wasu mutane na
dabam wadanda ba su je maka ba,
suna karkatar da zance daga bayan
wurarensa, suna cewa: "Idan an ba
ku wannan, to, ku^karba, kuma
idan ba a ba ku shT ba, to, ku yi
sauna." Kuma wanda Allah Ya yi
nufin fitinarsa, to, ba za ka mallaka
masa kome ba daga Allah. Wadan-
nan ne wadanda Allah bai yi nufin
Ya tsarkake zukatansu ba. Suna da
kunya a cikin duniya, kuma suna da
wata azaba mai girma a cikin
Lahira.
42. Masu yawan saurare (1) ga
karya ne, masu yawan ci ga haram,
to, idan sun zo maka, sai ka yi
hukunci a tsakaninsu, ko ka bijira
daga gare su. Kuma idan ka bijira
daga gare su, to, ba za su cuce ka da
.g^^Jj^^vfi^
(«' '** *" {?'
v& v d^J p-f**** u^>> J J*-gf \
a >' *
"t
&\o£jjfe*$~£^y A <±^h$j&^
' >< *"f x > '**
^J*><& ^-L\*»> ^j<CJL-3 4tt \2jJ>^a j
t^*"* ft '^ ^ *>" " '- • \ "
( 1 ) An bai wa Annabi zabi da ya yi hukunci ko kada ya yi, a tsakanin kafirai biyu,
idan sun yarda da hukuncinsa. Wannan dama tana aiki a kotunan Musulmi ga abin da ya
shafi hakkoki kawai, amma ga 'jara'im' a kasar Musulmi tilas sai a bi shari'ar Musulunci
domin tsaron aminci, sai dai kafiri yana iya shan giyarsa, ga misali a boye, banda a cikin
jama'a. Haka kuma laifuka na al'adunsu kuma Musulmi ba za su ta6a masu su ba, sai su yi
hukuncinsu a tsakaninsu.
166
5 — Suratul Ma'ida
%M%&-*
kome ba, kuma idan ka yi hukunci,
to, sai ka hukunta a tsakaninsu da
adalci. Lalle ne, Allah Yana son
masu adalci.
43. Kuma yaya suke gabatar da
kai ga hukunci, alhali a wurinsu
akwai Attaura, a cikinta akwai hu-
kuncin Allah, sa'an nan kuma suna
karkacewa a bayan wannan? Wa-
dannan ba muminai ba ne!
44. Lalle ne Mu, Mun saukar da
Attaura, a cikinta akwai shiriya da
haske, annabawa wacfanda suke
sun sallama, suna yin hukunci da ita
ga wadanda suka tuba (Yahudu), da
malaman tarbiyya, da manyan ma-
lamai ga abin da aka neme su da su
tsare daga Littafin Allah, kuma sun
kasance, a kansa, masu ba da shai-
da. To, kada ku ji tsoron mutane,
kuma ku ji tsoroNa, kuma kada ku
sayi 'yan kucfi kadan da ayoyiNa.
Wanda bai yi hukunci ba da abin da
Allah Ya saukar, to, wadannan su
ne kafirai.
45. Kuma Mun rubuta a kansu,
a cikinta cewa, lalle (ana kashe) rai
saboda rai, kuma (ana cfebe) ido
saboda ido, kuma (ana katse) hand
saboda hanci, kuma kunne saboda
kunne, kuma hakori saboda hakori,
kuma a raunuka a yi sakayya. To,
wanda ya yi sadaka da shi, to, shi
kaffara ce a gare shi. Kuma wanda
bai yi hukunci ba da abin da Allah
Ya saukar, to, wadannan su ne
azzalumai.
46. Kuma Muka biyar a kan
gurabansu da Tsa dan Maryama,
>\ r ^
(>j\jL£=zy$* ^ s^-J X^aJ {j+-3 <j0 L*a3
167
5 — Suratul Ma'ida
m&m-
yana mai gaskatawa ga abin da
yake a gaba gare shi daga Attaura,
kuma Muka ba shi Injila, a cikinsa
akwai shiriya da haske, yana mai
gaskatawa ga abin da yake a gaba
gare shi daga Attaura, kuma shi
shiriya ne da wa'azi ga masu taka-
wa.
47. Kuma sai mutanen Injila su
yi hukunci da abin da Allah ya
saukar a cikinta. Kuma wanda bai
yi hukunci ba da abin da Allah ya
saukar, to, wacfannan su ne fasikai.
48. Kuma Mun saukar da Littafi
zuwa gare ka da gaskiya, yana mai
gaskatawa ga abin da yake a gaba
gare shi daga Littafi (Taurata da
Injila), kuma mai halartawa a kan-
sa. Sai ka yi hukunci a tsakaninsu
da abin da Allah Ya saukar, kuma
kada ka bibiyi son zuciyoyinsu daga
abin da ya zo maka daga gaskiya (1) .
Ga kowanne daga gare ku Mun
sanya sharl'a da hanya (ta bin ta).
Kuma da Allah Ya so, da Ya sanya
ku aPumma guda, kuma amma do-
min Ya jarraba ku a cikin abin da
Ya ba ku. Sai ku yi tsere ga ayyukan
alheri. Zuwa ga Allah makomarku
take gaba cfaya. Sa'an nan Ya ba ku
labari ga abin da kuka kasance
kuna sa6awa a cikinsa.
49. Kuma ka yi hukunci a tsaka-
ninsu da abin da Allah Ya saukar,
kuma kada ka bibiyi son zuci-
yoyinsu, kuma ka yi saunar su fitine
^* llKS Jl^£ &%\ C^$Jt iU i^U^j
y ^* ^ y
•*" y 9 ^y^ ** 9 yy *^l/ ^~* y 9,t y ** '"' 'y
>rs " <* s G- y*y* "*<*
jy^lAJo'^-Aj-^'j
(1) Allah. Kuma Mun bai wa kowa shari'o'insa da dokokinsa, sa'an nan kuma da
hanyar da ake bi wajen zartar da shari'ar.
168
5 — Suratul Ma'ida
«^- (
ka daga sashen abin da Allah Ya
saukar zuwa gare ka. To, idan sun
juya baya, to, ka sani cewa, kawai
Allah yana nufin Ya same su da
masTfa ne saboda sashen zunu-
bansu. Kuma lalle^ne, masu yawa
daga mutane, hakTka, fasikai ne.
50. Shin, hukuncin Jahiliyya (1)
suke nema? Kuma wane ne mafi
kyau ga hukunci daga Allah saboda
mutane wacfanda suke yin yakmi
(tabbataccen Tmani)?
51. Ya ku wacfanda suka yi Tma-
ni ! Kada ku riki Yahudu da Nasara
majibinta. Sashensu majibinci ne ga
sashe. Kuma wanda ya jibince su
daga gare ku, to, lalle ne shi, yana
daga gare su. Lalle Allah ba Ya
shiryar da mutane azzalumai.
52. Sai ka ga wadanda a cikin
zukatansu akwai cuta, suna tseren
gaugawa a cikinsu, suna cewa:
"Muna tsoron kada wata maslfa ta
same mu." To, akwai tsammanin
Allah Ya zo da bucfi, ko kuwa wani
umurni daga wurinSa, har su wayi
gari a kan abin da suka boye a cikin
zukatansu, suna masu nadama.
53. Kuma wadanda suka yi Tma-
ni suna cewa : "Shin, wadannan ne
wadanda suka yi rantsuwa da Allah
iyakar rantsuwoyinsu, cewa su, lalle
suna tare da ku?" Ayyukansu sun
bad, saboda haka suka wayi gari
suna masu hasara.
< *-*
^ ojtez^yl
\>'S' &f'*^
^ t ' r. ^ > s
(1) Hukuncin Jahiliyya shi ne wanda ake ginawa a kan son rai da al'ada da kuma
ra'ayin azzalumai, ba ya da wani asali daga wani littafi na Allah.
169
5 - Suratul Ma'ida
"MM^ - o
54. Ya ku wadanda suka yilma-
ni ! Wanda ya yi ridda daga gare ku
daga addininsa, to, Allah zai zo da
wasu mutane, Yana son su kuma
suna son Sa, masu tawalu'i a kan
muminai, masu izza a kan kafirai.
Suna yin jihadi a cikin hanyar Al-
lah, kuma ba su tsoron zargin wani
mai zargi. Waccan falalar Allah ce,
Yana bayar da ita ga wanda Yake
so. Kuma Allah Mayalwaci ne, Mai
ilmi.
55. Abin sani kawai, majibin-
cinku Allah ne da^ ManzonSa, da
wadanda suka yi imani, wadanda
suke suna tsayar da salla, kuma
suna bayar da zakka kuma suna
ruku'i.
56. Kuma wanda ya jibinci Allah
da ManzonSa da wadanda suka yi
Imani, to, kungiyar Allah su ne
masu rinjaya.
57. Yaku wadanda suka yi Ima-
ni ! Kada ku riki wadanda suka riki
addininku bisa izgili da wasa, daga
wadanda aka bai wa Littafi daga
gabaninku da kafirai, masoya.
Kuma ku bi Allah da takawa idan
kun kasance muminai.
58. Kuma idan kuka yi kira
zuwa ga salla, sai su rike ta bisa
izgili da wasa. Wannan domin lalle
ne su, mutane ne (wadanda) ba su
hankalta.
59. Ka ce : " Ya Mutanen Littafi !
Shin, kuna ganin wani laifi daga
jare mu? Face dai domin mun yi
imani da Allah da abin da aka
saukar zuwa gare mu da abin da aka
^'.^s
y\' >t *"'*&
' <'S>> ' >
~* m 'SS.'
^l4>iQjljj^Uja^\3Ji^\Jj^blS|j
^^'£SV&$csJf£M&Kj
170
Suratul Ma'ida
tmm-o
saukar daga gabani, kuma domin
mafi yawanku fasikai ne."
60. Ka ce: "Shin, in gaya muku
mafi sharri daga wannan, domin
sakamako (1) daga wurin Allah?
Wanda Allah Ya la'ane shi kuma Ya
yi fushi da shi, kuma Ya sanya daga
gare su birai da aladai, kuma ya
bauta wa T)aguta. Wadannan ne
mafiya sharrin wuri, kuma mafiya
Bata daga tsakar hanya."
61. Kuma idan sun zo muku sai
su ce : "Mun yilmani. " Alhali kuwa
hakika, sun shigo da kafirci, kuma
su lalle ne, sun fita da shi, kuma
Allah ne Mafi sani ga abin da suka
kasance suna Boyewa.
62. Kuma kana ganin masu
yawa daga gare su, suna tseren
gaugawa a cikin zunubi da zalunci
da cinsu ga haram. Hakika, tir da
abin da suka kasance suna aika-
tawa.
63. Don me Malaman Tar-
biyya (2) da manyan malamai (na
Yahudu) ba su hana su daga fadar-
su ga zunubi da cinsu ga haram
ba? Hakika, tir daga abin da suka
kasance suna sana'antawa.
64. Kuma Yahudu suka ce:
"Hannun Allah abin yi wa kuku-
mi ne (3) ." An sanya hannuwansu a
J J l^J-b Oji) \^-^ Jjfci-J *~&^ ««J?CJ4JU1
>J3
-'K
(1) Kuna son in gaya muku ba domin ku ba ni wani sakamako ba, sai domin Allah Ya
saka mini. Mutanen da aka juyar suka koma birai da aladai kuma suka bauta wa wanin
Allah, su ne mafi sharrin mutane.
(2) Don me malamansu ba su yin wa'azi ga jahilansu? Tir da rashin wa'azi!
(3) Suna nufin wai Allah marowaci ne.
171
5 - Suratul Ma'ida
mm~>
cikin kukumi ! Kuma an la'ane su
saboda abin da suka farfa. A'a,
hannuwanSa biyu shimfirfarfrfu ne,
Yana ciyarwa yadda Yake so.
Kuma lalle ne abin da aka saukar
zuwa gare ka yana kara wa masu
yawa daga gare su, girman kai da
kafirci. Kuma Mun jefa a tsaka-
ninsu, kiyayya da keta, zuwa Ranar
Kiyama, ko da yaushe suka hura
wata wuta domin yaki, sai Allah Ya
bice ta. Suna aiki a cikin kasa domin
6arna, alhali kuwa Allah ba Ya son
masu fasadi.
65. Kuma da dai lalle Mutanen
Littafi sun yj Imani, kuma sun yi
takawa, hakika, da Mun kankare
miyagun ayyukansu daga gare su,
kuma da Mun shigar da su gidajen
Aljannar Ni'ima.
66. Kuma da dai lalle su, sun
tsayar da Attaura da Injila da abin
da aka saukar zuwa gare su daga
Ubangijinsu, hakika, da sun ci daga
bisansu da kuma daga karkashin
kafafunsu. Daga gare su akwai
wata al'umma mai tsakaitawa,
kuma masu yawa daga gare su, abin
da suke aikatawa ya munana.
67. Ya kai Manzo ! Ka iyar da (1 }
abin da aka saukar zuwa gare ka
daga Ubangijinka. Kuma idan ba
ka aikata ba, to, ba ka iyar da
manzancinSa ba ke nan. Kuma Al-
lah Yana tsare ka daga mutane.
Lalle ne, Allah ba Ya shiryar da
mutane kafirai.
*s < Y^ "■Si's" ' ' s **})>'*' ' "st' * 9 ^s
»t r? • '*'*<"
£*£i*&3 bL-*3«jfe/ir ^OjaI^j
r'^~*-1
^W^YMf^JPW'0;
(1) Wannan aya ta kafirta dukan wanda ya ce ko ya yarda da cewa Annabi ya 66ye
wani abu daga Allah, ko kuma ya ke6e wasu mutane da wani abu daga manzancinsa daga
Allah.
172
Suratul Ma'ida
iSS31j&-.
68. Ka ce: "Ya ku Mutanen Lit-
tafi ! Ba ku zama a kan kome ba, sai
kun tsayar da Attaura da Injila da
abin da aka saukar zuwa gare ku
daga Ubangijinku." Kuma lalle ne,
abin da aka saukar zuwa gare ka
daga Ubangijinka, yana kara wa
masu yawa daga gare su girman kai
da kafirci. To, kada ka yi bakin ciki
a kan mutane kafirai.
69. Lalle ne, wadanda suka yi
Tmani da wadanda suka tuba (Ya-
hudu) da Karkatattu da Nasara,
wanda ya yi imani da Allah da
Ranar Lahira, kuma ya aikata aiki
na kwarai, to, babu tsoro a kansu,
kuma ba su zamo suna bakin ciki
ba.
70. Lalle ne hakTka, Mun riki
alkawarin Bani Isra'Tla, kuma Mun
aiki manzanni zuwa gare su, ko da
yaushe wani manzo ya je musu da
abin da rayukansu ba su so, wani
6angare sun karyata, kuma wani
6angare suna kashewa.
71. Kuma suka yi zaton cewa
wata fitina ba za ta kasance ba, sai
suka makanta, kuma suka kurunta,
sa'an nan Allah Ya kar6i tuba a
gare su, sa'an nan suka makanta
kuma suka kurunta masu yawa
daga gare su, alhali Allah Mai gani
ne ga abin da suke aikatawa.
72. Lalle ne, hakTka, wadanda (1)
suka ce: "Lalle ne Allah, ShT ne
> <,
< " . £:t *'XX" *X '\' *' \ ' '*kX'
j^>\ y ^ ^ y
'•s".\>'''\
l^L-^j \y*-£' (*^j> jAc> 4jil^_ r ^) t
(l) Su ne Ya'aJcubiyya. Bayan bayani a kan aibobin Yahudu sai Ya shiga bayani a
kan aibobin Nasara.
173
5 - Suratul Ma'ida
*mm>-*
Maslhu, cfan Maryama," sun kafir-
ta. Alhali kuwa MasThu ya ce: "Ya
BanT Isra'Ila! Ku bauta wa Allah
Ubangijina, kuma Ubangijinku."
Lalle ne shi, wanda ya yi shirki da
Allah, to, lalle ne, Allah Ya haram-
ta masa Aljanna. Kuma babu wasu
mataimaka ga azzalumai.
73. Lalle ne, haklka, wacfanda
suka ce: "Allah na ukun uku ne,"
sun kafirta, kuma babu wani abin
bautawa face Ubangiji Guda.
Kuma idan ba su hanu daga abin da
suke fatfa ba, haiaka, wata azaba
mai radadi tana shafar wadanda
suka kafirta daga gare su.
74. Shin fa, ba su tuba zuwa ga
Allah, kuma su neme Shi gafara,
alhali kuwa Allah Mai gafara ne,
Mai jin kai?
75. MasThu dan Maryama bai
zama ba face Manzo ne kawai,
haklka, manzanni sun shige daga
gabaninsa, kuma uwarsa siddika (1)
ce. Sun kasance suna cin abinci. Ka
duba yadda Muke bayyana musu
ayoyi. Sa'an nan kuma ka duba
yadda ake karkatar da su.
76. Ka ce: "Ashe, kuna bauta
wa, baicin Allah, abin da ba ya
mallakar wata cuta saboda ku,
kuma haka wani amfani (2) , alhali
kuwa Allah Shi ne Mai ji, Masani?"
A*
:-A.f.f .1 X
G
~y J*
> *•> < »^
(1) SiddTk shi ne mai yawan gaskatawar annabawa, shi ne mafi cfaukakar daraja a
waliyyan Allah, kamar Abubakar SiddTk Sahabin Annabi.
(2) Idan bauta wa Tsa. Annabin Allah, ya zama kafirci, bauta wa waliyyi ya zama
hiyaka. Kuma idan Tsa bai mallaki kome ba, to, waliyyi hiyaku.
174
5 - Suratul Ma'ida
JKE2I!j»-o
77. Kace:"YakuMutanenLit-
tafi! Kada ku zurfafa a cikin
addininku, abin da ba gaskiya ba,
kuma kada ku blbiyi son zuciyoyin
wacfansu mutane wacfanda suka riga
suka 6ace a gabani, kuma suka
Batar da wasu masu yawa, kuma
suka 6ace daga tsakar hanya."
78. An la'ani wacfanda suka ka-
firta daga Bam IsraTla a kan har-
shen Dawuda da Tsa dan Maryama.
Wannan kuwa saboda saBawar da
suka yi ne, kuma sun kasance suna
ta'addi {1) .
79. Sun kasance ba suhanajuna
daga abin £i, wanda suka aikata.
HakTka, abin da suka kasance suna
aikatawa ya munana.
80. Kana ganin masu yawa daga
gare su, suna jiBintar wacfanda suka
kafirta. Haiuka, tir da abin da
rayukansu suka gabatar saboda su,
watau Allah Ya yi fushi da su , kuma
a cikin azaba su masu dawwama ne.
81. Kuma da sun kasance suna
Tmani da Allah da Annabi da abin
da aka saukar zuwa gare shi, da ba
su rike su masoya ba. Kuma amma
masu yawa daga gare su, fasikai ne.
82. Lalle ne kana samun mafiya
tsananin mutane a adawa ga wa-
cfanda suka yi Tmani, Yahudu ne da
wacfanda suka yi shirki. Kuma lalle
ne kana samun mafiya kusantarsu a
soyayya ga wacfanda suka yi Tmani
su ne wacfanda suka ce: "Lalle mu
."t \><
di*Z^x*}Sj^^CA
• m y ~<*
1 <>^<i^-> **)\* $~4fe
.*£*
'I'*! >' ' 'St
1 ^ . J6\JLjI CaaJ3^JSJ \jjd=^Z£j&\
Jp j dJ jl (*-*> Ju<il U^Ji — y L.j
(1) Ta'addi shi ne £etare iyaka da nufin zalunci.
175
5 - Suratul Ma'ida
*mm-<>
ne Nasara/' Wancan kuwa saboda
akwai KissTsuna da ruhubanawa (1)
daga cikinsu. Kuma lalle ne su, ba
su yin girman kai.
83. Kuma idan suka ji abin da
aka saukar zuwa ga Manzo, kana
ganin idanunsu suna zubar da ha-
waye, saboda abin da suka sani
daga gaskiya, suna jcewa: "Ya
Ubangijinmu ! Mun yilmani, sai ka
rubuta mu tare da masu shaida.
84. "Kuma mene ne yake gare
mu, ba za mu yilmani da Allah ba,
da kuma abin da ya zo mana daga
gaskiya, kuma muna gurin Ubangi-
jinmu Ya shigar da mu tare da
mutane salihai?"
85. Saboda haka, Allah Ya saka
musu, domin abin da suka fada, da
gidajen Aljanna (wadanda) koramu
suna gudana a karkashinsu, suna
madawwama a cikinsu, kuma wan-
nan ne sakamakon masu kyauta-
tawa.
86. Kuma wadanda suka kafirta,
kuma suka karyata game da
ayoyinMu, wadancan ne abokan
wuta.
87. Ya ku wadanda suka yi ima-
ni! Kada ku haramta abubuwa
masu dadi da Allah Ya halatta
muku, kuma kada ku ketare haddi.
S < 9 SZi^S
A > ' + y ~+s ' t '
IOC
-Jill
ii^j j^ts^iL y.j^ji^&tfji \j
i£&
(1) FCissisi shi ne fimanin kiristawa, ruhubananci shT ne mutum ya tsabbace daga
mutane domin ibada, kuma ba ya yin aure. Baruhubane guda, ruhubanawa jam'i.
176
5 — Suratul Ma'ida
xmm>-*
Lalle ne, Allah ba Ya son masu
ketare haddi. (1)
88. Kuma ku ci daga abin da
Allah Ya arzuta ku, halat mai dadi,
kuma ku bi Allah da takawa, Wan-
da yake ku, masu Tmani ne da Shi.
89. Allah ba Ya kama ku saboda
yasassa (2) a cikin rantsuwoyinku,
kuma amma Yana kama ku da abin
da kuka kudurta rantsuwoyi (a kan-
sa). To, kaffararsa ita ce ciyar da
misklni goma daga matsakaicin
abin da kuke ciyar da iyalanku, ko
kuwa tufatar da su, ko kuwa 'yanta-
war wuya. Sa'an nan wanda bai
samu ba, sai azumin kwana uku.
Wannan ne kaffarar rantsu-
woyinku, idan kun rantse. Kuma ku
kiyaye rantsuwoyinku. Kamar
wannan ne Allah Yake bayyana
muku ayoyinSa, tsammaninku
kuna godewa.
90. Ya ku wadanda suka yi Tma-
ni ! Abin sani kawai, giya da caca da
off
(pC£Al£jt
(1) Haramta abin da Allah Ya halatta ko kuwa halatta abin da Allah Ya haramta
kafirci ne, domin wanda ya ketare haddi da kansa, ya yi da'awar Ilahiyya ko annabci, haka
wanda ya bi shi a kan wannan abin, ya yi shirki da Allah, domin ya sami wani mai wadansu
dokoki wanda ba Allah ba, kuma ya bi shi a kansu, ko kuwa ya bi wani mai da'awar
annabci, bayan Alkur'ani ya ce an rufe annabci daga Annabi Muhammadu, tsira da aminci
su tabbata a gare shi.
(2) Rantsuwa alkawari ce da sunan Allah, cewa mai rantsuwar zai aikata, ko kuwa ba
zai aikata ba, ko kuwa a kan tabbatar wani abu a kan sifar da ya ambata, ko kuwa
koruwarsa daga wannan sifar. Wanda ya yi rantsuwa sa'an nan ya yi hinsi, to, sai ya yi
kaffara, kamar yadda aka ambata a cikin ayar. Sai fa idan ta zama yasassar rantsuwa ce,
wadda mutum ya yi a kan saninsa, sa'an nan sanin nan ya warware, saboda bayyanar wani
abu. Wasu sun ce ita ce rantsuwar da ake yi a cikin magana ba da nufi ba, kamar a'a
wallahi, ko T, wallahi. Kuma akwai rantsuwar gamusa a kan karya. Ita ma babu kafiara
saboda ita, sai tuba zuwa ga Allah da istigfari, kuma tana sanya tsiya.
177
5 — Suratul Ma'ida
mm-
refu da kiban £uri'a, (1) kazanta ne
daga aikin Shaicfan, sai ku nTsance
shi, wa la'alla ku ci nasara.
91. Abin sani kawai, Shaidan
yana nufin ya aukar da adawa da
keta a tsakaninku, a cikin giya da
caca, kuma ya kange ku daga amba-
ton Allah, kuma daga sallah. To,
shin, ku masu hanuwa ne?
92. Ku yi da'a ga Allah, kuma ku
yi da'a ga Manzo, kuma ku kiyaye.
To, idan kun juya, to, ku sani abin
da kawai yake kan ManzonMu,
iyarwa bayyananniya.
93. Babu laifi a kan wadanda
suka yi Tmani, kuma suka aikata
ayyukan kwarai, a cikin abin da
suka ci, idan sun yi takawa kuma
suka yi Tmani, kuma suka aikata
ayyukan kwarai, sa'an nan suka yi
takawa kuma suka yi Tmani, sa'an
nan kuma suka yi takawa kuma
suka kyautata. (2) Kuma Allah Yana
son masu kyautatawa.
94. Ya ku wacfanda suka yi Tma-
ni ! Lalle ne, Allah zai jarraba ku da
wani abu daga farauta, hannu-
wanku da masunku suna samun sa,
domin Allah Ya san wanda yake
tsoron Sa a fake. To, wanda ya yi
ta'addi a bayan wannan, to, yana da
azaba mai ratfadi.
j£U •jX^lt JllaliJ \^ot J^rJ^J
fit < > \ r -
(1) Yin caca da shan giya da refu da kiban kuri'a, aikatar da su warware alkawari ne
na hana cin dukiyar mutane da badili (karya), da tsaron salla da Allah Ya yi umurni a
tsare; watau rashin takawa ke nan.
(2) Ya yi takararin takawa sau uku ga wanda ya tuba da shan giya da caca domin ya
nuna nauyinsu. Wanda ya sha giya ko ya yi caca, ya keta haddin Allah da alfarmar mutane
da darajar kansa. Sai ya yi takawa daga wadannan zai iya rabuwa da su. Tsare su yana
cikin cika alkawari a tsakanin mutum da Allah da kuma mutane da ransa.
178
Suratul Ma'ida
*m$&-o
95. Yaku wacfandasukayiTma-
ni! Kada ku kashe farauta alhali
kuna masu harama (1) . Kuma wan-
da ya kashe shi daga gare ku, yana
mai ganganci, sai sakamako, misa-
lin abin da ya kashe, daga dabbobin
ni'ima, ma'abuta adalci biyu daga
cikinku suna yin hukunci da shi. Ya
zama hadaya mai isa ga Ka'aba, ko
kuwa kaffara da abincin miskmai,
ko kuwa a matsayinsa ya yi azumi,
domin ya dandani masifar al'ama-
rinsa. Allah Ya yafe laifi daga abin
da ya gabata. Kuma wanda ya
koma, to, Allah zai yi azabar ramu-
wa daga gare shi, kuma Allah Ma-
buwayi ne, ma'abucin azabar
ramuwa.
96. An halatta muku farautar
ruwa da abincinsa, domin jin dacfi a
gare ku, kuma domin matafiya.
Kuma an haramta farautar tudu a
kanku, matukar kun dawwama
masu harama. Kuma ku bi Allah da
takawa, Wanda yake zuwa gare Shi
ne ake tara ku.
97. Allah Ya sanya Ka'aba,
TDaki Tsararre, ma'aunin addini ga
mutane, kuma Ya sanya Wata Mai
alfarma da hadaya da ratayoyin
hadaya, domin ku sani cewa lalle
Allah Ya san abin da yake a cikin
M j\2&\y*j^wj^£\^r*.$
6p ^Jy^^^^LS^^y^j
(1 ) Barin farauta a cikin Harami yana a cikin cikawa da alkawari. Wanda ya sa6a, sai
ya yi fansa da biyan misalin abin da ya kashe daga dabbobin gida na jin dacfi ; watau a biya
barewa da akuya ko tunkiya. Amma kuma sai an sami mutum biyu adalai sun hukunta
abin da mutum zai bayar din. Idan ba ya da dabbar, sai ya biya lumarta da abinci, ya bai
wa kowane misklni daya mudu guda. Idan ba ya iyawa kuwa, sai ya yi azumi, kowane
mudu guda kwana daya, guntun mudu a biya shi da cikakken kwana.
179
Suratul Ma'ida
vmm-*
sammai da abin da yake a cikin
kasa, kuma cewa lalle Allah, ga
dukkan kome, Masani (1) ne.
98. Ku sani cewa lalle Allah Mai
tsananin ukuba ne, kuma lalle Allah
Mai gafara ne, Mai jin kai.
99. Babu abin da yake a kan
Manzo, sai iyarwa, kuma Allah
Yana sanin abin da kuke bayya-
nawa da abin da kuke Boyewa.
100. Ka ce: "Mummuna da mai
kyau ba su daidaita, kuma ko da
yawan mummunan ya ba ka
sha'awa. Saboda haka ku bi Allah
da takawa, ya ma'abuta hankula ko
la'alla za ku ci nasara."
101. Ya ku wacfanda suka yi
Tmani ! Kada ku yi tambaya ga abu-
buwa, idan an bayyana muku
(hukuncinsu) su Bata muku rai.
Kuma idan kuka yi tambaya a gare
su a 16kacin (2) da ake saukar da
Alkur'ani, za a bayyana muku. Al-
lah Ya yafe laifi daga gare su, Allah
Mai gafara ne, Mai hakuri.
102. Lalle ne wasu mutane sun
tambaye su daga gabaninku, sa'an
nan kuma suka wayi gari da su suna
kafirai.
(1) Domin ku san haka kuma ku himmatu ga tsare alkawurranSa.
(2) Wannan lokacin ya nuna shi cfai ne lokacin saukar hukunci kowane iri ne daga
Allah. Wanda ya ce Annabi ya fada masa wani hukunci a kan wata mas'ala, bayan
wafatinsa, tsTra da aminci su tabbata a gare shi, to, ba za a karBar masa ba, domin ya sa6a
wa nassin Alkur'ani. Kuma mafarki ba ya zama hujja, balle a dauke shi hukunci wanda ake
yin aiki da shi. Mafarkin annabawa ko mafarkin da annabawa suka tabbatar, shi ne
gaskiya, saura kuma sai abin da ya bayyana, kuma bai sa6a wa sharT'a ba.
180
Suratul Ma'ida
mm-i
103. Kuma Allah bai sanya wata
bahlra ba^kuma haka sa'iba, kuma
haka wasila, kuma haka hami, (1)
amma wadanda suka kafirta, su
suke kirkira karya ga Allah, kuma
mafi yawansu ba su hankalta.
104. Kuma idan aka ce musu:
"Ku zo zuwa ga abin da Allah Ya
saukar, kuma zuwa ga Manzo," sai
su ce: "Mai isarmu shi ne abin da
muka iske ubanninmu a kansa."
Shin, kuma ko da ubanninsu sun
kasance ba su sanin kome, kuma ba
su shiryuwa?
105. Ya ku wacfanda suka yi
Tmani! Ku lazimci (2) rayukanku,
wanda ya 6ace ba zai cuce ku ba
idan kun shiryu, zuwa ga Allah
makdmarku take gaba daya. Sa'an
nan Ya ba ku labari ga abin da kuka
kasance kuna aikatawa.
106. Ya ku wadanda suka yi
Tmani! Shaidar (3) tsakaninku, idan
.<• T'^ <" ' '
f >-r<^^t^
b *lSC iJ^lS J^jU LlJXJJ) L5 Sy^}\
, • > • »^ »> "£
=au*>£
"2t '
^si^^&c^ck
(1) BahTra da sa'iba da wasfla da hami sunayen dabbobi nejvadanda ake ban domin
tsafi. Bukhari ya ruwaito daga Sa'Td dan Musayyab ya ce : "BahTra ita ce rakumar da ake
hana nononta domin aljannu, babu mai tatsar ta daga mutane. Sa'iba kuma suna 'yanta ta
domin gumaka, ba a cfaukar kome a kanta. Kuma wasila ita ce rakuma budurwa wadda ta
fara haifuwar mace, a ciki na farko, sa'an nan kuma na biyu haka mace. Suna barin ta ga
gumaka idan ta sadar da rakuma mata biyu babu namiji a tsakaninsu. Hami kuwa shT ne
katon rakumi wanda ya yi barbara shekaru sanannu a wurinsu. Idan ya kare, sai su bar shi
ga gumaka, ba a aza kome a kansa. Kuma wadannan dabbobin duka, masu hidimar
gumakan, su ne suke cin su."
(2) Wanda yake son ya gyara wani sai ya gyara kansa daga farko. Wanda ya gyara
kansa 6atar wani ba ta cutarsa. Ba a nufin a bar wa'azi watau a Ryale mutane da jahilcinsu.
(3) Idan husuma ta auku a tsakanin Musulmi da tsakanin kaflrai, kuma su kafiran
suka zama mudda'a alaihim (wadanda ake tuhuma), kuma babu wata shaida sai su, to, sai
su yi rantsuwa a wurin ibadarsu, a kan su ne da gaskiya, a hukumta musu da hakkin.
Bayan haka, idan an sami wata shaida a kan karyarsu ana warware hukuncin a bayan
mudda'i (masu kara) biyu Musulmi sun yi rantsuwa cewa abin da wadancan suka fada
karya ne, abin da shaidunsu suka yi shaida da shi, shi ne gaskiya.
181
Suratul Ma'ida
*m$&-*
mutuwa ta halarci cfayanku, a loka-
cin wasiyya, maza biyu ne ma'abuta
adalci daga gare ku, ko kuwa wasu
biyu daga wasunku idan kun tafi a
cikin kasa sa'an nan masTfar mutu-
wa ta same ku. Kuna tsare su daga
bayan salla har su yi rantsuwa da
Allah; idan kun yi shakka: "Ba mu
sayen kucfi da shi, ko da ya kasance
ma'abucin zumunta, kuma ba mu
66ye shaidar Allah. Lalle ne mu, a
lokacin, haklka, muna daga masu
zunubi."
107. To, idan aka gane cewa lalle
su, sun cancanci zunubi, to, sai
wasu biyu su tsayu matsayinsu daga
wacfanda suka kar6a daga gare su,
mutane biyu mafiya cancanta, sa'an
nan su yi rantsuwa da Allah: "Lalle
ne shaidarmu ce mafi gaskiya daga
shaidarsu, kuma ba mu yi zalunci
ba. Lalle mu, a lokacin, hakTka,
muna daga azzalumai."
108. Wannan ne mafi kusantar
su zo da shaida a kan fuskarta, ko
kuwa su yi tsoron a ture rantsuwoyi
a bayan rantsuwoyinsu. Kuma ku
bi Allah da takawa, kuma ku sau-
rara, kuma Allah ba Ya shiryar da
mutane fasikai.
109. A ranar da Allah Yake tara
manzanni, sa'an nan Ya ce: "Mene
ne aka kar6a muku?" (Za) su ce:
"Babu ilmi a gare mu. Lalle ne Kai,
Kai ne Masanin abubuwan
fake." (1)
A*> .
\j i$)\* o^^3^^<SJC^i
S^i^S^ hfilffilifi 1
*>" < %l.'i<St
(1) A nan hukunce-hukuncen alkawurra suka kare a wannan sura daga aya ta sama
da wannan. Kuma da wannan aya ta 109 Allah Yana yi mana hikayar abin da zai auku a
Lahira da bincinkenSa ga tsare alkawari, ko rashin tsarewa. Ya fara da annabawanSa da
182
5 — Suratul Ma'ida
jMi&-*
770. A lokacin da Allah Ya ce:
"Ya Tsa cfan Maryama! Ka tuna
ni'imaTa a kanka, kuma a kan
mahaifiyarka, a lokacin da Na kar-
fafa ka da Ruhul Kudusi, kana yi
wa mutane magana a cikin shimfi-
tfar jariri, da kuma kana dattijo.
Kuma a lokacin da Na sanar da kai
rubutu da hikima, da Attaura da
InjTla, kuma a lokacin da kake yin
halitta daga laka kamar surar tsunt-
su da iziniNa, sa'an nan ka hura a
cikinta, sai ta zama tsuntsu da izi-
mNa, kuma kana warkar da haifaf-
fen makaho da kuturu, da izimNa,
kuma a lokacin da kake fitar da
matattu da iziniNa, kuma a lokacin
da Na kange Banllsra'ila daga gare
ka, a lokacin da ka je musu da
hujjoji bayyanannu, sai wadanda
suka kafirta daga cikinsu suka ce:
'Wannan ba kome ba ne, face sihiri
bayyananne.'
777. "Kuma a lokacin da Na yi
wahayi zuwa ga Hawariyawa (1)
cewa ku yi Tmani da Ni, kuma da
ManzoNa. Suka ce: "'Mun yi Tma-
ni, kuma ka shaida da cewa lalle
mu, masu sallamawa ne.'"
772. A lokacin da Hawariyawa
suka ce: "Ya Tsa dan Maryam!
Shin, Ubangijinka Yana iyawa Ya
saukar da ka6aki a kanmu daga
'**\'u-.:
/ s St 9 ''' * S ^* * C *' 9 "
\^yy*yy^ s ' ^ t i" tf 'T,- .»,
Ya aiko, da karin bayani a kan irin muhawarar da za ta shiga a tsakaninSa da annabawa.
Ya yi misali da Tsa domin mutanensa na nan a cikin wannan al'umma, ana kiran su zuwa
ga Musulunci, kuma domin shi ne annabi na karshen da ba a manta abubuwan da
mutanensa suka yi ba a gabanin dauke shi, da kuma a bayan dauke shi din.
(1) Hawariyawa su ne Sahabban Tsa, amincin Allah ya tabbata a gare shi. Suna
sanyawar fararen tufafi, domin haka aka yi musu suna da haka.
183
Suratul Ma'ida
MM& - o
sama?" (Tsa) Ya ce: "Ku bi Allah
da taicawa idan kun kasance mu-
minai."
1 13. Suka ce : "Muna nufin mu ci
daga gare shi ne, kuma zukatanmu
su natsu, kuma mu san cewa lalle
ne, ka yi mana gaskiya, kuma mu
kasance daga masu shaida a
kansa."
1 14. Tsa dan Maryam ya ce : " Ya
Allah. Ubangijinmu ! Ka saukar da
ka6aki a kanmu daga sama domin
ya zama Tdi ga na farkonmu da na
icarshenmu, kuma ya zama aya
daga gare Ka. Ka arzuta mu, kuma
Kai ne MafTficin masu arzuta wa."
115. Allah Ya ce: "Lalle ne NT,
mai saukar da shi ne a kanku, sa'an
nan wanda yajcafirta daga gare ku,
to, lalle ne NT, Tna azabta shi, da
wata azaba wadda ba Ni azabta ta
ga kowa daga talikai."
116. KumaalokacindaAllahYa
ce: "Ya Tsa dan Maryama! Shin,
kai ne ka ce wa mutane, 'Ku riice ni,
ni da uwata, abubuwan bautawa
biyu, baicin Allah'?" (Tsa) Ya ce:
"Tsarkinka ya tabbata! Ba ya
kasancewa a gare ni, in facfi abin da
babu wani hakki a gare ni. Idan na
kasance na fade shi, to lalle Ka san
shi, Kana sanin abin da ke a cikin
raina, kuma ba ni sanin abin da ke a
cikin nufinKa. Lalle ne Kai Masa-
nin abubuwan fake ne.
117. "Ban facfa musu ba, face
abin da Ka umurce ni da shi; wa-
tau: 'Ku bauta wa Allah, Uban-
gijina kuma Ubangijinku' ; kuma na
^Mj^yr
L^^«I^lJfl3jl^J^=»Uol-AjJ>^jJ&
^> 'x' 'Z ' s *C
\~£}&b
X 1.S '** 9*^ '
7A3 ApW GlJ^^^l^bj^Cu
^^-Jb^L* /v*-^^ 4 *^-*^ -Xi3j^Ca3C^o 0i<3^V
iJ^^U^it^piis £
r&
Jf*~J>J
184
Suratul Ma'ida
M$%& - o
kasance mai shaida a kansu matu-
kar na dawwama a cikinsu, sa'an
nan a lokacin da Ka kar6i raina (1) ,
Ka kasance Kai ne mai tsaro a
kansu, kuma Kai, a kan dukkan
kome, Halartacce ne.
1 18. "Idan Ka azabta su, to, lalle
ne su, bayinKa ne, kuma idan Ka
gafarta musu, to, lalle ne Kai ne
Mabuwayi Mai hikima."
119. Allah Ya ce: "Wannan ce
ranar da masu gaskiya, gaskiyarsu
take amfaninsu. Suna da gidajen
Aljanna, koramu suna gudana daga
karkashinsu, suna madawwama a
cikinsu har abada. Allah Ya yarda
da su, kuma sun yarda da Shi.
Wannan ne babban rabo mai
girma.
120. Allah ne da mallakar sam-
mai da kasa da abin da ke a cikinsu,
kuma Shi, a kan dukkan kome, Mai
Tkon yi ne.
*>- » ^- »<n^ '' > "lVA'Si"tl-
(1) Kar6ar ran Tsa biyu ne, na duniya da na mutuwa.
185
6 — Suratul An 'am
&m-^
Tana karantar da tauhldi da tsarkake aklda da ayyuka daga
al'adu na shirki da kafirci.^Babu mai yanka hukunci a kan kome sai
Allah kawai, watau TauhTdin Rububiyya ke nan.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Godiya ta tabbata ga Allah
Wanda Ya halitta sammai da kasa,
kuma Ya sanya duffai da haske (1) ,
sa'an nan kuma wacfanda suka ka-
firta, da Ubangijinsu suke karka-
cewa.
2. Shi ne Wanda Ya halitta ku
daga laka, sa'an nan kuma Ya yan-
ka ajali, alhali wani ajali ambatacce
yana wurinSa. Sa'an nan kuma ku
kuna yin shakka.
3. Kuma Shi ne Allah a cikin
sammai, kuma a cikin kasa, Yana
sanin aslrinku da bayyanenku,
kuma Yana sanin abin da kuke yi
na tsirfa.
4. Kuma wata aya daga Uban-
gijinsu ba za ta je musu ba, face sun
kasance, daga gare ta, masu biji-
rewa.
^'iJ^jr "1
(1) Duffai na dare da zalunci da bin hukunce-hukuncen al'adu, haske kuma shine na
taurari da wuta da sharfu na Littafi da annabci.
186
Suratul An'am
if|£~-n
5. Saboda haka, lalle sun kar-
yata (Manzo) game da gaskiya, a
lokacin da ta je musu, to, labarun
abin da suka kasance suna izgili da
shi, za su je musu.
6. Shin, ba su gani ba, da yawa
Muka halakar da wani karni daga
gabaninsu, Mun mallaka musu, a
cikin kasa, abin da ba Mu mallaka
muku ba, kuma Muka saki sama a
kansu tana ta zuba, kuma Muka
sanya koguna suna gudana daga
karkashinsu, sa'an nan Muka hala-
ka su saboda zunubansu, kuma
Muka kaga halittar wani karni na
dabam daga bayansu?
7. Kuma da Mun sassaukar da
wani littafi, zuwa gare ka, a cikin
takarda, sa'an nan suka taba shi da
hannuwansu, lalle da wadanda
suka kafirta sun ce: "Wannan bai
zama ba, face sihiri bayyananne."
8. Suka ce : "Don me ba a saukar
da wani mala'ika ba a gare shi?"
To, da Mun saukar da mala'ika,
haklka, da an hukunta al'amarin (1) ,
sa'an nan kuma ba za a yi musu
jinkiri ba.
9. Kuma da Mun sanya mala'ika
ya zama manzo, lalle ne da Mun
mayar da shi mutum, kuma da Mun
rikita musu abin da suke rikitawa.
10. Kuma lalle ne, haklka, an yi
izgili da manzanni daga gabaninka,
sai wadanda suka yi izgilin, abin da
suka kasance suna izgili da shi ya
fatfa musu.
\jXm \ p^o la 0>-*» *-* «■ U- U (J>iJ b 1 \£ JO JLA3
Uj3pJ* Juo^ bUl^lj^jpJo^yjJbld
tej&J^*
<' > "*S>S <s
(1) Da an hukunta al'amari da halakarsu, domin idan mala'ika ya sauka ga mutanen
da ake yi wa wa'azi bayyane, to, halakarsu ta je ke nan.
187
Suratul An'am
&m>-^
11. Ka ce: "Ku yi tafiya a cikin
kasa, sa'an nan kuma ku duba yad-
da akibar masu karyatawa ta
kasance."
12. Ka ce: "Na wane ne abin da
yake a cikin sammai da kasa?" Ka
ce: "Na Allah ne. Ya wajabta raha-
ma ga kanSa. Lalle ne Yana tara ku
zuwa ga Ranar Kiyama, babu shak-
ka a gare Shi. Wadanda suka yi
hasarar rayukansu, to, su ba za su yi
Tmani ba.
13. "Kuma Shi ne da mallakar
abin da ya yi kawaici a cikin dare da
yini, kuma Shi ne Mai ji, Masani."
14. Ka ce: "Shin, wanin Allah
nike riko maji6inci, (alhali Allah
ne) Mai kaga halittar sammai da
kasa, kuma Shi, Yana ciyarwa,
kuma ba a ciyar da Shi?" Ka ce:
"Lalle ne nl, an umurce ni da in
kasance farkon wanda ya sallama,
kuma kada lalle ku kasance daga
masu shirki."
15. Ka ce : "Lalle ne nl, ina tsoron
azabar Yini Mai girma, idan na
sa6a wa Ubangijina.
16. "Wanda aka juyar da shi
daga gare shi, a wannan ranar, to,
lalle ne, (Allah) Ya yi masa rahama.
Kuma wannan ne tsTra bayya-
nanniya.
17. "Idan Allah Ya shafe ka da
wata cuta, to, babu mai kuranyewa
gare ta, face ShT, kuma idan Ya
shafe ka da wani alheri, to, Shine, a
kan kome, Mai ikon yi.
^
(^^ ' •""' *>"f S X v-"V < x " v ' v**"' <>f
> v^
188
6 — Suratul An'am
&m>- n
18. "Kuma ShT ne Tankwasa a
kan bayinSa, kuma Shi ne Mai
hikima, Masani."
19. Ka ce: "Wane abu ne mafi
girma ga shaida?" Ka ce: "Allah ne
Shaida a tsakanina da tsakaninku.
Kuma an yiwo wahayin wannan
Alkur'ani domin in yi muku gargacfi
da shi, da wanda labari ya kai gare
shi. Shin lalle ne ku, haklka, kuna
shaidar cewa, lalle ne tare da Allah
akwai wasu abubuwan bautawa?"
Ka ce: "Ba zan yi shaidar (haka)
ba." Ka ce: "Abin sani, Shi ne Abin
bautawa Guda, kuma lalle ne nT,
barrantacce ne daga abin da kuke yi
na shirki."
20. Wadanda Muka ba su Littafi
suna sanin sa (1) kamar yadda suke
sanin cfiyansu. Wadanda suka yi
hasarar rayukansu, to, su ba su yin
Tmani.
21. Wane ne mafi zalunci daga
wanda yake kirkira karya ga Allah,
ko kuwa ya karyata game da
ayoyinSa? Lalle ne shT, azzalumai
ba za su ci nasara ba.
22. Kuma ranar da Muka tara su
gaba daya, sa'an nan Mu ce wa
wadanda suka yi shirki : "Ina abo-
kan tarayyarku wadanda kuka ka-
sance kuna riyawa?"
'+•"$<, »\
(1) Yahudu da Nasara suna sanin Annabi Muhammadu, tsTra da aminci su tabbata a
gare shi, da abin da ya zo da shi na Al£ur'ani, kamar yadda suka san cfiyan tsatsonsu;
kamar yadda Abdullahi dan Sallami ya ce wa Umar: "Lalle ne na san shi a lokacin da na
gan shi, kamar yadda nake sanin dana, kuma lalle ne, ni, mafi tsananin sani ne ga
Muhammadu fiye da dana."
189
6 — Suratul An'am
WW&Vt
sg£-i
23. Sa'an nan kuma fitinarsu ba
ta kasance ba, face domin sun ce:
"Muna rantsuwa da Allah Ubangi-
jinmu, ba mu kasance masu yin
shirki ba."
24. Ka duba yadda suka karyata
kansu! Kuma abin da suka kasance
suna kirkira karyarsa, ya Bace daga
gare su.
25. Kuma daga cikinsu akwai
wanda yake saurare gare ka. Kuma
Mun sanya abubuwan rufi a kan
zukatansu, domin kada su fahimce
shi, kuma a cikin kunnuwansu
(Mun sanya) wani nauyi. Kuma
idan sun ga kowace aya ba za su yi
Tmani da ita ba, har idan sun je
maka suna jayayya da kai, wacfanda
suka kafirta suna cewa: "Wannan
bai zama ba face tatsuniyoyin mu-
tanen farko."
26. Kuma suna hanawa daga
gare shi, kuma suna msanta daga
gare shi, kuma ba su halakarwa,
face kansu, kuma ba su sansan-
cewa.
27. Kuma da kana gani, a 16-
kacin da aka tsayar da su a kan
Wuta, sai suka ce: "Ya kaitonmu!
Da ana mayar da mu, kuma ba za
mu karyata ba daga ayoyin Ubangi-
jinmu, kuma za mu kasance daga
muminai."
28. A'aha, abin da suka kasance
suna boyewa, daga gabani, ya
bayyana a gare su. Kuma da an
mayar da su, lalle da sun koma ga
abin da aka hana su daga barinsa.
Kuma lalle ne su, hakTka, makar-
yata ne.
M*iM$Zig&.
'^-i .&#A
fa'dfjffic&r,
J^»j |^~jm 3Hj! •& <Jl5 Jts\
^ >*
^fe£&^j&\yzcf ( ££
ftp ojjt&ffljAxAjrll
190
6 — Suratul An 'am
S&-i
29. Kuma suka ce: "Ba ta zama
ba, face rayuwarmu ta duniya,
kuma ba mu zama wacfanda ake
tayarwa ba."
30. Kuma da kana gani, a loka-
cin da aka tsayar da su ga Ubangi-
jinsu, Ya ce: "Ashe, wannan bai
zama gaskiya ba?" Suka ce:
"Na'am, muna rantsuwa da
Ubangijinmu!" Ya ce: "To, ku
dancfani azaba saboda abin da kuka
kasance kuna yi na kafirci."
31. Lalle ne, wacfanda suka kar-
yata game da gamuwa da Allah sun
yi hasara, har idan Sa'a ta je musu
kwatsam, sai su ce: "Ya nadam-
armu a kan abin da muka yi sakaci a
cikinta!" Alhali kuwa su, suna dau-
kar kayansu masu nauyi a kan
bayayyakinsu. To, abin da suke
cfauka ya munana.
32. Kuma rayuwar duniya ba ta
zama ba, face wasa da shagala,
kuma lalle ne Lahira ce mafi alheri
ga wacfanda suka yi takawa. Shin,
ba za ku yi hankali ba?
33. Lalle ne Muna sani cewa,
hakTka, abin da suke fada yana 6ata
maka rai. To, lalle ne su, ba su
karyata ka (a cikin zukatansu),
kuma amma azzalumai da ayoyin
Allah suke musu.
34. Kuma lalle ne, haklka, an
karyata manzanni daga gabaninka,
sai suka yi hakuri a kan abin da aka
karyata su, kuma aka cutar da su,
har taimakonMu ya je musu, kuma
babu mai musanyawa ga kalmomin
Allah. Kuma lalle ne (abin da yake
**< %"f~Zi:s*%<
^S^ ' > m ~* ''\* >*" 1*3**" *s <•*
191
Suratul An'am
mtm-^
natsar da kai) ya zo maka daga
labarin (annabawan) farko.
35. Kuma idan ya kasance cewa
finjirewarsu ta yi nauyi a gare ka,
to, idan kana iyawa, ka nemi wani
5ulo a cikin £asa, ko kuwa wani
tsani a cikin sama domin ka zo
musu da wata aya, (sai ka yi). Kuma
da Allah Ya so, haklka, da Ya tara
su a kan shiriya. Saboda haka, kada
lalle ka kasance daga jahilai.
36. Abin sani kawai, wadanda
suke saurare ne suke karBawa, ku-
ma matattu Allah Yake tayar da su,
sa'an nan kuma zuwa gare Shi ake
mayar da su.
37. Kumasukace:"Donmebaa
saukar da aya ba, a kansa, daga
Ubangijinsa?" Ka ce: "Lalle ne
Allah Mai Tko ne a kan Ya saukar
da aya, kuma amma mafi yawansu,
ba su sani ba."
38. Kuma babu wata dabba a
cikin £asa, kuma babu wani tsuntsu
wanda yake hTra da fukafukinsa,
face arumma ne misalanku. Ba Mu
yi sakacin barin kome ba a cikin
Littafi, sa'an nan kuma zuwa ga
Ubangijinsu ake tara su.
39. Kuma wadanda suka kar-
yata game da ayoyinMu, kurame ne
kuma bebaye, a cikin duffai. Wanda
Allah Ya so Yana 5atar da shi,
kuma wanda Ya so zai sanya shi a
kan hanya madaidaiciya.
40. Ka ce: "Shin, kun gan ku,
idan azabar Allah ta zo muku, ko
sa'ar Tashin Kiyama ta zo muku,
>>}'*' 'I*'*" ' >' <
9 ' \" * \ ' ~\' '%' **" ?f •
E s '^*<» s?<Z' '*->*> 'Jit *•.***
192
Suratul An'am
&\\\z<A
wmk-^
shin wanin Allah kuke kira, idan dai
kun kasance masu gaskiya?"
41. "A'a, ShJdai kuke kira sai Ya
kuranye abin da kuke kira zuwa
gare Shi, idan Ya so, kuma kuna
mantawar abin da kuke yin shirkin
tare da shi."
42. Kuma lalle Mun aika zuwa
ga aFummai daga gabaninka, sai
Muka kama su da tsanani da cuta,
tsammaninsu za su kankan da kai.
43. To, don me, a lokacin da
tsananinMu ya je musu ba su yi
tawalu'i ba? Kuma amma zuka-
tansu sun kekashe, kuma Shaicfan
ya kawata musu abin da suka kas-
ance suna aikatawa.
44. Sa'an nan kuma a lokacin da
suka manta da abin da aka tunatar
da su da shi, sai Muka bude, a
kansu, kofofin dukkan kome, har a
lokacin da suka yi farin ciki da abin
da aka ba su, Muka kama su, kwat-
sam, sai ga su sun yi tsuru-tsuru.
45. Sai aka katse karshen muta-
nen, wacfanda suka yi zalunci.
Kuma godiya ta tabbata ga Allah
Ubangijin talikai.
46. Ka ce: "Shin, kun gani, idan
Allah Ya rike jinku, da ganananku,
kuma Ya sanya hatimi a kan zuka-
tanku, wane abin bautawa ne, wa-
nin Allah, zai je muku da shi?" Ka
duba yadda Muke sarrafa ayoyi,
sa'an nan kuma su, suna finjirewa.
47. Ka ce: "Shin, kun gan ku,
idan azabar Allah ta je muku, kwat-
sam, ko kuwa bayyane, shin, ana
3 J^J^^>Sl)\S^X 2&\j±jA XtXliS
As"
^$$± ' -% *' ** ^-4
193
Suratul An'am
^m-^
halakarwa, face dai mutane azza-
lumai?"
48. Kuma ba Mu aikawa da
manzanni face masu bayar da bus-
hara, kuma masu gargadi. To, wan-
da ya yi Tmani kuma ya gyara aiki,
to, babu tsoro a kansu, kuma ba su
yin bakin ciki.
49. Kuma wadanda suka karya-
ta game da ayoyinMu, azaba tana
shafar su saboda abin da suka ka-
sance suna yi na fasikanci.
50. Ka ce: "Ba zan ce muku, a
wurina akwai taskokin Allah ba.
Kuma ba ni sanin gaibi, kuma ba ni
gaya muku cewa ni mala'ika ne. Ba
ni bi, face abin da ake yiwo wahayi
zuwa gare ni." Ka ce : "Shin, maka-
fo da mai gani suna daidaita? Shin
fa, ba ku yin tunani?"
51. Kuma ka yi gargadi da shi ga
wadanda suke jin tsoron a tara su
zuwa ga Ubangijinsu, ba su da wani
masoyi baicinSa, kuma babu mai
ceto, tsammaninsu, suna yin
takawa.
52. Kuma kada ka kori wadan-
da (1) suke kiran Ubangijinsu safe
da maraice, suna nufin yardarSa,
babu wani abu daga hisabinsu a
kanka, kuma babu wani abu daga
hisabinka a kansu, har ka kore su,
ka kasance daga azzalumai.
^pM\'£\^\J^& sj^-jT
< '■"■%?&
£ $$>&<&
Tf^-> x "ff >t" > •"
(1) Musulunci addinin Allah ne, wanda yake fakirin dukiya da mawadacinta, duka
daya suke a gare shi. Saboda haka wanda duka ya rigayi wani a cikinsu, to, ba za a kore shi
ba domin dayan ya shiga. Allah Tmani Yake so, ko daga wane inn mutum yake, ba Ya
bukatar dukiya.
194
Suratul An'am
l^\t«3> s .
IB8&-1
53. Kuma kamar wannan ne,
Muka fitini sashensu da sashe, do-
min su ce: "Shin, warfannan ne
Allah Ya yi falala a kansu daga
tsakaninmu?" Shin, Allah bai zama
Mafi sani ba ga masu godiya?
54. Kuma idan watfanda suke
yin Tmani da ayoyinMu suka je
maka, sai ka ce: "Aminci ya tabba-
taagareku : Ubangijinku Ya wajabta
rahama ga kanSa, cewa lalle ne
wanda ya aikata aibi da jahilci daga
cikinku, sa'an nan kuma ya tuba
daga bayansa, kuma ya gyara, to,
lalle Shi, Mai gafara ne, Mai jin kai."
55. Kuma kamar wannan ne
Muke bayyana ayoyi, daki-daki,
kuma domin hanyar masu laifi ta
bayyana.
56. Ka ce: "Lalle ne ni, an hana
ni in bauta wa watfanda kuke kira
daga baicin Allah." Ka ce: "Ba ni
bin son zuciyoyinku, (domin in na
yi haka) lalle ne, na Bace. A sa'an
nan, kuma ban zama daga shirya-
yyu ba."
57. Ka ce: "Lalle ne ina kan
hujja daga Ubangijina, kuma kun
karyata (ni) game da Shi; abin da
kuke neman gaugawarsa, ba ya wu-
rina, hukunci kuwa bai zama ba
face ga Allah, Yana bayar da laba-
rin gaskiya, kuma Shine mafi alhe-
rin masu rarrabewa."
58. Ka ce : "Lalle ne, da a wurina
akwai abin da kuke neman gauga-
wa da shi, hakika, da an hukunta
aFamarin, a tsakanina da tsaka-
ninku, kuma Allah Shine Mafi sani
ga azzulumai."
\yyQ u^V! p-p^g*! ^** — Mi-^*""^
&S2^&^®&3sd
*■* < *-^ *'..
^ ' ->tf
- •>>
<\> *~~z %&** F**
C >» ? '
4^0*j^<3P4lJ*
A »"-<*
195
6 — Suratul An'am
mm-^
59. Kuma a wurinSa mabu-
dan (1) gaibi suke, babu wanda yake
sanin su face Shi, kuma Yana sanin
abin da ke a cikin tudu da ruwa,
kuma wani ganye ba ya fatfuwa,
face Ya san shi, kuma babu wata
kwaya a cikin duffan kasa, kuma
babu danye, kuma babu kekas-
asshe, face yana a cikin wani Littafi
mai bayyanawa.
60. Kuma Shi ne Wanda Yake
kar6ar (2) rayukanku da dare, kuma
Yana sanin abin da kuka yaga da
rana, sa'an nan Yana tayar da ku a
cikinsa, domin a hukunta ajali
ambatacce, sa'an nan kuma zuwa
gare Shi makomarku take, sa'an
nan kuma Ya ba ku labari da abin
da kuka kasance kuna aikatawa.
61. Kuma ShT ne Mai rinjaya
bisa ga bayinSa, kuma Yana aikan
masu tsaro a kanku, har idan mutu-
wa ta je wa cfayanku, sai man-
zanninMu su karbi ransa, alhali su,
ba su yin sakaci.
62. Sa'an nan kuma a mayar da
su zuwa ga Allah Ubangijinsu na
gaskiya. To! A gare Shi hukunci
yake, kuma Shi ne Mafi gaugawar
masu bincike.
Jb V ^L^JLjoV <J»JA\ £^\jla# JLJ^j 4§£
'" .V*'
3 c^l+jo pjS\ZLj
i*^r>>' <££*
r>> \*' *< <,j^>^
(1) Lokacin aukuwar abubuwa na alheri da na azaba da rayuwa da mutuwa da
sauransu, babu wanda ya san su sai Allah. Wanda ya ce ya san wani abu na gaibi alhali
kuwa, shlba wani manzon Allah ba, to, kafiri ne. Haka kuma wanda yake cewa, annabawa
sun san dukkan gaibi, kamar yadda Allah Ya sani, shT ma kafiri ne.
(2) Kar6ar rai da dare domin barci, tayarwa a cikin rana, watau yini daga barci.
Akwai misalta dare da duniya kuma rana^da Ranar Kiyama, kuma mutuwa da barci, da
farkawa daga barci da Tashin Kiyama. Ayar ta kunsa asTrai masu yawa.
196
6 — Suratul An'am
&\\\ 1 £<A
V&SZ-I
63. Ka ce: "Wane ne Yake tslrar
da ku daga duhuhuwan tudu da
ruwa, kuna kiran Sa bisa ga kankan
da kai, kuma a boye: 'Lalle ne idan
Ka tslrar da mu daga wannan (ma-
sTfa), haklka, muna kasancewa
daga masu godiya?'"
64. Ka ce: "Allah ne Yake tslrar
da ku daga gare ta, kuma daga
dukan bakin ciki, sa'an nan kuma
ku, kuna yin shirki!"
65. Ka ce : "Shi ne Mai Tko a kan
Ya aika da wata azaba a kanku,
daga bisanku, ko kuwa daga kar-
kashin kafafunku, ko kuwa Ya gau-
raya ku kungiyoyi, kuma Ya dan-
dana wa sashenku masTfar sashe."
Ka duba yadda Muke sarrafa
ayoyi, tsammaninsu suna fahimta!
66. Kuma mutanenka sun kar-
yata (ka) game da shi, alhali kuwa
shi ne gaskiya. Ka ce : "Nlban zama
waklli a kanku ba.
67. "Akwai matabbata ga du-
kan labari, kuma za ku sani."
68. Kuma idan ka ga wadanda
suke kutsawa a cikin ayoyinMu, to,
ka bijire daga gare su, sai sun kutsa
a cikin wani labari waninsa. Kuma
imma dai Shaicfan lalle ya mantar
da kai, to, kada ka zauna a bayan
tunawa tare da mutane azzalumai.
69. Kuma babu wani abu daga
hisabinsu (masu kutsawa a cikin
ayoyin Allah) a kan masu takawa,
amma akwai tunatarwa (a kansu),
tsammaninsu (masu kutsawar) za
su yi takawa.
J^i*< *\'k<' £*'\' "" \S'* \-\a* r
£Cr > A rV W*' V-- ' *&
,^,^ • »fr.' ^ . * > >^^ -tf^ Vi x . ^
rO*Oji^»Clls^'Jpt»J
><^ »>^<
j>j2ij j^fU i£^=>> <j— ^J
197
Suratul An'am
&<SAtt<!A.
zm$&-^
70. Kuma ka bar wacfanda suka
riki addininsu abin wasa (1) da wargi
alhali rayuwar duniya ta riicfe su,
kuma ka tunatar game da shi
(Alkur'ani) : Kada a jefa rai a cikin
halaka saboda abin da ya tsirfanta:
ba shi da wani majiBinci baicin
Allah, kuma babu wani mai ceto:
kuma ko ya daidaita dukan fansa,
ba za a karBa ba daga gare shi.
Watfancan ne aka yanke wa tsam-
mani, saboda abin da suka tsir-
fanta: suna da wani abin sha daga
ruwan zafi, da wata azaba mai ratfa-
di, saboda abin da suka kasance
suna yi na kafirci.
71. Ka ce: "Shin, za mu yi kiran
abin da ba ya amfaninmu, baicin
Allah, kuma ba ya cutar da mu, —
kuma a mayar da mu a kan dugadu-
ganmu, a bayan Allah Ya shiryar da
mu, — kamar wanda shaidanu suka
kayar da shi a cikin kasa, yana mai
dimuwa, yana da abokai suna kiran
sa zuwa ga shiriya, 'Ka zo
mana (2 }9 " ?Kace : "Lallene, shiriyar
Allah ita ce shiriya. Kuma an umur-
ce mu, mu sallama wa Ubangijin
talikai.
72. "Kuma (an ce mana) : Ku tsai
da salla kuma ku blShi (Allah) da
takawa, kuma Shi ne Wanda Yake,
zuwa gare Shi ake tara ku."
(4^-4 v^-> ^-^P '_>* ^ <s -**
•<i <
>xM&\
(1) Suka sanya sababbin abubuwa a cikinsa, wacfanda suke babu su a cikinsa, kamar
Khawarijawa da sashen wanda ke da'awar danganuwa zuwa ga salihai, inda suka sanya
Tarika mai sadarwa zuwa ga Allah, bandiri da algaita, kuma suka fara abubuwa wacfanda
ba su halatta ba ga shari'a. Daga SawT.
(2) Shi kuma ba ya kar6awa balle ya nufi wurin shiriyar da suke kiran sa ya tail ,
saboda ya riga ya fadi daga sama zuwa kasa, kuma dimuwa ta kama shi.
198
Suratul An'am
&g&m-^
73. Kuma ShT ne Wanda Ya ha-
litta sammai da kasa da mulkinSa,
kuma a ranar da Yake cewa: "Ka
kasance," sai abu ya yi ta kasan-
cewa. MaganarSa ce gaskiya, kuma
gare Shi mulki yake a ranar da ake
busa a cikin kaho. Masanin fake da
bayyane ne, kuma Shi ne Mai hiki-
ma Masani.
74. Kuma a lokacin da Ibrahlma
ya ce wa ubansa Azara : "Shin, kana
rikon gumaka abubuwan bautawa?
Lalle nT, ina ganin ka kai da muta-
nenka, a cikin 6ata bayyananniya."
75. Kuma kamar wancan ne,
Muke nuna wa Ibrahlma mulkin
sammai da kasa, kuma^domin ya
kasance daga masu yaklni.
76. To, a lokacin da dare ya rufe
a kansa, ya ga wani tauraro, ya ce:
"Wannan ne, ubangijina?" Sa'an
nan a lokacin da ya facfi, ya ce: "Ba
ni son masu faduwa."
77. Sa'an nan a lokacin da ya ga
wata yana mai bayyana, ya ce:
"Wannan ne Ubangijina?" Sa'an
nan a lokacin da ya facfi, ya ce:
"Lalle ne idan Ubangijina bai shir-
yar da ni ba, haklka, ina kasancewa
daga mutane 6atattu."
78. Sa'an nan a lokacin da ya ga
rana tana bayyana, ya ce : "Wannan
shl ne Ubangijina, wannan ne mafi
girma?" Sa'an nan a lokacin da ta
facfi, ya ce : " Ya mutanena ! Lalle ne
ni barrantacce nake daga abin da
kuke yi na shirki.
79. "Lalle ne nT, na fuskantar da
fuskata ga Wanda Ya kaga halittar
^3$&1*&2&3L ^s&%
} > >'s*ss*s"'
9 <\X>\ S c 4 \X • £ < *'" > xX>Xi>'\'
< > "*'<
6p CjOL^II
ss* '"ir'4 / " I, *> <
199
Suratul An'am
tf'\\\z<*
$tB8£-l
sammai da £asa, ina mai karkata
zuwa ga gaskiya, kuma ba ni cikin
masu shirki."
80. Kuma mutanensa suka yi
musu da shi. Ya ce: "Shin kuna
musu da ni a cikin sha'anin Allah,
alhali kuwa Ya shiryar da ni ? Kuma
ba ni tsoron abin da kuke yin shirki
da shi, face idan Ubangijina Ya so
wani abu. Ubangijina Ya yalwaci
dukkan kome da ilmi. Shin, ba za
ku yi tunani ba?
81. "Kuma yaya nake jin tsoron
abin da kuka yi shirki da shi, kuma
ba ku tsoron cewa lalle ne ku, kun yi
shirki da Allah, abin da (Allah) bai
saukar da wata hujja ba game da
shi? To, wane 6angare daga sashen
biyu ne mafi cancanta da aminci,
idan kun kasance kuna sani?
82. "Wadanda suka yi Tmani,
kuma ba su gauraya Tmaninsu da
zalunci ba, wadannan suna da
aminci, kuma su ne shiryayyu."
83. Kuma waccan ita ce hujjar-
Mu, Mun bayar da ita ga Ibrahima
a kan mutanensa. Muna daukaka
wanda Muka so da darajoji. Lalle
ne Ubangijinka Mai hikima ne,
Masani.
84. Kuma Muka ba shi Is'haka
da Yakubu, dukansu Mun shiryar,
kuma Nuhu Mun shiryar da shi a
gabani, kuma daga zuriyarsa akwai
Dawuda da Sulaimanu da Ayyuba
da Yusufu da Musa da Haruna,
kuma kamar wancan ne Muke saka
wa masu kyautatawa.
^ *C- *$'*>> '*&{' *\'\ <*"> '
*&$&&$$&$&
>s*'Z- »' Ss
200
6 — Suratul An'am
^m-^
85. Da Zakariyya da Yahaya da
Tsa da Ilyasu dukansu daga salihai
suke.
86. Da Isma'ila da Alyasa'a da
Yunusa da Ludu, kuma dukansu
Mun ffiita su a kan talikai.
87. Kuma daga ubanninsu, da
zuriyarsu, da 'yan'uwansu, kuma
Muka zaBe su, kuma Muka shiryar
da su zuwa ga hanya madaidaiciya.
88. Wancan ne shiryarwar Al-
lah, Yana shiryar da wanda Yake so
daga bayinSa. Kuma da sun yi shir-
ki da, hakika, abin da suka kasance
suna aikatawa ya lalace.
89. Wadancan ne wadanda
Muka bai wa Littafi da hukunci da
annabci. To, idan wadannan (muta-
ne) sun kafirta da ita, to, hakTka,
Mun wakkala wasu mutane gare ta,
ba su zama game da ita kafirai ba.
90. Wadancan ne Allah Ya shir-
yar, saboda haka ka yi koyi da
shiryarsu. Ka ce : "Ba ni tambayar
ku wata ijara. ShT (Alkur'ani) bai
zama ba face tunatarwa ga talikai."
91. Kuma ba su kaddara Allah a
kan hakkin kaddara Shi ba, a loka-
cin da suka ce : "Allah bai saukar da
kome ba ga wani mutum." Ka ce:
"Wane ne ya saukar da Littafi wan-
da Musa ya zo da shi, yana haske da
shiriya ga mutane, kuna sanya shi
takardu, kuna bayyana su, kuma
kuna 66ye mai yawa, kuma an sa-
nar da ku abin da ba ku sani ba, ku
»<>s^ .*
201
Suratul An'am
&&m&-^
da ubanninku?" Ka ce: "Allah," (1)
sa'an nan ka bar su a cikin
sharholiyarsu suna wasa.
92. Kuma wannan Littafi ne,
Mun saukar da shi, mai albarka ne,
mai gaskata wanda yake a gabansa
ne, kuma domin ka yi gargacfi ga
Uwar Alkaryu (Makka) da wanda
yake gefenta. Kuma wacfanda suke
yin Tmani da Lahira suna Tmani da
shi (Alkur'ani), kuma su, a kan
sallarsu, suna tsarewa.
93. Kuma wane ne mafi zalunci
daga wanda ya kirkira karya ga
Allah, ko kuwa ya ce: "An yi wa-
hayi zuwa gare ni," alhali kuwa ba a
yi wahayin kome ba zuwa gare shi,
da wanda ya ce: "Zan saukar da
misalin abin da Allah Ya saukar"?
Kuma da ka gani, a lokacin da
azzalumai suke cikin mayen mutu-
wa, kuma mala'iku suna masu
shimficfa hannuwansu, (suna ce
musu) "Ku fitar da kanku: a yau
ana saka muku da azabar wula-
kanci saboda abin da kuka kasance
kuna facfa, wanin gaskiya, ga Allah,
kuma kun kasance daga ayoyinSa
kuna yin girman kai."
94. Kuma lalle ne, hakTka, kun
zo Mana cfai cfai, kamar yadda
Muka halitta ku a farkon lokaci.
Kuma kun bar abin da Muka mal-
laka muku a bayan bayayyakinku,
kuma ba Mu gani a tare da ku ba,
s s *s »> t^
(l) Allah ne Ya saukar da shi, saboda haka ba zai zama abin mamaki ba ko abin
musu ga Ya saukar da wani littafi kamar Alkur'ani ga wani mutum a bayan Taurata ga
Musa. Kuma a cikin Tauratar ba a ce ita ce karshen Littafin Allah ba, kuma Musa ba shi
ne karshen annabawa ba.
202
6 — Suratul An'am
*#*&&- <\
macetanku wacfanda kuka riya
cewa lalle ne su, a cikinku masu
tarayya ne. Lalle ne, haklka, kome
ya yanyanke a tsakaninku, kuma
abin da kuka kasance kuna riyawa
ya Bace daga gare ku.
95. Lalle ne, Allah ne Mai tsage-
war kwayar hatsi da kwalfar gurtsu.
Yana fitar da mai rai daga mamaci,
kuma (Shi) Mai fitar da mamaci ne
daga mai rai (1) . Wannan ne Allah.
To, yaya ake karkatar da ku?
96. Mai tsagewar safiya, kuma
Ya sanya dare mai natsuwa, kuma
da rana da wata a bisa lissafi. Wan-
nan ne kaddarawar Mabuwayi
Masani.
97. Kuma Shi ne Ya sanya muku
taurari domin ku shiryu da su a
cikin duffan tudu da ruwa. Lalle ne
Mun bayyana ayoyi daki-daki, ga
mutane wadanda suke sani.
98. Kuma shi ne Ya kaga hali-
ttarku daga rai guda, sa'an nan da
mai tabbata da wanda ake ajewa.
Lalle ne Mun bayyana ayoyi daki-
daki, ga mutane wacfanda suke fah-
imta.
99. Kuma Shi ne Ya saukar da
ruwa daga sama, Muka fitar da
tsiron dukan kome game da shi,
sa'an nan Muka fitar da kore daga
gare shi, Muna fitar da kwaya
By c*j+ey
"-"$&
9 >±*
(1) MaiTmani daga kaflri ko kafiri daga maiTmani, da mai arziki daga matalauci da
matalauci daga mawadaci, sarki daga talaka da talaka daga sarki, da mai sanyi daga mai
zafi ko mai zafi daga mai sanyi, haka dai ga kome Allah Yana fitar da kTshiyarsa.
203
6 — Suratul An 'am
&$m-^
cfamfararriya daga gare shi (ko-
ren), (1) kuma daga dablno daga
hirtsinta akwai dumbuje-dumbuje
makusanta, daga gonaki daga ina-
bobi da zaituni da rummani, masu
kama da juna da wasun masu kama
da juna. Ku duba zuwa 'ya'yan
itacensa, idan ya yi 'ya'yan, da
nunarsa. Lalle ne a cikin wannan
akwai ayoyi ga wacfanda suke yin
Imani.
100. Kuma suka sanya wa Allah
abokan tarayya, aljannu, alhali
kuwa (Shi) Ya halitta su. Kuma sun
£ir£ira masa cfiya da 'y^'ya, ba da
ilmi ba. TsarkinSa ya tabbata!
Kuma Ya cfaukaka daga abin da
suke sifantawa.
101. Mafarin (2) halittar sammai
da £asa. Yaya da zai zama a gare
Shi, alhali kuwa mata ba ta kasance
ba a gare Shi, kuma Ya halitta
dukan, kome, kuma Shi, game da
dukan kome, Masani ne?
102. Wancan ne Allah Uban-
gijinku. Babu wani abin bautawa
face Shi, Mahaliccin dukan kome.
Saboda haka ku bauta Masa, kuma
Shi ne Waklli a kan dukan kome.
103. Gannai ba su iya risku-
warSa, kuma Shi, Yana riskuwar
gannai, kuma Shi ne Mai tausa-
sawa, Masani.
(1) Allah na halitta koren ganye daga hasken rana, sa'an nan Ya halitta garin kwaya
daga koren.
(2) Shi ne wanda Ya fan halitta su ba da Ya koya daga wani ba. Sautin jan wasalin fa
zai yi sama domi bambanci daga mafari watau sababin abu, ana mike sautin maddi a gare
shi.
204
6 — Suratul An 'am
i^XllttH
S»-i
104. Lalle ne, abubuwan lura
sun je muku daga Ubangijinku, to,
wanda ya kula, to, domin kansa,
kuma wanda ya makanta, to, laifi
yana a kansa, kuma nl, a kanku, ba
mai tsaro ba ne.
105. Kamar wannan ne, Muke
sarrafa ayoyi, kuma domin su ce:
"Ka karanta!" Kuma domin Mu
bayyana shi ga mutane wadanda
suna sani.
106. Ka bi abin da aka yi wahayi
zuwa gare ka daga Ubangijinka:
Babu wani abin bautawa face Shi,
kuma ka bijire daga masu shirki.
107. Kuma da Allah Ya so, da ba
su yi shirki ba, kuma ba Mu sanya
ka mai tsaro a kansu ba, kuma ba
kai ne wakili a kansu ba.
108. Kuma kada ku zagi wadan-
da suke kira, baicin Allah, har su
zagi Allah bisa zalunci, ba da ilmi
ba. Kamar wannan ne Muka kawa-
ta ga kowace al'umma aikinsu,
sa'an nan zuwa ga Ubangijinsu ma-
komarsu take, sa'an nan Ya ba su
labari da abin da suka kasance suna
aikatawa.
109. Kuma suka yi rantsuwa da
Allah iyakar rantsuwoyinsu (cewa)
lalle ne idan wata aya ta je musu,
haklka, suna yin Tmani da ita. Ka
ce: "Abin sani kawai, ayoyi a wurin
Allah suke. Kuma mene ne zai sa-
nya ku ku sansance cewa, lalle ne su,
idan ayoyin sun je, ba za su yi Tmani
ba?"
110. Kuma Muna jujjuya zuka-
tansu da ganansu, kamar yadda ba
tf£% ^ >X" ''x*'*'**'
\yb\^j^X^i Ji^^ppti) &\jrJLtLp
\>
^po^ll^
£Cpf iC- o\! ^^} a^^U^*15»j
205
Siiratul An'am
^H%&-^
su yi Tmani da shi ba a farkon lokaci,
kuma Muna barin su a cikin kutsa-
warsu, suna cfimuwa.
777. Kuma da a ce, lalle Mu,
Mun saukar da mala'iku zuwa gare
su, kuma matattu suka yi musu
magana, kuma Muka tara dukan
kome a kansu, gungu-gungu, ba su
kasance suna iya yin Tmani ba, sai fa
idan Allah Ya so, kuma amma mafi
yawansu suna jahiltar haka.
772. Kuma kamar wancan ne
Muka sanya wa kowane annabi
makiyi; shaidanun mutane da al-
jannu, sashensu yana yin ishara (1)
zuwa sashe da kawataccen zance
bisa ga rucfi. Kuma da Ubangijinka
Ya so, da ba su aikata shi ba, don
haka ka bar su da abin da suke
kirkirawa.
775. Kuma domin zukatan wa-
cfanda ba su yi Tmani da Lahira ba
su karkata saurare zuwa gare shi,
kuma domin su yarda da shi, kuma
domin su kamfaci abin da suke
masu kamfata.
114. Shin fa, wanin Allah nake
nema ya zama mai hukunci (2) , alha-
li kuwa Shi ne Wanda Ya saukar
> • •»<<'£-"♦*?
zj&j&2Ji*J$?$&*&ii
oify^i&tfpX&ZZ&j
'*x»> *
> * \\'
<'< <>
J^tS^^j'-^^J^^ 1 ^-^^
(1) Wahayin shaicfanu sashensu zuwa ga sashe da £awata karya ta zama kamar
gaskiya. Kamar Shaicfan ya sanya wasiwasi : da da'awar annabi gaskiya ce, ai da manyan
mutane ne za su fara bin ta, ba matalauta ba, ko kuwa annabi mai sihiri ne domin yana
raba miji da mata, da da da uba. Watau su karkatar da magana, domin su karkatar da
wawaye daga bin gaskiya.
(2) Duka wanda ya shirya wani abu wanda shan'a ba ta zo da shi ba, sa'an nan ya
nemi mutane su hau shi, su yi aiki da shi, ya zama mai hukunci, wanin Allah. Wanda ya bT
shi da da'a kan bidi'arsa, to, ya yi shirki da Allah, ya riki wanin Allah mai yi masa
hukunci ke nan.
206
6 — Suratul An'am
(S&-1
muku da Littafi abin rabewa daki-
daki ? Kuma wadanda Muka bai wa
Littafi suna sanin cewa lalle shi
(Alkur'ani) abin saukarwa ne daga
Ubangijinka, da gaskiya? Saboda
haka kada ku kasance daga masu
shakka.
115. Kuma kalmar Ubangijinka
ta cika, tana gaskiya (1) da adalci.
Babu mai musanyawa ga kalmo-
minSa, kuma Shi ne Mai ji, Masani.
116. Kuma idan ka bi mafiya
yawan wadanda suke a cikin kasa
da tfa'a suna 6atar da kai daga
hanyar Allah. Ba su bin kome sai
face £addari-fadi (2) suke yi.
117. Lalle ne Ubangijinka Shine
Mafi sani ga wanda yake Bacewa
daga hanyarsa kuma Shi ne Mafi
sani ga Masu shiryuwa.
118. Saboda haka ku ci daga
abin da aka ambaci sunan Allah (3)
kansa, idan kun kasance masuTma-
ni da ayoyinSa.
119. Kuma mene ne ya same ku,
ba za ku ci ba daga abin da aka
ambaci sunan Allah a kansa, alhali
kuwa, haklka, Ya rarrabe muku
daki-daki, abin da Ya haramta a
*> » K "Z
^ $ * -s
r*a£>o&* ^l5j^o^<j^»o*
\JSA9*
j^jJL^ L. ^ I f>ib fLP-L* p^sJ Jlvi3 JL5J
(1) Musulunci ko Al£ur'ani ne cikon addinin Allah, babu mai iya zowa da wani abu
sabo ko ya £ara wani abu a cikinsa ta kowace hanya kuma babu mai iya musanya wani abu
a cikinsa. Ya cika ya kammala, sai biya kawai. Annabi ya ce, "Wanda ya yi wani aiki ba da
umurninsa a kan abin da ya aikata din nan ba, to, an mayar masa; ba a karba ba."
(2) Kamar maganarsu cewa mushe wanda Allah da kansa Ya kashe, ya fi dacewa da a
ci shi, bisa ga abin da mutane suka yanka.
(3) An sani daga nan cewa ambaton sunan Allah wajen yankan dabba wajibi ne, idan
an tuna. Wanda ya manta, ana cin yankansa, amma wanda ya bari da gangan, ba za a ci
yankansa ba.
207
Suratul An'am
)gbWz&-^
kanku, face fa abin da aka bukatar
da ku bisa lalura zuwa gare shi?
Kuma lalle ne masu yawa suna
Batarwa, da son zuciyoyinsu, ba da
wani ilmi ba. Lalle ne Ubangijinka
Sti! ne Mafi sani ga masu ta'addi.
120. Kuma ku bar bayyanannen
zunubi da Boyayyensa. Lalle ne
wacfanda suke tsiwurwurin zunubi
za a saka musu da abin da suka
kasance suna kamfata.
121. Kada ku ci daga abin da ba
a ambaci sunan Allah ba a kansa (1 \
Kuma lalle ne shi, fasiicanci ne.
Kuma lalle ne, shaidanu, haklka,
suna yin ishara zuwa ga masoyansu,
domin su yi jayayya da ku. Kuma
idan kuka yi musu da'a, lalle ne ku,
haklka, masu shirki ne.
122. Shin, kuma wanda ya ka-
sance matacce, sa'an nan Muka
rayar da shi, kuma Muka sanya
wani haske dominsa, yana tafiya da
shi, yana zama kamar wanda misa-
linsa yana cikin duffai, shi kuma ba
mai fita ba daga gare su? Kamar
wancan ne aka kawata wa kafirai
abin da suka kasance suna aika-
tawa.
123. Kuma kamar wancan ne,
Mun sanya a cikin kowace alkarya,
shugabanni su ne masu laifinta,
domin su yi makirci a cikinta, alhali
'<, c >^t l"
X'
yy oj^A^lyo ujojj 3 ^-^ f^oy^^
j*$$ wJ>£*Q -Zls^&A \ Qj ^jli)
wu
j^&y$&&?&s&
(1) Saboda haka ba a cin yankan majusu. Ana cin yankan Bakitabe, babu ruwanmu
da abin da yake fada, tun da Allah Ya halatta mana cin abincinsu alhali kuwa Ya san sun
riga sun musanya addininsu. Idan Musulmi ya bar sunan Allah da gangan, amma bai
ambaci sunan kowa ba, to, akwai riwaya biyu game da haka, ci ko rashin ci. Amma idan ya
hada sunan Allah da na wani, to, ba za a ci ba, domin ya yi ridda.
208
Suratul An 'am
WVjC&V*
IS^-n
kuwa ba su yin makirci face ga
rayukansu, kuma ba su sans-
ancewa.
124. Kuma idan wata aya ta je
musu sai su ce: "Ba za mu yilmani
ba, sai an kawo mana kamar abin
da aka kawo wa manzannin Allah."
Allah Mafi sanin inda Yake
sanya manzancinSa (1) . Wani wula-
£anci (2) a wurin Allah da wata
azaba mai tsanani za su sami
wacfanda suka yi laifi, saboda abin
da suka kasance suna yi na makirci.
125. Domin haka wanda Allah
Ya yi nufin ya shiryar da shi sai ya
bucfa icirjinsa domin Musulunci,
kuma wanda Ya yi nufin Ya Batar
da shi, sai Ya sanya icirjinsa mai
icunci matsattse, kamar dai yana
takawa (3) ne a cikin sama. Kamar
wannan ne Allah Yake sanyawar
Icazanta a kan wadanda ba su yin
Tmani.
126. Wannan ita ce hanya ta
Ubangijinka madaidaiciya. Lalle ne
Mun bayyana ayoyi daki-daki ga
mutane masu kar6ar tunatarwa.
127. Suna da gidan aminci a wu-
rin Ubangijinsu, kuma Shine Maji-
Bincinsu, saboda abin da suka ka-
sance suna aikatawa.
S^r < » 9 ' K "~ •.tvM< >
J^.vt^U^4llU» Jjij ^L. JJU.
c,~
^i^j^f^i^^ii^,
^ Oj£^J>Kuj
(1) Manzanci da zabin Allah yake, ba da kudi ko 'ya'ya ko kabTla yake ba, sai a wurin
da Allah Ya aza shi.
(2) Mai girman kai ga bin umurnin Allah, sakamakonsa wulakanci ne.
(3) Mai takawa zuwa sama kirjinsa kunci yake yi, saboda iskar numfashi tana raguwa
gare shi. Kuma shi yana shasshekar gajiya da rashin iska. Wannan ilmi yana a cikin
mu'ujizar Alkur'ani.
209
6 — Suratul An'am
^•.\ttc^.
iSS^-i
128. Kuma ranar da yake tara su
gaba cfaya (Yana cewa): "Ya ja-
ma'ar aljannu ! Lalle ne kun yawaita
kanku daga mutane." Kuma maji-
Bantansu daga mutane suka ce:
"Ya Ubangijinmu! Sashenmu (1) ya
ji dadi da sashe, kuma mun kai ga
ajalinmu wanda Ka yanka mana!"
(Allah) Ya ce: "Wuta ce mazau-
narku, kuna madawwama a cikinta,
sai abin da Allah Ya so. Lalle ne
Ubangijinka Mai hikima ne,
Masani."
129. Kuma kamar wancan ne
Muke jiBintar da sashen azzalumai
ga sashe, saboda abin da suka ka-
sance suna tarawa.
130. Ya jama'ar aljannu da mu-
tane! Shin, manzanni daga gare ku
ba su je muku ba, suna labarta
ayoyiNa a kanku, kuma suna yi
muku gargadin haduwa da wannan
yini naku? Suka ce : "Mun yi shaida
a kan kawunanmu." Kuma rayu-
war duniya ta rude su. Kuma suka
yi shaida a kan kawunansu cewa,
lalle ne su, sun kasance kafirai.
131. Wancan kuwa saboda
Ubangijinka bai kasance Mai ha-
laka allcaryoyi saboda wani zalunci
ba ne, alhali kuwa mutanensu suna
jahilai. (2)
C^Zfi^\J^Sj> £s$&
ESso
jlyDUj
tV >'*\\ <^\\ 9 *'$i *c
(1) Haka dai mai lafi a bayan azabar laifinsa ta tabbata a kansa ba yo boyewar abin
da ya riga ya bayyana, sai ya farfa da kansa domin ya bayyanar da nadamarsa a lokacin da
nadama ba ta da amfani.
(2) Allah ba Ya halaka mutane saboda wani laifl, sai bayan Ya aiki mai gargacG ya
tafi ya yi musu gargadi, sun san laifinsu, sun £i bari, sa'an nan azaba ta je musu.
210
6 — Suratul An'am
'smm-^
132. Kuma ga kowanne (1) , ak-
wai darajoji daga abin da suka ai-
kata. Kuma Ubangijinka bai zama
Mai shagala ba daga abin da suke
aikatawa.
133. Kuma Ubangijinka Wa-
datacce (2) ne Ma'abucin rahama.
Idan Ya so, zai tafi da ku, kuma Ya
musanya daga bayanku, abin da
Yake so, kamar yadda Ya icaga
halittarku daga zuriyar wasu muta-
ne na dabam.
134. Lalle ne abin da ake yi
muku wa'adi, lalle mai zuwa ne,
kuma ba ku zama masu buwaya ba.
135. Ka ce: "Ya ku mutanena!
Ku yi aiki a kan halinku, lalle ne nT,
mai aiki ne, sa'an nan da sannu za
ku san wanda alcibar gida za ta
kasance a gare shi. Lalle ne shi,
azzalumai ba za su ci nasara ba."
136. Kuma sun sanya wani rabo
ga Allah daga abin da Ya halitta
daga shuka da dabbobi, sai suka ce :
"Wannan (3) na Allah ne", da riya-
warsu "Kuma wannan na abu-
buwan shirkinmu ne." Sa'an nan
^JJ^\^^Ij\2\
(1) Kowace jama'a, ta masu cfa'a da ta masu sa66, suna da sakamako gwargwadon
matsayin kowanne, ga Tmaninsa da aikinsa ko kuwa kafircin saBonsa.
(2) Rashin gaugawar yin sakamako ga masu laifi saboda wadatar Allah ne. Ba Shi yin
u£uba domin Ya yi fushin an rage masa mulki, haka kuma ba Shi yin ni'ima domin an £ara
Masa mulki. Sai dai domin Ya nuna adalci da falala ne kawai.
(3) Sun kasance a cikin Jahiliyya idan suka yi noma ko kuwa idan suka sami 'ya'yan
itace, sai su sanya wani juz'i daga gare shi ga Allah, wani juz'i kuma ga gumaka. Abin da
yake rabon gumaka, sai su tsare shi, kuma su lissafce shi. Idan wani abu ya facfi daga abin
da aka ambace shi ga Samad, sai su mayar da shi zuwa ga rabon gumaka, amma rabon
gumakan, ba ya zuwa ga na Allah. Ana bayar da rabon Allah ga misklnai, kuma rabon
gumaka ga matsaransu.
211
6 — Suratul An'am
fc^\!l&!4
mm-^
abin da ya kasance na abubuwan
shirkinsu, to, ba ya saduwa zuwa
Allah, kuma abin da ya kasance na
Allah, to, shuyana saduwa zuwa ga
abubuwan shirkinsu. Tir da hukun-
cinsu!
137. Kuma kamar wancan ne
abubuwan shirkinsu suka kawata
wa masu yawa, daga masu shirkin;
kashewar (1) 'ya'yansu, domin su
halaka su, kuma domin su rikitar da
addininsu a gare su, kuma da Allah
Ya so, da ba su aikata shi ba. Sabo-
da haka, ka bar su da abin da suke
kirkirawa.
138. Kuma suka ce : "Wadannan
dabbobi da shuka hanannu ne;
babu mai dandanar su face wanda
muke so," ga riyawarsu. Da wasu
dabbobi an hana bayayyakinsu, da
wasu dabbobi ba su ambatar sunan
Allah a kansu, bisa kirkiren karya
gare Shi. Zai saka musu da abin da
suka kasance suna kirkirawa.
139. Kuma suka ce: "Abin da
yake a cikin cikkunan wadannan
dabbobi keBantacce ne ga maza-
nmu, kuma hananne ne a kan ma-
tan aurenmu. Kuma idan ya ka-
sance mushe, to, a cikinsa, su, abo-
kan tarayya ne." Zai saka musu
sifantawarsu. Lalle ne ShT, Mai hi-
kima ne, Masani.
z>\
2^ ^iffe j^TC^^iTjLlJ
Ir^s^jy?**
(1) Suna turbude 'ya'ya mata, domin tsoron talauci ko domin tsoron kunya. Sai mai
haihuwa ta haihu a bakin rami, idan mace ta haifa, sai ta tura ta cikin ramin, ta rufe, idan
kuma namiji ne sai ta bar shi. Haka kuma kashe 'ya'ya, a kan bakance da alwashi, suna
ganin sa ibada ne.
212
6 — Suratul An'am
*^m-^
140. Lalle ne wacfanda suka kas-
he diyansu saboda wauta, ba da ilmi
ba, sun yi hasara! Kuma suka ha-
ramta abin da Allah Ya arzuta su,
bisa kirkira karya ga Allah. Lalle
ne, sun Bace, kuma ba su kasance
masu shiryuwa ba.
141. Kuma ShT ne Wanda Ya
kaga halittar gonaki masu rumfuna
da wasun masu rumfuna, da dabT-
nai da shuka, mai saBawa ga
'ya'yansa na ci, da zaituni da rum-
mani mai kama da juna da wanin
mai kama da juna. Ku ci daga
'ya'yan itacensa, idan ya yi 'ya'yan,
kuma ku bayar da hakkinSa a ranar
girbinsa, kuma kada ku yi Barna.
Lalle ne Shi, ba Ya son maBarnata.
142. Kuma daga dabbobi (Ya
kaga halittar) mai daukar kaya da
kanana: Ku ci daga abin da Allah
Ya arzuta ku, kuma kada ku bi
zambiyoyin Shaidan : Lalle ne shi, a
gare ku, makiyi ne bayyananne.
143. Nau'o'i takwas daga tuma-
kai biyu, kuma daga awakai biyu;
ka ce, shin mazan biyu ne Ya ha-
ramta ko matan biyu, ko abin da
mahaifar matan biyu suka tattara a
kansa? Ku ba ni labari da ilmi, idan
kun kasance masu gaskiya.
144. Kuma daga rakuma akwai
nau'i biyu, kuma daga shanu biyu;
ka ce, shin, mazan biyu ne Ya hana
ko matan biyu Ya hana, ko abin da
mahaifar matan biyu suka tattara a
kansa? Ko kun kasance halarce ne a
lokacin da Allah Ya yi muku wa-
siyya da wannan? To, wane ne mafi
<*Zl>A\\',
'•A
tfl^lij^jS
? * \' * s' •.
f *K
.<o
ly Uj^JI l%o^J^ \££^a£Xa
<jCJ»U
&^&£te
'T-» . - r-fs
o^i
213
6 — Suratul An'am
&\\\ l i<*
$M-i
zalunci daga wanda ya kirkira ka-
rya ga Allah, domin ya Batar da
mutane, ba da wani ilmi ba? Lalle
ne, Allah ba Ya shiryar da mutane
azzalumai.
145. Ka ce: "Ba ni samu (1) , a
cikin abin da aka yo wahayi zuwa
gare ni, abin haramtawa, a kan
wani mai ci wanda yake cin sa face
idan ya kasance mushe, ko kuwa
jini abin zubarwa, ko kuwa naman
alade, to, lalle ne shi kazanta ne, ko
kuwa fasikanci wanda aka kuru-
ruta, domin wanin Allah, da shi."
Sa'an nan wanda larura ta kama
shi, ba mai fita jama'a ba, kuma ba
mai ta'addi ba, to, lalle Ubangijin-
ka Mai gafara ne, Mai jin kai.
146. Kuma a kan wadanda suka
tuba (Yahudu) Mun haramta (2) du-
kan mai akaifa, kuma daga shanu
da bisashe Mun haramta musu kit-
sattsansu face abin da bayukansu
suka dauka, ko kuwa kayan ciki, ko
kuwa abin da ya garwaya da kashl
Wannan ne Muka saka musu, sabo-
da zaluncinsu, kuma Mu, hakTka,
Masu gaskiya ne.
147. To, idan sun karyata ka, sai
ka ce: "Ubangijinku Ma'abucin
rahama ne Mai yalwa; kuma ba a
mayar da azabarSa daga mutane
masu laifi."
3j>jLUJL3ij r
6U
~>u
*>J^
(1) Bayanin abubuwan da aka haramta cinsu daga dabbobi wacfanda Allah Ya hana,
ba wacfanda al'ada ta hana ba.
(2) Bayanin abubuwan da Allah Ya hana a kan Yahudu, shi ma hanin an yi shi
saboda wani laifinsu ne.
214
6 — Suratul An 'am
tig&m-^
148. Wacfanda suka yi shirki (1)
za su ce : "Da Allah Ya so, da ba mu
yi shirki ba, kuma da ubanninmu ba
su yi ba, kuma da ba mu haramta
wani abu ba." Kamar wannan ne
mutanen da suke a gabaninsu suka
Jcaryata, har suka dancfani aza-
barMu. Ka ce : "Shin, kuna da wani
ilmi a wurinku domin ku fito mana
da shi? Ba ku bin kome face zato,
kuma ba ku zama ba face Iciri-fadl
kawai kuke yi."
149. Ka ce: "To, Allah ne da
hujja isasshiya, saboda haka: da Ya
so, da Ya shiryar da ku gaba daya."
150. Ka ce: "Ku kawo shaidu-
nku, wadanda suke bayar da shai-
dar cewa Allah ne Ya haramta wan-
nan." To, idan sun kawo shaida,
kada ka yi shaida tare da su. Kuma
kada ka bi son zuciyoyin warfanda
suka icaryata, game da ayoyinMu,
da wadanda ba su yin imani da
Lahira, alhali kuwa su daga
Ubangijinsu suna karkacewa.
151. Ka ce: "Ku zo, in karanta
abin da Ubangijinku Ya haramta."
Wajibi ne a kanku kada ku yi shir-
kin kome da Shi, kuma ga mahaifa
biyu (ku kyautata) kyautatawa,
kuma kada ku kashe cfiyanku sabo-
da talauci, Mu ne Muke arzuta ku,
ku da su, kuma kada ku kusanci
abubuwan alfasha, abin da ya
I'll
06^
(1) Wahayin Shaicfan zuwa ga masu shirki da hana dabbobi da kaga wasu hukunce-
hukunce. Kalmar gaskiya ce ake yin nufin karya da ita, da bayanin warware rikicin. Juyar
da maganar gaskiya domin a yi karya da ita yana sabbaba saukar azaba. Kuma dukan
maganar da ba ta da asali ga Littafi ko sunna, to, ba gaskiya ba ce, bin ta nau'in shirki ne.
215
6 — Suratul An'am
&m&-^
bayyana daga gare ta da abin da ya
66yu, kada ku kashe rai wanda
Allah Ya haramta, face da hakki.
Wannan ne (Allah) Ya yi muku
wasiyya da shi : tsammaninku, kuna
hankalta.
152. Kada ku kusanci dukiyar
maraya face da wadda take ita ce
mafi kyau, har ya kai ga karfinsa.
Kuma ku cika mudu da sikeli da
adalci, ba Mu kallafa wa rai face
iyawarsa. Kuma idan kun facfi ma-
gana, to, ku yi adalci, kuma ko da
ya kasance ma'abucin zumunta ne.
Kuma da alkawarin Allah ku cika.
Wannan ne Ya yi muku wasiyya da
shi: tsammaninku, kuna tunawa.
153. Kuma lalle wannan ne ta-
farkTNa, yana madaidaici : sai ku b!
shi, kuma kada ku bi wasu hanyoyi,
su rarrabu da ku daga barin hany-
aTa. Wannan ne Allah Ya yi muku
wasiyya da shi, tsammaninku, kuna
yin takawa.
154. Sa'an nan kuma Mun bai
wa Musa Littafi, yana cikakke bisa
ga wanda ya kyautata (hukuncin
Allah) da rarrabewa, daki-daki, ga
kowane abu, da shiriya da rahama,
tsammaninsu (1) , suna yinTmani da
haduwa da Ubangijinsu.
755. Kuma wannan Littafi ne,
Mun saukar da shi, mai albarka ne,
sai ku bi shi kuma ku yi takawa,
tsammaninku, ana jin kanku.
\-l * "" j Vj.Lu.in <w«J£jV V ~*\ \i
|p dyes (% ^ 5 =Ja^pSsL^>j p>4»i
4JT-JJ c$ JJbj f(S * JSJ y^^aJUj <>~^i
T- >\A
l^lji^U Jjt2 aiJj^\ vLioJ jc*j
5p 'oy^jSXA
(1) Mabiya Littafin Musa watau Yahudu, idan sun san cewa Alkur'ani kamar
Attaura yake daga Allah aka saukar da shi, kuma Muhammadu Annabin Allah ne kamar
Musa kuma su duka suna gaskata juna, sai su ji saukin Tmani da shi.
216
6 — Suratul An'am
t)g&m-^
156. (Domin) kada ku ce : "Abin
sani kawai, an saukar da Littafi a
kan kungiya (1) biyu daga gaba-
ninmu, kuma lalle ne mu, munjca-
sance daga karatunsu, haklka,
gafilai."
157. Ko kuwa ku ce: "Da dai
lalle mu, an saukar da Littafi a
kanmu, haklka, da mun kasance
mafiya shiryuwa daga gare su." To,
lalle ne wata hujja bayyananniya,
daga Ubangijinku, ta zo muku, da
shiriya da rahama. To, wane ne
mafi zalunci daga wanda ya karyata
game da ayoyin Allah, kuma ya
hinjire daga barinsu? Za Mu saka
wa wacfanda suke hinjirewa daga
barin ayoyinMu da mugunyar aza-
ba, saboda abin da suka kasance
suna yi na hinjirewa.
158. Shin, suna jiran (wani abu),
face dai mala'iku (2) su je musu, ko
kuwa Ubangijinka Ya je, ko kuwa
sashen ayoyin Ubangijinka ya je. A
ranar da sashen ayoyin Ubangijin-
ka yake zuwa,Imanin rai wanda bai
kasance ya yi Tmanin ba a gabani,
ko kuwa ya yi tsiwirwirin wani
alheri, ba ya amfaninsa. Ka ce: "Ku
yi jira: Lalle ne mu, masu jira ne."
,a. „- **' *' >s Xr \'-' l>:
IOJ
(1) Ana magana da masu shirkin Larabawa, kungiyoyin biyu kuwa su ne Yahudu da
Nasara, littafln shT ne Attaura da LinjTla.
(2) Zuwan mala'iku domin kar6ar rayukansu, zuwan Allah umurninSa da a yake su
domin ya fi haushi kansu, zuwan sashen ayoyin Ubangiji shl ne fltowar rana daga yamma
da fitar Rakumar SalThu. Wacfannan abubuwa duka idan sun auku a kan wanda ba shi da
Imani a gabanin aukuwarsu, kuma ya zama ya aikata ayyukan alheri da shari'a ta umurce
shi da yi, to, ba za a kar6i wani imaninsa ba.
217
6 — Suratul An'am
&*M<*
g^t^-n
159. Lalle ne wacfanda (1) suka
rarraba addininsu, kuma suka ka-
sance kungiya-kungiya, kai ba ka
zama daga gare su ba, a cikin kome :
abin sani kawai, al'amarinsu zuwa
ga Allah yake. Sa'an nan Ya ba su
labari game da abin da suka kasan-
ce suna aikatawa.
160. Wanda ya zo da kyakkya-
wan aiki guda, to, yana da goma cfin
misalansa. Kuma wanda ya zoda
mugun aiki guda, to, ba za a saka
masa ba face da misalinsa. Kuma su,
ba a zaluntar su.
161. Ka ce: "Lalle m, Ubangi-
jina Ya shiryar da ni zuwa ga tafarki
madaidaici, addini, klmantawa (ga
abubuwa), mai akidar Ibrahim, mai
karkata zuwa ga gaskiya, kuma bai
kasance daga masu shirki ba."
162. Ka ce: "Lalle ne sallata, da
baikona, da rayuwata, da mutu-
wata, na Allah ne Ubangijin talikai.
163. "Babu abokin tarayya a
gare Shi. Kuma da wancan aka
umurce ni, kuma ni ne farkon
masu sallamawa."
164. Ka ce: "Shin, wanin Allah
nake nema ya zama Ubangiji, alhali
< ^r^N/^r. \i A\ «'.'*<& i<<<\\
\S'-/ -- *t \ '
" t, *>
(1) Bayan bayanin wanda bai yilmani ba sai bayanin sababin rashin karftarTmanin ya
zo, sai kuma ya ci gaba da bayanin cewa, ko wanda ya yi Tmanin idan ya kara wasu
abubuwa a cikin addini bisa ga abin da Allah Ya saukar, ta haka har mutane suka zama
kungiya kungiya, kamar masu cfarikoki na tasawwufi, to, su ma Annabi ba ya tare da su ga
kome domin sun koma wa hanyar Jahiliyya a lokacin da wasu suke kaga hukunce-hukunce
a kan mutane, suka zama da yin haka nan abubuwan bautawa, kuma masu bin su suka
zama mushirikai. Daga nan har zuwa ga karshen Surar duka ta'allki ne ga dukan abin da
Surar ta kunsa na TauhTdin Rububiyya da takaitawa ga bayanin muhimman mas'alolin da
ta kunsa. Saninata shi ne ruhin addini.
218
Suratul An'am
a&B8*--i
kuwa ShT ne Ubangijin dukan
kome? Kuma wani rai ba ya yin
tsirfa face domin kansa, kuma mai
cfaukar nauyi, ba ya cfaukar nauyin
wani, sa'an nan kuma komawarku
zuwa ga Ubangijinku take: sa'an
nan Ya ba ku labari ga abin da kuka
kasance, a cikinsa, kuna saBa wa
juna?
165. "Kuma ShT ne Wanda Ya
sanya ku masu maye wa juna ga
kasa. Kuma Ya cfaukaka sashenku
bisa ga sashe da darajoji : domin Ya
jarraba ku, a cikin abin da Ya ba
ku." Lalle ne, Ubangijinka Mai
gaggawar ukuba ne, kuma lalle ne
Shi, hakTka, Mai gafara ne, Mai jin
kai.
<S>bjj v&jph {^c^lo-* J^=
& 'X *>>
^jJcfjrJ (<JuiU ^£==z\jc>-<sJi lytj
»>'
Tana karantar da tsere a tsakanin gaskiya da karya, tun farko,
kuma halin ba zai gushe ba yana a kan haka, har Tashin Sa'a.
* J* ' L * S *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
1. A. L. M. S.
2. Littafi ne aka saukar zuwa
gare ka, kada wani kunci ya kasan-
ce a cikin kirjinka daga gare shi,
domin ka yi gargacfi da shi. Kuma
tunatarwa ne ga muminai.
219
7 — Suratul A'araf
tQ&M-V
3. Ku bi abin da aka saukar
zuwa gare ku daga Ubangijinku,
kuma kada ku dinga bin wasu maji-
6inta, baicinSa. Kacfan kwarai kuke
tunawa.
4. Kuma da yawa wata alkarya
Muka halaka ta, sai azabarMu ta je
mata da dare ko kuwa suna masu
kailula.
5. Sa'an nan babu abin da yake
da'awarsu, a lokacin da azabarMu
ta je musu, face suka ce: "Lalle ne
mu muka kasance masu zalunci,"
6. Sa'an nan lalle ne Muna tam-
bayar wacfanda aka aika zuwa gare
su, kuma lalle Muna tambayar
Manzannin.
7. Sa'an nan, hakTka, Muna ba
su labari, da ilmi, kuma ba Mu
kasance Masu fakuwa ba.
8. Kuma awo a ranar nan ne
gaskiya. To, wanda sikelansa suka
yi nauyi, to, wacfannan su ne masu
cin nasara.
9. Kuma wanda sikelansa suka
yi sauki, to, wadannan ne wadanda
suka yi hasarar rayukansu, saboda
abin da suka kasance, da ayo-
yinMu, suna yi na zalunci.
10. Kuma lalle ne, hakTka, Mun
sarautar da ku, a cikin kasa, kuma
Mun sanya muku abubuwan rayu-
wa, a cikinta; kadan kwarai kuke
godewa.
11. Kuma lalle ne, hakTka, Mun
halitta ku, sa'an nan kuma Mun
suranta ku, sa'an nan kuma Mun ce
wa mala'iku: "Ku yi sujada ga
l<^rt S > ><C ' ' S ' ^ £ ft
p Ojpoi ^*5L^o^^
220
Suratul A'araf
ifi^-V
Adam." Sai suka yi sujada face
IblTs, bai kasance daga masu yin
sujadar ba (1) .
12. Ya ce : "Mene ne ya hana ka,
ba ka yi sujada ba, a lokacin da Na
umurce ka?" Ya ce: "Nine mafTfici
daga gare shi, Ka halitta ni daga
wuta, alhali kuwa Ka halitta shi
daga laka."
13. Ya ce: "To, ka sauka daga
gare ta: domin ba ya kasancewa a
gare ka ga ka yi girman kai a cikin-
ta. Sai ka fita. Lalle ne kana daga
masu kaskanci."
14. Ya ce: "Ka yi mini jinkiri
zuwa ga ranar da ake tayar (2) da
su."
75. Ya ce: "Lalle ne, kana daga
wacfanda aka yi wa jinkiri. " (3)
16. Ya ce: "To, ina rantsuwa da
halakarwar da Ka yi mini, lalle ne,
ina zaune musu tafarkinKa madai-
daici.
17. "Sa'an nan kuma, haklka, ina
je musu daga gaba gare su (4) , kuma
daga baya gare su, kuma daga barin
f*f^'o^f*4^J£J ftr*^ S#<^
(1) Allah Ya kidanya ni'imomin da Ya yi wa mutane daga talittarsu da suranta su da
Ya yi, kuma Ya girmama su da sanyawar mala'iku su yi sujada ga ubansu Adam, sa'an nan
kuma Ya nuna musu cewa Shaicfan ya ki bin umurninSa ga girmama ubansu Adam,
saboda haka su ma su yi tsoron makiyin kakansu.
(2) Ya roki kada ya mutu, domin a Ranar Rayarwa babu sauran wata mutuwa.
(3) Wannan ya nuna cewa, kowa ya roki Allah wani abu, to, zai ba shi gwargwadon
yadda Yake so, Shi Ubangijin.
(4) Shaicfan yana isa ga dan Adam daga gaba da baya gare su kawai amma wajen
dama da wajen hagu, zai gudu daga barinsu, domin a nan ne mala'iku masu rubutun
ayyuka suke zama ga mutum. Amma sama an hana shi domin ba ya iya shamakance Allah
daga bawanSa, sai wajen kasa, a nan kuma girman kansa, yake hana shi^ya duka, domin
haka ba ya iya sanya waswasi a cikin sujada ga mutum, saboda haka HadTsin ya ce: "Mafi
kusan inda mutum zai sami Ubangijinsa, a wurin sujadarsa."
221
7 - Suratul A'araf
£<<*
tims®-v
jihohin damansu da barin jihohin
hagunsu : Kuma ba za Ka sami mafi
yawansu masu godiya ba.".
18. Ya ce: "Ka fita daga gare ta
kana abin zargi korarre. Lalle ne,
wanda ya bT ka daga gare su, haia-
ka, za Ni cika Jahannama daga gare
ku, gaba daya.
19. "Kuma ya Adam! Ka zauna
kai da matarka a Aljanna, sai ku ci
daga inda kuka so; kuma kada ku
kusanci wannan itaciya, har ku ka-
sance daga azzalumai."
20. Sai Shaidan ya sanya musu
waswasi domin ya bayyana musu
abin da aka rufe daga barinsu, daga
al'aurarsu, kuma ya ce: "Ubangi-
jinku bai hana ku daga wannan
itaciya ba face domin kada ku ka-
sance mala'iku biyu ko kuwa ku
kasance daga madawwama."
21. Kuma ya yi musu rantsuwa:
Lalle ne m, a gare ku, haiaica, daga
masu naslha ne.
22. Sai ya saukar da su da rudi.
Sa'an nan, a lokacin da suka dan-
dani itaciyar, al'aurarsu ta bayyana
a gare su, kuma suka shiga suna
likawar ganye a kansu daga ganyen
Aljanna. Kuma Ubangijinsu Ya
kira su : "Shin, Ban hana ku ba daga
waccan itaciya, kuma Na ce muku,
lalle ne Shaidan, a gare ku, makiyi
ne bayyananne?"
23. Suka ce: "Ya Ubangijinmu !
Mun zalunci kanmu. Kuma idan ba
Ka gafarta mana ba, kuma Ka yi
mana rahama, haklka, muna
kasancewa daga masu hasara."
w *"2'1* '•?*'*? \Y* "
ty<^&X%%tet*iZ
Q3 ^jJ^LSJ^jJaLJIo^LSJ J»l>i^J I
222
Suratul A'araf
im>-y
24. Ya ce: "Ku sauka, sashenku
zuwa ga sashe yana makiyi, kuma
kuna da matabbata a cikin kasa, da
dan jin dadi zuwa ga wani lokaci."
25. Ya ce: "A cikinta kuke rayu-
wa, kuma a cikinta kuke mutuwa,
kuma daga gare ta ake fitar da ku."
26. Ya diyan Adam! Lalle ne
Mun saukar da wata tufa (1) a kan-
ku, tana rufe muku al'aurarku,
kuma da £awa. Kuma tufar takawa
wancan ce mafi alheri. Wancan
daga ayoyin Allah ne, tsammaninsu
suna tunawa!
27. Yadiyan Adam! KadaShai-
dan, lalle, ya fitine ku, kamar yadda
ya fitar da iyayenku biyu daga Al-
janna, yana fizge tufarsu daga gare
su, domin ya nuna musu aTaurarsu.
Lalle ne sm, yana ganin ku, shi da
rundunarsa, daga inda ba ku ganin
su. Lalle ne Mu, Mun sanya Shai-
dan maji6inci ga wadanda ba su yin
Tmani.
28. Kumaidansukaaikataalfas-
ha (2) su ce: "Mun sami ubanninmu
a kanta ;" kuma "Allah ne Ya umur-
ce mu da ita." Ka ce: "Lalle ne,
Allah ba Ya umurni da alfasha:
Shin, kuna facfar abin da ba ku da
saninsa ga Allah?"
29. Ka ce: "Ubangijina Ya yi
umurni da adalci; kuma ku tsayar
^>-
****-** ~ .-ffljgTj
< >s.\
f^^!A^t54^^k4^' J*
(1) Tufar da aka saukar, ita ce addinin Allah. Wanda ya ri£a shi da takawa, to, ya
kyauta £awarsa.
(2) Alfasha ita ce dukan mugun aiki, watau abin da shan'a ba ta zo da shi ba, ko da
an jingina shi ga addini, kamar cfawafi uryan (tsirara) da bauta wa mala'iku da salihai, da
yin kowace ibada ba bisa ga yadda Annabi ya koyar da ita ba.
223
7 — Suratul A'araf
mm*-*
da fuskokinku a wurin kowane
masallaci, kuma ku roke Shi, kuna
masu tsarkake addini gare Shi. Ka-
mar yadda Ya fara halittarku kuke
komawa."
30. Wata kungiya (Allah) Ya
shiryar, kuma wata kungiya 6ata ta
wajaba a kansu; lalle ne su, sun riki
shaicfanu maji6inta, baicin Allah,
kuma suna zaton, lalle su, masu
shiryuwa ne.
31. Ya cfiyan Adam! Ku riki ka-
warku a wurin kowane masallaci,
kuma ku ci, kuma ku sha: kuma
kada ku yi 6arna. Lalle ne Shi (Al-
lah), ba Ya son masu 6arna.
32. Ka ce : "Wane ne ya haramta
kawar Allah, wadda Ya fitar saboda
bayinSa, da masu dadi daga
abinci?" Ka ce: "Su, domin wacfan-
da suka yi Tmani suke a cikin rayu-
war duniya, suna ke6antattu a Ra-
nar Kiyama." Kamar wannan ne
Muke bayyana ayoyi, daki-daki, ga
mutanen da suke sani.
33. Ka ce: "Abin sani kawai,
Ubangijina Ya hana abubwan al-
fasha: abin da ya bayyana daga
gare su da abin da ya 66yu, da
zunubi da rarraba jama'a, ba da
wani hakki ba, kuma da ku yi shirki
da Allah ga abin da bai saukar da
wani daffli ba gare shi, kuma da ku
fadi abin da ba ku sani ba, ga
Allah."
34. Kuma ga kowace aFumma
akwai ajali : sa'an nan idan ajalinsu
ya je, ba za a yi musu jinkiri ba, sa'a
guda, kuma ba za su gabace shi ba.
^^^^^^^•J^*l5^? 6 -**4 , ^^
>* *** .^f < 4 \i> 's "*' i
a&k / >t *4 >-f ^ > ^•Z'
[jrp J*r~J \ C*£ X4*\\ J>j~a Yj IjtrM*
Sjj^tii^^^y +&\ig j^jsjJhj
ip ^j^^oill^j^L-
224
7 — Suratul A'araf
fi!&fi&-V
35. Ya cfiyan Adam! Ko dai
wasu manzanni, daga cikinku, su je
muku, suna gaya muku ayoyiNa —
to, wanda ya yi takawa, kuma ya
gyara aikinsa — to, babu tsoro a
kansu, kuma ba su yin bakin ciki.
36. Kuma warfanda suka kary-
ata game da ayoyinMu, kuma suka
yi girman kai daga gare su, watfan-
nan su ne abokan wuta, su, a cikin-
ta madawwama ne.
37. To, wane ne mafi zalunci
daga wanda ya kirkira karya ga
Allah, ko kuwa ya karyata game da
ayoyinSa? Wadannan rabonsu
daga Littafi yana samunsu, har a
lokacin da ManzanninMu suka je
musu, suna kar6ar rayukansu, su
ce : "Tna abin da kuka kasance kuna
kira, baicin Allah?" Su ce: "Sun
6ace daga gare mu," kuma su yi
shaida a kansu cewa lalle su, sun
kasance kafirai.
38. Ya ce: "Ku shiga a cikin
al'ummai wadanda, haiaka, sun
shige daga gabaninku, daga aljannu
da mutane, a cikin wuta. A ko da
yaushe wata aFumma ta shiga sai ta
la'ani 'yar'uwarta, har idan suka
riski juna, a cikinta, gaba daya, ta
karshensu ta ce wa ta farkonsu:
'Ya Ubangijinmu! Wadannan ne
suka 6atar da mu, sai Ka kawo
musu azaba ninki daga wuta.'" Ya
ce: "Ga kowane (1) akwai ninki:
kuma amma ba ku sani ba."
by^aJU *S<^S^J Ji^2^bMr^*Tfi
** y .y,
'<i
(1) Shugabannin 6a ta su ne ke fara shiga wuta, sa'an nan mabiyansu, su shiga, domin
shugabanni suna da laifl biyu; nasu, na aikinsu, da kuma sababin da suka yi, na Batar da
mabiyansu. Kuma an fahimta daga nan cewa "Ina bin wane a kan Bata, shine ya Batar da
225
Suratul A'araf
llj^-v
39. Kuma ta farkonsu ta ce wa ta
karshe: "To, ba ku da wata falala a
kanmu, sai ku cfancfana azaba sabo-
da abin da kuka kasance kuna tar-
awa!"
40. Lalle ne wacfanda suka kar-
yata game da ayoyinMu, kuma
suka yi girman kai daga barinsu, ba
za a bubbucfe musu kofofin sama
ba, kuma ba su shiga Aljanna sai
gindi (1) ya shiga kafar allura, kuma
kamar wannan ne Muke saka wa
masu laifi.
41. Suna da wata shimficfa daga
Jahannama kuma daga samansu
akwai wasu murafai. Kuma kamar
wancan ne Muke saka wa azza-
lumai.
42. Kuma wacfanda suka yi Tma-
ni, kuma suka aikata ayyukan kwa-
rai — ba Mu kallafa wa rai face
iyawarsa — wacfannan ne abokan
Aljanna, su, a cikinta, madawwama
ne.
43. Kuma Muka fitar da abin da
yake a cikin kirazansu, daga
kiyayya, koramu suna gudana daga
karkashinsu, kuma suka ce: "G6-
diya ta tabbata ga Allah, Wanda Ya
shiryar da mu ga wannan. Kuma ba
mu kasance muna iya shiryuwa ba,
ba domin da Allah Ya shiryar da mu
<'•>>>
CU'o
ni," ba ya zama hujja mai hana shiga wuta, domin Allah Ya aza wa kowane baligi mai
hankali da ya yi binciken gaskiya gwargwadon iyawarsa. Allah ba Ya kama mutum da
abin da ba ya a cikin Tkonsa.
(1) Gindi shi ne igiya babba wadda ake hawan itacen dablno da shi, ko kuma a daure
doki da shi. Tun da gindi ba zai shiga a kafar allura ba haka miyagun malamai masu
kirkira karya su jingina ta ga Allah ko kuma su karyata ayoyin Allah, ba za su shiga
Aljanna ba, su da mabiyansu duka. Sun yi fada da gaskiya.
226
7 — Suratul A'araf
llM-v
ba. Lalle ne, hakiica, Manzannin
Ubangijinmu, sun je mana da gas-
kiya." Kuma aka kira su, cewa:
"Waccan Aljanna an gadar da ku
ita, saboda abin da kuka kasance
kuna aikatawa."
44. Kuma abokan Aljanna suka
kirayi abokan Wuta suka ce : "Lalle
ne mun sami abin da Ubangijinmu
Ya yi mana wa'adi, gaskiya ne. To,
shin, kun sami abin da Ubangijinku
Ya yi muku wa'adi, gaskiya?" Suka
ce: "Na'am." Sai mai sanarwa ya yi
yekuwa, cewa: "La'anar Allah ta
tabbata a kan azzalumai."
45. "Wadanda suke kangewa
daga hanyar Allah, kuma suna ne-
man ta ta zama karkatacciya, % kuma
su, game da Lahira, kafirai ne."
46. Kuma a tsakaninsu akwai
wani shamaki (1) , kuma a kan
A'araf akwai wasu maza suna sanin
kowa da alamarsu: Kuma suka ki-
rayi abokan Aljanna cewa: "Amin-
ci ya tabbata a kanku:" Ba su shige
ta ba, alhali kuwa su, suna tsamma-
ni.
47. Kuma idan an juyar da gan-
nansu wajen abokan Wuta, su ce:
"Ya Ubangijinmu! Kada Ka sanya
mu tare da mutane azzalumai."
48. Kuma abokan A'araf suka
kirayi wasu maza, suna sanin su da
alamarsu, suka ce: "Tarawar duki-
yarku da abin da kuka kasance
^J^ S" i'l' "
pLaUj ^il>- j^x-^l U \y 6
(1) A tsakanin Aljanna da Wuta akwai bango, ana ce masa A'araf, inda za a ajiye
mutanen da ayyukansu na kwarai suka yi daidai da miyagun ayyukansu. Suna ganin
mutanen Aljanna suna yi musu sallama suna gurin shigarta, kuma suna ganin mutanen
Wuta; suna la'anar su, suna neman nisanta daga gare ta.
227
7 - Suratul A'araf
($&!&& -V
kuna yi na girman kai, bai wadatar
ba daga barinku?"
49. "Shin, wadannan ne wadan-
da kuka yi rantsuwa, Allah ba zai
same su da rahama ba? Ku shiga
Aljanna, babu tsdro a kanku, kuma
ba ku zama kuna bakin ciki ba/ 9
50. Kuma abokan Wuta suka
kirayi abokan Aljanna cewa: "Ku
zubo a kanmu daga ruwa ko kuwa
daga abin da Allah Ya arzuta ku."
Su ce: "Lalle ne Allah Ya haramta
su a kan kafirai.
51. "Wadanda suka ri£i addi-
ninsu abin shagala da wasa, kuma
rayuwar duniya ta rude su." To, a
yau Muna mantawa da su, kamar
yadda suka manta da haduwa da
yininsu wannan, da kuma abin da
suka kasance da ayoyinMu suna
musu.
52. Kuma lalle ne, haklka, Mun
je musu da Littafi, Mun bayyana
shi, daki-daki, a kan ilmi, yana
shiriya da rahama ga mutane wa-
danda suke yin Tmani.
53. Shin, suna jira, face fassa-
rarsa, a ranar da fassararsa take
zuwa, wadanda suka manta da shi
daga gabani, suna cewa : "Lalle ne,
Manzannin Ubangijinmu sun je da
gaskiya. To, shin, muna da wasu
masu ceto, su yi ceto gare mu, ko
kuwa a mayar da mu, har mu aikata
wanin wanda muka kasance muna
aikatawa?" Lalle ne sun yi hasarar
rayukansu, kuma abin da suka ka-
sance suna klrkirawa ya Bace musu.
W-*b W (M^e^ JL ^ >tj ' ^*y"
Py ^>A^££^l*>
*>^.*t->
JE
c > ^ -x SA
-OS
228
Suratul A'araf
w*-i8^-v
54. Lalle ne Ubangijinku Allah
ne, wanda Ya halitta sammai da
kasa a cikin kwanaki shida, sa'an
nan kuma Ya daidaita a kan Al'ars-
hi, Yana sanya dare ya rufa yini,
yana neman sa da gaggawa, kuma
rana da wata da taurari horarru ne
da umurninSa. To, Shi ne da halit-
tar kuma da umurnin. Albarkar
Allah Ubangijin halittu ta bayyana !
55. Ku kirayi Ubangijinku da
kankan da kai, da kuma a 66ye:
lalle ne Shi, ba Ya son masu wuce
iyaka.
56. Kuma kada ku yi barna a
cikin kasa a bayan gyaranta. Kuma
ku kiraye Shi saboda tsoro da
tsammani: lalle ne, rahamar Allah
makusanciya ce daga masu kyau-
tatawa.
57. Kuma Shi ne Wanda Yake
aika iskoki, suna bishara gaba ga
rahamarSa, har idan sun cfauki
gizagizai masu nauyi, (1) sai Mu
kora su ga wani gari matacce, sa'an
nan Mu saukar da ruwa gare shi,
sa'an nan Mu fitar, game da shi,
^Ti^yjc-^Vt,
(1) Ya kamanta hadari da ruwa da Alihir'ani da abin da ya £unsa, da sifanta £asa
busasshiya da jahilci, da zuciyar imani da gari mai kyau, da ziiciyar kafirci da mugun gari,
kuma rayuwa daTmani da mutuwa da tashi. Annabi ya ce, "Misalin abin da Allah Ya aiko
ni da shi na ilmi da shiriya kamar ruwa ne mai yawa, ya sami wata £asa. To, ta zama daga
cikinta akwai mai kyau, ta karbi ruwa, sa'an nan ta tsirar da ciyawa da tsatse mai yawa.
Kuma ta zama daga gare ta akwai rafuka, suka ri£e ruwa Allah Ya amfani mutane da shi,
suka sha, suka shayar kuma suka yi shuka. Kuma daga cikinta akwai nau'i, fa£an£ani ba
ya ri£on ruwa, kuma ba ya tsirar da ciyawa, wannan shi ne misalin wanda ya fahimci
addinin Allah, kuma abin da Allah Ya aiko ni da shi, ya amfane shi, ya sani kuma ya sanar,
da wanda bai dauka kai ba gare shi, kuma bai karbi shiriyar Allah ba wadda aka aiko ni da
ita." Kuma ana fahimtar cewa kullum akwai fada mai dogewa a tsakaninsu, domin su,
kTshiyoyin juna ne.
229
7 - Suratul A'araf
m-v
daga dukkan 'ya'yan itace. Kamar
wancan ne Muke fitar da matattu:
tsammaninku, kuna tunani.
58. Kuma gari mai kyau, tsirinsa
yana fita da iznin Ubangijinsa,
kuma wanda ya munana (tsirinsa)
ba ya fita, face da wahala: kamar
wannane ne, Muka sarrafa ayoyi
domin mutane wacfanda suke
godewa.
59. Lalle ne, halaica, Mun aika
Nuhu zuwa ga mutanensa, sai ya ce :
"Ya mutanena ! Ku bauta wa Allah !
Ba ku da wani^abin bautawa wan-
inSa. Lalle ne nT, ina yi muku tsoron
azabar wani Yini mai girma."
60. Mashawarta (1) daga mu-
tanensa suka ce: "Lalle ne mu,
halaica, muna ganin ka a cikin bata
bayyananniya."
61. Ya ce: "Ya mutanena! Babu
bata guda gare ni, kuma amma nT,
Manzo ne daga Ubangijin halittu!
62. "Ina iyar muku da salconnin
Ubangijina: kuma ina yi muku na-
slha, kuma ina sani, daga Allah,
abin da ba ku sani ba.
63. "Shin, kuna mamakin cewa
ambato ya zo muku daga Ubangi-
jinku a kan wani namiji, daga gare
ku, domin ya yi muku gargacfi,
kuma domin ku yi talcawa, kuma
tsammaninku ana jin Icanku?"
pi&v£dxM,&\
If'***"' * >>y">> 9
»»^<^>^
^ S tf^~S »'. '£?+
*< <i \* > ST 1 * x 'f
9 %"\' *\\ ">\ " 9 < M*- %"w' <*\
3 j*~sJa&s y <*->\J^
Is**'.'
.JJL^^db^S ^y^xJ* 3^
l9 uv»
©o>j;A»jy^r
(1) Kissar Nuhu da mutanensa tana nuna yanda annabawa masu kawo gaskiya ke yin
facfa da miyagun mutane masu kin gaskiya, suna kokarin rufe ta. Haka kuma kissoshin da
ke tafe a bayanta suna nuna yadda karya ke facfa da gaskiya, ta hanyoyi dabam-dabam.
230
Suratul A'araf
«8&»-V
64. Sai suka karyata shi, sa'an
nan Muka tsTrar da shi da wacfanda
suke tare da shi, a cikin jirgin : kuma
Muka nutsar da wacfanda suka kar-
yata shi game da ayoyinMu. Lalle
ne su, sun kasance wasu mutane
cfimautattu.
65. Kuma zuwa ga Adawa, cfa-
n'uwansu Hudu, ya ce: "Ya^muta-
nena ! Ku bautanva Allah ! Ba ku da
wani abin bauta wa, waninSa. Shin
fa, ba za ku yi takawa ba?"
66. Mashawarta wacfanda suka
kafirta daga mutanensa suka ce:
"Lalle ne mu, hakTka, muna ganin
ka a cikin wata wauta ! Kuma lalle
ne mu, haklka, muna zaton ka daga
makaryata."
67. Ya ce: "Ya mutanena! Babu
wata wauta a gare ni, kuma amma
nl, Manzo ne daga Ubangijin
halittu!
68. "Ina iyar muku da sakonnin
Ubangijina, kuma m, gare ku, mai
nasTha ne amintacce.
69. "Shin, kuma kun yi mamaki
cewa ambato daga Ubangijinku ya
zo muku a kan wani namiji daga
gare ku, domin ya yi muku gargacfi ?
Kuma ku tuna a lokacin da Ya
sanya ku masu mayewa daga bayan
mutanen Nuhu, kuma Ya kara
muku zati a cikin halitta. Saboda
haka ku tuna ni'imomin Allah:
tsammaninku kuna cin nasara."
70. Suka ce: "Shin, ka zo mana
ne domin mu bauta wa Allah Shi
kacfai, kuma mu bar abin da
'< '.' >' °" s^i '* "\ \'~ » tl^iC
231
7 - Suratul A'araf
ig£M£-v
ubanninmu suka kasance suna bau-
ta wa? To, ka zo mana da abin da
kake yi mana wa'adi da shi, idan ka
kasance daga masu gaskiya."
71. Ya ce: "Hakika azaba da
fushi sun auku a kanku daga
Ubangijinku! Shin, kuna jayayya
da ni a cikin wasu sunaye wacfanda
ku ne kuka yi musu sunayen, ku da
ubanninku, Allah bai saukar da
wani dalili ba a gare su? To, ku yi
jira. Lalle ne ni, tare da ku mai jira
ne.
72. To, sai Muka tsTrar da shi,
shT da wadanda suke tare da shi
saboda wata rahama daga gare Mu,
kuma Muka katse karshen wadan-
da suka karyata game da ayo-
yinMu, kuma ba su kasance mumi-
nai ba.
73. Kuma zuwa ga Samudawa
dan'uwansu, Salihu, ya ce: "Ya
mutanena ! Ku bauta wa Allah ; ba
ku da wani abin bauta wa wannin-
Sa. HakTka hujja bayyananniya ta
zo muku daga Ubangijinku! Wan-
nan rakumar Allah ce, a gare ku,
wata aya ce. Sai ku bar ta ta ci, a
cikin kasar Allah, kuma kada ku
shafe ta da wata cuta har azaba mai
racfadi ta kama ku.
74. "Kuma ku tuna a lokacin da
Ya sanya ku mamaya daga bayan
Adawa, kuma Ya zaunar da ku a
cikin kasa, kuna rikon manyan gi-
daje daga tuddanta, kuma kuna
sassakar dakuna daga duwatsu; sa-
boda haka ku tuna ni'imomin Al-
»- sc*t * *> M^V^ It"
r > i ^
P^==£C* jn^^u 4 jJaJL- u^L^
k /ft"
232
7 — Suratul A'araf
v*rA$&~V
lah, kuma kada ku yi 6arna a cikin
kasa kuna masu fasadi." (1)
75. Mashawarta, wadanda suka
yi girman kai daga mutanensa suka
ce ga wadanda aka raunanar, (2) ga
wadanda suka yi Tmani daga gare
su: "Shin, kuna sanin cewa Salihu
manzo ne daga Ubangijinsa?" Suka
ce: "Lalle ne mu, da abin da aka
aiko shi, masu Tmani ne."
76. Wadanda suka yi girman kai
suka ce: "Lalle ne mu, ga abin da
kuka yi Tmani da shi kafirai ne."
77. Sai suka soke rakumar, ku-
ma suka kangare daga barin umu-
rnin Ubangijinsu, kuma suka ce:
"Ya Salihu ! Ka zo mana da abin da
kake yi mana wa'adi da shi, idan ka
kasance daga manzanni!"
78. Sai tsawa ta kama su, saboda
haka suka wayi gari a cikin gidansu
guggurfane !
79. Sai ya juya daga barinsu,
kuma ya ce: "Ya mutanena! Lalle
ne, hakTka, na iyar muku da man-
zancin Ubangijina. Kuma na yi
muku nasTha, kuma amma ba ku
son masu nasTha!"
80. Da Ludu, a lokacin da ya ce
wa mutanensa: "Shin, kuna je wa
alfasha, babu kowa da ya gabace ku
da ita daga halittu?
-**y ^l^ \jl£^===i^\<j^\ ^uii jis
• > *> ,f X
(1) Fasadi kalmar Larabci ce, ma'anarta Barna. Watau an ce musu kada su yi Barna
cikin Barna domin haka nan zai sanya Barnar ta game kasa duka har ba za a gane muninta
ba.
(2) Shugabanni suka ce wa mabiyansu masu rauni, wadanda suka yi Tmani da
Manzon Allah Salihu. Amma ba su yi magana da masu karfin Tmani ba, domin sun yanke
kauna daga gare su.
233
7 - Suratul A'araf
mm&-v
81. "Lalle ne ku, hakTka, kuna je
wa maza da sha'awa, baicin mata:
A'a, ku mutane ne ma6arnata."
82. Kuma babu abin da ya ka-
sance jawabin mutanensa, face dai
suka ce : "Ku fitar da su daga alkar-
yarku : lalle ne su, wasu mutane ne,
masu da'awar tsarki!"
83. Sai Muka tslrar da shi, shlda
iyalansa, face matarsa, ta kasance
daga masu wanzuwa.
84. Kuma Muka yi ruwa a kansu
da wani irin ruwa: sai ka duba
yadda akibar masu laifi ta kasance !
85. Kuma zuwa Madayana da-
n'uwansu Shu'aibu, ya ce: "Ya
mutanena! Ku bauta wa Allah; ba
ku da wani abin bauta wa, waninSa.
Lalle ne, wata hujja bayyananniya
daga Ubangijinku ta zo muku! Sai
ku cika mudu da sikeli, kuma kada
ku nakasa wa mutane kayansu,
kuma kada ku yi fasadi a cikin kasa
a bayan gyaranta. Wannan ne mafi
alheri a gare ku, idan kun kasance
muminai.
86. "Kuma kada ku zauna ga
kowane tafarki kuna kyacewa,
kuma kuna kangewa, daga hanyar
Allah, ga wanda ya yi Tmani da Shi,
kuma kuna neman ta ta zama
karkatacciya, kuma ku tuna, a 16-
kacin da kuka kasance kadan, sai
Ya yawaita ku, kuma ku duba yad-
da akibar masu fasadi ta kasance.
87. "Kuma idan wata kungiya
daga gare ku ta kasance ta yi Tmani
da abin da aka aiko ni da shi, kuma
wata kungiya ba ta yi Tmani ba, to,
o-
>j<>*r-*£/^
*' »'<
»Jv
/-. l\ >-^
S V-'
234
7 — Suratul A'araf
$&.$&- v
ku yi hakuri, har Allah Ya yi hukun-
ci a tsakaninmu ; kuma Shi ne Mafi
alherin masu hukunci."
88. Mashawarta wacfanda suka
kangare daga mutanensa, suka ce:
"Lalle ne, muna fitar da kai, Ya
Shu'aibu, kai da wacfanda suka yi
Tmani tare da kai, daga alkaryarmu ;
ko kuwa lalle ku komo a cikin
addininmu." Ya ce: "Ashe! Kuma
ko da mun kasance masu kl?"
89. "Lalle ne mun kirkira karya
ga Allah idan mun koma a cikin
addininku a bayan lokacin da Allah
ya tslrar da mu daga gare shi, kuma
ba ya kasancewa a gare mu, mu
koma a cikinsa, face idan Allah,
Ubangijinmu Ya so. Ubangijinmu
Ya yalwaci dukan kome ga ilmi. Ga
Allah muka dogara. Ya Ubangi-
jinmu! Ka yi hukunci a tsakaninmu
da tsakanin mutanenmu da gas-
kiya, kuma Kai ne Mafi alherin
masu hukunci."
90. Kuma mashawarta wacfanda
suka kafirta daga mutanensa, suka
ce: "Lalle ne, idan kun bi Shu'aibu,
haklka ku, a lokacin nan, masu
hasara ne."
91. Sai tsawa ta kama su, saboda
haka suka wayi gari, a cikin gidan-
su, suna guggurfane.
92. Wacfanda suka karyata
Shu'aibu kamar ba su zauna ba a
cikinta, wacfanda suka karyata Shu'-
aibu, sun kasance su ne masu
hasara !
93. Sai ya juya daga barinsu,
kuma ya ce: "Ya mutanena! Hakl-
235
Suratul A'araf
t^tl^-v
ka, na iyar muku da sakonnin
Ubangijina, kuma na yi muku nasT-
ha ! To, yaya zan yi bakin ciki a kan
mutane kafirai?"
94. Kuma ba Mu aika wani
annabi (1) a cikin wata alkarya ba,
face Mun kama mutanenta da aza-
ba da cuta, tsammaninsu suna yin
kaskantar da kai.
95. Sa'an nan kuma Muka mu-
sanya mai kyau a matsayin mum-
muna, har su yi yawa, kuma su ce :
"Cuta da azaba sun shafi uban-
ninmu." (Sai su koma wa
kafirci)... Sai Mu kama su kwat-
sam! alhali kuwa su, ba su sansan-
cewa.
96. Kuma da lalle mutanen alka-
ryu sun yi Tmani kuma suka yi
takawa, da, hakTka, Mun bucfe
albarkoki a kansu daga sama da
kasa, kuma amma sun karyata, don
haka Muka kama su da abin da
suka kasance suna tarawa.
97. Shin, mutanen alkaryu sun
amince wa azabarMu ta je musu da
dare, alhali kuwa suna barci?
98. K6 kuwa mutanen alkaryu
sun amince wa azabarMu ta je musu
da hantsi, alhali kuwa suna wasa?
99. Shin fa, sun amince wa
makarun Allah? To, babu mai
amince wa makarun Allah face mu-
tane masu hasara!
' \' .7r>:
*K*
^S*\*
> , s",s + s sis'
im oj-^t^Aj
» ^>^4il_^:
(1) Daga aya ta 94 zuwa ay a ta 103 duka tallki ne domin farkarwa ga muhimman
maganganu wacfanda kissoshin Annabawan nan da mutanensu suka kunsa, kuma aka ce
haka dai sauran annabawa da ba a facfa ba suka zauna da mutanensu a cikin facfa a
tsakanin gaskiya da karya.
236
Suratul A'araf
li^-V
100. Shin, kuma bai shiryar da
wacfanda suke gadon kasa ba daga
bayan mutanenta cewa da Muna so,
da Mun same su da zunubansu,
kuma Mu rufe a kan zukatansu, sai
su zama ba su ji?
101. Wadancan alkaryu Muna
gaya maka daga labaransu, kuma
lalle ne, haklka manzanninMu sun
je musu da hujjoji bayyanannu; to,
ba su kasance suna yin Tmani da
abin da suka karyata daga gabani
ba. Kamar wancan ne Allah Yake
rufewa a kan zukatan kafirai.
102. Kuma ba Mu sami wani
alkawari ba ga mafi yawansu, kuma
lalle ne, Mun sami mafi yawansu,
hakTka, fasikai.
103. Sa'an nan kuma Mun aika
Musa, (1) daga bayansu, da ay 6-
yinMu zuwa ga Fir'auna da maja-
lisarsa, sai suka yi zalunci game da
su. To, dubi yadda akibar maBar-
nata take.
104. Kuma Musa ya ce: "Ya
Fir'auna ! Lalle ne nl, manzo ne daga
Ubangijin halittu.
105. "Tabbatacce ne a kan kada
in facfi kome ga Allah face gaskiya.
Lalle ne, na zo muku da hujja
bayyananniya daga Ubangijinku:
sai ka saki BanTlsra'ila tare da ni."
106. Ya ce: "Idan ka kasance ka
zo da wata aya, to, ka kawo ta, idan
ka kasance daga masu gaskiya."
-^ J ^-H W ' ot <^Qg (j*** ££yu ' <^%
* ^ \\\' 9 "\"
bi>.j o[j ^4-^a* ^J^^X^^J^J
<UiLL^>
( 1 ) An fltar da Icissar Bani Isra'ila dabam, domin ta kunsa abubuwa masu yawa na
facfa a tsakanin karya da gaskiya, ta hanyoyi masu yawa, a bayyane da 66ye a cikin addini.
237
Suratul A'araf
fflgifflj^-v
707. Sai ya jefa sandarsa, sai ga
ta kumurci bayyananne!
108. Kuma ya fizge hannunsa,
sai ga shi fari ga masu dubi!
109. Mashawarta daga mutanen
Fir'auna suka ce: "Lalle ne, wan-
nan, hakika, masihirci ne mai ilmi."
110. "Yana son ya fitar da ku
daga kasarku: To, mene ne kuke
shawartawa?"
111. Suka ce: "Ka jinkirtar da
shi, shi da dan'uwansa, kuma ka
aika da masu gayyar mutane a cikin
garuruwa — .
112. "Su zo maka da duka masi-
hirci, mai ilmi."
113. Kuma masihirta suka je wa
Fir'auna, suka ce: "Lalle ne, shin,
muna da ijara, idan mun kasance
mu ne marinjaya?"
114. Ya ce: "Na'am, kuma lalle
ne kuna a cikin makusanta."
115. Suka ce : "Ya Musa ! Ko dai
ka jefa, ko kuwa mu kasance, mu
ne, masu jefawa?"
116. Ya ce: "Ku jefa." To, a
lokacin da suka jefa, suka sihirce
idanun mutane, kuma suka tsoratar
da su: kuma suka je da sihiri mai
girma.
117. Kuma Muka yi wahayi
zuwa ga Musa cewa: "Ka jefa
sandarka." Sai ga ta tana lakumar
abin da suke karya da shi!
118. Gaskiya ta auku, kuma
abin da suke aikatawa ya 6aci.
6. y * s y ^y y 9t s 9 9 ' \ y s *••* y y
238
Suratul A'araf
3*$&-v
119. Sai aka rinjaye su a can,
kuma suka juya suna kaskantattu.
120. Kuma aka jefar da masi-
hirta, suna masu sujada.
121. Suka ce: "Mun yi imani da
Ubangijin halittu.
122. "Ubangijin Musa da Ha-
riina."
123. Fir'auna ya ce: "Ashe, kun
yi imani da shi a gabanin in yi izni a
gare ku? Lalle ne, wannan, haJcTlca,
makirci ne kuka makirta a cikin
birni, domin ku fitar da mutanensa
daga gare shi: To, da sannu za ku
sani.
124. "Lalle ne, ina karkatse
hannayenku da kafafunku daga sa-
6ani, sa'an nan kuma, hakTka, ina
tsTre ku gaba daya."
125. Suka ce: "Lalle ne mu,
zuwa ga Ubangijinmu, masu ju-
yawa ne.
126. "Kuma ba ka zargin kome
daga gare mu face domin mun yi
Imani da ayoyin Ubangijinmu a
lokacin da suka zo mana! Ya
Ubangijinmu! Ka zuba hakuri a
kanmu, kuma Ka cika mana muna
Musulmai! (1) "
127. Kuma mashawarta daga
mutanen Fir'auna suka ce: "Shin,
(1) Musulmi shi ne wanda ya sallama kansa ga hukunce-hukuncen Allah wacfanda
wani annabin Allah ya zo da su, a cikin zamaninsa. Saboda haka ma'anar Musulmi shi ne
mai sallamawa ga hukuncin Allah, a kowane zamani, tun daga Adamu har zuwa Ranar
FCiyama. Sai dai wannan al'umma ta Muhammadu ta kebanta da sunan Musulmi, addinin
kuma da sunan Musulunci.
239
Suratul A'araf
$&»-v
za ka bar Musa da mutanensa, do-
min su yi Barna a cikin £asa, kuma
ya bar ka, kai da gumakanka?" Ya
ce : "Za mu yayyanka diyansu maza
kuma mu raya matansu; kuma lalle
ne mu, a bisa gare su, marinjaya
ne.
128. Musa ya ce wa muta-
nensa (1) : "Ku nemi taimako da
Allah, kuma ku yi haicuri : Lalle ne
£asa ta Allah ce, Yana gadar da ita
ga wanda Yake so daga bayinSa,
kuma a£iba ta masu ta£awa ce."
129. Suka ce: "An cutar da mu
daga gabanin ka zo mana, kuma
daga bayan da ka zo mana." Ya ce:
"Akwai tsammanin Ubangijinku,
Ya halaka ma£iyanku, kuma Ya
sanya ku, ku maye a cikin £asa,
sa'an nan Ya duba yadda kuke aika-
tawa."
130. Kuma lalle ne, haiclica, Mun
kama mutanen Fir'auna da tsa-
nanin shekaru (fari) da nakasa daga
'ya'yan itace: tsammaninsu suna
tunawa.
131. Sa'an nan idan wani alheri
ya je musu, sai su ce: "Wannan
namu ne," kuma idan maslfa ta
same su, sai su yi shu'umci da Musa
da wanda yake tare da shi! To,
shu'umcinsu a wurin Allah yake,
kuma amma mafi yawansu ba su
sani!
^Xr4p>
\~* »<" -Z' f >
its &> \^2>£ *jjdl\dJi
. -iff • * > -
*>'*^
0^^
(1) Maganar Musa ga Ban! Isra'ila ta nuna cewa sun ga azabar ta yi musu yawa, har
sun fara zargin Musa da cewa ya sabbaba musu tsananin fitinar, da zowarsa. Shi kuma ya
lallashe su da cewa, "Kome ya yi tsanani, to, saukinsa ya yi kusa."
240
Suratul A'araf
■$mm-v
132. Kuma suka ce: "K6 me ka
zo mana da shi daga aya, domin ka
sihirce mu da ita, to, ba mu zama,
saboda kai, masu Tmani ba."
133. Sai Muka aika a kansu da
cikowa, da fara, da kwarkwata da
kwacfi da jini : ayoyi abubuwan
rarrabewa (1) : sai suka kangare,
kuma suka kasance mutane masu
laifi.
134. Kuma a lokacin da maslfa
ta auku a kansu, sukan ce: "Ya
Musa! Ka rdJca mana Ubangijinka,
saboda abin da Ya yi alkwari a
wurinka, lalle ne idan ka kau da
azabar daga barinmu, haJoka muna
Tmani saboda kai, kuma muna sakin
Bam Isra'ila tare da kai."
135. To, a lokacin da Muka ku-
ranye azaba daga barinsu zuwa ga
wani ajali wanda suke masu iske shi
ne, sai ga su suna warwarewa!
136. Sai Muka yi azabar ramu-
wa, daga gare su, saboda haka
Muka nutsar da su a cikin teku,
domin lalle ne su, sun karyata game
da ayoyinMu, kuma sun kasance
daga barinsu, gafilai.
137. Kuma Muka gadar da mu-
tanen, wadanda sun kasance ana
raunana su, a gabacin kasa da
yammacinta, wadda Muka sanya
albarka a cikinta, kuma kalmar
Ubangijinka mai kyau ta cika a kan
llil^ Uj^LjJ j^o^^^^i*!? ^j
(1) Ayoyin da suka je musu a cikin lokatai daban-daban domin a ja hankalinsu, ko
za su yi Tmani. Kowace aya tana kwana bakwai suna wahala da ita, sa'an nan su ro£i Musa
ya yi addu'a a kuranye ta, sa'an nan a bayan wani lokaci sai su koma wa kafircinsu, kamar
yadda ayoyi masu biyar wannan suka bayyana.
241
Suratul A'araf
<&!&»- V
BanT Isra'ila, saboda abin da suka yi
na hakuri. Kuma Muka murtsuke
abin da Fir'auna da mutanensa,
suka kasance suna sana'antawa, da
abin da suka kasance suna shim-
fidawa. (1)
138. Kuma Muka ketarar da
BanT Isra'ila ga teku, sai suka je a
kan wasu mutane wadanda suna
lizimta da ibada a kan wasu gu-
maka, nasu, suka ce: "Ya Musa!
Ka sanya mana wani abin bautawa
kamar yadda suke da abubuwan
bautawa. " (2) Ya ce: "Lalle ne ku,
mutane ne kuna jahilta.
139. "Lalle newadannan, abin da
suke a cikinsa halakakke ne, kuma
abin da suka kasance suna aikatawa
karya ne."
140. Ya ce: "Shin, wanin Allah,
nike nema muku ya zama abin bau-
tawa, alhali kuwa Shi (Allah) Ya
fifita ku a kan halittu?"
141. Kuma a lokacin da Muka
tsTrar da ku daga mutanen Fir'au-
na, suna taya muku mugunyar aza-
ba. 'Suna karkashe diyanku maza,
kuma suna rayar da matanku.'
Kuma a cikin wancan akwai jarra-
bawa daga Ubangijinku, (3) Mai
girma.
(1) Wannan shi ne karshen kissar facfan gaskiya daga wajen Musa da karya daga
wajen Fir'auna da rundunarsa da dukiyarsa. Haka dai karya kome duhunta, to, na banza
ne, a karshe za ta watse.
(2) Farkon facfan karya da gaskiya a tsakanin BanT Isra'ila da Musa wajen son
komawa ga al'adu da kari a cikin addini ta hanyar bidi'a.
(3) Lamlrin Musulmi ne wacfanda ake yi wa magana yanzu a harshen Muhammadu,
domin su wa'aztu da labarun mutanen farko.
242
7 — Suratul A'araf
mmst-v
142. Kuma Muka yi wa'adi ga
Musa da dare talatin, (1) kuma
Muka cika su da goma, sai mikatin
Ubangijinsa ya cika dare arba'in.
Kuma Musa ya ce wa tfan'uwansa,
Haruna: "Ka maye mini a cikin
mutanena, kuma ka gyara, kuma
kada ka bi hanyar masu fasadi."
143. Kuma a lokacin da Musa ya
je ga mTkatinMu, kuma Ubangi-
jinsa Ya yi masa magana, shi Musa
ya ce: "Ya Ubangijina! Ka nuna
mini in yi dubi zuwa gare Ka!" Ya
ce: "Ba za ka gan Ni ba, kuma
amma ka duba zuwa ga dutse, to,
idan ya tabbata a wurinsa, to, za ka
gan Ni." Sa'an nan a lokacin da
Ubangijinsa, Ya kuranye zuwa ga
dutsen, Ya sanya shi nikakke.
Kuma Musa ya fadi somamme. To,
a lokacin da ya farka, ya ce: "Tsar-
kinKa ya tabbata! Na tuba zuwa
gare Ka, kuma ni ne farkon mumi-
nai."
144. Ya ce: "Ya Musa! Lalle ne
NT, Na za6e ka bisa ga mutane da
manzanciNa, kuma da maganaTa.
Saboda haka ka riki abin da Na ba
ka, kuma ka kasance daga masu
godiya."
l^-UJiJ^ Jr^ ftr>X^ (4-^J
C>j J 6>aJ»j ><u-Kj \^jl^ Cfy iW-l^j
E o^ <"< *'\*> '*-- *1 \< i^lil,
(I) Kissoshin da ke tafe daga nan, suna nuna hani ga a kara wani abu a cikin umarnin
Allah. Kowane irin kari shi ne ake cewa bidi'a, kuma ko da an yi shi ne da nufin kwarai.
Bidi'a tana kawo fitina ga masu ita kamar yadda yin asawaki ya tayar da Mikatin daga
kwana talatin zuwa kwana arba'in, har BanTlsra'ila suka bauta wa marakinsu a cikin karin
kwana gomar, kuma Annabi Musa ya fadi somamme saboda ya kara da neman ya yi
tsokaci zuwa ga Ubangijinsa. Sa'an nan wasu abubuwa masu yawa da nauyi suka auku a
kan Bam Isra'ila saboda karin asawaki kurum.
243
Suratul A'araf
ti<A
mm&-v
145. Kuma Muka rubuta masa a
cikin alluna daga kowane abu,
wa'azi da rarrabewa ga dukan ko-
wane abu: "Sai ka rike su da karfi,
kuma ka umurci mutanenka, su yi
riko ga abin da yake mafi kyaun-
su (1) : Za Ni nuna muku gidan fa-
sikai."
146. Za Ni karkatar da wadanda
suke yin girman kai a cikin kasa, ba
da wani hakki ba, daga ayoyiNa.
Kuma idan sun ga dukan aya, ba za
su yilmani da ita ba, kuma idan sun
ga hanyar shiriya, ba za su rike ta
hanya ba, kuma idan sun ga hanyar
6ata, sai su like ta hanya. Wancan
ne, domin lalle ne su, sun karyata da
ayoyinMu, kuma sun kasance, daga
barinsu, gafilai.
147. Kuma wadanda suka kar-
yata game da ayoyinMu da gamu-
wa da Lahira, ayyukansu sun 6aci.
Shin, ana saka musu, face da abin
da suka kasance suna aikatawa?
148. Kuma mutanen Musa suka
riki maraki (2) , jikin mutane, yana
ruri, daga bayan tafiyarsa, daga
kayan kawarsu. Shin, ba su gamba,
cewa lalle ne shi, ba ya yi musu
magana, kuma ba ya shiryar da su
ga hanya? Sun rika shi, kuma sun
kasance masu zalunci.
tffetfl
,, T . \ >Jt /
JU^l X^ (np^Vj
(1) Mafi kyau daga Taurata shi ne wanda yake bayyananne; watau kada a yi aiki da
abin da yake bai bayyana ba, sai da abin da ya bayyana, bayan an yarda cewa dukansu
daga Allah suke.
(2) Rikon maraki shi ne bauta masa. ShTmarakin an ylshi ne da mundayen kawarsu,
yana da jiki irin na mutane, kuma yana ruri kamar na shanu. Ba^shi yin magana. Sun bauta
masa a bayan tafiyar Musa, a cikin kwana goma na karin MTkatin.
244
7 — Suratul A'araf
a^ii^-v
149. Kuma a lokacin da suka yi
nadama, kuma suka ga cewa lalle ne
su, hakTka, sun 6ace, suka ce: "Ha-
kika, idan UbangijinMu bai yi
mana rahama ba, kuma Ya gafarta
mana, lalle ne muna kasancewa
daga masu hasara."
150. Kuma a lokacin da Musa ya
koma zuwa ga mutanensa, yana
mai fushi, mai bakin ciki, ya ce:
"Tir da abin da kuka yi mini wa-
kilci, a bayana! Shin, kun nemi
gaggawar umurnin Ubangijinku
ne?" Kuma ya jefar da Allunan,
kuma ya yi riko ga kan dan'uwansa
yana jan sa zuwa gare shi. Ya ce:
"Ya dan'uwata! Lalle ne mutanen,
sun cfauke ni mai rauni, kuma sun yi
kusa su kashe ni, saboda haka kada
ka darantar da makiya game da ni,
kuma kada ka sanya ni tare da
mutane azzalumai."
151. Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka
gafarta mini, m da dan'uwana,
kuma Ka shigar da mu a cikin
rahamarKa, alhali kuwa Kai ne
Mafi rahamar masu rahama!"
152. Lalle ne wadanda suka riki
marakin, wani fushi daga Ubangi-
jinsu da wani walakanci a cikin
rayuwar duniya, za su same su:
Kuma kamar wancan ne Muke
saka wa masu kirkira karya.
153. Kuma wadanda suka aikata
miyagun ayyuka, sa'an nan suka
tuba daga bayansu kuma suka yi
imani, lalle ne Ubangijinka daga
bayansu, haklka, Mai gafara ne,
Mai jin kai.
J^J (3^^ j^5^ X&^Cjt &y£tiL
" T^-vf'
^^^JfJ^J^^^^JO^
< ^ <^±*
^^-J
*+• >"i" 1*4
» '*»>
245
7 — Suratul A'araf
m-s
154. Kuma a lokacin da fushin
ya kwanta daga barin Musa, sai ya
riki Allunan, kuma a cikin kwa-
fensu akwai shiriya da rahama ga
wacfanda suke su, ga Ubangijinsu,
masu jin tsoro ne.
755. Kuma Musa ya za6i muta-
nensa, namiji saba'in, domin mika-
tinMu. To, a lokacin da tsawa ta
kama su, ya ce: "Ya Ubangijina!
Da Ka so, da Ka halakar da su daga
gabani, su da ni. Shin, za Ka halaka
mu, saboda abin da wawayen daga
gare mu suka aikata? Ba ta zama ba
face fitinarKa, Kana 6atarwa, da
ita, wanda Kake so, kuma Kana
shiryarwa, da ita, wanda Kake so;
Kai ne Maji6incinmu. Sai Ka gafar-
ta mana; kuma Ka yi mana raha-
ma, alhali kuwa Kai ne Mafi alherin
masu gafara.
156. "Kuma Ka rubuta mana
alheri a cikin wannan duniya, kuma
a cikin Lahira. Lalle ne mu, mun
tuba zuwa gare Ka." Ya ce: "Aza-
baTa Ina samu, da ita, wanda Nike
so, kuma rahamaTa, ta yalwaci
dukan kome. Sa'an nan za Ni rubu-
ta ta ga wacfanda suke yin takawa,
kuma suna bayar da zakka, da wa-
cfanda suke, game da ayoyinMu
muminai ne;
157. "Wacfanda suke suna bin
Manzo (1) , Annabi, Ummiyyi wan-
da suke samun sa rubuce ajvu-
rinsu, a cikin Attaura da LinjTla;
LOS u^jLjaJ y^-j <j\a~u>>4a^^£*>ja jU>-lj
(1) Bayanin bisharar Attaura da Linjila game da Annabi Muhammadu, tsira da
aminci su tabbata a gare shi. Kuma bisharar da Allah ya gaya wa Annabi Musa a wurin
MiRatinsa tare da mutane saba'in, domin maganar cfinke take.
246
Suratul A'araf
$&i8&-V
yana umurnin su da alheri, kuma
yana hana su daga barin abin da ba
a so; kuma yana halatta musu abu-
buwa masu dacfi, kuma yana
haramtarwar munana a kansu.
Kuma yana kayar da nauyinsu daga
barinsu, da kukummai wacfannan
da suka kasance a kansu. To, wa-
cfanda suka yi Tmani da shi kuma
suka karfafa shi, kuma suka tai-
make shi, kuma suka bi haske wan-
da aka saukar tare da shi, wacfan-
nan ne masfa cin nasara."
158. Ka ce: "Ya ku mutane ! (1 >
Lalle ne m manzon Allah ne zuwa
gare ku, gaba daya. (Allah) Wanda
Yake Shi ne da mulkin sammai da
kasa : Babu wani abin bautawa face
Shi, Yana rayarwa, kuma Yana
matarwa, sai ku yi Tmani da Allah
da ManzonSa, Annabi, Ummiyyi,
wanda yake yin Tmani da Allah da
kalmominSa: ku bT shi, tsamma-
ninku, kuna shiryuwa."
159. Kuma daga mutanen (2)
Musa akwai al'umma, suna shiryar-
wa da gaskiya, kuma da ita suke yin
adalci.
160. Kuma Muka yayyanka su
sibcfi goma sha biyu, al'ummai.
Kuma Muka yi wahayi zuwa ga
Musa a lokacin da mutanensa suka
neme shi, ga shayarwa, cewa: "Ka
>>> v
p£ri.J ^jj-*+> \if-*j-+
'j±&X#>&$&
<L*A
»A
*■* i
(1) Mutane a nan, ana nufin Yahudu da wasunsu. Ana kiran su zuwa ga abin da
Attaura ta yi musu bishara da zuwansa, a cikin sifofin da ta sifanta shi da su.
(2) Ana nuna *cewa duka yadda mutane suka baci, ba za a rasa na kirki a cikinsu ba.
247
Suratul A'araf
$&»-v
doki dutsen (1) da sandarka." Sai
marmaro goma sha biyu suka BuB-
Buga daga gare shi : Lalle ne kowa-
cfanne mutane sun san mashayarsu.
Kuma Muka saukar da darBa da
tantabaru a kansu. "Ku ci daga
masu dacfin abin da Muka arzuta
ku." Kuma ba su zalunce Mu ba;
kuma amma rayukansu suke zal-
unta.
161. Kuma a lokacin da aka ce
masu: "Ku zauna ga wannan alka-
rya (2) , kuma ku ci daga gare ta, inda
kuka so, kuma ku ce: 'Saryarwa,'
kuma ku shiga kofa kuna masu
sujada : Mu gafarta muku laifuffu-
kanku, kuma za Mu kara wa masu
kyautatawa."
162. Sai wacfanda suka yi zalunci
daga gare su, suka musanya maga-
na (3) watar wadda aka ce musu, sai
Muka aika azaba a kansu, daga
sama, saboda abin da suka kasance
suna yi na zalunci.
163. Kuma ka tambaye su daga
alkarya wadda ta kasance kusa ga
teku, a lokacin da suke ketare haddi
a cikin Asabar, a lokacin da
kTfayensu, suke je musu a ranar
/> *
0?\j\ iS^=> ?^p*& lX-1^ fl^l^ IjJul
k S • > > ^ S * S *s ^ s ** ft "
(1) Watau dutsen da ya gudu da tufafinsa ne a lokacin da yake yin wanka do-
min a nuna wa BanI Isra'ila, wacfanda suka soke shi da gwaiwa, cewa lafiya lau yake.
Kuma aka umurce shi da daukar dutsen, kuma yanzu aka umurce shi da ya doke shi domin
ruwa ya fito saboda shansu.
(2) Alkaryar ita ce Baitil Makdis, bisa shugabancin Yusha'u. 'Saryarwa' watau a
saryar mana da zunubinmu, ya Allah! 'Shiga kofa da sujada', watau da tawali'u.
(3) Suka musanya hidxfa da hincfa: watau alkama. (Aya ta 161) Sai aka saukar da
azaba a kansu, saboda haka wannan ya nuna cewa Allah ba ya son a musanya addininSa
da kome, sai dai mutum ya yi shi kamar yadda ya zo masa. Musanyawar umarnin, yaki ne
a tsakanin gaskiya da karya. Ma'anar hicfcfa ita ce kayar da zunubi.
248
7 — Suratul A'araf
l$&-v
Asabar (1) cfinsu jere. Kuma a ranar
da ba su yi Asabar ba, ba su zuwa
gare su: Kamar wancan ne Muke
jarraba su da abin da suka kasance
suna yi na fasikanci.
164. Kuma a lokacin da wata
al'umma daga gare su ta ce: "Don
me kuke yin wa'azi ga mutane wa-
cfanda Allah Yake Mai halaka su,
ko kuwa Mai yi musu azaba, azaba
mai tsanani?" Suka ce: "Domin
neman hanzari zuwa ga Ubangi-
jinku, kuma tsammaninsu, suna yin
takawa."
165. To, a lokacin da suka manta
da abin da aka tunatar da su da shi,
Mun tsTrar da wadanda suke hani
daga cuta, kuma Muka kama wa-
danda suka yi zalunci, da azaba mai
tsanani domin abin da suka kasance
suna yi, na fasikanci.
166. Sa'an nan a lokacin da suka
yi girman kai daga barin abin da
aka hana su daga gare shi, Muka ce
musu: "Ku kasance birai kaskanta-
ttu."
167. Kuma a lokacin da Ubangi-
jinku Ya sanar, lalle ne, za Ya aika a
kansu (Yahudu), zuwa Ranar Kiya-
ma, wanda zai dandana musu
> >:*'
A A ^
->--7-
jjJLy*Ju\yb u->
(1) Wata alkarya ana ce da ita Ailata a bakin ga6ar Bahr Al Kulzum a zamanin
Dawuda, Allah ya umurce su a kan harshen Dawuda su riki Jumma'a ranar Tdi, su yanke
aiki a ciki, domin ibada, sai suka ki Jumma'a suka za6i Asabar, ma'anarsa yankewa. To,
sai Allah ya tsananta musu, Ya hana su farautar kTfi a ranar Asabar, Ya halatta musu shi, a
sauran kwanukan mako. Sai a ranar Asabar, su sami kTfi wani kan wani, amma sauran
kwanuka ba su samunsa haka. Sai Iblis ya sanar da su ga su aikata matarar ruwa a gefen
tekun, a ranar Asabar, su bude kifi ya shiga su rufe, har ranar Lahadi su kama. Sai garin ya
kasu uku: kashi daya suka yi farauta, wasu suka hana, su kuma suka yi garu a
tsakaninsu da masu yi, na uku ba su yi farautar ba kuma ba su hana ba. A bayan 'yan
kwanaki sai aka mayar da masu farautar birai, sa'an nan suka mutu.
249
Suratul A'araf
*iM&-v
mummunar azaba, lalle ne Ubangi-
jinka, haklka, Mai gaggawar ukuba
ne, kuma ShT, hakika, Mai gafara
ne, Mai jin kai.
168. Kuma Muka yayyanka su,
a cikin kasa, al'ummomi, daga gare
su akwai salihai, kuma daga gare su
akwai wanda ba haka ba. Muka
jarrabe su da abubuwan alheri da
na musTfa: tsammaninsu, suna
komowa.
169. Sai wasu 'yan baya suka
maye daga bayansu, sun gaji Litta-
fin, suna kar6ar sifar (1) wannan
kaskantacciya, suna cewa: "Za a
gafarta mana." Idan kuma wata
sifa irinta ta zo, za su kar6e ta. Shin,
ba a kar6i alkawarin Littafi ba a
kansu cewa kada su facfa ga Allah,
face gaskiya, alhali kuwa sun ka-
ranta abin da yake a cikinsa, kuma
Gidan Lahira ne mafi alheri ga
wanda ya yi takawa? Shin, ba za ku
hankalta ba?
170. Kuma wacfanda suke
rikewa da Littafi, kuma suka
tsayar da salla, lalle ne Mu, ba Mu
tozarta ladar masu gyarawa.
171. Kuma a lokacin da muka
daukaka dutse (2) sama da su, ka-
^ ^rr > x „ -r-^ r-^ *> "1^ > -! * ?' >^ * , # ^
(1) Sifar kaskantacciya ita ce kayan duniya na haram, kamar rashawa. An kira ta sifa
domin ba aba ce mai tsayuwa da kanta ba, kuma ba sifar abin kirki ba, sai dai abin da
yake halaka ne nan da nan. Take gaskiya fada ne da addini, watau yaki a tsakanin gaskiya
da karya.
(2) A lokacin da Musa ya karanta wa Bani Isra'ila Attaura da hukunce-hukuncen da
suke a cikinta, masu wuya gare su, sai suka ki yarda da ita. Allah ya yanka dutse daidai da
garinsu, Ya daukaka shi a kansu, ko su yi aiki da ita ko ya fada a kansu. Daga nan idan
suna salla, sai su yi sujada da rabin goshi a kan tsagin hagu, suna kallon dutsen. Kuma yin
sujada a haka ya zama sunnarsu har yanzu. Watau ba a iya tsare gaskiya daga yakin karya
sai an yi amfani da wani karfi.
250
7 — Suratul A'araf
v^-4t^-v
mar dai shi girgije ne, kuma suka
hakkake, lalle ne shi, mai faduwa ne
a gare su, (aka ce): "Ku karbi abin
da Muka kawo muku da karfi,
kuma ku tuna abin da yake a cikin-
sa, tsammaninku kuna yin
takawa."
172. Kuma a lokacin da Uban-
gijinka Ya karbi (alkawari) daga
cfiyan Adam, daga bayayyakinsu, a
zuriyarsu, kuma Ya shaidar da su a
kan rayukansu, (Ya ce): "Shin, ba
NT ne Ubangijinku ba?" Suka ce:
"Na'am! Mun yi shaida!"(Ya ce):
"Kada ku ce a Ranar Kiyama:
Lalle ne mu, daga wannan, gafa-
lallu ne." (1)
173. K6 kuwa ku ce: "Abin sani
kawai, ubanninmu suka yi shirki
daga farko, kuma mu, mun kasance
zuriya daga bayansu. Shin fa, Kana
halaka mu, saboda abin da masu
batawa suka aikata?"
174. Kuma kamar haka Muke
rarrabe ayoyi, daki-daki; tsamma-
ninsu, suna komowa.
175. Ka karanta a kansu labarin
wanda Muka kawo masa (2) ayo-
yinMu, sai ya sabule daga gare su,
sai Shaicfan ya bi shi, sai ya kasance
a cikin halakakku.
(1) Watau kada ku ce ba ku san wannan alkawari ba.
(2) Asalin kissar ana cewa daga Bil'amu dan Ba'ura ne; Allah ya ba shi ilmi, sai ya bar
ilmin. Yana daga cikin malaman BanT isra'ila, ya kasance wanda ake karbar addu'arsa,
suna gabatar da shi a cikin tsanance-tsanance, sai Musa ya aike shi zuwa ga Sarkin
Madyana ya kiraye shi zuwa ga Allah. Sai Sarkin ya yanka masa kasa, ya ba shi, sai ya bi
addinin Sarkin, ya bar addinin Musa. Ya zama misali ga duk malamin da bai yi aiki da
ilminsa ba. Idan malami ya halaka, to, ya fi Shaicfan sharri domin haka Shaicfan yake binsa
wajen taimakon Rarya a kan gaskiya.
251
7 — Suratul A'araf
$M&-v
176. Kuma da Mun so, da Mun
cfaukaka shi da su, kuma amma shi,
ya nemi dawwama a cikin kasa,
kuma ya bi son zuciyarsa. To, misa-
linsa kamar misalin kare ne, idan ka
yi cfauki a kansa ya yi lallage, ko
kuwa ka bar shi sai ya yi lallage,
wannan ne misalin mutane wacfan-
da suka karyata game da ayo-
yinMu: Ka jeranta karatun laba-
run; tsammaninsu suna tunani.
777. Tir da zama misali, muta-
nen da suka karyata game da ayo-
yinMu, kuma kansu suka kasance
suna zalunta.
178. Wanda (1) Allah Ya shiryar,
to, shine Mai shiryuwa, kuma wan-
da Ya 6atar, to, wacfannan su ne
masu hasara.
1 79. Kuma lalle ne, hakTka, Mun
halitta, saboda Jahannama, masu
yawa daga aljannu da mutane, suna
da zukata, ba su fahimta da su,
kuma suna da idanu, ba su gani da
su, kuma suna da kunnuwa, ba su ji
da su: wacfancan kamar bisashe
suke. A'a, su ne mafi 6acewa: Wa-
cfancan su ne gafalallu.
180. Kuma Allah Yana da su-
naye masu kyau (2) : sai ku roke Shi
** ??> - f? ^-i^ „ C '4" >c\": »'<s
" 3fl '''It > > *'p ' 9> \\>\~ Iff * "
(1) An sifanta Musulmi da abin da aka sifanta Yahudu da shi cewa a cikinsu akwai na
kirki, kuma akwai miyagu, domin yaki a tsakanin gaskiya da karya ya doge.
(2) Wacfanda suke rokon Allah ba da sunayenSa masu kyau ba, su ne aka sifanta da
dabbobi, har dabbobi sun fi su, domin dabba tana gudun abin da yake cutar ta, amma su ba
su san abin da yake cutar su ba, balle su guje shi. Kuma ana fahimtar cewa ba a rokon Allah
da wani suna Nasa, idan bai kasance a cikin sunayenSa masu kyau ba, sai fa idan yazama a
dunkule ne, kamar a ce, "Ya Allah ina rokon Ka da sunayenKa wacfanda na sani da
wacfanda ban sani ba," domin Hadlsi ya nuna a yi haka. Kiran Allah ba da sunayenSa
masu kyau ba yana cikin yaki a tsakanin karya da gaskiya.
252
7 — Suratul A'araf
$&M-v
da su, kama ku bar wacfanda suke
yin ilhadi a cikin sunayenSa: Za a
saka musu abin da suka kasance
suna aikatawa.
181. Kuma daga wacfanda Muka
halitta akwai wata al'umma, suna
shiryarwa da gaskiya, kuma da ita
suke yin adalci.
182. Kuma wacfanda suka kar-
yata game da ayoyinMu, za Mu yi
musu istidraji daga inda ba su sani
ba.
183. Kuma Ina yi musu jinkiri,
lalle ne kaicfiNa, mai karfi ne.
184. Shin, ba su yi tunani ba,
cewa babu wata hauka ga ma'abu-
cinsu? (1) ShT bai zama ba face mai
gargacfi mai bayyanawa.
185. Shin, ba su yi dubi ba a cikin
mulkin sammai da kasa, da kuma
abin da Allah Ya halitta daga kome,
kuma akwai tsammani kasancewar
ajalinsu, hakTka, ya kusanta? To,
da wane labari a bayansa suke yin
Tmani?
186. Wanda Allah Ya 6atar, to,
babu mai shiryarwa a gare shi:
kuma Yana barin su, a cikin 6atarsu
suna cfimuwa.
187. Suna tambayar ka (2) daga
Sa'a, a yaushe tabbatarta take? Ka
\>\y K s ' *'* >' c ~"* »
\i?£
^H * ' 9 ^< .*>< xA'
(1) Watau, Annabi Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ba ya
da hauka sai hankali, saboda haka masu yin addini da hauka, kamar masu da'awar
tasawwufi, karya suke yi, suna facfa ne da gaskiya. Kuma sukar mai wa'azi da sunaye facfa
da gaskiya ne.
(2) Tambayar abin da Allah bai bayyana shi ba, kamar Ranar Tashin Kiyama, yaki ne
a tsakanin karya da gaskiya. Cewa wani mutum ya san gaibi ko yana iya kawo alheri ko ya
tunkucfe wani sharri, karya ne, kuma fada da gaskiya ne.
253
Suratul A'araf
l^-v
ce: "Abin sani kawai, saninta a
wurin Ubangijina yake. Babu mai
bayyana ta ga lokacinta face Shi. Ta
yi nauyi a cikin sammai da kasa. Ba
za ta zo muku ba face kwatsam."
Suna tambayar ka, kamar kai ma-
sani ne gare ta. Ka ce: "Abin sani
kawai, saninta a wurin Allah yake,
kuma amma mafi yawan mutane ba
su sani."
188. Ka ce: "Ba ni mallaka wa
raina wani amfani, kuma haka ban
tunkucfe wata cuta, face abin da
Allah Ya so. Kuma da na kasance
ina sanin gaibi, da lalle ne, na
yawaita daga alheri kuma cuta ba
za ta shafe ni ba, m ban zama ba
face mai gargadi, kuma mai bayar
da bishara ga mutane wadanda
suke yin Tmani."
189. Shine Wanda Yahahttaku
daga rai guda, kuma Ya sanya, daga
gare ta, ma'auranta, domin ya nat-
su zuwa gare (1) ta. Sa'an nan a
lokacin da ya rufe ta, ta yi ciki, ciki
sassauka, sai ta shutfe da shi. Sa'an
nan a lokacin da ya yi nauyi, sai
suka roki Allah, Ubangijinsu : "Lal-
le ne idan Ka ba mu abin kwarai,
haklka, za mu kasance daga masu
godiya."
o£Hi\4 c&jti y&S&y&^z
£-'
K*r'-'r*.*X'*
< y ' ' ' ' ' *+ - \y" AX'* A.
<*'•«■*'/*' A* * ^^y .
{yyQ UJLv^UJIjUovJ U-^jjSJiUjpS
(1) Asalin halitta, rai guda ce, watau Adam, Allah ya fitar da Hauwa'u daga Adamu,
ya mayar da ita matarsa, daga gare su zuriya ta yadu, kuma ya zama sunnar rai, namijin ya
natsu zuwa ga macen. Kuma daga nan zama ya ci gaba har idan mace ta yi ciki, ba ta
damuwa da shi sai ya yi nauyi, ita da miji su dinga addu'a, suna rokon Allah. Abayan
bukatarsu ta biya sai su manta da Allah, su dora jingina abubuwa zuwa ga sabubbansu, su
bar tunanin Mai sabbabawa. Daga nan abu ya yi zurfi har ya kasance shirki; bauta wa
wani tare da Allah, ya£i ne a tsakanin gaskiya da karya.
254
7 — SuratuI A'araf
M^'il^-V
190. To, a lokacin da Ya ba su
abin kwarai, suka sanya Masa abo-
kan tarayya a cikin abin da Ya ba
su. To, Allah Ya tsarkaka daga abin
da suke yi na shirki.
191. Shin, suna shirki da abin da
ba ya halittar kome, kuma su ne ake
halittawa?
192. Kuma ba su iya bayar da
taimako gate su, kuma kansu ma,
ba su iya taimaka!
193. Kuma idan kun kiraye su
zuwa ga shiriya, ba za su blku ba,
daidai ne a gare ku, shin, kun kiraye
su, ko kuwa ku masu kawaici ne!
194. Lalle ne wadannan da kuke
kira, baicin Allah, bayT ne misa-
lanku: to, ku kiraye su, sa'an nan su
kar6a muku, idan kun kasance
masu gaskiya!
195. Shin, suna da kafafu da
suke yin tafiya da su? Ko suna da
hannaye da suke damka da su? Ko
suna da idanu da suke gani da su?
Ko suna dakunnuwada suke saura-
re da su? Ka ce: "Ku kira wo abu-
buwan (1) shirkinku sa'an nan kuma
ku yi mini kaidi, sa'an nan kada ku
saurara mini.
196. "Lalle ne, maji6inclna Al-
lah ne Wanda Ya saukar da Littafi,
kuma Sin ne Yake ji6intar salihai.
197. "Kuma wadanda kuke kira,
baicinSa, ba su iya taimakon ku,
kuma kansu ma, ba su iya
taimaka."
v±\\
> *' ' \+4
9-A
(1) Bayar da tsoro da wani abin bautawa ko jingina wata bukata a gare shi, duka ya£i
ne a tsakanin gaskiya da karya.
255
7 - Suratul A'araf
1&&-V
198. Kuma idan ka kiraye su
zuwa ga shiriya, ba za su ji ba, kuma
kana ganin su, suna dubi zuwa gare
ka, alhali kuwa su, ba su gani.
799. Karikiabindayasaukaka;
kuma ka yi umurni da alheri, kuma
ka kau da kai daga jahilai. (1)
200. Kuma imma wata fizga
daga Shaicfan ta fizge ka, sai ka
nemi tsari ga Allah. Lalle ne Shi,
Mai jT ne, Masani.
201. Lalle ne wadanda suka yi
takawa idan wani tashin hankali
daga Shaicfan ya shafe su, sai su
tuna (Allah) sai ga su, sun zama
masu baslra.
202. Kuma 'yan'uwansu (shai-
cfanu) suna taimakon su a cikin
6ata, sa'an nan kuma ba su takai-
tawa.
203. Kuma idan ba ka je musu
da wata aya ba, su ce: "Don me ba
ka £aga ta ba?" Ka ce: "Abin sani
kawai, ina biyar abin da aka yo
wahayi zuwa gare ni ne, daga Uban-
gijina. Wannan abubuwan kula ne
daga Ubangijinku, da shiriya da
rahama ga mutane wadanda suke
yin imani."
204. Kuma idan an karanta (2)
Alkur'ani sai ku saurara gare shi,
kuma ku yi shim: tsammaninku,
ana yi muku rahama.
ju:
i**<4
* *'•>*
s s • ' **
iA Ap ( < u\>y&\£j$\ Zj\
(1) Bayanin sifofin mai wa'azi, watau mataimakin gaskiya a kan £arya.
(2) Bayan an sifanta Alkur'ani da cewa abin kula ne ga masu unani, sai kuma
ya yi umurni da saurare, a lokacin da ake karatunsa. Sauraren yana wajabta a cikin salla,
idan llman ya bayyana karatu kuma da a cikin hudubar Jumma'a. Yana zama mustahabbi
ga sauran lokatai. ICur'ani shi ne abin da ake wa'azi da shi kuma shi ne aya da kansa. Hana
saurarensa yaki ne da gaskiya.
256
8 - Suratul Anfal
m&&&-*
205. Kuma ka ambaci (1) Uban-
gijinka, a cikin ranka da kankan da
kai, da tsoro, kuma komabayan
bayyanawa na magana, da safe da
marece, kuma kada ka kasance
daga gafalallu.
206. Lalle ne, wadanda ke wurin
Ubangijinka ba su yin girman kai
ga bauta Masa, kuma suna tsarkake
Shi da tasbihi, kuma a gare Shi suke
yin sujada.
Tana karantar da cewa taimakon Allah, shine nasara ga masu
takawa, ba karfmsu ba, da kuma shiryarwa ga dokokin ya£i da abin
da ya ratayu da yaki domin cfaukaka kalmar Allah.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L Suna tambayar ka (2) ga gani-
ma. Ka ce: "Gamma ta Allah da
ManzonSa ce. Sai ku bi Allah da
takawa, kuma ku gyara abin da
' * If ' 'S *'*'
(1) Sa'an nan kuma ya yi umurni da ambaton Allah da addu'a a farko da karshen
rana kamar yadda ya yi umurni da yin salla a wadannan lokatai, watau wannan shi ne
makamin gaskiya a kan karya.
(2) Ya fara Surar da tambayar Sahabbai ga Annabi cewa wane ne ya fi cancanta da
dukiyar ganimar da aka samu a yakin Badar Babba, samari mayaka ko tsofaffi masu bayar
da shawara da ra'ayoyinsu, masu kyau. Sa'an nan Ya yi jawabi da cewa: "Ka ce ganimar ta
Allah ce da ManzonSa", saboda dalilan da suke tafe ga ayoyin da suke biye. Ana nufi
wanke soja daga jayayya a kan dukiya. Allah Ya fi sani.
257
8 - Suratul Anfal
^g^-A
yake a tsakaninku, kuma ku yi da'a
ga Allah da ManzonSa, idan kun
kasance muminai."
2. Abin sani kawai, muminai su
ne wadanda suke idan an ambaci,
Allah, zukatansu su firgita, kuma
idan an karanta ayoyinSa a kansu,
su kara musu waniTmani, kuma ga
Ubangijinsu suke ddgara;
5. Wadanda suke tsayar da salla,
kuma daga abin da Muka arzuta su
suna ciyarwa. (1)
4. Wadannan su ne muminai da
gaskiya. Suna da darajoji a wurin
Ubangijinsu, da wata gafara da
arziki na karimci.
5. Kamar yadda Ubangijinka Ya
fitar da kai daga gidanka da gas-
kiya, alhali kuwa lalle wani bangare
na muminai, hakTka, suna kyama.
6. Suna jayayya da kai a cikin
(sha'anin) gaskiya a bayan ta
bayyana, kamar dai lalle ana kora
su zuwa ga mutuwa ne alhali kuwa
suna kallo.
7. Kuma a 16kacin (2) da Allah
Yake yi muku alkawari da dayan
kungiya biyu, cewa lalle ita taku ce :
U^^^^Wp^C^b Vilify*
(1) Watau suna yin ibada ta jiki da ta dukiya, wajiba da nafila.
(2) Asalin fitar Musulmi zuwa Badar shi ne Annabi ya ji labarin Abu Sufyana ya fito
daga Makka da ayari zuwa Sham, watau "Syria", sai ya fita domin a kama shi, suka sami
Abu Sufyana ya shige da dukiya, saboda haka Annabi daga Badar ya koma Madma.
Wannan fita, ana kiran ta Badar Karama. Da Abu Sufyana ya sami labari, sai ya aika wa
Kuraishawa, domin su fito, su tsare dukiyarsu daga Musulmi. Annabi, da ya ji labarin
komowar Abu Sufyana, sai ya fita tare da jama'arsa, wanda ya ji yana son fita, kuma yana
da abin hawa. Abu Sufyana tare da ayari su ne wajen da babu kaya. Yakin Kuraishawa shi
ne wajen da yake da £aya. Musulmi a tsakiya. Abu Sufyana ya saki hanya ya tslra. Ya nemi
Kuraishawa da su koma, Abu Jahal ya ce sai Allah Ya yi hukunci a tsakaninsu da
Muhammadu wanda ya katse zumunta, ya bar addinin iyaye.
258
8 - Suratul Anfal
$2M2-a
kuma kuna gurin cewa lalle kungiya
wadda ba ta da kaya ta kasance
gare ku, kuma Allah Yana nufin
Ya tabbatar da gaskiya da kalmo-
minSa, kuma Ya katse karshen
kafirai;
8. Domin Ya tabbatar da gas-
kiya, kuma Ya Bata karya, kuma ko
da masu laifl sun ki.
9. A lokacin da kuke neman
Ubangijinku taimako, sai Ya karBa
muku cewa: "Lalle ne Nl, Mai
taimakon ku ne da dubu daga ma-
la'iku, jere."
10. Kuma Allah bai sanya shi ba
face domin bishara, kuma domin
zukatanku su natsu da shi, kuma
taimakon, bai zama ba face daga
wurin Allah : Lalle ne Allah Mabu-
wayi ne, Mai hikima.
11. A lokacin da (Allah) Yake
rufe ku da gyangyadi, domin aminci
daga gare Shi, kuma Yana saukar
da ruwa (1) daga sama, a kanku,
domin Ya tsarkake ku da shi, kuma
Ya tafiyar da kazantar Shaidan
daga barinku, kuma domin Ya dau-
re a kan zukatanku, kuma Ya tab-
batar da kafafu da shi.
12. A lokacin da Ubangijinka
Yake yin wahayi zuwa ga mala'iku
cewa: "Lalle ne Mu, Muna tare da
ku, sai ku tabbatar da wadanda
suka yi imani : za Ni jefa tsoro a
:>-
(1 ) A lokacin zafi ne na bazara, kuma aka faralta azumi, sai Allah Ya saukar da ruwa
daidai da sansanin Musulmi, suka sha, suka yi wanka sa'an nan kuma aka daddale musu
rairayi domin saukin tafiya.
259
8 - Suratul Anfal
rj^-A
cikin zukatan wacfanda suka ka-
firta, sai ku yi duka bisa ga wuyoyi
kuma ku yi duka daga gare su ga
dukan yatsu (1) .
13. Wancan ne, domin lalle ne
su, suna sa6a wa Allah da Manzon-
Sa. Kuma wanda ya sa6a wa Allah
da ManzonSa, to, lalle ne Allah Mai
tsananin ukuba ne.
14. Wancan ne: "Ku cfan-
tfane shi, kuma lalle ne akwai aza-
bar wuta ga kafirai".
15. Ya ku wadanda suka yi lina-
ni ! Idan kun hacfu da wacfanda suka
kafirta ga ya£i, to, kada ku juya
musu bayayyakinku.
16. Kuma duka wanda (2) ya juya
musu bayansa a yinin nan, face
wanda ya karkata domin kodayya,
ko kuwa wanda ya je domin hadu-
wa da wata kungiya, to, lalle ne ya
koma da fushi daga Allah, kuma
matattararsa Jahannama, kuma tir
da makoma ita!
17. To, ba ku ne kuka kashe su
ba; kuma amma Allah ne Ya kashe
su : kuma ba ka yi jSa ba a lokacin
da ka yi jlfa ; kuma amma Allah ne
Ya yi jifar (3) : Kuma domin Ya jar-
*£»i
^•*7
ftp J3\^ASc
*SSiSS »><
S* „> >> »- -J>
(1) Sa'an nan kuma Annabi da umurnin Allah ya debi tsakuwa da hannunsa mai
daraja ya jefa a jihar kafirai. Babu wanda ya rage a cikinsu, face tsakuwar nan ta shiga a
cikin idanunsa.
(2) Gudu a wurin yakin Jihadi shine mafi girman haram duka, matukar kafirai ba su
fi ninki biyu na adadin Musuhni ba, kamar yadda zai zo. Wanda ya yi gudu a wurin jihadi
kamar ya nemi kafirci ya rinjayi Musulunci ne.
(3) Kisan da aka yi musu, Allah ne Ya kashe su, haka Annabi ya debi tsakuwa da
hannunsa mai daraja ya jefa wa kafirai, tsakuwar ta shiga cikin idanun kowane daya
daga cikinsu. To, wannan jTfar daga Allah take. Saboda haka duk ganTmar dai ta Allah ce
da ManzonSa, sai yadda Ya so, za a raba ta.
260
8 - Suratul Anfal
dllS^I^-A
raba Musulmi da jarrabawa mai
kyau daga gare Shi. Kuma Allah
Mai ji ne, Masani.
18. Wancan ne, kuma lalle ne,
Allah Mai raunana kaidin kafirai
ne.
19. Idan kun yi alfanun cin nasa-
ra, to, lalle nasarar ta je muku,
kuma idan kun hanu, to, shi ne mafi
alheri a gare ku, kuma idan kun
koma za Mu koma, kuma jama'ar-
ku ba za ta wadatar muku da kome
ba, ko da ta yi yawa. Kuma lalle ne
cewa Allah Yana tare da muminai!
20. Ya ku wacfanda suka yi Tma-
ni! Ku yi da'a ga Allah da Man-
zonSa, kuma kada ku juya daga
barinSa, alhali kuna ji.
21. Kuma kada ku kasance ka-
mar wacfanda suka ce: "Mun ji,"
alhali kuwa su, ba su ji.
22. Lalle ne, mafi sharrin da-
bbobi a wurin Allah, su ne kurame,
bebaye, wacfanda ba su yin hankali.
23. Da Allah Ya san wani alheri
a cikinsu, da Ya jiyar da su, kuma
ko da Ya jiyar da su, haklka, da sun
juya, alhali su, suna masu hinjirewa.
24. Yaku wacfanda suka yiima-
ni! Ku karSa wa Allah, kuma ku
karSa wa Manzo, idan Ya kiraye ku
zuwa ga abin da Yake rayar da ku:
Kuma ku sani cewa Allah Yana
shamakacewa a tsakanin mutum da
zuciyarsa, kuma lalle ne ShT, a zuwa
gare Shi ake tara ku.
25. Kuma ku ji tsoron fitina
wadda ba ta samun wacfanda suka
r£+-J& \ (^=^ *W -XA3 1^>JJlL-5 o^
><*>
\i>l\\ **
261
8 - Suratul Anfal
mMm-*
yi zalunci daga gare ku ke6e, kuma
ku sani, lalle ne Allah Mai tsananin
ukuba ne.
26. Ku tuna a lokacin da kuke
kadan, wadanda ake raunanarwa a
cikin kasa, kuna tsoron mutane su
cafe ku, sai Ya tattara ku (a wurin
natsuwa, Macfiha), kuma Ya kar-
fafa ku da taimakonSa, kuma Ya
arzuta ku daga abubuwa masu
dacfi : tsammaninku, kuna godewa.
27. Ya ku wadanda suka yi Tma-
ni! Kada ku yaudari Allah da Man-
zonSa, kuma ku yaudari ama-
noninku, alhali kuwa kuna sane.
28. Kuma ku sani cewa abin sani
kawai, dukiyoyinku da 'ya'yanku,
wata fitina ce, kuma lalle ne Allah, a
wurinSa, akwai ijara mai girma.
29. Ya ku wacfanda suka yi Tma-
ni ! Idan kun bi Allah da taka wa, zai
sanya muku mararraba (da tsoro)
kuma Ya kankare kananan zunub-
anku daga barinku. Kuma Ya ga-
farta muku. Kuma Allah ne
Ma'abucin falala mai girma.
30. Kuma a lokacin da wa-
danda (1) suka kafirta suke yin
makirci game da kai, domin su
tabbatar da kai, ko kuwa su kashe
ka, ko kuwa su fitar da kai, suna
^ » t ' * 9 \ >' ,*\ < 'x
(1 ) Kuraishawa suka taru suna shawarar yadda za su yi da Muhammadu : ko su daure
shi a cikin gida, ko su kashe shi, ko su kore shi. Ra'ayinsu ya tsaya ga su kashe shi da
za6a66un mutane daga kowace kabila yadda danginsa, BanT Hashim, ba su iya facfa da
dukkan Larabawa, har su koma ga diyya. A ranar da suka shirya kashe shi, Allah Ya
umurce shi da hijira zuwa Madina. A lokacin da ya fita daga gidansa ya iske su tsaitsaye,
suna barci, ya zuba turftaya a kunnuwansu, sa'an nan ya shige suka tafl tare da Abubakar,
suka sauka a cikin kogon dutsen Hira. Bayan kwanaki uku, suka fita zuwa Madina.
262
8 - Suratul Anfal
dJJS^fj^-A
makirci kuma Allah Yana mayar
musa da makirci, kuma Allah ne
Mafificin masu makirci.
31. Kuma idan aka karanta,
ayoyinMu a kansu, sukan ce: "Lal-
le ne mun ji, da muna so, haklka, da
mun facfi irin wannan : wannan bai
zama ba face tatsuniyoyin mutanen
farko."
32. A lokacin da suka ce: "Ya
Allah! Idan wannan ya kasance shT
ne gaskiya daga wurinKa, sai Ka yi
ruwan duwatsu, a kanmu, daga
sama, ko kuwa Ka zo mana da wata
azaba, mai racfacfi."
33. Kuma Allah bai kasance
Yana yi musu azaba ba alhali kuwa
kai kana cikinsu, (1) kuma Allah bai
kasance Mai yi musu azaba ba alha-
li kuwa suna yin istigfari.
34. Kuma mene ne a gare su da
Allah ba zai yi musu azaba ba,
alhali kuwa su, suna kangewa daga
Masallaci Mai alfarma, kuma ba su
kasance majibintanSa ba? Babu
maji6intanSa face masu takawa.
Kuma mafi yawansu ba su sani ba.
35. Kuma sallarsu a wurin T)a-
kin ba ta kasance ba face shewa da
yaya;sai ku cfancfani azaba saboda
abin da kuka kasance kuna yi na
kafirci.
36. Lalle ne wacfanda suka ka-
firta, suna ciyar da dukiyoyinsu,
&*b Vyb \Xm> <^> bO [J>-4& > \f & >\j
ftp ^J\^*JLiuUi5\jl
•>£
\t >'
(1) Rayuwar Annabi a cikin mutane aminci ne daga azaba, haka kuma yin istigfari
aminci ne. Wanda ke son wadata da aminci daga Allah, sai ya lazimci istigfari da bin
sunnar Annabi, tslra da amincin Allah su tabbata a gare shi.
263
8 - Suratul Anfal
aa^i^-A
domin su kange daga hanyar Allah ;
to, za su ciyar da ita, sa'an nan
kuma ta kasance nadama a kansu,
sa'an nan kuma a rinjaye su. Kuma
wacfanda suka kafirta zuwa ga
Jahannama ake tara su;
37. Domin Allah Ya rarrabe mu-
mmuna daga mai kyau, kuma Ya
sanya mummunan, sashensa a kan
sashe, sa'an nan Ya shirga shi gaba
daya, sa'an nan Ya sanya shi a cikin
Jahannama. Wacfannan su ne masu
hasara.
38. Ka ce wa wacfanda suka ka-
firta idan sun hanu, za a gafarta
musu abin da ya riga ya shige, kuma
idan sun koma, to, hanyar kafiran
farko, halaica, ta shude.
39. Kuma ku yalce su har wata
fitina ba za ta kasance ba, kuma
addini dukansa ya kasance na Al-
lah. To, idan sun hanu, to, lalle ne,
Allah ga abin da kuke aikatawa
Mai gani ne.
40. Kuma idan sun juya, to, ku
sani cewa lalle Allah ne Majibin-
cinku: Madalla da Majibinci, kuma
madalla da Mai taimako, Shi.
41. Kuma ka sani, abin sani ka-
wai, abin da kuka sami (1) gamma
daga wani abu, to, lalle ne Allah
Yana da humusinsa kuma don
Manzo, kuma saboda masu zu-
munta da marayu da miskmai da
'J^^S-4^'uiC-i^^^jA^
•>f >'. ' , ?-">
C^JL^u C^*a* JLA3 \)2yo<JlJ<*JU^ 03U
JjaJI^jo S^y *u\o\ ^jJLpU \yyd\j
(1) Daga farkon Surar har zuwa a nan, ana bayanin cewa ganimar Badar ba ta kowa
ba ce face Allah da ManzonSa ; to, a nan yana bayanin yadda za a raba dukiyar, kuma
wannan rabon, ya zama sunna ga dukkan dukiyar gamma da Musulmi suka samu da ya£i
ko hari.
264
8 - Suratul Anfal
dJJ2^fi^-A
cfan hanya, idan kun kasance kun yi
Tmani da Allah da abin da Muka
saukar a kan BawanMu a Ranar
Rarrabewa, a Ranar da jama'a biyu
suka hacfu, kuma Allah ne, a kan
kowane abu, Mai Ikon yi.
42. A lokacin da kuke a ga6a ta
kusa su kuma suna a ga6a ta nesa,
kuma ayarin yana a wuri mafi
gangarawa daga gare ku, kuma da
kun yi wa juna wa'adi, da kun sa6a
ga wa'adin; kuma amma domin
Allah Ya hukunta abin da yake ya
kasance abin aikatawa. Domin
wanda yake halaka ya halaka daga
shaida, kuma mai rayuwa ya rayu
daga shaida, kuma lalle Allah ne,
haJalca, Mai ji, Masani.
43. A lokacin da Allah Yake
nuna maka su suna kacfan, a cikin
barcinka, kuma da Ya nuna maka su
suna da yawa, lalle ne da kun ji
tsoro, kuma lalle ne da kun yi jaya-
yya a cikin al'amarin, kuma amma
Allah Ya tsare ku: Lalle Shi ne
Masani ga abin da yake a cikin
kiraza.
44. Kuma a lokacin da Yake
nuna muku su, a lokacin da kuka
hacfu, a cikin idanunku suna kacfan,
kuma Ya karantar da ku a cikin
idanunsu, domin Allah Ya hukunta
wani al'amari wanda ya kasance
abin aikatawa : kuma zuwa ga Allah
ake mayar da al'umurra.
45. Ya ku wacfanda suka yi Tma-
ni ! Idan kun hacfu da wata kungiyar
yaki, to, ku tabbata, kuma ku am-
»> Z*s»'\' *' y S
<?&* £ '- *<\t* Y^V
Up J^$i3"0^^&wj
y*i' 9 S\ ^<' H ' V\ • ^"TTll
9> *' '"y 9 * r ^\/'^ *}*>* A'\'
s A**'?' z'% * >*\ . -^ Y\'- y '
^jy^^J^^lj^y^<^^==^
at.'**
\g& W^tyP^MQH
265
8 - Suratul Anfal
£1SM£-A
baci (1) Allah da yawa, tsamma-
ninku kuna cin nasara.
46. Kuma ku yi cfa'a ga Allah da
ManzonSa, kuma kada ku yi jaya-
yya har ku raunana kuma iskarku
ta tafi, kuma ku yi hakuri. Lalle ne
Allah Yana tare da masu hakuri.
47. Kada ku kasance kamar
wacfanda suka fita daga gida-
jensu (2) , suna masu alfahari da yin
riya ga mutane, kuma suna kange-
wa daga hanyar Allah : Kuma Allah
ne ga abin da suke aikatawa Mai
kewayewa.
48. Kuma a lokacin da Shai-
cfan (3) ya kawace musu ayyukansu,
kuma ya ce : "Babu marinjayi a gare
ku a yau daga mutane, kuma m
makwabci ne gare ku." To, a loka-
cin da kungiya biyu suka hadu, ya
koma a kan digadigansa, kuma ya
ce: "Lalle ne nT, barrantacce ne
daga gare ku! NTina ganin abin da
ba ku gani; ni ina tsoron Allah:
Kuma Allah Mai tsananin ukuba
ne.
49. A lokacin da munafukai da
wadanda suke akwai cuta a cikin
^\\j%^:
r%i" * '*l\A, >
fi^^&<^Zj&\j'^S*^^
(1) Ambaton Allah bayyane ya fl kyau a wurin yaki da wurin harama da hajji ko
umra, kuma da lokacin da ake fita zuwa ga masallacinldi. Wurin da ba wacfannan wurare
uku ba, ambaton Allah, ya zama asirce ya fi kyau.
(2) Kada Musulmi su fita zuwa yaki da nuna alfahari da kicfe-kicfe da giya da mata da
maganganun alfasha, kamar yadda Kuraishawa suka fita zuwa Badar; ku fita da tawalu'i
da zikirin Allah.
(3) Shaicfan ya fita zuwa ga Kuraishawa a cikin surar Suraktu bn Malik, ya ce musu
yana tare da su, kuma shi ne makwabcinsu; watau danginsa, Kasn'anawa, ba za su taBa su
ba da yaki, a lokacin da suke yaki da Muhammadu. Bayan haka da ya tafi Badar ya ga
mala'iku, shT ne ya koma baya, yana cewa wai shi yana tsoron Allah ; watau yana yi wa
Kuraishawa izgili; su ne ba su tsoron Allah.
266
8 - Suratul Anfal
IiraB8&-A
zukatansu, suke cewa: "Addinin
wadannan ya rude su". Kuma wanda
ya dogara ga Allah, to, lalle ne
Allah Mabuwayi ne, Mai hikima.
50. Kuma da ka gani, a lokacin
da mala'iku suke karbar rayukan
wadanda suka kafirta, suna dukar
fuskokinsu da duwawunsu, kuma
suna cewa: "Ku dancfani azabar
Gobara —
57. "Wancan saboda abin da
hannayenku suka gabatar ne:
Kuma lalle ne, Allah bai zama Mai
zalunci ba ga bayinSa.
52. "Kamar al'adar mutanen Fi-
r'auna da wacfanda suke gabaninsu,
sun kafirta da ayoyin Allah, sai
Allah Ya kama su da zunubansu:
Lalle Allah ne Mai karfi, Mai tsa-
nanin ukuba.
53. "Wancan ne, domin lalle ne,
Allah bai kasance Mai canza wata
ni'ima wadda ya ni'imtar da ita a
kan wasu mutane ba face sun sake
abin da yake ga rayukansu, kuma
domin lalle Allah ne Mai jT, Ma-
sani."
54. Kamar al'adar mutanen Fi-
r'auna da wadanda suke a gaba-
ninsu, sun karyata game da ayoyin
Ubangijinsu, sai Muka halaka su,
saboda zunubansu, kuma Muka
nutsar da mutanen Fir'auna : Kuma
dukansu sun kasance ne masu za-
lunci.
55. Lalle mafi sharrin dabbobi a
wurin Allah, su ne wacfanda suka
kafirta, sa'an nan ba za su yi Tmani
ba.
f*j->.^3 f-^frj -^>jj>*l
S o>* _>of
267
8 - Suratul Anfal
mM&->>
56. Wacfanda ka yi kullin alka-
wari da su, daga gare su, sa'an nan
kuma suna warwarewar alkawa-
rinsu a kowane lokaci, kuma su, ba
su yin ta£awa.
57. To, in dai ka kama su a cikin
ya£i, sai ka kore (1) wadanda suke a
bayansu, game da su, tsammaninsu,
za su dinga tunawa.
58. Kuma in ka ji tsoron wata
yaudara daga wasu mutane, to, ka
jefar da alkawarin, zuwa gare su, a
kan daidaita : lalle ne Allah, ba Ya
son mayaudara.
59. Kuma wadanda suka kafirta
kada su yi zaton sun tsere : lalle ne
su, ba za su gagara ba.
60. Kuma ku yi tattali, dominsu,
abin da kuka sami Tkon yi na wani
£arfi (2) , kuma da ajiye dawaki,
kuna tsoratarwa, game da shi, ga
maiayin Allah kuma ma£iyinku da
wasu, baicin su, ba ku san su ba,
Allah ne Yake sanin su, kuma abin
da kuka ciyar daga wani abu a cikin
hanyar Allah, za a cika muku
sakamakonsa, kuma ku ba a zalun-
tar ku.
61. Kuma idan sun karkata
zuwa ga zaman lafiya, to, ka karka-
ta zuwa gare shi, kuma ka dogara ga
Allah: lalle ne ShT, Mai ji ne,
Masani.
62. Kuma idan sun yi nufin su
yaudare ka, to, lalle ma'ishinka
>*">
^4^cs>j^*^^^y^\^^^
* %$2
' » ?*s Ss /
4$jJ& ^.CL>y^J Sf^ ^/j ^LSlJ
^iim
(1) Watau a kashe wacfanda aka kama domin saura su gani su ji tsoro.
(2) Tattali daga wani £arfi, ya hada dukkan abin da zai yiwu a yi yakin abokin gaba
da shi. A yanzu daga bindiga da abin da yake sama da ita, shi ne za a yi tattali.
268
8 - Suratul Anfal
mMm-*
Allah ne, Shi ne Wanda Ya karfafa
ka da taimakonSa, kuma da mumi-
nai.
63. Kuma Ya sanya soyayya a
tsakanin zukatansu. Da ka ciyar da
abin da yake cikin kasa, gaba cfaya,
da ba ka sanya soyayya a tsakanin
zukatansu ba, kuma amma Allah
Ya sanya soyayya a tsakaninsu.
Lalle Shi ne Mabuwayi, Mai
hikima.
64. Ya kai Annabi! Ma'ishinka
Allah ne, kai da wanda ya biye
maka daga muminai.
65. Ya kai Annabi! Ka kwadai-
tar da muminai a kan yaki. Idan
mutum ashirin masu hakuri sun
kasance daga gare ku, za su rinjayi
metan, kuma idan dari suka ka-
sance daga gare ku, za su rinjayi
dubu daga wadanda suka kafirta,
domin su, mutane ne, ba su fahimta.
66. A yanzu Allah Ya saukake
daga gare ku, kuma Ya sani cewa
lalle ne akwai masu rauni a cikinku.
To, idan mutum dari, masu hakuri,
suka kasance daga gare ku, za su
rinjayi metan, kuma idan dubu suka
kasance daga gare ku, za su rinjayi
dubu biyu, da iznin Allah. Kuma
Allah Yana tare da masu hakuri.
67. Ba ya kasancewa (1) ga wani
annabi, kamammu su kasance a
t^Vs^j^. Jjo\££jhy>
£ y »f ss
■ > 'six'**
Uj^L. l^iJo "t>y\^> AjU ^====C^i^jiSf
(1) Bayan da Musulmi suka ci nasara a Badar, suka kama Kuraishawa a cikinsu har
da Abbas baffan Annabi. Sai Annabi ya shawarci sahabbansa ga abin da za su yi da
kamammu. Abubakar ya ce wa Annabi, "Mutanenka ne, ka sake su." Sa'an nan ya nemi
Umar shawara, ya ce masa "Ka kashe su." Sai ya karbi fansa daga gare su. Bayan haka
Alkur'ani ya sauka da karfafa ra'ayin Umar na a kashe su, ya fi. Amma tun da an riga an
zartar da fansar, shT ke nan.
269
8 - Suratul Anfal
®m$m-*
gare shi sai (bayan) ya zubar da
jinainai a cikin kasa. Kuna nufin
sifar duniya kuma Allah Yana nufin
Lahira. Kuma Allah ne Mabuwayi,
Mai hikima.
68. Ba domin wani Littafi daga
Allah ba, wanda ya gabata (1) , da
azaba mai girma daga Allah ta
shafe ku a cikin abin da kuka kama.
69. Saboda haka, ku ci daga abin
da kuka samu gamma, yana halal
mai kyau. Kuma ku bi Allah da
takawa. Lalle Allah ne Mai gafara,
Mai jin kai.
70. Ya kai Annabi! Ka ce wa
wanda yake a cikin hannayenku
daga kamammu: "Idan Allah Ya
san akwai wani alheri a cikin zuka-
tanku, zai kawo muku mafi alheri
daga abin da aka kar6a daga gare
ku, kuma Ya yi muku gafara : Kuma
Allah ne Mai gafara, Mai jin kai."
71. Kuma idan sun yi nufin yau-
dararka, to, hakTka, sun yaudari
Allah daga gabani sai Ya bayar da
dama daga gare su: kuma Allah ne
Masani, Mai hikima.
72. Lalle ne wacfanda suka yi
Tmani, kuma suka yi hijira, kuma
suka yi jihadi da dukiyoyinsu da
rayukansu, a cikin hanyar Allah, da
wacfanda suka bayar da masauki,
kuma suka yi taimako. Wacfancan,
sashensu waliyyai ne ga sashe.
Kuma wacfanda suka yi Tmani
,> »/< r ,A
*r JjJl l^^Clll ^1 *$ o£«^£Vjl
Ujfeja£>^\j&
r-\A
\~ , >'<'\ '\' ' A\' *1
* >.1
(1) Abin da ya gabata na Littafi shi ne, amma Allah ne Masanin hakTka, abin da yake
a cikin Surar Al Imrana, aya ta 1 59, inda aka bai wa Annabi umurnin ya yi shawara da
sahabbansa ga abin da ya shafi yaki, sa'an nan kuma ya ddgara ga Allah wajen zartar da
abin da ya za6a daga shawarar da suka ba shi.
270
8 - Suratul Anfal
^l(^-A
kuma ba su yi hijira (1) ba, ba ku da
wani abu daga waliccinsu, sai sun yi
hijira. Kuma idan suka neme ku
taimako a cikin addini, to, taimako
ya wajaba a kanku, face a kan
mutane warfanda a tsakaninku da
tsakaninsu akwai wani alkwari.
Kuma Allah ne, ga abin da kuke
aikatawa, Mai gani.
73. Kuma wadanda suka kafirta,
sashensu ne waliyyan sashe, idan ba
ku aikata shi ba, wata fitina za ta
kasance a cikin Jcasa, da fasadi
babba.
74. Kuma wadanda suka yiTma-
ni kuma suka yi hijira, kuma suka yi
jihadi, a cikin hanyar Allah, kuma
da wadanda suka bayar da masauki,
kuma suka yi taimako, wadannan su
ne muminai da gaskiya, suna da
gafara da wani abinci na karimci.
75. Kuma wadanda suka yiTma-
ni daga baya, kuma suka yi hijira
kuma suka yi jihadi tare da ku, to,
wadannan daga gare ku suke.
Kuma ma'abuta zumunta, sashensu
ne waliyyan (2) sashe a cikin Littafin
Allah. Lalle Allah ne ga dukkan
kome Masani.
>iti
ufM
(1) A farkon Musulunci hijira sharacfi ce ga shiga cikin waliccin Musulmi, amma
bayan da Musulunci ya yi karfi, hijira ba ta zama sharacfi ba, sai dai tana wajaba ga
Musulmi ya tashi daga inda ba ya iya tsare addininsa zuwa ga inda yake iya tsare shi,
matu£ar babu wata wahala mai tsanani. Ana taimakon Musulmin da bai yi hijira ba ga
abin da bai shafi warware alkawarin Musulmi ba.
(2) Walicci shi ne kusanta da lizimtar wajabcin taimakon juna. A farkon Musulunci,
Musulmi ba su da walicci a kan wani Musulmi, sai idan ya yi hijira zuwa Macfina. Bayan
cin Makka da watsuwar Musulunci sai waliccin Musulmi ya wajaba a kan kowane
Musulmi a inda duk yake, a cikin duniya, gwargwadon hali, amma kuma a cikin haka mafi
kusantar zumunta shi ne mafi cancanta da waliccin kowane Musulmi, har dai ga abin da ya
shafi halaye na zaman mutum kamar aure da gado, da sauransu, kamar yadda littattafan
sunna suka bayyana, a can cikin babin walicci.
271
9 — Suratut Tauba
^mm-\
Tana bayani ga hukuncin yanke wa kafirai na kowane irin
kafirci, da irin alaka wadda take iya ragewa a tsakanin Musulmi da
kafiri da bayanin sifofin kafirai.
L Barranta daga Allah da Man-
zonSa zuwa ga wadanda kuka yi wa
alkawari daga masu shirki (1) .
2. Saboda haka ku yi tafiya a
cikin kasa wata hudu (2) , kuma ku
sani lalle ku, ba masu buwayar
Allah ba ne, kuma lalle Allah ne
Mai kunyatar da kafirai.
3. Kuma da yekuwa daga Allah
da ManzonSa zuwa ga mutane, a
Ranar Haji Babba cewa lalle ne
Allah Barrantacce ne daga masu
shirki, kuma ManzonSa (haka). To,
idan kun tuba, to, shi ne mafi alheri
a gare ku, kuma idan kun juya, to,
ku sani lalle ne ku, ba masu bu-
wayar Allah ba ne. Kuma ka bayar
da bishara ga wadanda suka ka-
firta, da azaba mai radacfi.
r
( 1 ) Kafirai iri uku ne : masu addmin al'ada kamar Larabawa, su ne masu shirki, sa'an
nan masu bin Littafi shafaffe watau Yahudu da Nasara, sa'an nan da munafukan wannan
al'umma. Ya fara da masu shirki da bayanin irin ayubansu, sa'an nan ya yi bayanin sauran
kamar haka.
(2) Bayan yanke sulhu, Allah Ya bai wa kafirai wata hucfu na amana, domin su kare
harkokinsu da wasu ma'amaloli da suka kulla tare da Musulmi, sa'an nan yaki ya tashi.
Ana nufin masu addinin al'ada na shirki a nan.
272
9 — Suratut Tauba
&m>-\
4. Sai wacfanda kuka yi wani
alkawari daga masu shirki, sa'an
nan kuma ba su rage ku da kome
ba, kuma ba su taimaki kowa a
kanku ba, to, ku cika alkawarin,
zuwa gare su, har ga iyakar yarjeje-
niyarsu. Lalle ne Allah Yana son
masu takawa.
5. Kuma idan watanni, masu al-
farma suka shige, to, ku yaki mushi-
rikai inda kuka same su, kuma ku
kama su, kuma ku tsare su, kuma
ku zaune musu dukkan madakata.
To, idan sun tuba, kuma suka
tsayar da salla, kuma suka bayar da
zakka, to, ku sakar musu da ha-
nyarsu. Lalle Allah ne Mai gafara,
Mai jin kai.
6. Idan wani daga mushirikai ya
nemi makwabtakarka, to, ka ba shi
makwabtakar har ya ji maganar
Allah, sa'an nan ka isar da shi ga
wurin amincewarsa. Wancan fa do-
min lalle ne su, mutane ne wacfanda
ba su sani ba.
7. Yaya wani alkawari a wurin
Allah a wurin ManzonSa yake ka-
sancewa ga mushirikai, face ga
wacfanda kuka yi wa alkawari wu-
rin Masallaci Mai alfarma? To,
matukar sun tsaya sosai gare ku, sai
ku tsayu sosai gare su. Lalle ne
Allah Yana son masu takawa.
8. Yaya, alhali idan sun ci nasara
a kanku, ba za su tsare wata zumun-
? .^
1* Tt "c" '"
273
Suratut Tauba
«8&-i
ta ba a cikinku, kuma haka wata
amana, suna yardar da ku da baku-
nansu, kuma zukatansu suna ki?
Kuma mafi yawansu fasikai ne.
9. Sun saya da ayoyin Allah,
'yan kudi katfan, sa'an nan suka
kange daga hanyar Allah. Lalle ne
su, abin da suka kasance suna aika-
tawa ya munana.
10. Ba su tsaron wata zumunta a
cikin muminai, kuma haka ba su
tsaron wata amana : kuma wadan-
nan ne masu ta'adi.
11. Sa'an nan idan sun tuba (1) ,
kuma suka tsayar da salla, kuma
suka bayar da zakka, to, 'yan'-
uwanku ne a cikin addini, kuma
Muna rarrabe ayoyi daki-daki, ga
mutane wadanda suke sani.
12. Kuma idan suka warware
rantsuwoyin amana daga bayan
alkawarinsu, kuma suka yi suka a
cikin addininku, to, ku yaki shuga-
bannin kafirci. Lalle ne su, babu
rantsuwoyin amana a gare su:
tsammaninsu suna hanuwa.
13. Shin, ba ku yakin mutane,
wadanda suka warware rantsu-
woyinsu, kuma suka yi niyya ga
fitar da Manzo, kuma su ne suka
fara muku, tun a farkon lokaci?
Shin, kuna tsoron su ne? To, Allah
ne Mafi cancantar ku ji tsoronSa,
idan kun kasance muminai!
\^ s <-<
d^ilrt/tl^j^
<<*r- •>«>*.
*xJ£\
r*
yy oj+xjo
> '* '**
(1) Rukunonin Musulunci biyar ne: Kalmar shahada da salla da azumi da zakka da
hajji ga T)akin Allah. Ana yakar mutum saboda barin uku daga cikinsu, watau kalmar
shahada da salla da zakka kawai. Kuma uku suna lazimtar mawadaci da matalauci. su ne
kalmar shahada da salla da azumi kawai. Amma zakka da hajji sai ga mai halin yi da
wadata.
274
Suratut Tauba
$&\*&-\
14. Ku yake su, Allah Ya yi musu
azaba da hannayenku, kuma Ya
kunyatar da su, kuma Ya taimake
ku, kuma Ya warkar da kirazan
mutane muminai.
75. KumaYatafTdafushinzuka-
tansu, kuma Ya karbi tuba a kan
wanda Ya so. Kuma Allah ne Masa-
ni, Mai hikima.
16. Ko kuna zaton (1) a bar ku,
tun Allah bai bayyana wacfanda
suka yi jihadi ba daga gare ku,
kuma su ba su riki wani shige ba,
baicin Allah da ManzonSa da mu-
minai? Kuma Allah ne Mai jarra-
bawa ga abin da kuke aikatawa.
17. Ba ya kasancewa ga masu
shirki su raya masallatan Allah,
alhali kuwa suna masu bayar da
shaida a kan rayukansu da kafirci,
wacfannan ayyukansu sun Bad,
kuma a cikin wuta su madawwama
ne.
18. Abin sani kawai, mai raya
masallatan Allah, shT ne wanda ya
yi Tmani da Allah da Ranar Lahira,
kuma ya tsayar da salla kuma ya
bayar da zakka, kuma bai ji tsoron
kowa ba face Allah. To, akwai
tsammanin wacfannan su kasance
daga shiryayyu.
' \ > • If
*t > \ * '" \' /f \ > ' '
At'
\yplJ\^j]^^^lJ^Jj
(1) Watau kuna zaton ku shiga Aljanna saboda cewarku, "Mun yi imam," kawai?
A'aha ! Sai Allah Ya bayyanar da mai gaskiyar Tmani game da jihadi, kuma gaskiyar Tmani
itace ce rashin soyayya da wanin Allah da ManzonSa da muminai, duka wanda ya so wani
abu baicinsu, to, ba mumini ba ne, ba zai shiga Aljanna ba domin wai ya yi Tmani kawai.
Ma'anar son Allah da son Annabi shi ne rashin sa6a wa umurninSa. Ma'anar son wanin
Allah da wanin Annabi, shi ne ka yi abin da wanin nan yake so, alhali kuwa a wajen yinsa
akwai sa6a wa Allah da ManzonSa.
275
9 - Suratut Tauba
G8SIK&-1
19. Shin, kun sanya shayar da
mahajjata da rayar da Masallaci
Mai alfarma kamar wanda ya yi
Tmani da Allah da Ranar Lahira,
kuma ya yi jihadi a cikin hanyar
Allah? Ba su daidaita a wurin Al-
lah. Kuma Allah ba Ya shiryar da
mutane azzalumai.
20. Wadanda suka yi Tmani,
kuma suka yi hijira, kuma suka yi
jihadi, a cikin hanyar Allah, da
dukiyoyinsu, da rayukansu, su ne
mafi girma ga daraja, a wurin Allah,
kuma wadannan su ne masu bab-
ban rabo.
21. Ubangijinsu Yana yi musu
bishara da wata rahama daga gare
Shi, da yarda, da gidajen Aljanna.
Suna da, a cikinsu, ni'ima zauna-
nniya.
22. Suna madawwama a cikinsu,
har abada. Lalle ne Allah a wurinSa
akwai lada mai girma.
23. Ya ku wadanda suka yi Tma-
ni! Kada ku riki ubanninku da
'yan'uwanku masoya, idan sun
nuna son kafirci a kan Tmani. (1)
Kuma wanda ya ji Since su daga
gare ku, to, wadannan su ne azza-
lumai.
24. Ka ce: "Idan ubanninku da
cfiyanku da 'yan'uwanku da matan-
ku da danginku da dukiyoyi, wa-
danda kuka yi tsiwirwirinsu, da
fatauci wanda kuke tsoron tasga-
ronsa, da gidaje wadanda kuke yar-
Moj>U\>
(1) Idan an umurci mutum ya rabu da ubansa da 'yan'uwansa kafirai, saboda shTyana
Musulmi, to, ga waninsu abin ya fi £arfi.
276
9 — Suratut Tauba
&m>-\
da da su, sun kasance mafiya soyu-
wa a gare ku daga Allah da Man-
zonSa, da yin jihadi ga hanyarSa,
to, ku yi jira har Allah Ya zo da
umurninSa! Kuma Allah ba Ya
shiryar da mutane fasikai.
25. Lalle ne, haklka, Allah Ya
taimake ku a cikin wurare masu
yawa, da Ranar Hunainu, (1) a loka-
cin da yawanku ya ba ku sha'awa,
sai bai amfanar da ku da kome ba,
kuma kasa ta yi kunci a kanku da
yalwarta, sa'an nan kuma kuka
juya kuna masu bayar da baya.
26. Sa'an nan kuma Allah Ya
saukar da natsuwarSa a kan Man-
zonSa, kuma a kan muminai, kuma
Ya saukar da rundunoni warfanda
ba ku gan su ba, kuma Ya azabtar
da warfanda suka kafirta: wancan
ne sakamakon kafirai.
27. Sa'an nan kuma Allah Ya
kar6i tuba daga bayan wancan a
kan wanda Ya so. Kuma Allah ne
Mai gafara, Mai rahama.
28. Ya ku warfanda suka yi Tma-
ni! Abin sani kawai, mushirikai
najasa ne, saboda haka kada su
kusanci Masallaci Mai alfarma a
bayan shekararsu wannan. Kuma
ifi% ^ T^ A •£'-* ">'x' > -Iff
<£ » > < yi f /
A^
*^ » <. »> < yi is
(1) Hunainu wani wadi ne a tsakanin Makka da T)a'ifa inda Musulmi suka yi yaki da
Hawazinawa, a cikin Shawwal shekara ta takwas. Yawan Musulmi ya rude su har suka ce,
"Yau ba za a rinjaye mu ba, saboda karanci." Yawansu ya kasance dubu goma sha biyu,
kuma kafirai dubu hudu, sai suka ji tsoro, suka gudu, suka bar Annabi a kan alfadararsa,
Baida'a, babu kowa tare da shi face Abbas da Abu Sufyana wanda yake rike da likkafar
Annabi. Annabi ya sanya Abbas ya yi ta kiran su, "Ya Ansar! Ya Muhajirun!' 1 har suka
komo aka ci nasara.
277
Suratut Tauba
&$®&-\
idan kun ji tsoron talauci (1) , to, da
sannu Allah zai wadata ku daga
falalarSa, idan Ya so. Lalle Allah ne
Masani, Mai hikima.
29. Ku yaki wacfanda (2) ba su
yin Tmani da Allah kuma ba su
imani da Ranar Lahira, kuma ba su
haramta abin da Allah da Manzon-
Sa Suka haramta, kuma ba su yin
addini, addinin gaskiya, daga
wadanda aka bai wa Littafi, har sai
sun bayar da jizya daga hannu,
kuma suna kaskantattu.
30. Kuma Yahudawa suka ce:
"Uzairu (fan Allah ne". Kuma Na-
sara suka ce: "Masihu (fan Allah
ne". Wancan zancensu ne da baku-
nansu. Suna kama da maganar wa-
danda suka kafirta daga gabani.
Allah Ya la'ance su ! Yaya aka kar-
katar da su?
31. Sun riki malamansu (3) (Ya-
hudu) da ruhubanawansu (Nasara)
ubannangiji, baicin Allah, kuma
sun riki MasThu (fan Maryama
(haka). Kuma ba a umurce su ba
face da su bauta wa Ubangiji Guda.
Babu abin bauta wa face Shi. Tsar-
c^
jLAp ^>cD^^oUaL^ ot
\ *-\ ^ '\i' "Ik' ^ * 'vK
^a>
L3 VO' AWl A-4-W-3
4-
■'MiiStf
(1) Idan kun ji tsoron talauci saboda nana mushirikai zuwa hajji, saboda fataucinku
da su zai rage, to, babu kome, arziki ga Allah yake, Yana bayar da shi ga wanda Yake so.
(2) Bayan gama hukuncin alakar Musulmi da kafiran farko, watau masu shirkin,
Larabawa, sai kuma ya far a bayanin alakar Musulmi kafirai na biyu ; watau Yahudu da
Nasara.
(3) Hibru shi ne malamin Yahudawa, Ruhubani mai ibada wanda ya yanke jin dadin
duniya daga kansa saboda ibada, daga cikin Nasara, mabiyan, gefen biyu sun riki
shugabanninsu ubanningiji suna bauta musu, watau suna yanka musu dokoki wadanda ba
na Allah ba, su kuma suna bin su a kan haka. Bautar da suke yi wa Uzairu ko MasThu, Tsa
dan Maryama domin sun ce su diyan Allah ne, watau sun zama juz'inSa ke nan. Tsarki ya
tabbata ga Allah daga wadannan siffofi duka.
278
Suratut Tauba
tmm-i
kinSa ya tabbata daga barin abin da
suke yin shirki da shi.
32. Suna nufin su bice hasken
Allah da bakunansu. Kuma Allah
Yana ki, face dai Ya cika haskenSa,
kuma ko da kafirai sun ki.
33. Shi ne Wanda Ya aiko man-
zonSa da shiriya da addinin gas-
kiya, domin ya bayyana shi a kan
addini dukansa, kuma ko da mushi-
rikai sun ki.
34. Ya watfanda suka yi Tmani !
Lalle ne masu yawa daga Ahbar (1)
da Ruhbanawa, haklka suna cin
dukiyar mutane da karya, kuma
suna kangewa daga hanyar Allah.
Kuma wadanda suke taskacewar
zmariya da azurfa, kuma ba su ciyar
da ita a cikin hanyar Allah, to, ka yi
musu bushara da azaba mai radadi.
35. A ranar da ake kona shi a
kanta a cikin wutar Jahannama, sai
a yi lalas da ita ga goshinansu da
sashinansu da bayayyakinsu, (a ce
musu) "Wannan ne abin da kuka
taskace domin rayukanku. To, ku
dancfani abin da kuka kasance kuna
sanyawa a taska."
36. Lallai ne kidayayyun watan-
ni a wurin Allah wata goma sha
biyu ne a cikin Littafin (2) Allah, a
jt^J^j^ b 4$ \jj \_£\ b)Q I ^L^>J^yi
/^ y^ >• ^\t
»^> y + W\'
^S J^li l3^UL^jj£2tf IXj^I
(1) Jam'in Hibru watan malamin Yahudawa.
(2) Ko da, a cikin wadannan watanni akwai masu alfarma, ko da yake su kafirai ba sa
kiyaye alfarmarsu ba, sun shigar da wani wayonsu a ciki wanda suke cewa NasT'u (watau
jinkiri) : Idan suna son su yi yaki a cikin dayan watannin, sai su halattar da shi, sa'an nan su
haramta wani wata a matsayinsa, su kara kaflrci a kan kafircinsu, da yin haka. Saboda
haka Allah Ya halattar da yaki a cikin kowanne wata domin kada a mamayi Musulmi.
Kuma yin jihadi yana cikin ayyukan ibada wadda Allah Yake ri6anya ladarta a cikin
watannin, masu alfarma.
279
Suratut Tauba
$M*&-\
ranar da Ya halicci sammai da kasa,
daga cikinsu akwai hutfu masu al-
farma. Wannan ne addini madai-
daici. Saboda haka kada ku zalunci
kanku a cikinsu. Kuma ku yaki
mushirikai gaba daya, kamar yadda
suke yakar ku gaba cfaya. Kuma ku
sani cewa lallai ne Allah Yana tare
da masu takawa.
37. Abin sani ka wai "Jinkirtawa"
kari ne a cikin kafirci, ana Batar da
wadanda suka kafirta game da shi :
suna halattar da wata a wata sheka-
ra kuma su haramtar da shi a wata
shekara domin su dace da adadin
abin da Allah Ya haramta. Saboda
haka suna halattar da abin da Allah
Ya haramtar. An kawace musu mu-
nanan ayyukansu. Kuma Allah ba
Ya shiryar da mutane kafirai.
38. Ya ku wadanda suka yi Ima-
ni ! Mene ne a gare ku, idan an ce
muku, "Ku fita da yaki a cikin
hanyar Allah", sai ku yi nauyi (1)
zuwa ga kasa. Shin, kun yarda da
rayuwar duniya ne daga ta Lahira?
To jin dadin rayuwar duniya bai
zama ba a cikin Lahira, face kadan.
39. Idan ba ku fita da yaki ba,
Allah zai azabta ku da azaba mai
radacfi, kuma Ya musanya wasu
mutane, wasunku (a maimakonku).
* S>*7^ **'»'
(1) Nauyi zuwa ga Rasa, watau ku kasa tashi tsaye balle ma ku fita zuwa yakin da aka
neme ku da shi (saboda shi). Fita da yaki a nan, ana nufin yakin Tabuka a cikin lokacin
bazara, kuma babu abinci domin Allah Ya jarrabi Musulmi, Ya fitar da muminai da kuma
munafukai, domin a san yadda za a yi ma'amala da su. Haka kuma a kowane lokaci Allah
Yakan sanya wani abin jarraba na wahala a cikin Musulmi domin Ya bambanta muminai
daga munafukai.
280
9 — Suratut Tauba
«&&-1
Kuma ba za ku cutar da Shi da
kome ba. Kuma Allah a kan dukan
kome Mai Tkon yi ne.
40. Idan ba ku taimake shi ba,
to, lalle ne Allah Ya taimake shi, a
lokacin da wadanda suka kafirta
suka fitar da shi, yana na biyun
biyu, a lokacin da suke cikin kogon
dutse, a lokacin da yake cewa da
sahibinsa: "Kada ka yi bakin ciki,
lalle ne Allah Yana tare da mu". Sai
Allah Ya saukar da natsuwarSa a
kansa, kuma Ya taimake shi da
wadansu rundunoni, ba ku gan su
ba, kuma Ya sanya kalmar wadan-
da suka kafirta makaskanciya,
kuma kalmar Allah ita ce madau-
kakiya. Kuma Allah ne Mabuwayi,
Mai hikima.
41. Ku fita da yaki kuna masu
saukakan kaya da masu nauyi,
kuma ku yi jihadi da dukiyoyinku
da kuma rayukanku a cikin hanyar
Allah. Wancan ne mafi alheri a gare
ku, idan kun kasance kuna sani.
42. Da ya kasance (1) wata sifar
duniya ce, makusanciya, da tafiya
matsakaiciya, da sun bTjca, kuma
amma fagen ya yi musu nTsa. Kuma
za su yi ta yin rantsuwa da Allah,
"Da mun sami dama, da mun tafi
tare da ku". Suna halakar da kansu
(da rantsuwar karya) ne, kuma Al-
lah Yana sanin lalle, hakika, su
makaryata ne.
oy^i
^yL-j&rj L-Ax^jvJ Jj^->o.d x2j\j $Jk>
(1) Ya shiga bayanin siffofin munafukai wacfanda suka ki fita da wadanda suk fita
zuwa Tabuka, da wadanda suka nemi wani uzuri, a cikin siffofi dabam-dabam da za a iya
gane munafukai da su a cikin kowane zamani na rayuwar Musulmi a duniya.
281
9 — Suratut Tauba
$$m&-\
43. Allah Ya yafe maka laifi.
Domin me ka yi musu izinin zama?
Sai wacfanda suka yi gaskiya sun
bayyana a gare ka, kuma ka san
makaryata.
44. Wacfanda suke yin Tmani da
Allah da Ranar Lahira, ba za su
nemi izininka ga yin jihadi da
dukiyoyinsu da rayukansu ba.
Kuma Allah ne Masani ga masu
takawa.
45. Abin sani kawai, wacfanda
ba sa Tmani da Allah da Ranar
Lahira, kuma zukatansu suka yi
shakka, su ne ke neman izininka,
sa'an nan a cikin shakkarsu suna ta
yin kai kawo.
46. Kuma da sun yi nufin fita, da
sun yi wani tattali saboda shi, kuma
amma Allah Ya ki zaburarsu, sai Ya
nauyayar da zamansu. Kuma aka
ce ku zauna tare da masu (1) zama.
47. Da sun fita a cikinku ba za su
kare ku da kome ba face da Barna,
kuma lalle da sun yi gaggawar sa-
nya annamlmanci a tsakaninku,
suna nema muku fitina. Kuma a
cikinku akwai 'yan rahoto saboda
su. Kuma Allah ne Masani ga
azzalumai.
48. Kuma lalle ne, hakTka, sun
nemi fitina daga gabani, kuma suka
juya maka al'amari, har gaskiya ta
zo (2) , kuma umurnin Allah Ya
bayyana, alhali suna masu kyama.
G5 o^ilJL^^liij
(1) Watau mata da yara da gajiyayyu.
(2) Tun farkon zuwan Annabi a Madina munafukai sun yi ta yin kaidi domin su 6ata
aramarin Annabi da Musulunci, suka kasa, har gaskiya ta bayyana, suka kama bakinsu
domin rashin abin da za su iya facfa a yarda da shi.
282
9 — Suratut Tauba
mm-*
49. Kuma daga cikinsu (1) akwai
mai cewa, "Ka yi mini izinin zama,
kuma kada ka fitine ni". To, a cikin
fitinar suka facfa. Kuma lalle ne
Jahannama, haklka, mai kewayewa
ce ga kafirai.
50. Idan wani alheri ya same ka,
zai 6ata musu rai, kuma idan wata
masifa ta same ka sai su ce, "Haki-
ka, mun rike aramarinmu daga
gabani". Kuma su juya, alhali kuwa
suna masu farin ciki.
51. Ka ce, "Babu abin da yake
samun mu face abin da Allah Ya
rubuta saboda mu. Shine Maji6in-
cinmu. Kuma ga Allah, sai mumi-
nai su dogara".
52. Ka ce, "Shin, kuna dako ne
da mu? Face dai da dayan abubu-
wan biyu (2) masu kyau, alhali kuwa
mu, muna dako da ku, Allah Ya
same ku da wata azaba daga gare
Shi, ko kuwa da hannayenmu. To,
ku yi dako. Lalle ne mu, tare da ku
masu dakon ne".
53. Ka ce, "Ku ciyar a kan yarda
ko kuwa a kan tllas. Ba za a karBa
daga gare ku ba. Lalle ne ku, kun
kasance mutane fasikai."
54. Kuma babu abin da ya hana
a kar6i ciyarwarsu daga gare su face
" TTvT' \ .'• W \*~ <S < > » ^
^t ^ • > V\ V K >1
<; >
.iwit4*yji
(1) Kuma a yanzu ga yakin Tabuka (munafukai) sun bayyana da irin uzurran da suke
kawowa domin kada su fita, kamar mai cewa, "To, Allah Ya nana zina, idan na fita na ga
matan Rumawa, ba zan iya yin hakuri daga barinsu ba. Saboda haka ina son a kar6i
uzurina kada a jefa ni a cikin fitina". Bai sani ba, da wannan rashin fitar ya jefa kansa a
cikin fitinar, domin za a bar shi tare da mata, su da shi kawai.
(2) T)ayan abubuwa biyu masu kyau, su ne mutuwa a kan shahada ko rinjaya da
samun gamma da izza.
283
9 — Suratut Tauba
t^JJ^-n
domin su, sun kafirta da Allah da
ManzonSa, kuma ba su zuwa ga
salla face Luma suna masu kasala,
kuma ba su ciyarwa face suna masu
kyama.
55. Saboda haka, kada dukiyo-
yinsu su ba ka sha'awa, kuma haka
'ya'yansu. Abin sani kawai, Allah
Yana nufin Ya yi musu azaba da su a
cikin rayuwar duniya, kuma rayu-
kansu su fita alhali kuwa suna ka-
firai.
56. Kuma suna rantsuwa da Al-
lah cewa, lalle ne su, haJolca, daga
gare ku suke, alhali kuwa ba su
zamo daga gare ku ba. Kuma amma
su mutane ne masu tsoro.
57. Da suna samun mafaka ko
kuwa wacfansu buloli, ko kuwa
wani mashigi, da sun juya zuwa
gare shi, kuma suna gaggawar
shiga.
58. Kuma daga cikinsu akwai
wanda yake zunden ka a kan
sha'anin dukiyoyin sadaka, sai idan
an ba su daga cikinta, su yarda,
kuma idan ba a ba su ba daga
cikinta sai su zamo suna masu fushi.
59. Kuma da dai su lalle sun
yarda da abin da Allah Ya ba su, da
ManzonSa, kuma suka ce, "Ma'is-
hinmu Allah ne, zai kawo mana
daga falalarSa kuma ManzonSa
(zai ba mu). Lalle ne mu, zuwa ga
Allah masu kwacfayi ne."
60. Abin sani kawai, dukiyoyin
sadaka na fakirai ne da miskinai da
masu aiki a kansu, da wacfanda ake
lallashin zukatansu, kuma a cikin
,>/.•;,/ > >*
'Ati-^x
y&. Jujl 0>ii^j I U^u <lL>j ~^-y
284
Suratut Tauba
$$m-\
fansar wuyoyi, da mabarta, da a
cikin hanyar Allah da dan hanya
(matafiyi). Farilla daga Allah.
Kuma Allah ne Masani, Mai hiki-
ma.
61. Kuma daga cikinsu akwai
wacfanda suke cutar Annabi, kuma
suna cewa, "Shi kunne (1) ne". Ka
ce: Kunnen alheri gare ku, yana
Tmani da Allah, kuma yana yarda
da muminai, kuma rahama ne ga
wacfanda suka yi Tmani daga gare
ku. Kuma wadanda suke cutar
Manzon Allah suna da azaba mai
racfacfi.
62. Suna rantsuwa da Allah sa-
boda ku, domin su yardar da ku.
Kuma Allah da ManzonSa ne mafi
cancantar su yardar da Shi, idan
sun kasance muminai.
63. Shin, ba su sani ba cewa,
"Lalle ne wanda ya saba wa Allah
da ManzonSa, hakiRa yana da wu-
tar Jahannama, yana madawwami
a cikinta? Waccan ita ce wula-
kantawa babba!"
64. Munafukai suna tsoron a
saukar da wata sura a kansu, wadda
take ba su labari ga abin da yake
cikin zukatansu. Ka ce, "Ku yi
izgili. Lalle ne, Allah ne Mai fitar da
abin da kuke tsoro."
\ >ss s < k i' > »>
\y
> > »> 1 ^^ >>
'<.'>
>. y *w><
?-> *' *
4*
>>-'*
(1) Shi kunne ne, ma'anarsa, kome ka gaya masa yana gaskatawa, watau wai ba shi
da wayon gane gaskiya da karya. Saboda haka Allah Ya ce, kunnen alheri, watau ya san
gaskiya kuma yana gaskata ta, kuma ya san karya, ba ya aiki da ita.
285
Suratut Tauba
&m>-\
65. Kuma lalle ne, idan ka tam-
baye (1) , su hakTka, suna cewa,
"Abin sani kawai, mun kasance
muna hira kuma muna wasa." Ka
ce, "Shin da Allah, da kuma ayo-
yinSa da ManzonSa kuka kasance
kuna izgili?"
66. Kada ku kawo wani uzuri,
hakTka, kun kafirta a bayan Imanin-
ku. Idan Mun yafe laifi ga wata
kungiya daga gare ku, za Mu azabta
wata kungiya saboda, lalle, sun
kasance masu laifi.
67. Munafukai maza da
munafukai mata, sashensu (2) daga
sashe, suna umurni da abin ki,
kuma suna hani daga alheri. Kuma
suna damkewar hannayensu. Sun
mance Allah, sai Ya manta da su.
Lalle ne munafukai su ne fasikai.
68. Allah ya yi wa'adi ga muna-
fukai maza da munafukai mata da
kafirai da wutar Jahannama, suna
madawwama a cikinta. Ita ce ma'is-
hiyarsu. Kuma Allah Ya la'ance su,
kuma suna da azaba zaunanniya.
69. Kamar wacfanda suke a
gabaninku, sun kasance mafi tsana-
nin karfi daga gare ku, kuma mafi
yawan dukiyoyi da dlya. Sai suka ji
dadi da rabonsu, sai kuka ji dadi da
rabonku kamar yadda wadanda
^ fa" 9 ' 9 i\"> *f '\' **'*'*'{
>^j£m \*S*^>\ U±=> ysJbX&f*LU^>\5
(1) Ana a cikin tafiya zuwa Tabuka sai wasu mutane daga cikin munafukai suka ce wa
junansu, "Wannan yana zaton ya ci gidajen Rumawa da Biranensu? Faufau." Sai Allah Ya
sanar da AnnabinSa (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) abin da suka facfa. Sai ya
ce, "Ku zo mani da wacfancan mutane." Da suka je masa ya ce musu 'Kun ce kaza da
kaza.' Sai suka yi rantsuwa da cewa: ba mu kasance ba sai muna hira muna wasa.
(2) Su duka daidai suke ga halinsu na sharri. Damke hannu shi ne rowa.
286
Suratut Tauba
&3&-\
suke a gabaninku suka ji dacfi, da
rabonsu, kuma kuka kutsa kamar
kutsawarsu. Wacfancan ayyukansu
sun 6aci a duniya da Lahira, kuma
wacfannan su ne masu hasara.
70. Shin, labarin wadanda suke a
gabaninsuj)ai je musu ba, mutanen
Nuhu da Adawa da Samudawa da
mutanen Ibrahim da Ma'abuta
Madyana da wadanda aka birkice?
Manzanninsu sun je musu da ayoyi
bayyanannu. To, Allah bai kasance
Yana zaluntar su ba, amma sun
kasance rayukansu suke zalunta.
71. Kuma mummunai maza da
mummunai mata sashensu maji-
6incin sashe ne, suna umurni da
alheri (1) kuma suna hani daga abin
da ba a so, kuma suna tsayar da
salla, kuma suna bayar da zakka,
kuma suna tfa'a ga Allah da Man-
zonSa. Wacfannan Allah zai yi
musu rahama. Lalle Allah ne Ma-
buwayi, Mai hikima.
72. Kuma Allah Ya yi wa'adi ga
mummunai maza da mummunai
mata da gidajen Aljanna koramu
suna gudana daga karkashinsu,
suna madawwama a cikinsu, da
wuraren zama masu dacfi a cikin
gidajen Aljannar. Kuma yarda
daga Allah ce mafi girma. Wancan
shi ne babban rabo, mai girma.
73. Ya kai Annabi ! Ka yaki kafi-
rai da munafukai kuma ka tsaurara
>. »<.
^>ff "»'z" • > "\\ ^ »y
(1) Abin da aka sani ga shan'a shine alheri, kuma abin da da ba a sani ba ga shan'a
shT ne abin £i wanda ba a so.
287
Suratut Tauba
««&-n
a kansu. Kuma matattararsu
Jahannama ce. Tir da ta zama
makomar!
74. Suna rantsuwa da Allah, ba
su facfa ba, alhali kuwa lalle ne,
haklka, sun facfi kalmar kafirci,
kuma sun kafirta a bayan musul-
untarsu, kuma sun yi himma ga
abin da ba su samu ba. Kuma ba su
zargi kome ba face domin Allah da
ManzonSa Ya wadatar da su daga
falalarSa. To, idan sun tuba zai
kasance mafi alheri gare su, kuma
idan sun juya baya, Allah zai azabta
su da azaba mai racfadi a cikin
duniya da Lahira, kuma ba su da
wani masoyi ko wani mataimaki a
cikin kasa.
75. Kuma daga cikinsu akwai
wacfanda suka yi wa Allah alka-
wari, "Lalle ne idan ya kawo mana
daga falalarSa, hakika, muna bayar
da sadaka, kuma lalle ne muna
kasance wa daga salihai."
76. To, a lokacin da Ya ba su
daga falalarSa, sai suka yi rowa da
shi, kuma suka juya baya suna
masu bijirewa.
77. Sai Ya biyar musu da muna-
funci a cikin zukatansu har zuwa ga
ranar da suke haduwa da Shi, sabo-
da saba wa Allah ga abin da suka yi
Masa alkawari, kuma saboda abin
da suka kasance suna yi na karya.
78. Shin, ba su sani ba cewa lalle
ne Allah Yana sanin asTrinsu da
ganawarsu, kuma lalle Allah ne
Masanin abubuwan fake?
* "\\ 'X * >* " »> ^v^ E » ~\'
288
Suratut Tauba
mm-*
79. Wacfanda suke aibanta masu
yin alheri daga mummunai a cikin
dukiyoyin sadaka, da wadanda ba
su samu face iyakar kokarinsu, sai
suna yi musu izgili. Allah Yana yin
izgili gare su. Kuma suna da azaba
mai ratfadi.
80. K6 ka nema musu gafara ko
ba ka nema musu ba, idan ka nema
musu gafara sau saba'in, to, Allah
ba zai gafarta musu ba. Saboda su,
sim kafirta da Allah da ManzonSa.
Kuma Allah ba Ya shiryar da muta-
ne fasikai.
81. Wadanda aka bari sun yi
farin ciki da zamansu a bayan Man-
zon Allah, kuma suka £i su yi jihadi
da dukiyoyinsu da rayukansu a ci-
kin hanyar Allah, kuma suka ce,
"Kada ku fita zuwa yaki a cikin
zafi." Ka ce, "Wutar Jahannama ce
mafi tsananin zafi." Da sun kasance
suna fahimta!
82. Saboda haka su yi dariya
kadan, kuma su yi kuka da yawa a
kan sakamako ga abin da suka
kasance suna tsirfatawa.
83. To, idan Allah Ya mayar da
kai zuwa ga wata kungiya daga gare
su, sa'an nan suka neme ka izni
domin su fita, to, ka ce, "Ba za ku
fita tare da m ba har abada, kuma
ba za ku yi yaki tare da m ba a kan
wani makiyi. Lalle ne ku, kun yarda
da zama a farkon lokaci, sai ku
zauna tare da mata masu zaman
gida."
84. Kuma kada ka yi salla a kan
kowa daga cikinsu wanda ya mutu,
><y >\i s <
>XSs'A '?£
jj^us
< > 7?'\\&\' V\''
3 O^— Jj^j »ji> © UJ *»
, -<7f <,>-f
'< <«• -. s>'s
289
9 — Suratut Tauba
fcSSlKgi-l
har abada, kuma kada ka tsaya a
kan kabarinsa. Lalle ne su, sun
kafirta da Allah da ManzonSa,
kuma sun mutu alhali kuwa suna
fasikai.
85. Kuma kada dukiyoyinsu da
diyansu su ba ka sha'awa. Abin sani
kawai, Allah Yana nufin Ya yi musu
azaba da su a cikin duniya, kuma
rayukansu su fita alhali kuwa suna
kafirai.
86. Kuma idan aka saukar da
wata Sura cewa: Ku yi Imani da
Allah kuma ku yi jihadi tare da
ManzonSa. Sai mawadata daga
gare su su nemi izninka, kuma su ce :
Ka bar mu mu kasance tare da
mazauna.
87. Sun yarda da su kasance tare
da mata masu zama (a cikin gidaje).
Kuma aka rufe a kan zukatansu,
saboda haka, su, ba su fahimta.
88. Amma Manzon Allah da wa-
cfanda suka yiTmani tare da shi, sun
yi jihadi da dukiyoyinsu da rayu-
kansu. Kuma wadannan suna da
ayyukan alheri, kuma wadannan su
ne masu cin nasara.
89. Allah ya yi musu tattalin
gidajen Aljanna, koramu suna gu-
dana daga karkashinsu, suna ma-
dawwama a cikinsu. Wancan ne
babban rabo mai girma.
90. Kuma masu uzuri daga £au-
yawa zuka zo domin a yi musu izini,
kuma wadanda suka yi wa Allah da
ManzonSa karya, suka yi zamansu.
Wata azaba mai radacfi za ta sami
wadanda suka kafirta daga gare su.
10 UrU^\^^Ol^j\jJL3j
290
9 — Suratut Tauba
M&&-1
91. Babu laifi a kan maraunana
kuma haka majinyata, kuma babu
laifi a kan wacfanda ba su samun
abin da suke ciyarwa idan sun yi
nas!ha (1) ga Allah da ManzonSa.
Kuma babu wani laifi a kan masu
kyautatawa. Kuma Allah ne Mai
gafara, Mai tausayi.
92. Kuma babu (laifi) a kan wa-
cfanda idan sun je maka domin ka
dauke su, ka ce, "Ba ni da abin da
nake tfaukar ku a kansa," suka juya
alhali kuwa idanunsu suna zubar da
hawaye domin bakin ciki cewa ba su
sami abin da suke ciyarwa ba.
93. Abin sani kawai, laifi yana a
kan wadanda suke neman izininka
alhali kuwa su mawadata ne. Sun
yarda su kasance tare da mata ma-
maya (gidaje), kuma Allah Ya dan-
ne a kan zukatansu, domin haka su,
ba su ganewa.
94. Suna kawo uzurinsu zuwa
gare ku idan kun koma zuwa gare
su. Ka ce, "Kada ku kawo wani
uzuri, ba za mu amince muku ba.
Haklka, Allah Ya ba mu labari daga
labarunku, Allah zai ga aikinku
kuma ManzonSa (zai gani). Sa'an
nan kuma a mayar da ku zuwa ga
Masanin gaibi da bayyane, sai Ya
ba ku labarin abin da kuka kasance
kuna aikatawa."
95. Za su yi rantsuwa da Allah a
gare ku idan kun juya zuwa gare su,
domin ku kau da kai daga gare su.
Mc&&%&zw$S$
pjjfi-*- ^jJ^-iV-" ot
>^*^»>^/
XSJ^A
^\^J^\V ^ ^-^ j J&1 5^4-*
(1) NasTha ita ce su fadi maganar £warai ; kyautatawa ita ce a yi aiki domin Allah, ba
domin neman duniya ba.
291
9 — Suratut Tauba
&m-\
To, ku kau da kai daga gare su don
ko su kazanta ne, kuma Jahannama
ce matattararsu bisa ga sakamakon
abin da suka kasance suna tsir-
fatawa.
96. Suna rantsuwa gare ku do-
min ku yarda da su. To, idan kun
yarda da su, to, lallai ne Allah ba
Shi yarda da mutane fasikai.
97. Kauyawa ne mafi tsananin (1)
kafirci da munafinci, kuma su ne
mafi kamanta ga rashin sanin
haddodin abin da Allah Ya saukar a
kan ManzonSa. Kuma Allah ne
Masani, Mai hikima.
98. Kuma daga kauyawa akwai
wacfanda (2) suke rikon abin da suke
ciyarwa a kan tara ce, kuma suna
sauraron aukuwar masTfa a gare ku,
aukuwar mummunar masTfa ta tab-
bata a kansu. Kuma Allah ne Mai ji,
Masani.
99. Kuma daga kauyawa akawi
wacfanda suke yinTmani da Allah da
Ranar Lahira, kuma suna rikon
abin da suke ciyarwa (tamkar) wa-
cfansu ibadodin neman kusanta ne a
wurin Allah da addu'o'in Man-
zonSa. To, lalle ne ita (ciyarwar
nan) ibadar neman kusanta ce a
gare su. Allah zai shigar da su a
cikin RahamarSa. Lalle Allah ne
Mai gafara, Mai jin kai.
tits
(1) Kauyawa ne mafi tsananin kafirci domin nTsansu daga sanin halayen girmamawa
da na zamantakewa, sa'an nan da nTsansu daga Annabi bar su saurari abin da ya zo da shi.
(2) Kauyawa kashi biyu ne: akwai wawaye munafukai masu ganin addmi ya cfora
musu nauyin biyan zakka da sauran ayyukan alheri, suna daukar sa kamar tara da biyan
kakkarai. Kuma akwai kauyawa masu hankali sun sani Annabi manzo ne daga Allah, suna
daukar abin da addmi ya aza musu duka ibada ne, suna fatar kusanta da shi zuwa ga Allah,
Ubangijinsu. To su mutanen kwarai ne, za su shiga Aljanna.
292
9 — Suratut Tauba
f^ll^-n
100. Kuma masu tserewa (1) na
farko daga Muhajirina da Ansar da
wacfanda suka bi su da kyautatawa,
Allah Ya yarda daga gare su su
kuma sun yarda daga gare Shi,
kuma Ya yi masu tattalin gidajen
Aljanna: koramu suna gudana a
karkashinsu, suna madawwama a
cikinsu har abada. Wancan ne ba-
bban rabo mai girma.
101. Kuma daga wacfanda suke a
gefenku daga kauyawa akwai
munafukai, (2) haka kuma daga
mutanen Macfiha: sun goge a kan
munafunci, ba ka sanin su, Mu ne
Muke sanin su. Za Mu yi musu
azaba sau biyu, sa'an nan a mayar
da su zuwa ga azaba mai girma.
102. Kuma da wacfansu, sun yi
furuci (3) da laifinsu, sun hacfa aiki na
kwarai da wani mummuna. Akwai
tsammanin Allah Ya kar6i tuba a
kansu. Lallai Allah ne Mai gafara,
Mai jin kai.
103. Ka kar6i sadaka daga
dukiyoyinsu ka tsarkake su, kuma
ka tabbatar da kirkinsu da ita.
Kuma ka yi musu addu'a. Lallai
addu'o'inka natsuwa ne a gare su.
Kuma Allah ne Mai ji, Masani.
\' * Z"
(1) Yakin Tabuka ya kasa jama'ar Musulmi gwargwadon Tmaninsu da ayyukansu da
gabatarsu a cikin addmi, cikin darajoji da rfabakoki. Darajar farko ita ce, Sahabban farko
wacfanda suka tsere wa sauran mutane ga shiga Musulunci da karfin imani da yawan aiki
da tsarkake zuciya ga aikin Allah.
(2) FCungiya ta biyu munafukai masu zurfin wayo, sun san yadda suke 66ye
munafuncinsu saboda gogewa da iya munafunci har mutane ba za su iya gane su ba, sai
Allah Ya tona su.
(3) Wata kungiya wadda ta yi munafunci, ta ki fita zuwa yaki amma kuma suka ga
sun yi laifi suka yi ikirari da cewa "sun yi laifi," sa'an nan suka tuba, Allah Ya kar6i
tubarsu.
293
Suratut Tauba
&i*&-\
104. Shin, ba su sani ba, cewa
lallai Allah ne Yake karbar tuba
daga bayinSa, kuma Yana karbar
sadakokinsu, kuma lalle Allah ne
Mai karbar tuba, Mai jin kai?
105. Kuma ka ce, "Ku yi aiki,
sa'an nan Allah zai ga aikinku, da
ManzonSa da Muminai, kuma
za a mayar da ku zuwa ga Masanin
fake da bayyane, sa'an nan Ya ba ku
labari ga abin da kuka kasance
kuna aikatawa."
106. Kuma da wadansu wa-
danda (1) aka jinkirtar ga umurnin
Allah, ko dai Ya yi musu azaba ko
kuma Ya karbi tuba a kansu. Kuma
Allah ne Masani, Mai hikima.
107. Kuma wadanda (2) suka riki
wani masallaci domin cuta da ka-
firci da neman rarrabewa a tsakanin
muminai da bagewa ga taimakon
wanda ya yaki Allah daManzonSa
daga gabani, kuma hakTka suna yin
rantsuwa cewa, "Ba mu yi nufin
komai ba face alheri" alhali kuwa
Allah Yana yin shaida cewa, su,
hakTka, makaryata ne.
108. Kada ka tsaya a cikinsa har
abada. Lalle ne, Masallaci wanda
*'\\ / \^' 9 \' ^ 9 >Y\ *s"'\'~ 9 '-'
(1) Wata kungiya wadda^ita ba munafuka ba ce, amma kuma ba su fita zuwa yakin
ba, kuma ba su da wani dalTli sai kasala kawai da taushewar Shaicfan. Wacfannan an
jinkirtar da al'amarinsu har Allah Ya yi hukunci a kansu.
(2) Wata kungiya ta munafukai masu aiki domin tum6uke karfin Musulmi ta hanyar
da ba a iya ganewa da sauri. Kamar su gina masallaci kusa da wani tsohon masallaci da
sunan taimakon addini amma da nufin su raba jama'ar Musulmi, kuma sun sami wurin da
za su rika taro da boye kayan yaki da shirin sharri ga Musulmi. Kamar ma'abuta Masjidil
Darar, wanda aka yi kusa da masallacin Kuba a Madlna. Aikinsu bai tsaya ga lokacin
yakin Tabuka ba, saboda haka aka ce, da bagewa ga wanda ya yaki Allah a gabani, watau
a gabanin bayyanar fallasar munafukai da yakin Tabuka.
294
9 — Siiratut Tauba
imm-i
aka yi harsashinsa a kan takawa tun
farkon yini, shT ne mafi cancantar
ka tsaya a cikinsa. A cikinsa akwai
wacfansu maza suna son su tsar-
kaka. (1) Kuma Allah Yana son
masu neman tsarkakuwa.
109. Shin, wanda ya sanya
harsashin gininsa a kan takawa
daga Allah da yarda, shi ne mafi
alheri ko kuwa wanda ya sanya
harsashin gininsa a kan ga6ar rami
mai tusgawa? Sai ya rusa da shi a
cikin wutar Jahannama. Kuma Al-
lah ba Ya shiryar da mutane azza-
lumai.
110. Gininsu, wanda suka gina,
ba zai gushe ba yana abin shakka a
cikin zukatansu, face idan zuka-
tansu sun yanyanke. Kuma Allah ne
Masani, Mai Hikima.
111. Lalle ne, Allah Ya saya (2)
daga mummunai, rayukansu da
dukiyoyinsu, da cewa suna da Al-
janna, suna yin yaki a cikin hanyar
Allah, saboda haka suna kashewa
ana kashe su. (Allah Ya yi) wa'adi a
kanSa, tabbace, a cikin Attaura da
LinjTla da Alkur'ani. Kuma wane ne
mafi cikawa da alkawarinsa daga
Allah? Saboda haka ku yi bushara
da cinikinku wanda kuka kulla da
j u-j ^wd ^3 *jA- > o' <3^'->» yt. yy <-£
(1) Suna son tsarkaka ta boye da ta bayyane. Ta boye sananniya ce, ita ce rashin
munafunci, kuma ta bayyane ita ce suna kama ruwa a bayan sun karce kashinsu da dutse,
kamar yadda ya zo a cikin Hadlsi. Allah ne Mafi sani.
(2) Bayan bayanin nau'ukan kafirai da alamominsu da yadda za a bi wajen yankewa
da su, da barin fage ga muminai na kwarai, sai kuma Ya kirayi muminai zuwa ga
mubaya'a ga Allah, watau ciniki, sa'an nan Ya bayyana musu kucfin saye da abin sayarwa,
ya ce: Allah Ya saya daga muminai...
295
9 — Suratut Tauba
imm-i
Shi. Kuma wancan shi ne babban
rabo, mai girma.
112. Masu (1) tuba, masu bau-
tawa, masu godewa, masu tafiya,
masu ruku'i, masu tawali'u, masu
umurni da alheri da masu hani daga
abin da aka ki da masu tsarewa ga
iyakokin Allah. Kuma ka bayar da
bushara ga muminai.
113. Ba ya kasancewa^ ga An-
nabi da wadanda suka yi imani, su
yi istigifari ga mushirikai, kuma ko
da sun kasance ma'abuta zumunta
ne daga bayan sun bayyana a gare
su, cewa lalle ne, su, 'y& n Jahim ne.
114. Kuma istigifarin Ibrahim
ga ubansa bai kasance ba face sabo-
da wani wa'adi ne da ya kulla
alkawarinsa da shi, sa'an nan a
lokacin da ya bayyana a gare shi
(Ibrahim) cewa lalle ne shi (ubansa)
makiyi ne ga Allah, sai ya barranta
daga gare shi. Lalle ne Ibrahim,
haklka, mai yawan kuka ne, (3) mai
hakuri.
115. Kuma Allah bai kasance
mai 6atar da mutane a bayan Ya
shiryar da su ba, sai Ya bayyana
musu abin da za su yi takawa da shi.
Lalle ne Allah, ga kome, Masani ne.
ftp >CZj&£RJZj
»• f ^ »- t A'"-* ' A"
=AZ\
^> » \' Z -zvi s '»A\ >9 *<*""- *'
c ^ >'
(1) Sa'an nan kuma ya bayyana a cikin wannan aya ta 112 siffofin muminai
wadanda aka fuskantar da kiran neman ciniki da su.
(2) Bayanin umurni da yanke wa kafirai, ko da sun mutu, da barin yi musu addu'ar
alheri.
(3) Ibrahim, mai yawan kuka ne saboda rashin musuluntar ubansa da yankewarsa
daga gare shi a duniya da Lahira. Kuma mai halcuri ne da abin da ya same shi a wannan abu
da waninsa na abubuwan jarrabawar Allah a gare shi.
296
Suratut Tauba
GM&-1
116. Lalle ne Allah Yana (1) da
mulkin sammai da kasa, Yana ra-
yarwa kuma Yana matarwa. Kuma
ba ku da wani masoyi, kuma ba ku
da mataimaki, baicin Allah.
117. Lallai ne, hakika, Allah Ya
kar6i tubar Annabi da (2) Muha-
jirina da Ansar wacfanda suka bi
shi, a cikin sa'ar tsanani, daga baya
zukatan wani 6angare daga gare su
sun yi kusa su karkata, sa'an nan
(Allah) Ya kar6i tubarsu. Lalle, ShT
ne Mai tausayi, Mai jin kai gare su.
118. Kuma (Allah) Ya kar6i
tuba a kan ukun (3) nan wacfanda
aka jinkirtar har kasa da yalwarta
ta yi kunci a kansu, kuma rayu-
kansu suka yi kunci a kansu, kuma
suka yi zaton babu wata mafaka
daga Allah face (komawa) zuwa
gare Shi. Sa'an nan Allah Ya kar6i
tubarsu, domin su tabbata a kan
i^\ »■ <, >%>>'* >~ \ < v ^ \" -?
(1) Wannan aya tana nuna cewa takllfin da Allah Yake aza wa bayinSa na ya£i da
waninSa, ba domin ya wahalar da su ba ne. Yana y\ ne domin alheri a gare su, ShT Allah
Mawadaci ne, Yana da £asa da sammai, kuma ShT ne Mai yin halittar kome.
(2) Ya fara gabatar da cewa "Allah Ya karfti tubar Annabi da wacfanda Ya ambata
tare da shi" domin ya biyar ayar da ke zuwa ta tubar wacfanda suka yi zamansu, ba da wani
uzuri ba, kuma su ba munaftucai ba, aka jinkirtar da maganar tubarsu har a bayan horon
kwana hamsin babu mai yi musu magana, bisa hanin Allah. Kuma da an ambaci karftar
tubarsu kawai ba da an gabatar da tubar wacfanda suka fita ba, da sai a ce sun fi wacfanda
suka fita, domin an yi nassi a kan tubarsu. Wanda aka yi nassi a kan tubarsa, ya fi wanda
aka bari a cikin duhu.
(3) Su mutane uku wacfanda aka jinkintar da al'amarinsu, a aya ta 106, su ne Ka'abu
bn Maliki da Mararatu bn RabT'a el Umary, da Halalu bn Umaiya el Waicify: sun £i fita,
ba da wani uzuri ba, kuma a lokacin da Annabi ya komo daga Tabuka, wacfanda ba su fita
ba suka tail suka facfi uzurorinsu na rashin fita. Annabi ya kar6a musu kuma ya nema
musu gafara. Amma su ukun, suka facfi gaskiya cewa sun zauna ne ba domin munafunci
ba, sai dai abin ya kasance haka kawai ba da wani uzuri ba. To, Annabi ya ce su dakata sai
abin da Allah Ya ce a kansu. Aka hana kowa ya yi musu magana a cikin MadTna, har
matansu na aure. Suka yi kwana hamsin a cikin matsuwa, sa'an nan Allah Ya sauko da
tubarsu.
297
9 — Suratut Tauba
«E&-n
tuba. Lalle Allah ne Mai kar6ar
tuba, Mai jin kai.
119. Ya ku wacfanda suka yilma-
ni ! Ku bi Allah da takawa, kuma ku
kasance tare da masu gaskiya.
120. Ba ya kasancewa (1) ga
mutanen Madina da wanda yake a
gefensu, daga kauyawa, su sa6a
daga bin Manzon Allah, kuma
kada su yi gudu da rayukansu daga
ransa. Wancan, saboda kishirwa ba
ta samun su, haka kuma wata wa-
hala, haka kuma wata yunwa, a
cikin hanyar Allah, kuma ba su
takin wani mataki wanda yake ta-
kaitar da kafirai kuma ba su samun
wani samu daga makiyi face an
rubuta musu da shi, ladar aiki na
kwarai. Lallai ne Allah ba Ya tozar-
ta ladar masu kyautatawa.
121. Kuma ba su ciyar da wata
ciyarwa, karama ko babba, kuma
ba su keta wani rafi sai an rubuta
musu, domin Allah Ya saka musu
da mafi kyawon abin da suka ka-
sance suna aikatawa.
122. Kuma ba ya kasancewa ga
muminai su fita zuwa yaki gaba
cfaya. (2) Saboda haka, don me ne
4±{^^\JjJlS\ O^j^ 'n^D o liij 1
(1) Bayanin falalar mutane da ke zaune a Madina tare da Annabi, a lokacinsa ko
bayansa.
(2) Bayan ya kare bayani a kan falalar da Allah Ya fffTta mazauna Madina da ita,
saboda haka ba ya halatta a gare su su sa6a wa Annabi da zama a bayan ya fita zuwa yaki.
Sa'an nan kuma ya yi idiraki da isharar cewa fita zuwa yaki farillar kifaya ce: wasu suna
dauke wa wasu. Kuma ba ya kyautuwa a ce kowa ya zama sojan yaki, a bar sauran ayyuka
na lalurar rayuwa kamar fita neman ilmi, shi ma farillar kifaya ne tTlas wasu su fita zuwa
nemansa domin idan sun koma ga mutanensu sai su karantar da su. Hikimar ayar ta fara
da maganar fita zuwa yaki kuma ta kare da sakamakon komowa daga makaranta domin
nunawar fita zuwa gare su duka wajibi ne: wanda wani ke iya dauke wa wani. Allah ne
Mafi sani.
298
9 — Suratut Tauba
«2&-1
wata jama'a daga kowane Bangare
daga gare su ba ta fita (zuwa neman
ilimi ba) domin su nemi ilimi ga
fahimtar addlni kuma domin su yi
gargacfi ga mutanensu idan sun
koma zuwa gare su, tsammaninsu,
suna yin sauna?
123. Ya ku wacfanda suka yilma-
ni! Ku yaki wacfanda suke kusan-
tar (1) ku daga kafirai. Kuma su
sami tsanani daga gare ku. Kuma
ku sani cewa Allah Yana tare da
masu takawa.
124. Kuma idan aka saukar (2)
da wata sura, to, daga gare su akwai
wacfanda suke cewa, "Wane a cikin-
ku wannan sura ta kara masa
Tmani?" To amma wacfanda suka yi
Tmani, kuma su, suna yin bushara
(da ita).
125. Amma kuma wacfanda suke
a cikin zukatansu akwai cuta, to, ta
kara musu kazanta zuwa ga kazan-
tarsu, kuma su mutu alhalin kuwa
suna kafirai.
126. Shin, ba su ganin cewa ana
fitinar su a cikin kowace shekara:
sau cfaya ko kuwa sau biyu, sa'an
nan kuma ba su tuba, kuma ba su
zama suna tunani ba?
127. Kuma idan haklka, aka
saukar da wata sura, sai sashensu ya
yi dubi zuwa ga wani sashe, (su ce),
"Shin, wani mutum yana ganin
ku?". Sa'an nan kuma sai su juya.
i^> \' ^ '\i\-\ '-\>
»>^ *A \ >
-V Jm \* ' - >:<"--> ~\.\T'\'\'
o?*?
*> > •" \$t'>
»< '♦r//, S
~>jy* CJjH \ b» \'Aj
(1) Bayanin yadda ake yin yaki ne; ba a facfa wa dukkan makiya gaba cfaya, na kusa
da na nesa. Sai an fara da na kusa tukuna sa'nan nan a dinga facfacfawa.
(2) Takaitawa da karin tanbihi ga abin da surar ta kunsa.
299
9 - Suratut Tauba
tmm-i
Allah Yajuyar da zukatansu, do-
min, hakika, su mutane ne, ba su
fahimta.
128. Lalle ne, haklka, Manzo (1)
daga cikinku ya je muku. Abin da
kuka wahala da shi mai nauyi ne a
kansa. Mai kwacfayi ne saboda ku.
Ga muminai Mai tausayi ne, Mai
jin Rai.
129. To, idan sun juya, sai ka ce :
Ma'ishlna Allah ne. Babu abin bau-
tawa face Shi. A gare Shi nake
dogara. Kuma Shi ne Ubangijin
Al'arshi mai girma.
Jr*
-^ii^VI^^
v>*\
3^^^\J^J^\i^^jcJ^==^y
Tana karantar da tauhidin Ubangiji game da jan hankali zuwa
ga abubuwan halitta wacfanda suka shafi mutane wajen amfani da
su.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. A. L. R. Wadancan ayoyin
littafi ne kyautatacce.
J| j^\^&\lLt^J\
(1) Bayanin rahamar Allah game da aiko Manzo daga cikin mutane, cewa wata falala
ce a gare su. Kuma shi Manzon nan cfan'uwansu ne wanda ba ya son su da wani abu sai
alheri, idan sun gane da sun bT shi, kuma idan ba su gane ba, to, Allah Ya tsare shi daga
sharrinsu, kuma Ya isar masa.
300
10 — Suratu Yunus
&S$^ - V
2. Shin, ya zama abin mamaki ga
mutane domin Mun yi wahayi zuwa
ga wani namiji daga gare su cewa,
"Ka yi gargacfi ga mutane kuma ka
yi bushara ga wadanda suka yi
imani da cewa : lalle ne suna da abin
gabatarwar gaskiya a wurin
Ubangijinsu." Kafirai ^suka ce,
"Lalle ne wannan, hakTka, masi-
hirci ne bayyananne."
3. Lalle Allah ne Ubangijinku
Wanda Ya halicci sammai da kasa a
cikin kwana shida, sa'an nan kuma
Ya daidaita a kan Al'arshi Yana
gudanar da al'amari. Babu wani
maceci face a bayan izninSa. Wan-
nan ne Allah, Ubangijinku, sai ku
bauta Masa. Shin fa, ba ku tunani?
4. Zuwa gare Shi makomarku
take gaba daya, wa'adin Allah gas-
kiya ne. HakTka, Shi ne Yake fara
halitta, sa'an nan kuma Ya mayar
da ita domin Ya saka wa wadanda
suka yi imani kuma suka aikata
ayyukan kwarai da adalci, kuma
wadanda suka kafirta suna da abin
sha daga ruwan zafi, da azaba mai
radacfi, saboda abin da suka kasan-
ce suna yi na kafirci.
5. Shi ne Wanda Ya sanya muku
rana, babban haske, da wata mai
haske, kuma Ya kaddara shi ga
Manziloli, domin ku san kidayar
shekaru da lissafi. Allah bai halitta
wannan ba, face da gaskiya, Yana
bayyana ayoyi daki-daki domin
mutane wadanda suke sani.
6. Lalle ne a cikin sabawar dare
da yini, da abin da Allah Ya halitta a
cikin sammai da kasa, haklka akwai
ilA^-^J ' * -^ Ij-JLjuJ J j \J^,o j -L3J
301
10 — Suratu Yunus
&$$& - V
ayoyi ga mutane wacfanda suke yin
takawa.
7. Lalle ne wacfanda ba su kau-
nar gamuwa da Mu, kuma suka
yarda da rayuwar duniya kuma
suka natsu da ita, da wadanda suke
gafalallu ne daga ayoyinMu,
8. Wadannan matattararsu
Jahannama ce saboda abin da suka
kasance suna tsirfatawa.
9. Lalle ne warfanda suka yi Tma-
ni kuma suka aikata ayyukan kwa-
rai, Ubangijinsu Yana shiryar da su
saboda Imaninsu, koramu suna gu-
dana daga karkashinsu, a cikin
gidajen Aljannar ni'ima.
10. Kiransu a cikinta, "Tsar-
kinKa ya Allah!" kuma gaisuwarsu
a cikinta, "Salamun" kuma karshen
kiransu, cewa, "Godiya ta tabbata
ga Allah Ubangijin halitta."
11. Kuma da Allah Yana gag-
gawa ga mutane da sharri kamar
yadda Yake gaggauta musu da alhe-
ri, hakTka da an hukunta ajalinsu
zuwa gare su. Saboda haka Muna
barin wadanda ba su kaunar gamu-
wa da Mu, a cikin kangararsu suna
ta cfimuwa.
12. Kuma idan cuta ta shafi mu-
turn, sai ya kiraye Mu, yana (kwan-
ce) ga sashensa ko kuwa zaune, ko
kuwa a tsaye. To, a lokacin da
Muka kuranye cutar daga gare shi,
sai ya shude kamar dai bai kiraye
Mu ba zuwa ga wata cuta wadda ta
shafe shi. Kamar wannan ne aka
kawata ga mabannata, abin da suka
kasance suna aikatawa.
\^x^M%&d4§
E
G3 ^CZ^yk^^^^^^J^^z^
j^) ol^=»J-^^Jr> <cx-LdLtS Ills u^lijl
302
10 — Suratu Yunus
£%&$& - V
13. Kuma, haklka, Mun halakar
da al'ummomi daga gabaninku, a
lokacin da suka yi zalunci, kuma
manzanninsu suka je musu da
hujjqji bayyanannu, amma ba su
kasance suna Tmani ba. Kamar
wannan ne, Muke sakawa ga muta-
ne masu laifi.
14. Sa'an nan kuma Muka sanya
ku masu mayewa a cikin kasa daga
bayansu, domin Mu ga yaya kuke
aikatawa.
15. Kuma idan ana karatun ayo-
yinMu bayyanannu a kansu, sai
wadanda ba su Raunar gamuwa da
Mu, su ce, "Ka zo da wani Alku-
r'ani, wanin wannan, ko kuwa ka
musanya shi." (1) Ka ce, "Ba ya
kasancewa a gare ni in musanya shi
da kaina. Ba ni biyar kome face
abin da aka yiwo wahayi zuwa gare
ni. Kuma, haklka, ni ina tsoro idan
na sa6a wa Ubangijina, ga azabar
wani yini mai girma."
16. Ka ce, "Da Allah Ya so da
ban karanta shi ba a kanku, kuma
da ban sanar da ku ba game da shi,
domin lalle ne na zauna a cikinku a
zamani mai tsawo daga gabanin
(fara saukar) sa. Shin fa, ba ku
hankalta?
17. "Saboda haka wane ne mafi
zalunci daga wanda ya kirkira ka-
rya ga Allah, ko kuwa ya karyata
ayoyinSa? Hakika, masu laifi ba su
cin nasara!"
*s( ~\X1 - ' " V/v/^
'<.< "* '*'S>>.
u
(1) Suna nufin idan ya musanya shi, su ce, "To, ga shi ka bayyana cewa kai ne mai
kirkira shi, kana jingina shi ga Allah."
303
10 — Suratu Yiinus
iiM^Sb^ ~~ \*
18. Kuma suna bauta wa, baicin
Allah, abin da ba ya cutar da su
kuma ba ya amfaninsu, kuma suna
cewa, "Watfannan ne macetanmu a
wurin Allah. ,, Ka ce, "Shin, kuna
bai wa Allah labari ne ga abin da bai
sani ba, a cikin sammai ko a cikin
kasa? TsarkinSa ya tabbata kuma
Ya daukaka daga gabin da duk suke
yin shirki da Shi."
19. Kuma mutane ba su kasance
ba face al'umma guda, sa'an nan
kuma suka sa6a wa juna, kuma ba
domin wata kalma ba wadda ta
gabata daga Ubangijinka, da an yi
hukunci a tsakaninsu a kan abin da
yake a cikinsa suke sa6a wa juna.
20. Kuma suna cewa, "Don me
ba a saukar da wata aya ba a gare
shi, daga Ubangijinsa?" To, ka ce,
"Abin sani kawai, gaibi ga Allah
yake. Sai ku yi jira. Lalle ne nl, tare
da ku, ina daga masu jira."
21. Kuma idan Muka dandana
wa mutane wata rahama, a bayan
wata cuta ta shafe su, sai ga su da
makirci a cikin ayoyinMu. Ka ce,
"Allah ne mafi gaggawar (saka-
makon) makirci. "Lalle neManzan-
ninMu suna rubuta abin da kuke yi
na makirci.
22. Shi ne wanda Yake tafiyar da
ku a cikin tudu da (kuma) teku, sai
idan kun kasance a cikin jirage, su
gudana tare da su da iska mai dacfi,
kuma su yi farin ciki da ita, sai wata
guguwa ta je wa jiragen, kuma tagu-
war ruwa ta je musu daga kowane
wuri, kuma su tabbata cewa su, an
kewaye su, sai su kirayi Allah,
lij^^ U4All^>J J o
<jl>~« J°02 f\>** ' r*-* **?3 <— JLy^L-c- ^VJ
304
10 — Suratu Yunus
@88& - V
suna masu tsarkake addini gare Shi,
(suna cewa) : Lalle ne idan Ka kuBu-
tar da mu daga wannan, haklka
muna kasancewa daga masu gddi-
ya.
23. To, a lokacin da Ya kuButar
da su, sai ga su suna zalunci a cikin
kasa, ba da wani hakki ba. Ya ku
mutane! Abin sani kawai, zalun-
cinku a kanku yake, a bisa rayuwar
duniya. Sa'an nan kuma zuwa gare
Mu makomarku take, sa'an nan
Mu ba ku labari game da abin da
kuka kasance kuna aikatawa,
24. Abin sani kawai, misalin
rayuwar duniya kamar ruwa ne
Muka saukar da shi daga sama,
sa'an nan tsiron kasa ya garwaya da
shi : daga abin da mutane da dabbo-
bi suke ci, har idan kasa ta ri£i
zinariyarta kuma ta yi kawa, kuma
mutanenta suka zaci cewa su ne
masu Tkon yi a kanta, sai umurn-
inMu ya je mata da dare ko kuma
da rana, sai Mu maishe ta girbabba
kamar ba ta wadata ba a jiya. Ka-
mar wannan ne Muke rarrabe
ayoyi, daki-daki, ga mutane wa-
cfanda suke tunani.
25. Kuma Allah Yana kira zuwa
ga gidan aminci, kuma Yana shiryar
da wanda Yake so zuwa ga tafarki
madaidaici.
26. Wadanda suka kyautata yi,
suna da abu mai kyawo kuma da
kari (1) , wata kura ba ta rufe fusko-
-^ TT 9 ' • "nF\ * < t 9 ' 9> v\ * > >
(1) Masu aikin £warai wacfanda suka kar6a kiran Allah suna da sakamakon abu mai
kyau, watau Aljanna, kuma da £ari, watau ganin Ubangijinsu a cikin Aljanna. Haka
Hadisi ya yi fassara.
305
10 — Suratu Yunus
&$*& - V
kinsu, kuma haka wani kaskanci.
Wacfancan ne abokan Aljanna,
suna madawwama a cikinta.
27. Kuma wacfanda suka yi tsir-
far munanan ayyuka, sakamakon
mummuna da kamarsa yake, kuma
kaskanci yana rufe su. Ba su da
wani matsari daga Allah, kamar an
rufe fuskokinsu da guntayen kira-
ruwa daga dare mai duhu. Watfan-
nan ne abokan wuta, suna madaw-
wama a cikinta.
28. Kuma a ranar da Muke tara
su gaba daya, sa'an nan kuma Mu
ce wa wadanda suka yi shirki, "Ku
kama matsayinku, ku da abubuwan
shirkinku." Sa'an nan Mu rarrabe a
tsakaninsu, kuma abubuwan shir-
kinsu su ce, "Ba mu kuka kasance
kuna bauta wa ba.
29. "To, kuma Allah Ya isa
zama Shaida a tsakaninmu da
tsakaninku. Hakika mun kasance
ba mu san kome ba na bauta warku
a gare mu!"
30. A can ne kowane rai yake
jarraba abin da ya bayar bashi,
kuma aka mayar da su zuwa ga
Allah, MajiBincinsu Tabbatacce,
kuma abin da suka kasance suna
kirkirawa ya Bace musu.
31. Ka ce, "Wane ne Yake arzuta
ku daga sama da kasa? Shin, ko
kuma Wane ne Yake mallakar jida
gam, kuma Wane ne Yake fltar da
mai rai daga mamaci, kuma Ya fltar
da mamaci daga mai rai, kuma
Wane ne Yake shirya aramari?"
To, za su ce, "Allah ne." To, ka ce,
"Shin fa, ba za ku yi takawa ba?"
i^r.
fc
E3 djW^lJJtt4HbjJyL~i
306
10 — Suratu Yunus
£m£$& - >•
32. To, wancan ne Allah, Uban-
gijinku Tabbatacce. To, mene ne a
bayan gaskiya face 6ata? To, yaya
ake karkatar da ku?
33. Kamar wancan ne kalmar
Ubangijinka, ta tabbata a kan wa-
cfanda suka yi fasikanci, cewa haki-
ka su, ba za su yi Tmani ba.
34. Ka ce, "Shin, daga abubu-
wan shirkinku akwai wanda yake
fara halitta, sa'an nan kuma ya
mayar da ita?" Ka ce, "Allah ne
Yake fara halitta, sa'an nan kuma
Ya mayar da ita. To, yaya ake juyar
da ku?"
35. Ka ce, "Shin, daga abu-
buwan shirkinku akwai wanda yake
shiryarwa zuwa ga gaskiya?" Ka ce,
"Allah ne Yake shiryarwa zuwa ga
gaskiya. Shin fa, wanda Yake shir-
yarwa ne mafi cancantar a bi Shi, ko
kuwa wanda ba ya shiryarwa face
dai a shiryar da shi? To, mene ne a
gare ku? Yaya kuke yin hukunci?"
36. Kuma mafi yawansu ba su
biyar kome face zato. Lalle ne zato
ba ya wadatar da kome daga gas-
kiya. Lalle Allah ne Masani ga abin
da suke aikatawa.
37. Kuma wannan Alkur'ani bai
kasance ga a kirkira shi ba daga
wanin Allah, kuma amma shi
gaskatawar wannan ne da yake a
gabaninsa da bayanin hukuncin lit-
taffan Allah, babu shakka a cikinsa,
daga Ubangijin halittu yake.
38. Ko suna cewa, "Ya kirkira
shi"? Ka ce. "Ku zo da sura guda
misalinsa, kuma ku kirayi wanda
*>*^r *-> ^-."^ 4 ^
307
10 — Suratu Yunus
&&J& - V
kuka iya duka, baicin Allah, idan
kun kasance masu gaskiya."
39. A 'a, sun karyata game da
abin da ba su kewaye da saninsa ba,
kuma fassararsa ba ta riga ta je
musu ba. Kamar wacfancan ne
wacfanda suke a gabaninsu. Sai ka
duba, yaya akibar azzalumai ta
kasance?
40. Kuma daga cikinsu akwai
wanda yake yinTmani da Shi, kuma
daga cikinsu akwai wanda ba ya yin
Tmani da Shi. Kuma Ubangijinka ne
Mafi sani ga mabarnata.
41. Kuma idan sun karyata ka,
to, ka ce, "Ina da aiklna kuma kuna
da aikinku, ku kubutattu ne daga
abin da nake aikatawa, kuma ni
kubutacce ne daga abin da kuke
aikatawa.''
42. Kuma daga cikinsu akwai
wacfanda suke saurare zuwa gare
ka. Shin fa, kai kana jiyar da kur-
ma, kuma ko da sun kasance ba su
hankalta?
43. Kuma daga cikinsu akwai
wanda yake tsokaci zuwa gare ka.
Shin fa, kai kana shiryar da makafi,
kuma ko da sun kasance ba su gani?
44. Lalle ne Allah ba Ya zaluntar
mutane da kome, amma mutanen
ne ke zaluntar kansu.
45. Kuma ranar da Yake tara su,
kamar ba su zauna ba face sa'a guda
daga yini. Suna gane juna a tsaka-
ninsu. Hakika, wacfanda suka kar-
yata game da gamuwa da Allah sun
yi hasara. Kuma ba su kasance
masu shiryuwa ba.
•>.r < *-
v^ ^ »>\f >',\ '£"
* S^iACB
308
10 — Suratu Yunus
&&$& - y
46. Kuma imma dai, haklka, Mu
nuna maka sashen abin da Muke yi
musu alkawari, ko kuwa Mu karbi
ranka, to, zuwa gare Mu mako-
marsu take. Sa'an nan kuma Allah
ne Shaida a kan abin da suke aika-
tawa.
47. Kuma ga kowace al'umma
akwai Manzo. (1) Sa'an nan idan
Manzonsu ya je, sai a yi hukunci a
tsakaninsu da adalci, kuma su, ba a
zaluntar su.
48. Kuma suna cewa, "A yaushe
wannan wa'adi zai auku, idan kun
kasance masu gaskiya?"
49. Ka ce, "Ba na mallaka wa
kaina wata cuta, haka kuma wani
amfani, sai abin da Allah Ya so. Ga
kowace al'umma akwai ajali, idan
ajalinsu ya zo, to, ba za su yi jinkiri
daga gare shi ba, ko da sa'a guda,
kuma ba za su gabata ba."
50. Ka ce, "Shin, kun gani, idan
azabarSa ta zo muku da dare ko da
rana? Mene ne daga gare shi masu
laifi suke neman gaggawarsa?"
57. Shin, sa'an nan kuma idan
har ya auku, kun yi Tmani da shi?
Ashe? Yanzu kuwa, alhali kun ka-
sance game da shi kuna neman
gaggawar aukuwarsa?
52. Sa'an nan kuma aka ce ga
wacfanda suka yi zalunci, "Ku dan-
cfani azabar dawwama! Shin, ana
saka muku face da abin da kuka
kasance kuna aikatawa?"
"i >>/ .<* / *
KS^j^y^J +^>A*g Oy*j*J" c}==4j
IIP dj^^y^j^^^j^^t
*> t>
^J j^X^j^J^ b\^y n JC*^ - °y^J
Sf^^^L^^i«% < ^^1^
'' -%>."* r^
4^U* j^^il^Ste JL$^\ T^V^jcJi ~£\ JkJ
^oy^ju**yij
.<".< ,s*" >\\* " y> \'-' ~*f '\ "l 9 *"A *-
j^jU *l>Uc- \yj3 jjJLk <j>yjj J^3p
(oy o
^^^Mo^^f Jj»
(1) Manzo na farko shT ne mai shiryar da su, Manzo na biyu shi ne ajalinsu.
309
10 — Suratu Yunus
(&&J& - V
53. Kuma suna tambayar ka:
Shin gaskiya ne? Ka ce, "T, ina
rantsuwa da Ubangijina. Lalle gas-
kiya ne, kuma ba ku zama masu
buwaya ba."
54. Kuma da kowane rai wanda
ya yi zalunci ya mallaki duka abin
da yake a cikin icasa, to, da ya yi
fansa da shi. Kuma suka dinga
nadama a lokacin da suka ga azaba.
Sa'an nan aka yi hukunci a tsaka-
ninsu da adalci, kuma ba za a zalun-
ce su ba.
55. To ! HaRlRa Allah Ya mallaki
abin da yake a cikin sammai da
Rasa. To! Hala£a wa'adin Allah
gaskiya ne. Amma kuma mafi
yawansu ba su sani ba.
56. Shi ne Yake rayarwa kuma
Yake matarwa. Kuma zuwa gare
Shi ne ake mayar da ku.
57. Ya ku mutane! Lalle wa'azi
ya je muku daga Ubangijinku, da
waraka ga abin da yake a cikin
Iciraza, da shiriya da rahama ga
muminai.
58. Ka ce, "Da falalar Allah da
rahamarSa. Sai su yi farin ciki da
wannan." Shi ne mafi alheri daga
abin da suke tarawa.
59. Ka ce, "Shin, kun ga abin da
Allah Ya saukar saboda ku na arzi-
ki, sai kuka sanya hukuncin haram-
ci da halacci a gare shi?" Ka ce,
"Shin, Allah ne Ya yi muku izni, ko
ga Allah kuke icirlarawar icarya?"
60. Kuma mene ne zaton wacfan-
da suke £ir£ira £arya ga^ Allah, a
Ranar Kiyama? Lalle haialca, Allah
>*» """ , i-^* %'\ ^\' > *.'*"
^ ^ *-z *iv £fc"\
310
10 — Suratu Yunus
&$$& ~ >•
Ma'abucin falala ne a kan mutane,
amma kuma mafi yawansu ba su
godewa.
61. Kuma ba ka kasance a cikin
wani sha'ani ba, kuma ba ka karan-
ta wani abin karatu daga gare shi
ba, kuma ba ku aikata wani aiki ba,
face Mun kasance Halarce a lokacin
da kuke zubuwa a cikinsa. Kuma
wani ma'aunin zarra ba zai yi nlsa
ba daga Ubangijinka a cikin kasa,
haka kuma a cikin sama, kuma
babu wanda yake mafi karanci daga
haka, kuma babu mafi girma, face
yana a cikin littafi bayyananne.
62. To, Lalle ne masoyan (1) Al-
lah babu tsoro a kansu, kuma ba za
su kasance suna yin bakin ciki ba.
63. Wacfanda suka yi Imani ku-
ma suka kasance suna yin takawa.
64. Suna da bushara a cikin
rayuwar duniya da ta Lahira. Babu
musanyawa ga kalmomin Allah.
Wancan shi ne babban rabo mai
girma.
65. Kada maganarsu (2) ta sanya
ka a cikin bakin ciki. Lalle ne alfar-
ma ga Allah take gaba daya. Shi ne
Mai jT, Masani.
piSJ^-^^m^i^
(1) Waliyyin Allah, shi ne masoyin Allah da sharacfin ya zama mumini mai takawa —
watau yana aiki da abin da Allah Ya umurce shi, kuma yana barin abin da Allah Ya hana
shi, bisa harshen Annabinsa wanda yake biya. Babu karin kome babu ragi. Bushararsu, ita
ce yabon mutane a gare su, ko kuma a lokacin mutuwarsu mala'iku su rika yi musu
bushara da gamuwa da Ubangijinsu, ko kuma a cikin kabari wajen tambaya. Allah ne
Mafi sani.
(2) Maganarsu ta izgili a gare ka. Idan Allah Ya cfaukaka ka, babu mai iya hanawa
domin Shi kacfai ne Mai izza kuma sai inda Ya sanya ta ga wanda Ya so.
311
10 — Suratu Yunus
£%&$& - >•
66. To! HaMa Allah Yana da
mulkin wanda ke a cikin sammai da
wanda ke a cikin kasa kuma wacfan-
da suke kiran wanin Allah, ba su
biyar wacfansu abokan tarewa (ga
Allah a Mulkinsa). Ba su biyar
kome face zato. Kuma ba su zama
ba face suna kiri facQ kawai.
67. ShT ne Wanda Ya sanya
muku dare, domin ku natsu a cikin-
sa, da yini mai sanya a yi gani. Lalle
ne a cikin wannan akwai ayoyi ga
mutane wacfanda suke ji.
68. Suka ce, "Allah Ya riki da".
Tsarkinsa ya tabbata ! Shi ne Wada-
tacce, Yana da mallakar abin da
yake a cikin sammai da abin da
yake a cikin kasa. A wurinku babu
wani dalTli game da wannan ! Shin,
kuna facfar abin da ba ku sani ba
game da Allah?
69. Ka ce, "Haklka wacfanda
suke kirkira karya ga Allah, ba za
su ci nasara ba."
70. Jin dacfi ne a cikin duniya,
sa'an nan kuma makomarsu zuwa
gare Mu take, sa'an nan Mu cfan-
cfana musu azaba mai tsanani sabo-
da abin da suka kasance suna yi na
kafirci.
71. Kuma ka karanta musu laba-
rin Nuhu, a lokacin da ya ce wa
mutanensa, "Ya mutanena! Idan
matsayma da tunatarwata game da
ayoyin Allah sun kasance sun yi
nauyi a kanku, to, ga Allah na
dogara. Sai ku tara al'amarinku, ku
da abubuwan shirkinku, sa'an nan
kuma kada al'amarinku ya kasance
y/O^j^i^t^^^ivl
.\f<,*u Xx+j
+.*.
£P^C^&\p&rS$S>
s ^rf * y /%' ^ *' " ' ?\i ^ **
M 04/00 jyl ^-^Uj jo jJj\<*J\ Juo\
312
10 — Suratu Yunus
&&Z& - >•
rufaffe a kanku, sa'an nan kuma ku
kashe ni, kada ku yi mini jinkiri.
72. "Kuma idan kuka juya baya,
to, ban tambaye ku wata ijara ba.
Ijarata ba ta zama ba face daga
Allah, kuma an umurce ni da in
kasance daga masu sallamawa. (1) "
73. Sai suka karyata shi, sa'an
nan Muka kubutar da shi, da wan-
da yake tare da shi, a cikin jirgi,
kuma Muka sanya su masu maye-
wa, kuma Muka nutsar da wacfanda
suka karyata ayoyinMu. Sai ka
duba yadda akibar wacfanda aka yi
wa gargacfi ta kasance.
74. Sa'an nan kuma Muka aika
wacfansu Manzanni daga bayansa
zuwa ga mutanensu, suka je musu
da hujjoji bayyanannu, to, ba su
kasance za su yi Tmani ba saboda
sun karyata shi a gabani. Kamar
wannan ne Muke rufewa a kan
zukatan masu ta'adi.
75. Sa'an nan kuma a bayansu
Muka aika Musa da Haruna zuwa
ga Fir'auna da mashawartansa, tare
da ayoyinMu. Sai suka kangara
kuma sun kasance mutane masu
laifi.
76. Sa'an nan a lokacin da gas-
kiya ta je musu dagaj*are Mu, suka
ce, "Wannan hakika sihiri ne
bayyananne."
77. Musa ya ce, "Shin, kuna
cewa ga gaskiya a lokacin da ta zo
\y^bj^^^^\^^XJs
i-U- 111 3^0y>^ ^-^ ^ ^
(1) Watau dukan abin da na zo muku da shi na umurni ko hani, to, ni ma an umurce
ni da yinsa ko barinsa. Kuma ba ni neman wata ijarar karantarwa daga gare ku domin
Allah Ya umarce ni da iyar da manzancinSa zuwa gare ku, saboda haka Shi ne zai biya ni
tsadar aikina.
313
10 — Suratu Yunus
&&%£> - v
muku? Shin, sihiri ne wannan? Lal-
le masihirci ba ya cin nasara."
78. Suka ce, "Shin, ka zo mana
ne domin ka juyar da mu daga abin
da muka iske ubanninmu a kansa,
kuma girma ya kasance gare ku, ku
biyu a^cikin kasa? Ba za mu zama
masu Tmani ba saboda ku."
79. Kuma Fir'auna ya ce, "Ku
zo mini da dukan masihirci,
masani."
80. To, a lokacin da masihirta
suka je, Musa ya ce musu, "Ku jefa
abin da kuke jefawa."
81. To, a lokacin da suka jefa,
Musa ya ce, "Abin da kuka zo da
shi sihirijie. Lalle ne Allah zai Bata
shi. HakTka Allah ba Ya gyara aikin
ma6arnata.
82. "Kuma Allah Yana tabbatar
da gaskiya da kalmominSa, ko da
masu laifi sun ki."
83. Sa'an nan babu wanda ya yi
Tmani da Musa face zuriya daga
mutanensa, a kan tsoron kada Fi-
r'auna da shugabanninsu su fitine
su. Lalle, hakika, Fir'auna marin-
jayi ne a cikin kasa, kuma lalle shT,
hakika, yana daga masu 6arna.
84. Kuma Musa ya ce, "Ya ku
mutanena ! Idan kun kasance kun yi
Tmani da Allah, to, a gare Shi sai ku
dogara, idan kun kasance Musul-
mi."
85. Sai suka ce, "Ga Allah muka
dogara. Ya Ubangijinmu ! Kada Ka
sanya mu fitina ga mutane azzalu-
mai.
$3jJ^^jl
*-' .*" 9 '*»-',£ .-
S-Ss jl y s y £ *■* it's 9y*** ^^v s ^/"s y
314
10 — Suratu Yunus
&*&$& - *•
86. "Kuma Ka ku6utar da mu
domin RahamarKa, daga mutane
kafirai."
87. Kuma Muka yi wahayi zuwa
ga Musa da cfan'uwansa, cewa : Ku
biyu, ku zaunar da mutanenku a
Masar a cikin wasu gidaje. Kuma
ku sanya gidajenku su fuskanci Al-
Ribla (1) , kuma ku tsayar da salla.
Kuma ku bayar da bushara ga masu
Tmani.
88. Sai Musa ya ce, "Ya Ubangi-
jinmu! HakTka Kai ne Ka bai wa
Fir'auna da majalisarsa Rawa da
dukiyoyi a cikin rayuwar duniya, ya
Ubangijinmu, domin su Batar (da
mutane) daga hanyarKa. Ya
Ubangijinmu! Ka shafe a kan du-
kiyarsu kuma Ka yi cfauri (2) a kan
zukatansu yadda ba za su yi Tmani
ba har su ga azaba mai racfadi."
89. (Allah) Ya ce, "Lalle ne an
karbi addu'arku. Sai ku daidaitu,
kuma kada ku bi hanyar wacfanda
ba su sani ba."
90. Kuma Muka ketarar da Bani
Isra'ila teku,^sai Fir'auna da rundu-
narsa suka bi su bisa ga zalunci da
ketare haddi, har a lokacin da
nutsewa ta riske shi ya ce, "Na yi (3)
Tmani cewa, hakTka, babu abin bau-
tawa face Wannan da Banu Isra'il
C& J^Cll J; &lz^£jjf*rj fy
> <, 'vyC
(1) Su sanya gidajensu suna fuskantar Alkibla ta Ka'aba domin su rika yin salla a
cikin gidajen, saboda tsoron in sun tafi masallaci za a facfa su da duka suna a cikin salla.
Wannan kuma ya nuna yadda ake son gidajen Musulmi su kasance a ko da yaushe.
(2) Musa ya yi addu'a a kansu, har da rashin Tmani saboda ya sami labarin ba za su yi
Tmani ba, kamar mutanen Nuhu.
(3) Tmani a bayan Manzon mutuwa ya isa ga kafiri ba zai yi masa amfani ba.
315
10 — Suratu Yunus
&&J& - >•
suka yi imani da Shi, kuma m, ina
daga Musulmi"
9L Ashe ! A yanzu ! Alhali kuwa,
hakika ka saBa a gabani, kuma ka
kasance daga masu 6arna?
92. To, a yau Muna kuButar (1)
da kai game da jikinka, domin ka
kasance aya ga wacfanda suke a
bayanka. Kuma lalle ne masu yawa
daga mutane, haklka, gafalallu ne
ga ayoyinMu.
93. Kuma lalle ne, haklka Mun
zaunar (2) daBani Isra'ila mazaunar
gaskiya kuma Muka arzuta su daga
abubuwa masu dacfi. Sa'an nan ba
su saBa ba har ilmi ya je musu. Lalle
ne Ubangijinka Yana yin hukunci a
tsakaninsu a Ranar Kiyama a cikin
abin da suka kasance suna sa6a wa
juna.
94. To, idan ka kasance a cikin
shakka daga abin da Muka saukar
zuwa gare ka, sai ka tambayi wa-
cfanda suke karatun Littafi daga
gabaninka. Lalle ne, haklka, gas-
kiya ta je maka daga Ubangijinka
domin haka kada ka kasance daga
masu kokanto.
95. Kuma kada ka kasance daga
wacfanda suke karyatawa game da
ayoyin Allah, har ka kasance daga
masu hasara.
96. Lalle ne wacfanda kalmar
Ubangijinka ta wajaba a kansu, ba
za su yi Imani ba.
(1) Kubutar da jikin Fir'auna: banda ruhinsa domin a tabbatar da ya mutu.
(2) Allah Ya bai wa BanT Isra'ila mulkin Masar da Falascfinu gaba cfaya a bayan
halaka Fir'auna da mutanensa.
316
10 — Suratu Yunus
(&$$&> ~ >•
97. Kumakodakowaceayataje
musu, sai sun ga azaba mai racfadi.
98. To, domin me wata alkarya
ba ta kasance ta yi (1) Tmani ba har
Tmaninta ya amfane ta, face muta-
nen Yunus? A lokacin da suka yi
Tmani, Mun janye azabar wulakanci
daga gare su a cikin rayuwar du-
niya. Kuma Muka jiyar da su dacfi
zuwa wani lokaci.
99. Kuma da Ubangijinka Ya
so, da wacfanda suke a cikin kasa
sun yi Tmani dukansu gaba cfaya.
Shin, kai kana tTlasta mutane ne har
su kasance masu Tmani?
100. Kuma ba ya kasancewa ga
wani rai ya yi Tmani face da iznin
Allah, kuma (Allah) Yana sanya
kazanta a kan wacfanda ba su yin
hankali.
101. Ka ce, "Ku dubi abin da
yake cikin sammai da kasa." Kuma
ayoyi da gargacfi ba su wadatarwa
ga mutane wacfanda ba su yin
imani.
102. To, shin sunajiran wani abu
face kamar misalin kwanukan wa-
cfanda suka shucfe daga gabaninsu?
Kace, "Ku yi jira! Lalle nT tare da
ku, ina daga masu jira."
103. Sa'an nan kuma Muna ku-
Butar da manzanninMu da wacfan-
da suka yi imani, kamar wannan ne,
~*\*^ . •Nil • ' "<\ '$>'£< S\'
(1) Alkaryun da aka aika da Manzanni cikinsu, ba su yi imani duka ba face mutum
daya, ko biyu a gabanin halaka ta sami mutanensu. Sai dai alkaryar Yunusa, ita kam ta ji
tsoro, ta yi Tmani a gabanin saukar azaba, saboda haka suka tsira, ba a halaka garin ba-
watau Ninawa. Watau babu mai iya samun Tmani sai Allah Ya nufe shi da haka. K6 da mai
yin gargacfin yakan yiwu ya karkace, sai da tsarin Allah.
317
10 — Suratu Yunus
&&$& - >•
tabbatacce nea gare Mu, Mu ku6u-
tar da masu Tmani.
104. Ka ce "Ya ku mutane ! Idan
kun kasance a cikin kokanto daga
addiiima, to, ba ni bauta wa wadan-
da kuke bauta wa, baicin Allah,
kuma amma ina bauta wa Allah
Wanda Yake kar6ar rayukanku.
Kuma an umurce ni da in kasance
daga masu Tmani.
105. "Kuma (an ce mini): Ka
tsayar da fuskarka ga addini, kana
karkata zuwa ga gaskiya, kuma
kada ka kasance daga masu shirka.
106. "Kuma kada ka kirayi, bai-
cin Allah, abin da ba ya amfanin ka
kuma ba ya cutar ka. To, idan ka
aikata haka, sa'an nan lalle kai, a
lokacin, kana daga masu zalunci."
107. Kuma idan Allah Ya shafe
ka da wata cuta, to, babu mai yaye
ta face Shi, kuma idan Yana nufin
ka da wani alheri, to, babu mai
mayar da falalarSa. Yana samun
wanda Yake so daga cikin bayinSa
da shi. Kuma Shi ne Mai gafara,
Mai jin kai.
108. Kace,"Yakumutane! Lalle
ne gaskiya ta zo muku daga
Ubangijinku. To, wanda ya shiryu,
ya shiryu ne domin kansa kawai,
kuma wanda ya 6ace yana 6acewa
ne ajcansa kawai. Kuma ban zama
wakTli a kanku ba."
109. Kuma ka bi abin da ake yin
wahayinsa zuwa gare ka, kuma ka
yi hakuri har Allah Ya yi hukunci.
Kuma SliT ne Mafi alherin masu
hukunci.
5>' <"<>'
> >*^./»'
^*^l / < \' " ■*-* SS
318
11 - Suratu Hud
s&i^-n
Tana karantar da cewa Manzannin Allah sun kirayi mutanensu
zuwa ga tauhTdi da nau'in kira guda, kuma mutanen sun fuskance su
da hali guda a musu da karyatawa, sai ka ce a zamani guda suke, ko
a cikin harshe guda suka yi magana.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L A. L. R. Littafi ne an kyautata
ayoyinsa, sa'an nan an bayyana su
daki-daki, daga wurin Mai hikima,
Mai kididdigewa.
2. Kada ku bauta wa kowa face
Allah. Lalle ne ni a gare ku mai
gargadi ne kuma mai bushara daga
gare Shi.
3. Kuma ku nemi gafara gun
Ubangijinku. Sa'an nan ku tuba
zuwa gare Shi, Ya jiyar da ku dadi,
jiyarwa mai kyau zuwa ga ajali
ambatacce, kuma Ya bai wa dukan
ma'abucin girma girmansa. Amma
idan kun juya, to, lalle ni, ina tsoron
azabar yini mai girma a kanku.
4. Zuwa ga Allah makomarku
take, kuma ShT a kan kome Mai
Tkon yi ne.
->^»-\"
319
11 - Suratu Hud
fi#8&-M
5. To, lalle su, suna karkatar (1)
da £irjinsu domin su 66ye daga gare
shi. To, a lokacin da suke lullu6ewa
da tufafinsu Yana sanin abin da
suke 6oyewa da abin da suke bayya-
nawa. Lalle Shi Masani ne ga abin
da yake a cikin kiraza.
6. Kuma babu wata dabba a ci-
kin kasa face ga Allah arzikinta
yake, kuma Yana sanin matabba-
tarta (2) da ma'azarta, duka suna
cikin littafi bayyananne.
7. Kuma Shi ne Wanda Ya halic-
ci sammai da kasa a cikin kwanaki
shida, kuma AFarshinSa ya kasance
a kan ruwa, (3) domin Ya jarraba ku,
wanne ne daga cikinku mafi kya-
won aiki. Kuma hakika idan ka ce,
"Lalle ku wadanda ake tayarwa ne
a bayan mutuwa," haicTka, wadan-
da suka kafirta suna cewa: "Wan-
nan bai zama ba face sihiri bayya-
nanne."
8. Kuma lalle ne idan Mun jin-
kirta da azaba gare su zuwa ga wani
lokaci kidayayye, haioka suna cewa
me yake tsare (4) ta? To, a ranar da
za ta je musu, ba ta zama abin
, ?^>-r <-
(1) Ba su son su ga mai yi musu wa'azi, saboda haka idan sun tsinkayi Annabi daga
nesa, sai su 6uya, domin kada ya gan su, balle ma har ya yi musu wa'azi. Kuma har idan ya
same su da wa'azinsa, sai su sanya tufafinsu su rufe idanunsu da kunnuwansu kamar
yadda mutanen Nuhu suka yi masa a lokacin da yake yi musu wa'azi. Ka duba Suratu
Nuh, Sura ta 71.
(2) Matabbata shT ne uba, kuma ma'aza ita ce uwa.
(3) Farkon halitta, Al'arshi ko ruwa. Ruwa da Al'arshi suna gaba da sammai da kasa.
Sa'an nan aka halicci kasa daga ruwa kuma aka mayar da ruwa hayaki, aka halicci sama.
Sa'an nan kuma aka mulmula £asa a cikin surar kwai. Allah ne Mafi sani.
(4) Me ke tsare ta, watau azabar — me ke hana ta ta zo yanzu?
320
1 1 - Suratu Hud
£$£&-»
karkatarwa ba daga gare su. Kuma
abin da suka kasance suna yin izgili
da shi, ya wajaba a kansu.
9. Kuma lalle ne idan Mun dan-
dana wa mutum wata rahama daga
gare Mu, sa'an nan kuma Muka
zare ta daga gare shi, lalle ne shT,
hakTka, mai yanke tsammani ne,
mai yawan kafirci.
10. Kuma lalle ne idan Mun dan-
dana masa ni'ima a bayan cuta ta
shafe shi, yana cewa munanan ha-
laye sun tafi daga wurina. Lalle shi
mai farin ciki ne, mai alfahari.
//. Sai wadanda suka yi hakuri
kuma suka aikata ayyuka na kwarai.
Wadannan suna da gafara da lada
mai girma.
12. Saboda haka tsammaninka,
kai mai barin sashen abin da aka yi
wahayi zuwa gare ka ne, kuma mai
kuntata kirjinka da shi ne domin
sun ce, "Domin me ba a saukar
masa da wata taska ba, ko kuma
Mala'ika ya zo tare de shi?" (1) Kai
mai gargadi ne kawai. Kuma Allah
ne Wakili a kan kome.
13. K6 suna cewa "Ya Rirkira (2)
shi ne." Ka ce, "Sai ku zo da surori
goma misalinsa kirkirarru, kuma
i]^> J^o *1±jo 4^3*\at±J)
9 - ^> »^ T**^ *^> •-'•■-• ^* * **- <
(1) Saboda zaman mutane ba su girmama mutum sai idan yana da wata dukiya ko
kuma akwai wani karfi bayyananne tare da shi, to, kai kuma ga zahiri, ba ka da dukiya ko
wani karfin da za ka iya tllasta su da shi a kan wani abu. Saboda haka kana tsoron iyar da
duka abin da aka umurce ka, domin kada a karyata ka. To, kada ka ji tsoron iyarwa, Allah
ne Wakili a kan kome.
(2) Ko kuwa ba za ka iyar da abin da aka aike ka ba domin tsoron su ce, "Kai ne ka
kirkira Alkur'ani, sa'an nan ka jingina shi ga Allah." To, sai ka ce, "Ni mutum ne
kamarku, idan n!na kirkira Alkur'ani, to, ba zai gagare ku ku kirkira irinsa ba, sai ku zo da
surori goma irinsa."
321
11 - Suratu Hud
&*$&-*
ku kirayi wanda kuke iyawa, baicin
Allah, idan kun kasance masu gas-
kiya."
14. To, idan ba su amsa muku
ba, to, ku sani cewa an saukar da shi
kawai ne da sanin Allah, kuma cewa
babu abin bauta wa face Shi. To,
shin, ku masu sallamawa ne?
15. Wanda ya kasance ya yi nu-
fin rayuwar duniya da kawarta,
Muna cika musu ayyukansu zuwa
gare su a cikinta, kuma a cikinta ba
za a rage su ba.
16. Wadannan ne wadanda ba su
da kome a cikin Lahira face wuta,
kuma abin da suka sana'anta a
cikinta (duniya) ya 6aci, kuma abin
da suka kasance suna aikatawa 6a-
tacce ne.
17. Shin, wanda ya kasance a
kan hujja bayyananna daga
Ubangijinsa, kuma wata shaida
tana biyar sa daga gare Shi, kuma a
gabaninsa akwai littafln Musa abin
koyi da rahama? Wadannan suna
yin Tmani da shi, kuma wanda ya
kafirta da shi daga kungiyoyi, to,
wuta ce makomarsa. Saboda haka
kada ka kasance a cikin shakka
daga gare shi. Lalle shi ne gaskiya
daga Ubangijinka, amma Jcuma
mafi yawan mutane ba su yin Tmani.
18. Kuma wane ne mafi zalunci
daga wanda ya kirkira karya ga
Allah? Wadannan ana gitta su ga
Ubangijinsu, kuma masu shaida su
ce, "Wadannan ne suka yi karya ga
Ubangijinsu. To, la'anar Allah ta
tabbata a kan azzalumai."
%?"**■•-'*<•'{■' *>*< a
5-T <>*.>•
322
1 1 - Suratu Hud
£$£&-»
19. Wacfanda suke kangewa
daga hanyar Allah kuma suna ne-
man ta karkace, kuma su ga Lahira
suna kafirta.
20. Wadannan ne ba su kasance
mabuwaya ba a cikin kasa, kuma
wadansu masoya ba su kasance ba a
gare su, baicin Allah. Ana ninka
musu azaba, ba su kasance suna iya
ji ba, kuma ba su kasance suna gani
ba.
21. Wadannan ne wadanda suka
yi hasarar rayukansu, kuma abin da
suka kasance suna kirkirawa ya
6ace musu.
22. Babu makawa cewa, hakika,
su a Lahira, su ne mafi hasara.
23. Lalle ne wadanda suka yi
Tmani kuma suka aikata ayyukan
kwarai, kuma suka yi tawalu'i zuwa
ga Ubangijinsu, wadannan ne abo-
kan Aljanna, suna madawwama a
cikinta.
24. Misalin Bangaren biyu ka-
mar makaho ne da kurma, da mai
gani da mai ji. Shin, suna daidaita
ga misali? Ashe, ba ku yin tunani?
25. Kuma, hakika, Mun aika
Nuhu zuwa ga mutanensa, (ya ce) :
"Lalle ne ni, a gare ku mai gargacfi
bayyananne ne.
26. "Kadakubautawakowaface
Allah. Lalle nT, ina jin tsoron azabar
yini mai radacfi a kanku."
27. Sai mashawarta wadanda
suka kafirta, daga mutanensa, suka
ce, "Ba mu ganin ka face mutum
kake kamarmu, kuma ba mu ganin
t>"
3 Ojy^^^V^==>Uj «-Lll J^ o^uK^jtyDU
>/»<['»
S* & ' ,1 XI '
" s y " »- X/^
^^pi~l^>.jU^£sy>!l
323
1 1 - Suratu Hud
&%&-\s
wani ya bi ka face wadanda suke su
Raskantattunmu ne masu ra'ayin
kauye. Kuma ba mu ganin wata
falala a gare ka a kanmu. A 'a, muna
zaton ku makaryata ne."
28. Ya ce, "Ya mutanena! Shin,
kun gani idan na kasance a kan
wata hujjja bayyananna daga
Ubangijina, kuma Ya ba ni wata
Rahama daga wurinSa, sa'an nan
aka rufe ta (ita Rahamar) daga gare
ku, shin, za mu tTlasta muku ita,
alhali kuwa ku masu ki gare ta ne?
29. "Kuma ya mutanena IBazan
tambaye ku wata dukiya ba a kan-
sa, ijarata ba ta zama ba, face daga
Allah, kuma ban zama mai korar
wadanda suka yi Tmani ba. HakTka
su, masu hacfuwa da Ubangijinsu
ne, kuma amma ni, ina ganin ku
mutane ne jahilai.
30. "Kuma ya mutanena! Wane
ne yake taimakona daga Allah idan
na kore su? Ashe, ba ku tunani?
31. "Kuma ba nice muku a wuri-
na taskokin Allah suke, kuma ba
ina sanin gaibi ba ne. Kuma ba ina
cewa ni Mala'ika ba ne. Kuma ba ni
cewa ga wadanda idanunku suke
wulakantawa, Allah ba zai ba su
alheri ba. Allah ne Mafi sani ga abin
da yake cikin zukatansu. Lalle ne ni,
idan (na yi haka) da ina daga cikin
azzalumai.
32. Suka ce, "Ya Nuhu, lalle ne
ka yi jayayya da mu, sa'an nan ka
yawaita yi mana jidali, to, ka zo
mana da abin da kake yi mana
wa'adi idan ka kasance daga masu
gaskiya."
ll$^^^5^^^5f^
Cft
' »^>-r
324
11 - Suratu Hud
33. Ya ce, "Allah kawai ne Yake
zo muku da shi idan Ya so. Kuma
ba ku zama mabuwaya ba.
34. "Kuma nasThata ba za ta am-
fane ku ba, idan na yi nufin in yi
muku naslha, idan Allah Ya kasan-
ce Yana nufin Ya halaka ku. Shi ne
Ubangijinku, kuma zuwa gare Shi
ake mayar da ku."
35. Ko suna cewa: (Nuhu) ya
kirkira shi. Ka ce, "Idan iiT (Nuhu)
na kirkira shi, to, laifina a kaina
yake, kuma nlmai barranta ne daga
abin da kuke yi na laifi."
36. Kuma aka yi wahayi zuwa ga
Nuhu cewa: Lalle ne babu mai yin
Tmani daga mutanenka face wanda
ya riga ya yi Tmanin, saboda haka
kada ka yi bakin ciki da abin da
suka kasance suna aikatawa.
37. Kuma ka sassaka jirgi da
kyau bisa ganinMu da wahayinMu,
kuma kada ka yi Mini magana a
cikin sha'anin wacfanda suka kafir-
ta, lalle ne su, wacfanda ake nutsar-
wa ne.
38. Kuma yana sassaka jirgin
cikin natsuwa, kuma a koyaushe
wadansu shugabanni daga muta-
nensa suka shucfe a gabansa, sai su
yi izgili gare shi. Ya ce^"Idan kun yi
izgili gare mu, to, hakTka mu ma za
mu yi izgili gare ku, kamar yadda
kuke yin izgili.
39. "Sa'an nan da sannu za ku
san wanda azaba za ta zo masa, ta
wulakanta shi (a duniya), kuma
wata azaba zaunanna ta sauka a
kansa (a Lahira)."
^\< > &\* *»~ '*C\'
Z$s±j*,j*CJ* b fe \La \jj>i**A O \p 64^1^.
lJ^>U*
OjJ*~*
icr
325
1 1 - Suratu Hud
S&&&-H
40. Har a lokacin da umurnin-
Mu ya je, kuma tanda ta 6ul6ula.
Muka ce, "Ka cfauka, a cikinta,
daga kome, ma'aura biyu, da kuma
iyalanka, face wanda magana ta
gabata a kansa, (1) da wanda ya yi
imani." Amma kuma babu wacfan-
da suka yi Imani tare da shi face
kadan.
41. Kuma ya ce, "Ku hau a ci-
kinta, da sunan Allah magudanarta
da matabbatarta. Lalle ne Ubangi-
jlna, haklka, Mai gafara ne, Mai jin
feu."
42. Kuma ita tana gudana da su
a cikin taguwar ruwa kamar du-
watsu, sai Nuhu ya kirayi cfansa
alhali^kuwa ya kasance can wuri
mai nTsa. "Ya karamin cfana ! Zo ka
hau tare da mu, kuma kada ka
kasance tare da kafirai!"
43. Ya ce, "Zan tattara zuwa ga
wani dutse ya tsare ni daga ruwan."
(Nuhu) ya ce, "Babu mai tsare wa a
yau daga umurnin Allah face wan-
da Ya yi wa rahama." Sai taguwar
ruwa ta shamakace a tsakaninsu,
sai ya kasance daga wadanda aka
nutsar.
44. Kuma aka ce, "Ya kasa! Ki
hacfiye ruwanki, kuma ya sama ! Ki
kame." Kuma aka fakar da ruwan,
kuma aka hukunta aFamarin,
kuma jirgin ya daidaita a kan Judiy-
\'.'<> > rf"V t- '" \^\2 ' YA
xE_
(1) jyalan Nuhu sun yi imani banda dansa Yamu, da matarsa guda kafira. Wacfanda
suka yi imani daga sauran mutanensa tamanin ne maza da mata. Amma kuma an ce
mutane saba'in da biyu ne, kuma an ce goma ne. Allah ne Mafi sani.
326
1 1 - Suratu Hud
$*$&-«
yi, (1) kuma aka ce, "NTsa ya tabbata
ga mutane azzalumai."
45. Kuma Nuhu ya kira Ubangi-
jinsa, sa'an nan ya ce, "Ya Ubangi-
jina! Lalle ne rfana na daga iyalina!
Kuma haklka wa'adinKa gaskiya
ne, kuma Kai ne Mafi hukuncin
masu yin hukunci."
46. Ya ce, "Ya Nuhu ! Lalle ne shi
ba ya a cikin iyalanka, lalle ne shi,
aiki ne wanda ba na kwarai ba,
saboda haka kada ka tambaye Ni
abin^da ba ka da ilmi a kansa.
Haklka, NT Ina yi maka gargacfi
kada ka kasance daga jahilai."
47. Ya ce, "Ya Ubangijina! Lalle
ne ni, ina neman tsari gare Ka da in
tambaye Ka abin da ba ni da wani
ilmi a kansa. Idan ba Ka gafarta
mini ba, kuma Ka yi mini rahama,
zan kasance daga masu hasara."
48. Aka ce, "Ya Nuhu ! Ka sauka
da aminci daga gare Mu da albarka
a kanka, kuma rahama ta tabbata a
kan wadansu al'umm6mi daga wa-
cfanda suke tare da kai. Da wadansu
arummomi da za Mu jiyar da su
dacfi, sa'an nan kuma azaba mai
racfadi ta shafe su daga gare Mu."
49. Waccan kissa tana daga la-
baran gaibi, Muna yin wahayinsu
zuwa gare ka (Muhammadu). Ba ka
kasance kana sanin su ba, haka
kuma mutanenka ba su sani ba
daga gabanin wannan. Sai ka yi
hakuri. Lalle ne akiba tana ga masu
takawa.
~ ->»r v' >*. /u't • 'A**\ > > ' 1i-
t^a ' \ '\X'
0^fe&A^f
\ Jib S-fot &jX>&n l^U)
(1) Judiyyu sunan wani dutse ne a cikin Jazira. Jirgin Nuhu ya zauna a kansa, har
mutanen farko na wannan al'umma sun gan shi. Sa'an nan ya halaka.
327
1 1 - Suratu Hud
ft$J3£-M
50. Kuma zuwa ga Adawa,
(Mun aika) cfan'uwansu Hudu. Ya
ce, "Ya ku mutanena ! Ku bauta wa
Allah. Ba ku da wani abin bautawa
face Shi. Ba ku kasance ba face
kuna masu kirkirawa.
51. ' ' Ya ku mutanena ! Ba ni tam-
bayar ku wata ijara a kansa, ijarata
ba ta zama ba, face ga Wanda Ya
kaga halittata. Shin fa, ba ku
hankalta?"
52. "Kuma, ya mutanena! Ku
nemi Ubangijinku gafara, sa'an nan
kuma ku tuba zuwa gare Shi, zai
saki sama a kanku, tana mai yawan
zubar da ruwa, kuma Ya kara muku
wani karfi ga Rarfinku. Kuma kada
ku juya kuna masu laifi."
53. Suka ce, " Ya Hudu ! Ba ka zo
mana da wata hujja bayyananna ba,
kuma ba mu zama masu barin
abubuwan bautawarmu ba domin
maganarka, kuma ba mu zama
masu yin Tmani da kai ba.
54. "Ba mu cewa, sai dai kurum
sashen abubuwan bautawarmu ya
same ka da cutar hauka." Ya ce,
"Lalle ne ni, ina shaida wa Allah,
kuma ku yi shaidar cewa, "lalle ne
nT mai barranta ne daga abin da
kuke yin shirki da shi,
55. "Baicin Allah : Sai ku yi mini
kaidi gaba cfaya, sa'an nan kuma
kada ku yi mini jinkiri.
56. "Haklka, ni nadogaraga Al-
lah, Ubangijma kuma Ubangijinku.
Babu wata dabba face Shi ne Mai
v 9> Ayr**- *>ijr<'\ > . rcf ^ "
3 ojjjkS^ij^ tLir- <3j jJS* *j * ot
E
328
1 1 - Suratu Hud
6&S&-M
ri£o gajcwarkwacfarta. (1) Ha£i£a,
UbangijTna Yana (umurni) a tafarki
madaidaici.
57. "To ! Idan kun juya, ha£i£a,
na iyar muku abin da aka aiko nida
shi zuwa gare ku. Kuma UbangijTna
Yana musanya wadansu mutane,
wacfansunku su maye muku. Kuma
ba ku cutar Sa da kome. Lalle
Ubangijina a kan dukan kome,
Matsari ne."
58. Kuma a lokacin da umur-
ninmu ya je, Muka kubutar da
Hudu da wacfanda suka yi Tmani
tare da shi, saboda wata rahama
daga gare Mu. Kuma Muka ku6u-
tar da su daga azaba mai kauri.
59. Haka Adawa suka kasance,
sun yi musun ayoyin Ubangijinsu,
kuma sun saba wa ManzanninSa,
kuma sun bi umurnin dukan mai
girman kai, makangari.
60. Kuma an biyar musu da
la'ana a cikin wannan duniya da
Ranar Kiyama. To ! Lalle ne Adawa
sun kafirta da Ubangijinsu. To,
Nisa ya tabbata ga Adawa, muta-
nen Hudu!
61. Kuma zuwa ga Samudawa
(an aika) dan'uwansu Salihu. Ya ce,
"Ya mutanena ! Ku bauta wa Allah.
Ba ku da wani abin bautawa face
Shi. Shine Ya £aga halittarku daga
£asa, kuma Ya sanya ku masu yin
kyarkyara a cikinta. Sai ku neme
Shi gafara, sa'an nan kuma ku tuba
zuwa gare Shi. Lalle Ubangijina
Makusanci ne Mai kar6awa."
~"t*^
4^ ^l-^^ Vj**^
(1) Gashin goshin dabba.
329
11 - Suratu Hud
fi#i$&-H
62. Suka ce, "Ya Salihu ! Haklka,
ka kasance a cikinmu, wanda ake
fatan wani alheri da shi a gabanin
wannan. Shin kana hana mu bauta
wa abin da ubanninmu suke bauta
wa? Kuma hakika mu, muna cikin
shakka daga abin da kake kiran mu
gare shi, mai sanya kokanto."
63. Ya ce, "Ya mutanena! Kun
gani? Idan na kasance a kan hujja
bayyananna daga Ubangijina,
kuma Ya ba ni rahama daga gare
Shi, to, wane ne zai taimake ni daga
Allah idan na sa6a Masa? Sa'an
nan ba za ku kare ni da kome ba
face hasara.
64. "Kuma ya mutanena! Wan-
nan rakumar Allah ce, tana aya a
gare ku. Sai ku bar ta ta ci a cikin
kasar Allah, kuma kada ku shafe ta
da wata cuta, kar azaba makus-
anciya ta kama ku."
65. Sai suka soke ta. Sai ya ce,
"Ku ji dacfi a cikin gidajenku kwana
uku. Wannan wa'adi ne ba abin
karyatawa ba."
66. To, a lokacin da umurninMu
ya je, Muka kuButar da Salihu da
wacfanda suka yi Tmani tare da shi,
saboda wata rahama daga gare Mu,
kuma daga wulakancin ranar nan.
Lalle ne, Ubangijinka ShT ne Mai
karfi, Mabuwayi.
67. Sai tsawa ta kama wacfanda
suka yi zalunci, sai suka wayi gari
suna guggurfane a cikin gidajensu.
68. Kamar dai ba su zauna a
cikinta ba. To ! Lalle ne Samudawa
sun kafirce wa Ubangijinsu. To,
NTsa ya tabbata ga Samudawa.
j^t> /Tf-J ^tf^ /V'* .
330
1 1 - Suratu Hud
e$i$&-H
69. Kuma hakika, manzan-
ninMu sun je wa Ibrahim da bus-
hara, suka ce, "Aminci". Ya ce,
"Aminci (ya tabbata a gare ku)."
Sa'an nan bai yi jinkiri ba ya je da
maraki kawatacce.
70. Sa'an nan a lokacin da ya ga
hannayensu ba su saduwa zuwa
gare shi (marakin), sai ya yi kya-
marsu, kuma ya ji tsoronsu. Suka
ce, "Kada ka ji tsoro, lalle ne mu, an
aiko mu ne zuwa ga mutanen Ludu."
71. Kuma matarsa tana tsaye (1) .
Ta yi dariya. Sai Muka yi mata
bushara (da haihuwar) Is'haka,
kuma a bayan Is'haka, Yakubu.
72. Sai ta ce, "Ya kaitona! Shin,
zan haihu ne alhali kuwa ina tsohu-
wa, kuma ga mijina tsoho ne? Lalle
wannan, hakika, abu ne mai ban
mamaki.''
73. Suka ce, "Shin kina mamaki
ne daga al'amarin Allah? Rahamar
Allah da albarkarSa su tabbata a
kanku, ya mutanen babban gida!
Lalle ne Shi abin godewa ne, Mai
girma."
74. To, a lokacin da firgita ta tafi
daga Ibrahim, kuma bushara ta je
masa, yana mai jayayya a gare Mu
saboda mutanen Ludu!
75. Lalle Ibrahim, hakika mai
hakuri ne, mai yawan kuka, mai
tawakkali.
:^T?V-f-f
bfiPi
(1) Matar Ibrahim Sariyah tana tsaye ga yi musu hidima, sai ta yi dariyar mamaki,
domin ba£in sun Ri cin abinci. Wadansu na fassarawa — ta yi haila. Wannan bai dace ba.
331
11 - Suratu Hud
fi#!S&-M
76. Ya Ibrahim! Ka bijira daga
wannan. Lalle shi, hakika, umurnin
Ubangijinka ne ya zo, kuma lalle ne
su, abin da yake mai je musu azaba
ce wadda ba a iya hanawa.
77. Kuma a lokacin da man-
zanninMu suka je wa Ludu, aka
6ata masa rai game da su, ya kun-
tata rai saboda su. Ya ce, ^Wannan
yini ne mai tsananin maslfa."
78. Kuma mutanensa suka je
masa suna gaggawa zuwa gare shi,
kuma a gabani, sun kasance suna
aikatawar munanan ayyuka. Ya ce,
"Ya mutanena! Wadannan 'ya'-
yana, (1) su ne mafiya tsarki a gare
ku. Sai ku bi Allah da takawa, kuma
kada ku wulakanta ni a cikin baki-
na. Shin, babu wani namiji shiryay-
ye daga gare ku?"
79. Suka ce, "Lalle, haklka ka
sani, ba mu da wani hakki a cikin
'ya'yanka, kuma lalle kai hakika,
kana sane da abin da muke nufi."
80. Ya ce, "Da dai ina da wani
karfi game da ku, ko kuwa ina da
goyon baya daga wani rukuni (2)
mai karfi?"
81. (Manzannin) Suka ce, "Ya
Ludu ! Lalle mu, manzannin Ubangi-
jinka ne. Ba za su iya saduwa zuwa
gare ka ba. Sai ka yi tafiyarka a
Wl < r ^ r ^ Mi \ XJb ouycj j
feJJu
§) j*jC%A&\j
(1) 'Ya'yansa-yana nufin matan aurensu, domin kowane Annabi uban al'ummarsa ne.
Ba ya kamata a ce wai yana kiran mazan gari zuwa ga 'ya'yansa uku, domin babu wata
shari'a ta Allah, ga saninmu, wadda ta halatta hacfuwar maza biyu ko fiye da biyu a kan
auren mace guda.
(2) Ya facfi haka domin ba shi da dangi a cikinsu. Daga gare shi ba a koma aiko
wani Annabi ba sai a cikin wadatar danginsa.
332
11 - Suratu Hud
wani yankin dare da iyalinka, kuma
kada wani daga gare ku ya waiwaya
face matarka. Lalle ne abin da ya
same su mai samunta ne. Lalle
wa'adinsu lokacin safiya ne. Shin
lokacin safiya ba kusa ba ne?"
82. Sa'an nan a lokacin da umur-
ninMu ya je, Muka sanya na sa-
manta ya zama na kasanta, kuma
Muka yi ruwan duwatsu a kanta
(kasar Ludu) daga ta6o curarre.
83. Alamtacce a wurin Uban-
gijinka. Kuma ita (kasar Ludu) ba ta
zama mai nlsa ba daga azzalumai
(Kuraishawa).
84. Kuma zuwa ga Madyana
(Mun aika) dan'uwansu (1) Shu'-
aibu. Ya ce, "Ya Mutanena! Ku
bauta wa Allah. Ba ku da wani abin
bautawa face Shi, kuma kada ku
rage mudu da sikeli. Lalle m, ina
ganin ku da wadata. (2) Kuma lalle
ina jT muku tsoron azabar yini mai
kewayewa.
85. "Ya mutanena! Ku cika
mudu da sikeli da adalci, kuma
kada ku nakasta wa mutane
kayansu, kuma kada ku yi 6arna a
cikin kasa kuna masu fasadi.
86. "Falalar Allah mai wanzuwa
ita ce mafi alheri a gare ku idan kun
kasance muminai, kuma ni ba
mai tsaro ne a kanku ba."
'<: . .»•. y ■
^^ s~~> >kJ- ^ "
J^^==^\^\^y^ IS 3 C^^ '
(1) Larabawa ne, suna zaune a tsakanin Hijaz da Sham.
(2) Ina ganin ku a cikin wadata: ba ku da bukatar rage wa mutane kayansu. Saboda
haka ku yi adalci ga mutane wajen ciniki ya fi muku alheri daga dukiyar haram mai karewa
kome yawanta.
333
1 1 - Suratu Hud
$$&-U
87. Suka ce, "Ya Shu'aibu! Shin
sallarka ce take umurtar ka ga mu
bar abin da ubanninmu suke bau-
tawa, ko kuwa mu bar aikata abin
da muke so a cikin dukiyoyinmu?
Lalle, hafaka kai ne mai hakuri,
shiryayye!"
88. Ya ce, "Ya mutanena! Kun
gani idan na kasance a kan hujja
bayyananniya daga Ubangijina,
kuma Ya arzuta m da arziki mai
kyawo daga gare Shi? Kuma ba ni
nufin in saBa muku zuwa ga abin da
nake hana ku daga gare shi. Ba ni
nufin kome face gyara, gwarg-
wadon da na sami dama. Kuma
muwafakata ba ta zama ba face
daga Allah. A gare Shi na dogara,
kuma zuwa gare Shi na wakkala.
89. "Kuma ya mutanena! Kada
saBa mini ya dauke ku ga misalin
abin da ya sami mutanen Nuhu ko
kuwa mutanen Hudu ko kuwa mu-
tanen Salihu ya same ku. Mutanen
Lucfu ba su zama a wuri mai nTsa ba
daga gare ku.
90. "Kuma ku nemi Ubangi-
jinku gafara, sa'an nan kuma ku
tuba zuwa gare Shi. Lalle Ubangi-
jina Mai jin kai ne, Mai nuna soy-
ayya."
91. Suka ce, "Ya Shu'aibu! Ba
mu fahimta da yawa daga abin da
kake fadi, kuma muna ganin ka mai
rauni a cikinmu. Kuma ba domin
jama'arka ba da mun jefe ka, sabo-
da ba ka zama mai daraja a gunmu
ba."
^q£=£>^o
^-i-J <^W? ±JJ (^ £=^*&> ll&J^l)
.-^»>'»
&WJ*-*?
334
11 - Suratu Hud
fi#i&-n
92. Ya ce, "Ya mutanena! Ashe,
jama'ata ce mafi daraja a gare ku
daga Allah, kuma kun rike Shi a
bayanku abin jefarwa? Lalle ne
Ubangijma Mai kewayewa ne ga
abin da kuke aikatawa.
93. "Kuma ya mutanena ! Ku yi
aiki a kan halinku. Lalle nTmai aiki
ne. Da sannu za ku san wane ne
azaba za ta zo masa, ta wulakanta
shi, kuma wane ne makaryaci.
Kuma ku yi jiran dako, lalle ni mai
dako ne tare da ku."
94. Kuma a lokacin da umur-
ninMu ya je, Muka kubutar da
Shu'aibu da wacfanda suka yilmani
tare da shi, saboda wata rahama
daga gare Mu. Kuma tsawa ta
kama wacfanda suka yi zalunci. Sai
suka wayi gari guggurfane a cikin
gidajensu.
95. Kamar ba su zauna ba a
cikinsu. To, halaka ta tabbata ga
Madyana kamar yadda Samudawa
suka halaka.
96. Kuma hakTka Mun aiki
Musa da ayoyinMu, da daffli
bayyananne.
97. Zuwa ga Fir'auna da maja-
lisarsa. Sai suka bi umurnin Fir'au-
na, amma aFamarin Fir'auna bai
zama shiryayye ba.
98. Yana shugabantar muta-
nensa a Ranar Kiyama, har ya tuz-
gar da su a wuta. Kuma tir da irin
tuzgawarsu.
99. Kuma aka biyar musu da
la'ana a cikin wannan duniya da
*x ' "\ 9 K 'f' Y i V 9 \ 9 'f"
??-'(*"
4'~'\ X S »>
OJuo
'zmS£>>&
i^%> ><
©■^
6p ^J.^^t^j
^y-jL* 4*^ T-£> 4iJu^£-XUb<JJ !>*->-* L>
335
1 1 - Suratu Hud
$&%&-W
Ranar Kiyama. Tir da kyautar (1)
da ake yi musu.
100. Wancan yana daga labaran
alkaryoyi. Muna ba ka labarinsu,
daga gare su akwai wanda ke tsaye
da kuma girbabbe. (2)
101. Kuma ba Mu zalunce su ba,
amma sun zalunci kansu, sa'an nan
abubuwan bautawarsu wadanda
suke kiran su, baicin Allah, ba su
wadatar musu kome ba a lokacin da
umurnin Ubangijinka ya je, kuma
(gumakan) ba su kara musu wani
abu ba face hasara.
102. Kuma kamar wancan ne
kamun Ubangijinka, idan Ya kama
alkaryoyi alhali kuwa suna masu
zalunci. Lalle kamunSa mai racfacfi
ne, mai tsanani.
103. Lalle ne a cikin wancan
akwai aya ga wanda ya ji tsoron
azabar Lahira. Wancan yini ne
wanda ake tara mutane a cikinsa,
kuma wancan yini ne abin halarta.
104. Ba Mu jinkirta shi ba face
domin ajali kidayayye.
105. Ranar da za ta zo wani rai
ba ya iya magana face da izninSa.
Sa'an nan daga cikinsu akwai sha-
kiyyi da mai arziki.
106. To, amma wadanda suka yi
shakawa, to, suna a cikin wuta.
Suna masu kara da sheka a cikinta.
*5.
i^jJ^^O^^lt^ii^ifriciO^
\»
*j4r~ A
(1) Kyautar la'ana ita ce wadda ake la'antar su da ita a duniya da Lahira.
(2) Daga nan zuwa karshen sura ta'aliki ne domin farkarwa. Mai tsayi — watau tana
nan tsaye, alamominta ba su 6ace ba, kuma akwai wadanda suka halaka kamar karan da
aka girbe.
336
1 1 - Suratu Hud
&&i&-»
107. Suna madawwama a ci-
kinta, matukar sammai da kasa sun
dawwama, face abin da Ubangi-
jinka Ya so. Lalle Ubangijinka Mai
aikatawa ne ga abin da Yake nufi.
108. Amma wacfanda suka yi ar-
ziki, to, suna a cikin Aljanna suna
madawwama, a cikinta, matukar
sammai da kasa sun dawwama, face
abin da Ubangijinka Ya so. Kyauta
wadda ba ta yankewa.
109. Saboda haka kada ka ka-
sance a cikin shakka daga abin da
wacfannan suke bautawa. Ba su
wata ibada face kamar yadda uban-
ninsu ke aikatawa a gabani. Kuma
hakika Mu, Masu cika musu rabon-
su ne, ba tare da nakasawa ba.
110. Kuma haklka, Mun bai wa
Musa littafi, sai aka sa6a (1) wa juna
a cikinsa. Kuma ba domin wata
kalma wadda ta gabata daga
Ubangijinka ba, hakika, da an yi
hukunci a tsakaninsu. Kuma hakl-
ka, suna a cikin wata shakka, game
da shi, mai sanya kokanto.
111. Kuma lalle, haklka,
Ubangijinka Mai cika wa kowa
(sakamakon) ayyukansa ne. Lalle
Shi, Mai kididdigewa ne ga abin da
suke aikatawa.
112. Sai ka daidaitu (2) kamar
yadda aka umurce ka, kai da wa-
Jejti'\jCSj£\ ^ j£l^^^£-
<*»
&j&<£)ffi
< >>*'\' xMS »»'\C*
fv\
'^<Jfy*^Ji c 'pr*r? >
y > * f y '
^jfc~\b <w. .i~ 5~~ =: ^ * <s*y ^^* ^j
***** *r** fV . * »>«' 1 '
aE>p^i-s>J ui y& 61 j
^jJLtf"" ^ **' 1
\jda> j j kZXma l- >«<>•-> *--L/*.' *^ r v ^ '**^
(1) Yahudawa sun saba wa juna a cikin littattafan da aka bai wa Musa. To, ku
Musulmi kada ku bi hanyarsu, har ku saba wa Allah, har abin da ya same su ya same ku.
(2) Wannan aya tana hana dukan bidi'a a cikin addini. Tun da ba a yarda Annabi ya
£ara ra'ayinsa ba sai dai ya bi umurnin Allah kamar yadda Ya yi umurnin, kuma haka ne
Ya umurci wanda ya bi Annabi. Saboda haka mai saba wa umurnin Allah da kari ko ragi,
ba ya cikin mabiyan Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.
337
1 1 - Suratu Hud
&&J&-U
cfanda suka tuba tare da kai, kuna
ba masu £etara haddi ba. Lalle ShT,
Mai gani ne ga abin da kuke aika-
tawa.
1 13. Kada ku karkata ( * } zuwa ga
wacfanda suka yi zalunci har wuta
ta shafe ku. Kuma ba ku da wa-
dansu maji&inta baicin Allah, sa'an
nan kuma bazaa taimake ku ba.
114. Kuma ka tsai da sal la a
gefe guda biyu na yini da wani yanki
daga dare. Lalle ne ayyukan kwarai
suna kore munanan ayyuka. Wan-
can (2) ne tunatarwa ga masu tuna-
wa.
115. Kuma ka yi ha£uri. Allah
ba Ya tdzartar da ladar masu
kyautatawa. (3)
116. To, don me masu hankali
ba su kasance daga mutanen £ar-
nonin da suke a gabaninku ba, suna
hani daga 6arna a cikin Rasa? Face
kacfan daga wanda Muka ku6utar
daga gare su (sun yi hanin). Kuma
wacfanda suka yi zalunci suka bi
abin da aka ni'imtar da su a cikinsa,
suka kasance masu laifl.
117. Kuma Ubangijinka bai ka-
sance Yana halakar da alicaryu sa-
1^%* ' ^ -\' -\S >'A
*0fc''"<\ *v\: '.AVu'^rc-^'
rOj3\3;i^Ci1-
^m^\^\t\^>
p»j£$\dx&lX> '&-<£
(1) Ba ya halatta ga Musulmi ya karkata zuwa ga kafirai kamar yadda ba ya halatta
ya karkata a cikin addininsa. Wannan shT ne babban makami a kan makTya.
(2) Tsayar da salloli farillai tare da Llman a cikin masallatai shT ne zikiri ga mai son
zikirin gaskiya. Ayyukan kwarai suna shafe miyagu.
(3) Hakuri a kan ibada wajibi ne, haka kuma kyautatawa, watau shT ne yin kowane
aiki na ibada tsantsa kamar salla ko na ma'amala kamar ciniki da aure, domm Allah
kawai. An yi wa wannan fanni na biyu suna da "Tasawwuf", bidi'a ne domin bai taho daga
Sunna ba. Asalinsa "theosophy" daga lugar Ajam, ma'anarsa neman hikima ta Allah a
halin ke6ance kai a cikin kacfaita da wasu aikace-aikace na ibada, kamar girka ga 'yanbori.
338
1 1 - Suratu Hud
(&$&-«
boda wani zalunci ba, alhali muta-
nensu suna masu gyarawa. (1)
118. Kuma da Ubangijinka Ya
so, da Ya sanya mutane al'umma
guda. Kuma ba za su gushe ba suna
masu sa6a wa juna.
119. Sai wanda Ubangijinka Ya
yi wa rahama, kuma domin wan-
nan (2) ne Ya halicce su. Kuma kal-
mar Ubangijinka "Lalle ne za Ni
cika Jahannama da aljannu da mu-
tane gaba daya" ta cika.
120. Kuma dubi dai Muna ba da
labari a gare ka daga labarun Man-
zanni, abin da Muke tabbatar da
zuciyarka da shi. Kuma gaskiya ta
zo maka a cikin wannan, da wa'azi
da tunatarwa ga masu Tmani.
121. Kuma ka ce wa watfanda ba
su yin unani, "Ku yi aiki a kan
halinku, lalle mu masu aiki ne.
122. "Kuma ku yi jiran dako,
lalle mu masu jiran dako (3) ne."
123. Kuma ga Allah gaibin sam-
mai da £asa yake. Kuma zuwa gare
Shi ake mayar da dukan aFamari.
Saboda haka ku bauta Masa kuma
ku dogara a kanSa. Kuma Ubangi-
jinka bai zama Mai gafala daga
abin da kuke aikatawa ba.
*JS <Cu*3>j j*4**>- &y-xj ^JfzJo^l
(1) Wannan aya da ta sama da ita suna nuna muhimmancin wa'azi a cikin kowane
hali na al'umma, domin tsarewar zamanta arumma.
(2) Allah ya halicci mutane da halaye dabam-dabam domin su saba wa juna.
(3) Ku yi jira ku gani wane ne zai ci nasara; mu da muka bi umurnin Allah, ko kuwa
ku da kuke bin zuciyoyinku. Akiba dai tana ga masu takawa. Allah ya tabbatar da mu a
kan binSa a kan takawa. Amin.
339
12 — Suratu Yusuf
££$£&-«■
Tana karantar da halayen rayuwar mutum a cikin duniya tare
da abokan zama a kowane matsayi.
-* J* ■* . *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
/. A. L. R. Wacfancan ayoyin
Littafi mai bayyanawa ne.
2. Lalle ne Mu, Mun saukar da
shi, yana abin karantawa na Larab-
ci; tsammaninku, kuna hankalta.
3. Mu, Muna bayar da labari a
gare ka, mafi kyawon labari ga abin
da Muka yi wahayin wannan Alku-
r'ani zuwa gare ka. Kuma lalle ne ka
kasance a gabaninsa, haklka, daga
gafalallu.
4. A lokacin da Yusufu ya ce
wa ubansa, "Ya baba! Lalle ne nl,
na ga taurari goma sha daya, da
rana da wata. Na gan su suna masu
sujada a gare ni."
5. Ya ce, "Ya karamin dana!
Kada ka facfi mafarkinka ga 'ya-
n'uwanka, har su kulla maka wani
kaidi. Lalle ne Shaidan ga mutum,
haklka, makiyi ne bayyananne. (1)
( 1 ) Tarbiyyar uba ga cfansa. Yaro icarami ana renon sa da jawabi mai laushi a fahimtar
matsayin yaron.
340
12 - Suratu Yusuf
&X&&A
£->V
6. "Kuma kamar wancan ne,
Ubangijinka Yake za6en ka, kuma
Ya sanar da kai daga fassarar laba-
rai, kuma ya cika ni'imominSa a
kanka, kuma a kan gidan Yakuba
kamar yadda ya cika su a kanuban-
ninka biyu, a gabani, Ibrahim da
Is'haka. Lalle Ubangijinka ne Ma-
sani, Mai hikima."
7. Lalle ne, haklka, ayoyi (1) sun
kasance ga Yusufu da 'yan'uwan-
sa (2) domin masu tambaya.
8. A lokacin da suka ce (3) , lalle
ne Yusufu da dan'uwansa ne ma-
fiya soyuwa ga ubanmu daga gare
mu, alhali kuwa mu jama'a guda ne.
Lalle ubanmu, hakika, yana cikin
6ata bayyananniya.
9. Ku kashe Yusufu, ko kuwa ku
jefa shi a wata kasa, fuskar ubanku
ta wofinta saboda ku, kuma ku
kasance a bayansa mutane salihai.
10. Wani mai magana daga ci-
kinsu ya ce, "Kada ku kashe Yusu-
fu. Ku jefa shi a cikin duhun rtjiya,
wasu matafiya su tsince shi, idan
kun kasance masu aikatawa ne."
Cp j£*^-j>Ac> <&j o[
(1 ) Ayoyi a nan, ana nufin halaye wadanda suka zama darussa na koyarwa ga mutane
domin tarbiyya ga yara da manya na kowane matsayi ga rayuwar dan Adam.
(2) Yusufu da dan'uwansa shakTki, Binyamlnu, da sauran goma. Babbansu ga
shekaru,^hi ne RaubTlu, kuma sai Lawaya. A cikin gidansa aka yi Annabawa, sai Yahuza
kuma shi ne shugabansu a ra'ayi, shT ne uban sarakunansu, saboda haka sunansa ya
rinjaya a kan kabilar, aka ce musu Yahudu.
(3) Hlrar yara a tsakaninsu. Suna tunanin soyayyar ubansu ga dayansu wanda ba ya
cikinsu yanzu. Suna tunanin yadda za su sami adalcin daidaitawar so daga ubansu baki
dayansu. T)an'uwansu wanda ubansu yake so, watau Yusufu, ya sami bakin jini daga gare
su domin ubansu yana sonsa. Saboda haka Shaidan yana sanya musu tunanin su yi
zunubin rabuwa da shi, sa'an nan su tuba ga Allah.
341
12 - Suratu Yusuf
%?*»&<*
-W
11. Suka ce, "Ya babanmu! (1)
Mene ne a gare ka ba ka amince
mana ba a kan Yusufu, alhali kuwa
lalle ne mu, haklka, masu nasTha
muke ne a gare shi?
12. "Ka bar shi tare da mu a
gobe, ya ji dacfi, kuma ya yi wasa.
Kuma lalle ne mu, a gare shi, masu
tsaro ne."
13. Ya ce, "Lalle ne ni, haklka,
yana Bata mini rai ku tafi da shi.
Kuma ina tsoron kerkeci ya cinye
shi, alhali ku kuwa kuna masu sha-
gala daga gare shi."
14. Suka ce, "Haklka, idan ker-
keci ya cinye shi, alhali kuwa muna
dangin juna, lalle ne mu, a sa'an
nan, hakika, mun zama masu ha-
sara."
15. To, a 16kacin (2) da suka tafi
da shi, kuma suka yi niyyar su sanya
shi a cikin duhun rijiya, Muka yi
wahayi zuwa gare shi, "Lalle ne,
kana ba su labari game da wannan
aFamari nasu, kuma su ba su sani
ba."
16. Kuma suka je wa ubansu da
dare suna kuka.
17. Suka ce, "Ya babanmu! (3)
Lalle ne, mun tafi muna tsere, kuma
*.< S.f.s .'.ts»>-
(1) Sun fara zartar da abin da suka shirya, watau dauke Yusufu daga gaban ubansa.
Sun fara da maganar da ubansu yake so game da su tattara da dan'uwansu karami. Suna
muhawara da ubansu suna neman yardarsa don ya bar su su tafi da Yusufu.
(2) Suka cire rigarsa, suka jefa shi da guga a cikin rijiya. Sa'an nan suka sanya wa
rigarsa jinin wata dabba da suka yanka, domin ya zama jilamar cewa kerkeci ya cinye
Yusufu. Ga rigarsa ta 6aci da jinin jikinsa. Watau jinin shi ne alamar ya mutu. Sai suka
manta cewa kafin kerkeci ya cinye yaro a cikin rigarsa, sai ya kekketa rTgar tukun.
(3) Muhawararsu tare da ubansu. Ya nuna bakin ciki, amma kuma ya mayar da
al'amari ga Allah.
342
12 — Suratu Yusuf
32$3£&-W
muka bar Yusufu a wurin kayan-
mu, sai kerkeci ya cinye shi, kuma
kai, ba mai amincewa da mu ba ne,
kuma ko da mun kasance masu
gaskiya!"
18. Kuma suka je, a jikin rigarsa
akwai wani jinin karya. Ya ce, "A'a,
zukatanku suka kawata muku wani
al'amari. Sai hakuri mai kyau!
Kuma Allah ne Wanda ake neman
taimako (a gunSa) a kan abin da
kuke sifantawa."
19. Kuma wani ayari (1) yaje, sai
suka aika mai neman musu ruwa,
sai ya zura gugansa, ya ce, "Ya
busharata! Wannan yaro ne."
Kuma suka kama shi yana abin
sayarwa. Kuma Allah ne Masani ga
abin da suke aikatawa.
20. Kuma suka sayar (2) da shi da
'yan kucfi kacfan, dirhamomi kida-
yayyu. Kuma sun kasance, a wurin-
sa, daga masu isuwa da abu kadan.
21. Kuma wanda ya saye shi
daga Masar (3) ya ce wa matarsa,
"Ki girmama mazauninsa, akwai
tsammanin ya amfane mu, ko kuwa
mu rike shi cfa." Kuma kamar wan-
can ne Muka tabbatar ga Yusufu, a
cikin kasa, kuma domin Mu sanar
da shi daga fassarar labaru, kuma
**' s *A'
JJ&- *)\j>*Jj>*J£> 4)!>\j
3 ^J^ty&^f^&J
(1) Ayari ya je kusa da rijiyar Yusufu, har suka kama shi ya zama bawa abin sayarwa
a hannunsu.
(2) Ayarin, sun tafi da shi, sun sayar da shi a kan kucfi kacfan, domin sun sani, shi ba
bawansu ba ne, tsinto shi suka yi. Saboda haka kome suka samu game da shi, rlba ce a gare
su. Kuma gudun kada iyayensa su gane shi, su rasa kome daga gare shi gaba cfaya.
(3) Yusufu a gidan sarauta, kuma a cikin halin girma da cfaukaka. Gidan Azizi
Masar, watau Firayim Minista, babban wazirin Masar.
343
12 - Suratu Yusuf
&2#£&-tt
Allah ne Marinjayi a kan al'amar-
inSa, kuma amma mafi yawan mu-
tane ba su sani ba.
22. Kuma a lokacin da ya isa
mafi karfinsa, Muka ba shi hukunci
da ilmi. Kuma kamar wancan ne
Muke saka wa masu kyautatawa.
23. Kuma wadda yake (1) acikin
cfakinta, ta neme shi ga kansa,
kuma ta kukkulle kofofi, kuma ta ce,
"Ya rage a gare ka!" Ya ce, c ^Ina
neman tsarin Allah! Lalle Shi ne
Ubangijina. Yajcyautata mazau-
nina. Lalle ne shi, masu zalunci ba
su cin nasara!"
24. Kuma lalle ne, ta himmantu
da shi. Kuma ya himmantu da ita in
ba domin ya ga dalTlin Ubangijinsa
ba. Kamar haka dai, domin Mu
karkatar da mummunan aiki da
alfasha daga gare shi. Lalle ne shi,
daga bayinMu salihai yake.
25. Kuma suka yi tsere (2) zuwa
ga kofa. Sai ta tsage rigarsa daga
baya, kuma suka iske mijinta a
wurin kofar. Ta ce, "Mene ne saka-
makon wanda ya yi nufin cuta game
\s <, " **
LJj ij^j j \y* > *S*a~& cj J&j ^ U \ LiJLuj^
(1) Yusufu ya shiga cikin fitinar uwar cfakinsa, ZalTha. Ya mai da al'amarinsa ga
Ubangijinsa wanda ya fltar da shi daga rijiya zuwa gidan sarautar Masar, kuma Ya ba shi
hukunci, watau Annabci da ilmi da Ya saukar masa na ibada da mu'amala. Ya sanar da shi
halal da haram kuma ya sanya masa tsaro daga zunubi.
(2) Idan namiji da mace sun hacfu, to, ba ya halatta ga namijin ya dogara ga Uminsa
na amanarsa, ya zauna tare da fitinar Shaicfan. Saboda haka Yusufu ya gudu, ta bl shi da
halin kasawar mutum ga halin so har bakin dofa. Suka hacfu da mijinta. Ta mayar da
maganar rawatsa (karya) a kan Yusufu. Shi kuma ya kare kansa da maganar gaskiya. Sai
shaida za a nema. Ta himmantu da dukarsa domin ya ki ya yi mata cfa'a ga abin da take so
daga gare shi alhali yana bawanta, shT kuma ya himmantu da dukarta domin ya tunkude
macuci. Alfashar ita ce zina, cutar kuwa ita ce duka, dalilin Ubangijinsa shi ne bin shari'ar
Allah.
344
12 — Suratu Yusuf
CCM&X*
-\r
da iyalinka? Face a cfaure shi, ko
kuwa a yi masa wata azaba mai
racfadi."
26. Ya ce, "Ita ce ta neme ni a
kaina." Kuma wani mai shaida
daga mutanenta ya bayar da shai-
da : (1) "Idan rigarsa ta kasance an
tsage ta daga gaba, to, ta yi gaskiya,
kuma shT ne daga makaryata.
27. "Kuma idan rigarsa ta kasan-
ce an tsage ta daga baya, to, ta yi
karya, kuma shT ne daga masu gas-
kiya."
_ 28. Sa'an nan a lokacin da ya ga
rigarsa an tsage ta daga baya, ya ce,
"Lalle ne shi, daga kaidinku ne,
mata ! Lalle ne kaidinku mai girma
ne!
29. " Yusufu ! Ka kau da kai daga
wannan. Kuma ki nemi gafara (2 >
domin laifinki. Lalle ne ke, kin
kasance daga masu kuskure."
30. Kuma wadansu mata (3) a
cikin Birnin suka ce, "Matar AzTz
tananeman hadiminta daga kansa !
Haklka, ya rufe zuciyarta da so.
Lalle ne mu, muna ganin ta a cikin
6ata bayyananna."
>^1
GpdA^tii'o^
(1) Bayar da shaida a kan al'ada, mai bayar da shaidar yana gabatar da ita da magana
a kan Yusufu, domin a ganinsa tuhuma a kanta, ta fi karfi, kuma zumuntarsa da ita ba ta
cfauke shi ba ga karkatar da magana domin ya taimake ta.
(2) Mai gida ya yi hukunci da yabon girman halin Yusufu da kuma neman ya kashe
maganar a nan.
(3) Tsegumin mata a cikin gari da yadda matar AzTz ta yi maganin tsegumin, ta
hanyar yi wa matan liyafa. Mace ba ta kunyar mata 'yan'uwanta ga irin wannan fitina idan
ta same ta, ita kacfai, balle mata ga su duka sun kamu a cikin tarkon da ya kama ta. Sai ta
gaya musu gaskiyar abin da ya auku a tsakaninta da Yusufu, a bayan ta rama zargin da
suka yi mata.
345
12 - Suratu Yusuf
WZi<*
&-\t
31. Sa'an nan a lokacin da ta ji
labari game da makircinsu, sai ta
aika kiran liyafa zuwa gare su,
kuma ta yi tattalin abincin da ake
dogara wajen cinsa, kuma ta bai wa
kowace cfaya daga cikinsu wuka,
kuma ta ce, "Ka fito a kansu." To, a
lokacin da suka gan shi, suka gir-
mama shi, kuma suka yanyanke
hannayensu, kuma sukace, "Tsarki
yana ga Allah ! Wannan ba mutum
ba ne! Wannan bai zama ba face
Mala'ika ne mai daraja!"
32. Ta ce, 'To wannan ne fa
wanda kuka zarge^ ni a cikinsa!
Kuma lalle ne, haklka, na neme shi
daga kansa, sai ya tsare gida, kuma
m ina rantsuwa, idan bai aikata
abin da nake umurnin sa ba, hakika,
ana cfaure shi. Hakika, yana kasan-
cewa daga kaskantattu."
33. Ya ce, "Ya Ubangijina ! Kur-
kuku ne mafi soyuwa a gare ni daga
abin da suke kira na zuwa gare shi.
Kuma idan ba Ka karkatar da kai-
dinsu daga gare ni ba, zan karkata
zuwa gare su, kuma in kasance daga
jahilai."
34. Sai Ubangijinsa Ya kar6a
masa, saboda haka Ya karkatar^ da
kaidinsu daga gare shi. Lalle Shi ne
Mai jT, Masani.
35. Sa'an nan kuma ya bayyana
a gare su a bayan sun ga alamomin,
fjX o j£c- \j ,jjj ^oJu»}! c&s^i. c-a^^
^ Jlo *c^ c^-vo^A^a) c-j L>JL** Is
/f^> rtf> <tf x> *?i
(1) A cikin maganar matar AzTz a tsakanin mata babu wata kunya, domin ta nuna
kasawarsu. Kuma akwai tsoratarwa ga Yusufu idan bai yi mata cfa'a ba ga bukatarta gare
shi.
346
12 — Suratu Yusuf
■C?*Xi<*
js.-^
lalle ne dai su cfaure shi har zuwa
wani lokaci.
36. Kuma wacfansu samari biyu
suka shiga kurkuku tare da shi. (1)
T)ayansu ya ce, "Lalle ne nl, na yi
mafarkin ga ni ina matsar giya."
Kuma cfayan ya ce, "Lalle ne ni, na
yi mafarkin ga ni ina cfauke da
waina a bisa kaina, tsuntsaye suna
ci daga gare ta. Ka ba mu labari
game da fassararsu. Lalle ne mu,
muna ganin ka daga masu kyauta-
tawa."
37. Ya ce, "Wani abinci ba zai zo
muku ba wanda ake arzuta ku da
shi face na ba ku labarin fassarar-
sa (2) , kafin ya zo muku. Wannan
kuwa yana daga abin da Ubangijlna
Ya sanar da ni. Lalle ne ni, na bar
addinin mutane wadanda ba su yi
Tmani da Allah ba, kuma game da
Lahira, su kafirai ne.
38. "Kuma na bi addinin iya-
yena, Ibrahim da Is'haka da Yaku-
ba. Ba ya yiwuwa a gare mu mu yi
shirka da Allah da kome. Wannan
yana daga falalar Allah a kanmu da
mutane, amma mafi yawan mutane
ba su godewa.
39. "Ya abokaina biyu na kur-
kuku! Shin iyayen giji dabam-da-
bam ne mafiya alheri ko kuwa Allah
Makadaici Mai tankwasawa?
S^dS^"
j\^\^\^\j
(1) Yusufu a cikin kurkuku tare da abokan shigarsa kurkukun. Kuma yana fassara
mafarki a bay an kiransa zuwa ga addini.
(2) Kowane irin abin ne kafin in gan shi da idona, zan iya gaya mukunau'insa, kamar
yadda Tsa ya ce, "Ina ba ku labarin abin da kuke ci a gidajenku." A Surar Al Imrana aya ta
49.
347
12 - Suratu Yusuf
&&M-"
40. "Ba ku bauta wa kome, bai-
cinSa, face wacfansu sunaye wacfan-
da kuka ambace su, ku da uban-
ninku. Allah bai saukar da wani
dalili ba game da su. Babu hukunci
face na Allah. Ya yi umurnin kada
ku bauta wa kowa face Shi. Wan-
can ne addini madaidaici, kuma
amma mafi yawan mutane ba su
sani ba.
41. "Ya abokaina biyu, na kur-
kuku! Amma cfayanku, to, zai sha-
yar da uban gidansa giya, kuma
gudan, to, za a tsTre shi, sa'an nan
tsuntsaye su ci daga kansa. An hu-
kunta aFamarin, wanda a cikinsa
kuke yin fatawa."
42. Kuma ya ce da wanda ya
tabbatar da cewa shi mai ku6uta ne
daga gare su, "Ka ambace ni a
wurin uban gidanka." Sai Shaicfan
ya mantar da shi tunawar ubangi-
jinsa, saboda haka ya zauna a cikin
kurkuku 'yan shekaru.
43. Kuma sarki ya ce. "Lalle ne,
na yi mafarki; (1) na ga shanu bak-
wai masu kiba, wacfansu bakwai
ramammu, suna cin su, da zangarku
bakwai kore-kore da wacfansu ke-
kasassu. Ya ku jama'a! Ku yi mini
fatawa a cikin mafarklna, idan kun
kasance ga mafarki kuna fassa-
rawa."
C« JL r L^ fc^j <w$UtX: *^wc*(j^±==»b
(I) Mafarkin Sarki wanda zai zama sanadin fitar Yusufu daga kurkuku. Wannan
yana nuna ba a kebance yin mafarki ga Musulmi kawai, kafiri ma yana yin mafarki. Ba
a iya fassara mafarki sai da ilmin Alicur'ani da Hadisi da kuma sanin al'adun mutane.
Mafarki ba ya zama hujja sai idan wani annabi ya fassara shi.
348
12 — Suratu Yusuf
&$>M-^
44. Suka ce, "Yaye-yayen ma-
farki ne, kuma ba mu zamo masana
ga fassarar yaye-yayen mafarki
ba."
45. Kuma wannan da ya ku6uta
daga cikinsu ya ce, a bayan ^a yi
tunani a lokaci mai tsawo, "Ni, ina
ba ku labari game da fassararsa. Sai
ku aike ni."
46. "Ya Yusufu! Ya kai mai ya-
wan gaskiya! Ka yi mana fatawa a
cikin shanu bakwai masu kiba, wa-
dansu bakwai ramammu suna cin
su, da zangarku bakwai koraye da
wadansu kekasassu, tsammanina in
koma ga mutane, tsammaninsu za
su sani."
47. Ya ce, "Kuna shuka, shekara
bakwai tutur, sa'an nan abin da
kuka girbe, sai ku bar shi, a cikin
zanganniyarsa, (1) sai kadan daga
abin da kuke ci.
48. "Sa'an nan kuma wadansu
bakwai masu tsanani su zo daga
bayan wancan, su cinye abin da
kuka gabatar dominsu, face kadan
daga abin da kuke adanawa.
49. "Sa'an nan kuma wata she-
kara ta zo daga bayan wancan, a
cikinta ake yi wa mutane ruwa mai
albarka, kuma a cikinta suke mat-
sar abin sha."
50. Kuma sarkin ya ce, "Ku zo
mini da shi." To, a lokacin da man-
zo ya je masa (Yusufu), ya ce, "Ka
koma zuwa ga uban gidanka, sa'an
•2
SpO--tr^
(1) Barin hatsi a cikin zanganniyarsa shi ne maganin ru6ewarsa, ko wacfansu tsutsotsi
da suke cin sa.
349
12 - Suratu Yusuf
&&££<*.
&_tt
nan ka tambaye shi : Mene ne halin
matayen nan wacfanda suka ya-
nyanke hannayensu? Lalle ne
Ubangijina ne Masani game da
kaidinsu."
51. Ya ce, "Mene ne babban
al'amarinku, a lokacin da kuka
nemi Yusufu daga kansa?" Suka ce,
"Tsarki ga Allah yake! Ba mu san
wani mummunan aiki a kansa ba."
Matar Aziz ta ce, "Yanzu fa gas-
kiya (1) ta bayyana. Nice na neme
shi daga kansa. Kuma lalle ne shT,
haklka, yana daga masu gaskiya.
52. "Wancan ne, domin ya san
cewa lalle ne ni ban yaudaure shi ba
a Boye, kuma lalle Allah ba Ya
shiryar da kaidin mayaudara.
53. "Kuma ba ni kuButar da kai-
na. Lalle ne rai, haklka, mai yawan
umurni ne da mummunan aiki, face
abin da Ubangijina Ya yi na raha-
ma. Lalle Ubangijina Mai gafara
ne, Mai jin kai."
54. Kuma sarkin ya ce, "Ku zo
mini da shi in keBe shi ga kaina."
To, a lokacin da Yusufu ya yi masa
magana sai ya ce, "Lalle ne kai a
yau, a gunmu, mai daraja ne,
amintacce." (2)
55. Ya ce, "Ka sanya ni a kan
taskokin kasa. Lalle ne ni, mai tsa-
rewa ne, kuma masani."
<i^ C.^> — T- — ' | — ' »■ | ■ — ' i • — " "i y y ■*-*
( 1 ) Da wannan magana ta matar AzTz ZalTha ana fahimtar ita ta musulunta ta hannun
Yusufu kafin a daure shi.
(2) Magnar da Yusuf ya gaya wa sarki lokacin da ya je masa ba a fade ta ba, sai dai an
nuna ta kayatar da shi har ya yabe shi da cewa shi mai daraja ne amintacce.
350
12 — Suratu Yusuf
«**&<?>,
m?-*
56. Kuma kamar wancan ne
Muka bayar da Tko ga Yusufu a
cikin kasa (1) yana sauka a inda duk
yake so. Muna samun wanda Muke
so da rahamarMu, kuma ba Mu
tozartar da ladar masu kyautatawa.
57. Kuma lalle ladar Lahira ce
mafi alheri ga wacfanda suka yi
Imani, kuma suka kasance masu
takawa.
58. Kuma 'yan'uwan (2) Yusufu
suka je, sa'an nan suka shiga a gare
shi, sai ya gane su, alhali kuwa su,
suna masu musunsa.
59. Kuma a lokacin da ya yi
musu tattali da tattalinsu, ya ce,
"Ku zo mini da wani cfan'uwa naku
daga ubanku. Ba ku gani ba cewa
lalle ne m, ina cika ma'auni, kuma
nine mafi alherin masu saukarwa?
60. "Sa'an nan idan ba ku zo
mini da shi ba, to, babu awo a gare
ku a wunna, kuma kada ku kasance
ni."
61. Suka ce, "Za mu neme shi
daga ubansa. Kuma lalle ne mu,
ha£i£a, masu aikatawa ne."
62. Kuma ya ce wa yaransa, "Ku
sanya hajjarsu a cikin kayansu,
tsammaninsu suna gane ta idan sun
juya zuwa ga mutanensu, tsamma-
ninsu, za su komo."
(1) Lokacin da Yusufu yana aikin tattalin arzikin Rasa a cikin shekarar wadata, ya
mallake Rasar Masar duka a lokacin da wahala da yunwa suka auku.
(2) 'Yan'uwan Yusufu sun zo suna neman awo a gunsa, ya gane su domin bakauye ko
matalauci bai faye canja kamanninsa ba, amma su, ba su gane shi ba, saboda haibar mulki
ka kwarjinin halittarsa a bayan ya zama babban mutum ga idonsu a inda ba su zaton sa.
351
12 - Suratu Yusuf
<S5$£&-W
63. To, a lokacin da suka koma
zuwa ga ubansu, suka ce, "Ya ba-
banmu! An hana mu awo, sai ka
aika dan'uwanmu tare da mu.^Za
mu yi awo. Kuma lalle ne, hakika
mu, masu lura da shi ne."
64. Ya ce, "Ashe, za ni amince
muku a kansa? Face dai kamar
yadda na amince muku a kan dan-
'uwansa daga gabani, sai dai Allah
ne Mafificin masu tsari, kuma Shi
ne Mafi rahamar masu rahama."
65. Kuma a lokacin da suka
bude kayansu, suka sami hajjarsu
an mayar musu da ita, suka ce, "Ya
babanmu ! Ba mu zalunci ! Wannan
hajjarmu ce an mayar mana da ita,
kuma mu nemo wa iyalinmu abinci,
kuma mu kiyaye dan'uwanmu,
kuma mu kara awon kayan rakumi
guda, wancan awo ne mai sauki."
66. Ya ce, "Ba zan sake shi tare
da ku ba, sai kun kawo mini alka-
warinku daga Allah, hakTka, kuna
dawo mini da shi, sai fa idan an
kewaye ku." To, a lokacin da suka
yi masa alkawari, ya ce, "Allah ne
WakTli a kan abin da muke facfa."
67. Kuma ya ce, "Ya cfiyana!
Kada ku shiga ta kofa guda, ku
shiga ta kofofi dabam-dabam, (1)
6
^H *isZAZ'\' Y &\ 1i- * y '---*'
(1) Yakubu ya umurci cfiyansa su shiga garin, ta kofofi dabam-dabam, yana nuna
cewa yana gudun kyawunsu da yawansu zai ja hankalin mutane zuwa gare su. A cikin
mutane akwai masu kambun baka da mugun nufi ko da yake Yakuba a cikin halin haka ya
aza tawakkalinsa ga Allah. Ya yi abin da yake zaton alheri ne, wanda bai sa&a wa shan'a
ba. Amma kuma ya yi haka ne a kan wani ilmi da Allah Ya sanar da shi cewa a wannan
fltar tasu ce Allah zai yi sanadin sake saduwarsu da Yusufu, saboda haka ya umurce su da
su shiga ta kofofi dabam-dabam, domin mutum shi kacfai ya fi samun damar ta'ammalin
ganin mutane da abubuwa. Kuma ta yin haka, yana tsammanin waninsu zai ga Yusufu.
352
12 - Suratu Yusuf
&%m-"
kuma ba na wadatar muku kome
daga Allah. Babu hukunci face
daga Allah, a gare Shi na dogara,
kuma a gare Shi masu dogara sai su
dogara."
68. Kuma a lokacin da suka Shi-
ga daga inda ubansu ya umurce su
wani abu bai kasance yana wada-
tarwa ga barinsu daga Allah ba face
wata bukata ce a ran Yakubu, y&
bayyana ta. Kuma lalle ne shi, hakl-
ka, ma'abucin wani ilmi ne ga abin
da Muka sanar da shi, kuma mafi
yawan mutane ba su sani ba.
69. Kuma a lokacin da suka Shi-
ga wajen Yusufu, ya tattara cfan-
'uwansa zuwa gare shi, ya ce, "Lalle
nl ne cfan'uwanka, saboda haka
kada ka yi bakin ciki da abin da
suka kasance suna aikatawa."
70. Sa'an nan a lokacin da ya yi
musu tattali da tattalinsu, sai ya
sanya ma'auni a cikin kayan cfan-
'uwansa sa'an nan kuma mai yeku-
wa ya yi yekuwa, "Ya ku ayari!
Lalle ne, haklka ku 6arayi ne."
71. Suka ce, kuma suka fuskanta
zuwa gare su, "Mene ne kuke
nema?"
72. Suka ce, "Muna neman
ma'aunin sarki. Kuma wanda ya zo
da shi, yana da kayan rakumi cfaya,
kuma ni ne lamuni game da shi."
73. Suka ce, "Tallahi! Lalle ne,
haklka, kun sani, ba mu zo don mu
yi 6arna a cikin kasa ba, kuma ba
mu kasance Barayi ba."
i ' - * *'
s&zt^"*
I *^ • -'i--'rf<^^ » -\" *'<•' Si"
353
12 - Suratu Yusuf
&&M-"
74. Suka ce, "To, mene ne saka-
makonsa idan kun kasance makar-
yata?"
75. Suka ce, "Sakamakonsa,
wanda aka same shi a cikin kayan-
sa, to, shi ne sakamakonsa, (1) ka-
mar wancan ne muke saka wa azza-
lumai."
76. To, sai ya fara (bincike) da
jikunansu a gabanin jakar rfan'-
uwansa. Sa'an nan ya fitar da ita
daga jakar dan'uwansa. Kamar
wancan muka shirya wa Yusufu.
Bai kasance ya kama dan'uwansa
a cikin addinin (dokokin) sarki ba,
face idan Allah Ya so. Muna dau-
kaka darajoji ga wanda Muka so,
kuma a saman kowane ma'abucin
ilmi akwai wani masani.
77. Suka ce, "Idan ya yi sata, to,
lalle ne wani dan'uwansa ya taba
yin sata a gabaninsa." Sai Yusufu
ya boye (2) ta a cikin ransa. Kuma
bai bayyana ta ba a gare su, ya ce,
"Ku ne mafi sharri ga wuri. Kuma
Allah ne Mafi sani daga abin da
kuke sifantawa."
^^^^^^ : ^
*''> '* rv <-
1 jr^>J «,Wj J^^I^-^U Ijui
(1) Shariar BanT Ya'a£ubu ita ce ana bautar da barawo shekara guda. Wannan shine
sharTar da Turawa suka dauka suka mayar da ita daurin kurkuku da bautar da barawo a
cikin mudda ayyananna.
(2) Tan'uwan Yusufu sun fadi cewa dan'uwan Binyaminu ya taba yin sata, domin
su nuna cewa a wajen ubansu tsarkakakku ne daga yin sata. Shi kuma wanda ya yi satan ya
gade ta ne daga wajen uwarsa, domin wani shaklkinsa (Yusufu) ya taba yin sata. To, sai
Yusufu ya ce a ransa "Ku ne dai mafi sharrin mutane, Allah ne Mafi sani daga abin da
kuke sifantawa."
Asalin wannan magana wata goggonsa ce (Shi Yusufu) cfiyar Is'haica, ta riice shi, yana
yaro, har a lokacin da ubansa (Yakubu) ya so ya karbe shi daga gare ta, sai ta yi kaidin
sanya kayan sata a cikin rigarsa (Yusufu) domin ta hana uban daukarsa.
A wata ruwaya kuma an ce shi (Yusufu) ya dauke wani mutummutumi ne na zmari
(gunki) ya karairaya shi. Don haka 'yan'uwansa suke jingina sata a gare shi.
354
12 - Suratu Yusuf
*"*\z<*
&->r
78. Suka ce, "Ya kai Azizu ! Lai-
le ne yana da wani uba, tsoho mai
daraja, saboda haka, ka kama
cfayanmu a matsayinsa. Lalle ne mu,
muna ganin ka daga masu kyauta-
tawa.
79. Ya ce, "Allah Ya tsare mu
daga mu kama wani face wanda
muka sami kayanmu a wurinsa.
Lalle ne mu, a lokacin nan, haklka,
azzalumai ne."
80. Saboda haka, a lokacin da
suka yanke tsammani daga gare shi,
sai suka fita suna masu ganawa. (1)
Babbansu ya ce, "Shin, ba ku sani
ba cewa lalle ne ubanku ya riki
alkawari daga Allah a kanku, kuma
daga gabanin haka akwai abin da
kuka yi na sakaci game da Yusufu?
Saboda haka, ba zan gushe daga
kasar nan ba face ubana ya yi mini
izni, ko kuwa Allah Ya yi hukunci a
gare ni, kuma Shi ne Mafi alherin
mahukunta.
81. "Ku koma zuwa ga ubanku,
ku gaya masa : Ya babanmu, lalle ne
cfanka ya yi sata, kuma ba mu yi
shaida ba face da abin da muka
sani, kuma ba mu kasance mun san
gaibu ba.
82. "Kuma ka tambayi alkarya
wadda muka kasance a cikinta, da
ayari wanda muka gabato a cikinsa,
kuma lalle ne, hakika, mu masu
gaskiya ne."
&^£l(lr$&^0$)£
(1) 'Yan'uwan Yusufu sun yanke tsammanin samun Binyaminu daga shari'a, sun
koma suna ganawa a tsakaninsu. Sai dai wacfannan dlyansu ne domin su, suna Masar.
355
12 - Suratu Yusuf
&&M-"
83. Ya ce, "A 'a, zukatanku sun
kawata wani aramari a gare ku. Sai
hakuri mai kyawo, akwai tsam-
manin Allah Ya zo mini da su gaba
cfaya (Yusufu da 'yan'uwansa). Lal-
le ne Shine Masani, Mai hikima."
84. Kuma ya juya daga gare su,
kuma ya ce, "Ya bakin cikina a kan
Yusufu!" Kuma idanunsa suka yi
fari saboda huznu sa'an nan yana ta
hadewar haushi.
85. Suka ce, "Tallahi! Ba za ka
gushe ba, kana ambaton Yusufu, (1)
har ka kasance mai rauni kwarai,
ko kuwa ka kasance daga masu
halaka."
86. Ya ce, "A bin sani kawai, ina
kai karar bakin cikina da sunona
zuwa ga Allah, kuma na san abin da
ba ku sani ba daga Allah.
87. "Ya diyana! Sai ku tafi ku
nemo labarin Yusufu (2) da cfan-
'uwansa. Kada ku yanke tsammani
daga rahamar Allah. Lalle ne, babu
mai yanke tsammani daga rahamar
Allah face mutane kafirai."
88. Sa'an nan a lokacin da suka
shiga gare shi suka ce, "Ya kai
Azizu! Cuta ta shafe mu, mu da
iyalinmu, kuma mun zo da wata
haja maras lama. Sai ka cika mana
ma'auni, kuma ka yi sadaka a gare
* -»~ '<^:\/<r>>.\s<r\ -
t' < > > < x
t &C&foJ& J £s' dyj
• *l^_I^
(1) Mai tsohon laifi ba ya son ya ji ana ambatonsa, saboda haka ('yan'uwan Yusufu)
suke zargin babansu da ambaton (tuna) Yusufu.
(2) A nan Ya£ubu ya bayyana irin ilmin da Allah Ya sanar da shi, cewa Yusufu yana
nan da ransa, kuma sun yi kusa su sadu da juna.
356
12 — Suratu Yusuf
&?*&<*
ii. — \r
mu. Lalle ne Allah Yana saka wa
masu yin sadaka (1) ."
89. Ya ce, "Shin, kun (2) san
abin da kuka aikata ga Yusufu da
tfan'uwansa a lokacin da kuke
jahilai?"
90. Suka ce, "Shin ko, lalte ne,
kai ne Yusufu?" Ya ce,_"N7 ne
Yusufu, kuma wannan shT ne dan-
'uwana. Haklka Allah Ya^yi fala-
la a gare mu. Lalle ne, shT wanda
ya bi Allah da takawa, kuma ya yi
hakuri, to, lalle ne Allah ba Ya
tdzarta ladar masu kyautatawa."
97. Suka ce, "Tallahi! Lalle ne
haklka, Allah Ya zabe ka a kanmu,
kuma lalle ne mun kasance, hakika,
masu kuskure."
92. Ya ce, "Babu zargi a kanku a
yau, Allah Yana gafarta muku,
kuma ShT ne Mafi rahamar masu
rahama.
93. "Ku tafi da rlgata wannan,
sa'an nan ku jefa ta a kan fuskar
mahaifina, zai koma mai gani.
Kuma ku zo mini da iyalinku baki
daya."
94. Kuma, a lokacin da ayari (3)
ya bar (Masar) ubansa ya ce, "Lalle
ne, nl ina shakar iskar Yusufu, ba
domin kuna karyata ni ba."
1^% ^ - * ''At
G3 u^^-...*>uJt
.-" <> «*■<* ^ ^<i^ »^<
(1) Wannan ya niina ba a haramta sadaka ba ga Annabawan da suka gabata, sai ga
Annabinmu Muhammadu, tsTra da amincin Allah su tabbata a gare shi, shT da danginsa na
kusa aka hana wa cin sadaka.
(2) Yusufu ya bayyana ga 'y anuw ansa, kuma sun yafe wa juna laifi.
(3) Yakuba da jikokinsa. Yana gaya musu, cewa yana shakar kanshin Yusufu, su
kuma suna jingina shi ga rudewar tsufa domin rabonsa da Yusufu shekara talatin da biyar
zuwa arba'in.
357
12 — Suratu Yiisuf
^Mitf*
^L — \r
95. Suka ce, "Tallahi, lalle ne,
kai, haklka, kana a cikin 6atarka
dacfacfcfa."
96. Sa'an nan a lokacin da mai
bayar da bushara ya je, sai ya jefa ta
a kan fuskarsa, sai ya koma mai
gani. Ya ce. "Shin, ban gaya muku
ba, lalle ne, ni ina sanin abin da ba
ku sani ba daga Allah?"
97. Suka ce, "Ya ubanmu ! (1 > Ka
nema mana gafara ga zunubanmu,
lalle ne mu, mun kasance masu
kuskure."
98. Ya ce, "Da sannu za ni nema
muku gafara daga Ubangijina. Shi
ne Mai gafara, Mai jin kai."
99. Sa'an nan a lokacin (2) da
suka shiga gun Yusufu, ya tattara
mahaifansa biyu a gare shi, kuma
ya ce, "Ku shiga Masar in Allah Ya
so, kuna amintattu."
100. Kuma ya cfaukaka iyayensa
biyu a kan karaga, sa'an nan suka
facfi a gare shi, suna masu sujada. (3)
Kuma ya ce, "Ya babana! Wannan
ita ce fassarar mafarkin nan nawa.
Lalle ne Ubangijina Ya sanya shi ya
tabbata sosai, kuma lalle ne Ya
Pp>-> JC^^JiJlS J$ Ji^b^U
'*{.'/<>> >\\*<' u*'\tV »'A'<"
(1) T)iyan Yakubu suna ikrari da laifinsu, suna neman Allah Ya gafarta musu gaba
cfaya. Ubansu yana jinkirta nema musu gafara gun Allah har a lokacin asuba ko kuwa
daren Jumma'a domin ya yi roko a lokacin karbar addu'a. Wannan ya nuna ana iya neman
mai albarka ko wani mutum ya yi wa wani mutum addu'a.
(2) Yusufu ya sadu da ubansa da uwarsa. A Larabci ana rinjayar da uba a kan uwa, a
ce ubanni biyu, kuma ga Hausa ana rinjayar da uwa a kan uba, a ce uwaye biyu.
(3) Sujada idan ta zama da umurnin Allah ne ga kowa, to, ba ta da laifi duk yadda
take, amma idan an yi ta ba inda Allah Ya ajiye ta ba, to, ta zama kafirci. A Musulunci
gaisuwa da dukawar kai haram ce, wacfansu Malamai sun ce idan ba ta kai ga ruku'i ba,
makaruhi ce, amma idan ta kai ga ruku'i ta zama haram un ga duka malamai, watau
ijma'in malamai sun haramta dukawar da ta kai ga ruku'i.
358
12 — Suratu Yusuf
r Wi<*
£,-\S
kyautata game da ni a lokacin da Ya
fitar da ni daga kurkuku. Kuma Ya
zo da ku daga kauye, a bayan Shai-
cfan ya yi fisgar 6arna a tsakanina
da tsakanin 'yan'uwana. Lalle ne
Ubangijina Mai tausasawa ne^ga
abin da Yake so. Lalle ne ShT, Shine
Masani, Mai hikima.
101. "Ya Ubangijina, (1) lalle ne
Ka ba ni daga mulki, kuma Ka
sanar da ni daga fassarar labaru.
Ya Mahaliccin sammai da kasa!
Kai ne Maji6incina a duniya da
Lahira, Ka kar6i raina ina Musul-
mi, kuma Ka riskar da ni ga sa-
lihai."
102. Wannan daga (2) labarun
gaibi ne, Muna yin wahayinsa zuwa
gare ka, kuma ba ka kasance a
wurinsu ba a lokacin da suke yin
niyyar zartar da al'amarinsu, alhali
suna yin makirci.
103. Kuma mafi yawan mutane
ba su zama masu Imani ba, ko da ka
yi kwacfayin haka.
104. Kuma ba kajtambayar su
wata lada a kansa. ShT bai zama ba
face ambato domin halittu.
105. Kuma da yawa, wata aya a
cikin sammai da kasa, suna shu-
dewa a kanta, kuma su, suna biji-
rewa daga gare ta.
-/< <=- „s*
'A" .r>rf^
^sli&j <j)^\o* < ^£\*-&<> r >j
vSi>Uj vibl [±^.y <Jj& %S\{y* vllVi
(1) Yusufu yana addu'a a karshen rayuwarsa, yana neman Allah Ya cika masa da
imani.
(2) Karfafawa da karin tambThi daga abin da surar ta £unsa, daga nan har zuwa
karshenta.
359
12 - Suratu Yusuf
C&X\i<*
£_\r
106. Kuma mafl yawansu ba su
yin Tmani da Allah face kuma suna
masu shirki.
107. Shin fa, sun amince cewa
wata masTfa daga azabar Allah ta zo
musu ko kuwa Tashin Kiyama ta zo
musu kwatsam, alhali su ba su sani
ba?
108. Ka ce, "Wannan ce han-
yata (1) ;jna kira zuwa ga Allah a
kan basira, ni da wacfanda suka bi
ni^kuma tsarki ya tabbata ga Allah !
Ni kuma, ban zama daga masu
shirki ba."
109. Kuma ba Mu aika ba a
gabaninka face mazaje, Muna wa-
hayi zuwa gare su, daga mutanen
kauyuka. Shin fa, ba su yi tafiya a
cikin kasa ba, domin su duba yadda
akibar wacfanda suka kasance daga
gabaninsu ta zama? Kuma lalle ne
gidan Lahira shT ne mafi alheri ga
wacfanda suka yi takawa? Shin fa,
ba ku hankalta?
110. Har a lokacin da Manzanni
suka yanke tsammani, kuma suka
yi zaton cewa an jingina su ga
karya, sai taimakonMu ya je masu,
sa'an nan Mu tserar da wanda
Muke so, kuma ba a mayar da
azabarMu daga mutane masu laifi.
111. Lalle ne, haklka, abin kula
ya kasance a cikin kissoshinsu
ga masu hankali. Bai kasance
"**
\y£\^^&J^~&J>^\j\jhj
%'Ar* \<' \>><\'\
->* s»*
(1) Bin hukuncin Allah kamar yadda kissar Yusufu ta nuna cewa,ja kowane hali
mutum ya kasance akwai yadda Allah Ya yi umurni a wannan halin da a bT Shi, wanda ya
bi umurnin Allah, to, zai daukaka a duniya kuma Allah ba zai tozartar da ladarsa a Lahira
ba.
360
13 — Suratur Ra'ad
c&m-\r
wani Rirkiran labari ba, kuma
amma shi gaskatawa ne ga abin da
yake a gaba gare shi, da rarrabewar
dukan abubuwa, da shiriya da raha-
ma ga mutane wacfanda suka yi
Tmani.
&
Tana karantar da tauhidi, bisa jan hankali ga duba zuwa ga
ayoyin halitta, da bayanin kiran Allah zuwa ga mutane, da tabbatar
da Manzancin Annabi Muhammadu, a cikin magana mai zurfi ga
hankali.
j*'>+ ^ >*
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. A. L. M. R. Wacfancan ayoyin
littafi ne, kuma abin da aka saukar
gare ka daga Ubangijinka ne gas-
kiya, kuma amma mafi yawan mu-
tane ba su yin Tmani.
2. Allah Shi ne Wanda Ya cfau-
kaka sammai, ba da ginshikai ba
wacfanda kuke ganin su. Sa'an nan
kuma Ya daidaita a kan Al'arshi,
kuma Ya hore rana da wata, kowa-
ne yana gudana zuwa ga ajali amba-
tacce. Yana shirya al'amari, Yana
rarrabe ayoyi daki-daki, mai yiwu-
wa ne ku yi yakini da hacfuwa da
Ubangijinku.
361
13 — Suratur Ra'ad
tm$&-\r
3. Kuma Shi ne Wanda Ya shim-
ficfa kasa, kuma Ya sanya duwatsu
da koguna a cikinta, kuma daga
dukan 'ya'yan itace Ya sanya
ma'aura biyu cikinsu. Yana sanya
dare ya rufe^yini. Lalle ne a cikin
wancan, haklka akwai ayoyi ga mu-
tane wacfanda suke yin tunani.
4. Kuma a cikin kasa akwai yan-
kuna masu makwabtaka, da gonaki
na inabobi da shuka, da dabinai iri
guda, da wacfanda ba iri guda ba,
ana shayar da^su da ruwa guda.
Kuma Muna fifita sashensa a kan
sashe a wajen ci. Lalle ne, a cikin
wancan akwai ayoyi ga mutane wa-
cfanda suke hankalta.
5. Kuma idan ka yi mamaki, to,
mamakin kam shi ne maganarsu,
"Shin, idan muka kasance tur6aya,
za mu zama a cikin wata halitta
sabuwa? Wacfancan ne, wacfanda
suka kafirta da Ubangijinsu, kuma
wacfanda akwai kukumai a cikin
wuyoyinsu, kuma wacfancan ne
abokan wuta. Su, a cikinta, masu
dawwama ne.
6. Kuma suna neman ka da gag-
gawa da azaba a gabanin rahama,
alhali kuwa abubuwan misali sun
gabata a gabaninsu. Kuma lalle ne
Ubangijinka, haklka, Ma'abucin
gafara ne ga mutane a kan zalun-
cinsu, kuma lalle ne Ubangijinka,
haklka, Mai tsananin ukuba ne.
7. Kuma wacfanda suka kafirta
suna cewa, don me ba a saukar da
wata aya a gare shi ba daga Ubangi-
jinsa? Abin sani kawai, kai dai mai
S'4'y yy t y. <yy ' y & 7' Cy If'*'
y <" * »). 9s** *s * y y y s s y ** * "\/ y
0jj>C^^j3l«^^^i 4c>tSv^ '
'*+»<, y y » y y '%»•
y ,** * » '.y y » y y '4»'\ m „* 7' . '
£U>^~*> O^y-ifJ^j O]y^e0^J faJJ
<*■>'*'•* B££X
w
^Cw^>JI Jji ^l^\^^_^ZiL^j
'£''*'*■> 'S'Xl *
»,
i^\.
362
13 — Suratur Ra'ad
&\m-v
gargacfi ne kuma a cikin kowacfanne
mutane akwai mai shiryarwa.
8. Allah Yana sanin abin da ko-
wace mace take cfauke da shi a
cikinta, da abin da mahaifu suke
ragewa (1) da abin da suke karawa.
Kuma dukkan kome, a wurinSa, da
gwargwado yake.
9. Shi ne Masanin fake da bayya-
ne, Mai girma, Macfaukaki.
10. Daidai ne daga gare ku, wan-
da ya asirta magana da wanda ya
bayyana game da ita, da wanda
yake shi mai neman 66yewa ne da
dare, da mai bayyana a cikin
kawalwalniyar (2) rana da rana.
77. (Kowannenku) Yana da wa-
dansu mala'iku masu maye wa juna
a gaba gare shi da baya gare shi,
suna tsare shi daga umurnin Allah.
Lalle ne, Allah ba Ya canja abin da
yake ga mutane sai sun canja abin
da yake ga zukatansu. Kuma idan
Allah Ya yi nufin wata azaba game
da mutane, to, babu mai mayar da
ita, kuma ba su da wani majibinci (3)
baicin Shi.
12. Shi ne Wanda Yake nuna
muku walkiya domin tsoro da
tsammani, kuma Ya kaga halittar
giragizai masu nauyi.
13. Kuma aradu tana tasbThi
game da gode Masa, da mala'iku
domin tsoronSa. Kuma Yana aiko
-i-5 .
^ \ y - >'.
£3 Jl^^^^UJljlj>iLj
x- >**h > ^ />'
(1) Ragowar lokacin cikin ko karuwarsa.
(2) Hasken rana mai kama da ruwa ga idon mai dubi daga nesa.
(3) Babu wani majirMnci baicin Allah, wanda zai iya tsirar da su daga azabarSa.
363
13 - Suratur Ra'ad
&\m-\r
tsawawwaki, sa'an nan Ya sami
wanda Yake so da su, alhali kuwa
su, suna jayayya^a cikin (aramarin)
Allah, kuma ShT ne mai tsananin
hlla. (1)
14. Yana da kiran gaskiya, kuma
wacfanda (kafirai) suke kira bai-
cinSa, ba su kar6a musu da kome,
face kamar mai shimficfa tafukansa
zuwa ga ruwa (na girgije) domin
(ruwan) ya kai ga bakinsa, kuma shi
ba mai kaiwa gare shi ba. Kuma
kiran kafirai (ga wanin Allah) bai
zama (2) ba face yana a cikin 6ata.
15. Kuma saboda Allah, wanda
yake a cikin sammai da kasa suke
yin sujada, so da ki, kuma da
inuwoyinsu, a safe da maraice.
16. Ka ce, "Wane ne Ubangijin
sammai da kasa?" Ka ce, "Allah".
Ka ce, "Ashe fa, kun riki wacfansu
masoya baicin Shi, wacfanda ba su
mallaka wa kansu wani amfani ba,
kuma haka ba su ture wata cuta?"
Ka ce, "Shin makaho da mai gani
suna daidaita? Ko shin, duhu da
haske suna daidaita? Ko sun sa-
nya ga Allah wacfansu abokan ta-
rayya wacfanda suka yi halitta ka-
mar halittarSa, sa'an nan halittar ta
yi kama da juna a gare su?" Ka ce,
"Allah ne Mai halitta kome, kuma
Shine Macfaukaki, Marinjayi."
(1) Hlla, ita ce makirci, Allah Yana azabta masu yin hlla ga addininSa, da azaba mai
tsanani, kuma Ya kama su da hTlarsu ta hanyar da ba su sani ba.
(2) Allah Mammallakin ruwa, Yana kiran mutane domin Ya ba su ruwan, su sha. Su
kuma kafirai suna kiran wacfansu abubuwa dabam wacfanda ko karba musu kiran ba za su
iya yi ba, kuma suna neman ruwa daga gare su, alhali kuma ba su mallaki kome ba. Watau
Mai abu Yana kiran su domin Ya ba su, sun ki karba masa, sai suna kiran wani wanda bai
mallaki kome ba, suna rokon sa ruwa.
364
13 - Suratur Ra'ad
&\$& - \r
17. Ya saukar da ruwa daga
sama (1) , sai magudanai suka gu-
dana da gwargwadonsu. Sa'an nan
kogi ya dauki kumfa mai karuwa,
kuma daga abin da suke zuga a
kansa (azurfa ko zinari ko karfe) a
cikin wuta, domin neman ado ko
kuwa kayan daki akwai kumfa mi-
salinsa (kumfar ruwa). Kamar wan-
can ne Allah Yake bayyana gaskiya
da karya. To, amma kumfa, sai ya
tafi kekasasshe, kuma amma abin
da yake amfanin mutane sai ya
zauna a cikin kasa. Kamar wancan
ne Allah Yake bayyana misalai.
18. Ga wadanda (2) suka karba
wa Ubangijinsu akwai abu mafi
kyau a gare su, kuma wadanda suke
ba su kar6a Masa ba, to, lalle da
suna da abin da yake a cikin kasa
gaba daya da misalinsa tare da shi,
hakika, da sun yi fansa da shi.
Wadancan suna da mummunan
bincike, kuma matabbatarsu
Jahannama ce, kuma tir da ita ta
zama shimfida.
(1) Idan ruwa ya sauka daga sama sa'an nan ya gudana a cikin rafuna zai yi kumfa.
Sai ruwa mai amfanin mutane ya nutse a Rasa ya zauna, sa'an nan kumfan kuma ya
kekashe ya lalace. Haka kuma idan an sanya karfe na zinari ko na azurfa ko bakin karfe a
cikin wuta, aka zuga ta a kansa, zai fitar da kumfa, watau tsakin tama wanda za a fitar
domin rashin amfaninsa, domin zmariyar kwarai mai amfani ta wanzu. To haka ga kome
akwai kumfa marashin amfani da mai kyawo mai amfani.
(2) Bayan da ya facfi cewa Allah Yana kira, kiran gaskiya a cikin aya ta 14, kuma
wacfansu mutane sun ki karbar kiran Allah, sai suna kiran wacfansu abubuwa dabam, sai
ya bayyana, a nan, sakamakon wanda ya karbi kiran Allah samun ruwan sha, saboda Mai
abu ne Ya kirawo shi, Ya kuma ba shi, ya sha a hankali kwance, sa'an nan kuma Allah zai
ba shi abin da ya fi ruwan kyau, watau Aljanna. Amma wanda ya ki kar6awa, to, ya yi
hasara biyu, bai sami ruwan da ya yi kiran wani ya ba shi ba, sa'an nan kuma ya hacfu da
azabar da take zai iya bayar da dukan abin da ya mallaka domin ya yi fansar kansa da ita.
365
13 — Suratur Ra'ad
o&m-n
19. Shin, fa, wanda yake sanin
cewa lalle abin da aka saukar zuwa
gare ka daga Ubangijinka ne gas-
kiya yana zama kamar wanda yake
makaho? Abin sani kawai, masu
hankali su ke yin tunani.
20. Su ne wacfanda suke cikawa
da alkawarin Allah, kuma ba su
warware alkawari.
21. Kuma su ne wacfanda suke
sadar da abin da Allah Ya yi umurni
da shi domin a sadar da shi, kuma
suna tsoron Ubangijinsu, kuma
suna tsoron mummunan bincike.
22. Kuma wacfanda suka yi ha-
iairi domin neman yardar Ubangi-
jinsu, kuma suka tsayar da salla,
kuma suka ciyar da abin da Muka
arzuta su da shi, a asirce da bay-
yane, kuma suna tunkucfe mummu-
nan aiki da mai kyau. Wacfancan
suna da aicibar gida mai kyau.
23. Gidajen Aljannar zama, suna
shigarsu, su da wacfanda suka kyau-
tatu daga iyayensu, da matansu da
zuriyarsu. Kuma mala'iku suna
shiga zuwa gunsu ta kowace kofa.
24. "Aminci (1) ya tabbata a kan-
ku saboda abin da kuka yi wa ha£u-
ri. Saboda haka madalla da ni'imar
a£ibar gida."
25. Kuma wacfanda (2) suka war-
ware alkawarin Allah daga bayan
{ y^>y^AiA^\^\ u o£^iU& \)
• ^ r^-> ^ > f »>£
W ^ •*' *^^
^^>Jt)^j *£kj\r2 (%Hg^i;li* \juftj
( 1 ) Sallamar mala'iku a kansu idan sun shiga a gare su, it ce su ce musu "Aminci ya
tabbata a gare ku".
(2) Bayanin siffofin wacfanda suka £i karBar kiran Allah. Watau akasin wacfanda aka
yi bayaninsu a baya.
366
13 - Suratur Ra'ad
tg@\$&-\r
kulla shi, kuma suna yanke abin da
Allah Ya yi umurni da shi domin a
sadar da shi kuma suna Barna a
cikin kasar. Wacfancan suna da
wata la "ana, kuma suna da munin
gida.
26. Allah ne Yake (1) shimficfa
arziki ga wanda Yake so, kuma
Yana kuntatawa. Kuma sun yi farin
ciki da rayuwar duniya, alhali kuwa
rayuwar duniya ba ta zama ba dan-
gane ga ta Lahira face jin dadi
kacfan.
27. Kuma wancfanda suka ka-
firta, suna cewa, "Don me ba a
saukar da wata aya ba a kansa daga
Ubangijinsa?" Ka ce, "Lalle ne
Allah Yana Batar da wanda Yake so
kuma Yana shiryar da wanda ya
tuba zuwa gare Shi."
28. Wacfanda suka yi imani
kuma zukatansu sukan natsu da
ambaton Allah. (2) To, da ambaton
Allah zukata suke natsuwa.
29. Wacfanda suka yi Imani,
kuma suka aikata aiki nagari, farin
ciki ya tabbata a gare su, da kyak-
kyawar makoma.
30. Kamar wancan ne Muka aika
ka a cikin aFumma wanda take wa-
dansu al'ummai sun shude daga
gabaninta, domin ka karanta musu
-f'U \> <y > 9 -"i\<" '\'""\\ \»»'**\
^^C^Z^^\\Ju^
( 1 ) Ta'akibi da tambThi ne da karin bayani ga mai hankali domin ya zabura ga karbar
kiran Allah.
(2) Ambaton Allah, shi ne hukunce-hukuncenSa ga kome. Umar cfan K hat tab ya ce,
"Mafificin ambaton Allah, shi ne wanda aka yi a wurin umurninSa ko haninSa. Wanda
yake yin zikirin baki ba da yana aiki da hukunce-hukuncen Allah ba a cikin ibadarsa da
mu'amalansa, to, shi mai izgih kawai ne da sunan Ubangijinsa, ba mai yin zikiri ba ne.
367
13 - Suratur Ra'ad
&@sm-\r
abin da Muka yi wahayi zuwa a
gare ka, alhali kuwa su, suna kafirta
da Rahaman. (1) Ka ce, "Shi ne
Ubangijlna, babu abin bautawa
face Shi, a gare Shi na ddgara, kuma
zuwa gare Shi tubata take."
31. Kuma da lalle an saukar da
wani littafi abin karatu wanda ake
tafiyar da duwatsu game da shi, ko
kuma aka yanyanke kasa da shi, ko
kuwa akayi magana da matattu da
shi (da ba su yi imani ba). A'a ga
Allah al'amari yake gaba daya!
Shin fa, wadanda suka yi Imani ba
su yanke tsammani ba da cewa, da
Allah Ya so, da Ya shiryar da muta-
ne gaba daya? Kuma wadanda suka
yi kafirci ba za su gushe ba wata
masTfa tana samun su saboda abin
da suka aikata,kokuwakasauka (2)
kusa da gidajensu, har wa'adin Al-
lah Ya zo. Kuma lalle ne Allah ba ya
saba wa lokacin alkawari.
32. Kuma lalle ne, haklka, an yi
izgili da M anzanni kaflnka, sai Na
yi jinkiri ga wadanda suka kafirta,
sa'an nan Na kama su. To, yaya
ukubaTa take?
33. Shin fa, Wanda Shi Yake
tsaye a kan kowane rai game da
abin da ya tanada (zai zama kamar
wanda ba haka ba)? Kuma suka
j j4j^£ib a \ ^jb^^uj ^js c. v>yZi
<U1
(1) Sunan Allah Rahman, daga rahama, watau Mai Rahama wadda yake dukan
alheri yana shiga a cikin ma'anarta^a wajen halitta da rayuwa da bayar da lafiya da
shiryarwa. Mafi girman ni'imarSa shi ne aikowar Manzon Allah daga gare mu zuwa gare
mu. Kafirai ba su yi tunani ba a kan wadannan rahamomi, balle su yi godiya, saboda haka
sai kafirci suke yi.
(2) Annabi ya sauka kusa da gidajen Kuraishawa a ranar bude Makka. Kuma
wannan hukunci yana nan yana aiki ga masu £iyayya da addini, kullum maslfu suna
aukuwa a kansu har ranar da Musulunci ya rinjaye su.
368
13 - Suratur Ra'ad
i\$£-\r
sanya abokan tarayya ga Allah ! Ka
ce, "Ku ambaci sunayensu." Ko
kuna bai wa Allah labari ne game
da abin da bai sani ba a cikin £asa?
K6 da bayyananniyar magana kuke
jfin shirka, (banda a cikin zuciya)?
Aa, an dai kawata wa wadanda
suka kafirta makircinsu, kuma an
kange su daga hanya. Kuma wanda
Allah Ya 6atar, to, babu wani mai
shiryarwa a gare shi!
34. Suna da wata azaba a cikin
rayuwar duniya, kuma haklka aza-
bar Lahira ce mafi tsanani, kuma
babu wani mai tsare su daga Allah.
35. Misalin Aljanna wadda aka
yi alkawarinta ga masu takawa,
koramu suna gudana daga karka-
shinta. Abincinta yana madaw-
wami da inuwarta. Waccan ce
akibar wadanda suka yi takawa,
kuma akibar kafirai, ita ce wuta.
36. Kuma wadanda Muka ba su
Littafi suna farin ciki da abin da aka
saukar zuwa gare ka, kuma daga
kungiyoyi akwai mai musun sas-
hensa. Ka ce, "Abin sani kawai, an
umurce ni da in bauta wa Allah,
kuma kada in yi shirka da Shi.
Zuwa gare Shi nake kira, kuma
zuwa gare Shi makomata take."
37. Kuma kamar wancan ne
Muka saukar da shi, (1) Hukunci a
cikin Larabci. Kuma lalle ne idan
ka bi son zuciyoyinsu a bayan abin
da ya zo maka na ilmi, babu wani
E3 ^>\LA$J$ij
( I ) Kamar yadda littattafan farko suke, haka Alkur'ani yake daga Allah, sai dai shi
Al£ur'ani an saukar da shi a cikin Larabci.
369
13 - Suratur Ra 4 ad
Q&m-yr
masoyi a gare ka mai kare ka daga
Allah, kuma babu matsari.
38. Kuma lalle ne, hakika, Mun
aika wadansu manzanni daga
gabaninka, kuma Muka sanya ma-
tan aure a gare su da zuriyya, kuma
ba ya kasancewa ga wani Manzo ya
zo da wata aya, sai da iznin Allah.
Ga kowane ajah (1> akwai littafi.
39. Allah Yana shafe abin da
Yake so, kuma Yana tabbatarwa,
kuma a wurinSa asalin Littafin
yake.
40. Kuma imma lalle Mu
nuna (2> maka sashen abin da Muke
yi musu wa'adi, ko kuwa lalle Mu
karbi ranka, to, abin sani kawai,
iyarwa ce a kanka, kuma hisabi
yana gare Mu.
41. Shin, kuma ba su gani ba
cewa, lalle ne, Muna je wa kasar
(su), Muna rage ta daga gefunanta?
Kuma Allah ne Yake yin hukun-
cinSa. Babu mai bincike ga hukun-
cinSa. Kuma Shine Mai gaggawar
sakamako. (3>
t$^j%$Joi
* ?'-$&C8S\ *- ~
p4A^£fe£plJtt*L$
-<^ E ^
(1) Aikowar Manzanni da littattafai ba ya nana Allah Ya aiko wani Manzo daga baya
da wani littafi wanda ya shafe abin da yake cikin littattafan farko. Allah Ya tabbatar da
abin da Yake so na hukunce-hukuncen da suka gabata domin dogewar aikinsu ga mutane
har yanzu, kuma Ya shafe abin da Yake so saboda amfaninsu da hukuncinsu ya shige,
saboda wata hikima da Allah Ya sani, amma asalin littattafan duka wanda ba zai canja ba,
a cikin sanin Allah, yana wurinSa.
(2) Idan Mun so Mu yi musu azaba a gaban idonka za Mu yi musu, kuma idan Mun
so Mu jinkirta musu har a bayan ka mutu, wannan ba aikinka ba ne, Namu ne. Abin da
yake aikinka shi ne iyar da manzanci kawai. Yin hisabi a kansu alhakin Allah cfai ne.
(3) Gaggawar sakamako ga wanda ya £i bin umurnin Allah wanda AnnabinSa ya iyar
zuwa gare shi. Asalin hisabi, shi ne bincike domin a sami abin da aka yi na alheri ko na
sharri, amma abin da ake nufi a nan, makasudin bincike, shine sakamako da alheri ko da
azaba gwargwadon nufinSa.
370
13 - Suratul Ra'ad
o®m-n
42. Kuma lalle ne, wadanda suke
a gabaninsu sun yi makirci. To, ga
Allah makircin yake gaba daya. Ya
san abin da kowane rai yake tana-
da. Kuma kafirai za su sani, ga
wane akibar gida take.
43. Kuma wadanda suka kafirta
suna cewa, "Ba a aiko ka ba." Ka
ce, "Allah Ya isa zama Shaida a
tsakanina da tsakaninku, da wanda
yake a wurinsa akwai ilmin (1) Lit-
tafi."
V
.A ~^- 3-
t)o?*<
&JJM&Q
Tana karantar da yadda ake yin wa'azi da shiryarwa a game da
abin da ya auku ga aFummomin da suka shude, na kwarai da
miyagu.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
L A. L. R. Littafi ne, mun sau-
kar da shi zuwa gare ka domin ka
fitar da mutane daga duhunhuna
zuwa ga haske, da iznin Ubangi-
jinsu, zuwa ga tafarkin Mabuwayi,
Abin godewa.
±&&-t£ o&jjSttl^&U
(1) Allah Ya isa zama Shaida, haka wanda yake a kan wani ilmi daga Allah kamar
Yahudu da Nasara suna isa zama shaida a tsakanina da ku a kan gaskiyar da'awata cewa nT
abin aikowa ne daga Allah zuwa gare ku, domin akwai wannan magana a cikin
littattafanku.
371
14 — Suratu Ibrahim
&ms&-M
2. Allah, Wanda Yake Yana da
abin da ke cikin sammai da cikin
kasa. Kuma bone ya tabbata ga
kaflrai daga azaba mai tsanani.
3. Wadanda suka fi son rayuwar
duniya fiye da ta Lahira, kuma suna
kangewa daga hanyar Allah, kuma
suna neman ta karkace. Wadancan
na a cikin 6ata mai msa.
4. Kuma ba Mu aika wani Man-
zo ba face da harshen mutanensa,
domin ya bayyana musu. Sa'an nan
Allah Ya 6atar da wanda Yake so,
kuma Ya shiryar da wanda Yake so.
Kuma Shine Mabuwayi, Mai hiki-
ma.
5. Kuma lalle ne, haklka, Mun
aika Musa game da ayoyinMu
cewa, "Ka fitar da mutanenka daga
duhu zuwa ga haske. Kuma ka
tunar musu da kwanukan (musi-
fun) Allah." Lalle ne a cikin wancan
akwai ayoyi domin dukan mai ya-
wan hakuri, mai godiya.
6. Kuma a lokacin da Musayace
wa mutanensa, "Ku tuna ni'imar
Allah a kanku, a lokacin da Ya
tsTrar da ku daga mutanen Fir'-
auna, suna yi muku mummunar
azaba, kuma suna yanyanka diyan-
ku, kuma suna rayar da matanku.
Kuma a cikin wancan akwai jarra-
bawa mai girma daga Ubangi-
jinku."
7. Kuma a lokacin da Uban-
gijinku Ya sanar, "Lalle ne idan
kun gode, hakika, Ina kara muku,
kuma lalle ne idan kun kafirta,
hakika azabaTa, tabbas, mai tsana-
ni ce."
J?}i \J&j oyl'TA i&>% <£$*&
<^»r *
Jb.-Li» kJ\ ^&^^Japs& S^JJ
[Tl
cAli&L
\» v' 9> s
> -^ -^
»> »<^ s
372
14 — Suratu Ibrahim
mm*-*
8. Kuma Musa ya ce, "Idan kun
kafirta, ku da wadanda suke a cikin
£asa, gaba daya, to, lalle ne Allah,
ha£?£a Mawadaci ne, Mai yawan
godiya."
9. Shin, labarin wadanda suke a
gabaninku, mutanen Nuhu da
Adawa da Samudawa, bai zo muku
ba? Kuma da wadanda suke daga
bayansu babu wanda yake sanin su
face Allah? Manzanninsu sun je
musu da hujjoji mabayyana, sai
suka mayar da hannayensu a cikin
bakunansu, kuma suka ce, "Lalle
ne mu, mun kafirta da abin da aka
aiko ku da shi. Kuma lalle ne mu,
ha£lka, muna a cikin shakka da
abin da kuke kiran mu zuwa gare
shi, mai sanya kokanto."
10. Manzanninsu suka ce,
"Ashe, akwai shakka a cikin (sha'-
anin) Allah, Mai £aga halittar sam-
mai da Icasa, Yana kiran ku domin
Ya gafarta muku zunubanku, kuma
Ya jinkirta muku zuwa ga ajali
ambatacce?" Suka ce, "Ba ku zama
ba face mutane misalinmu, kuma
nufinku ku kange mu daga abin da
iyayenmu suka kasance suna bau-
tawa, sai ku zo mana da dafili
mabayyani."
11. Manzanninsu suka ce musu,
"Ba mu zama ba face mutane misa-
linku, kuma amma Allah Yana yin
falala a kan wanda Yake so daga
bayinSa, kuma ba ya kasancewa^a
gare mu, mu zo muku da wani dallli
face da iznin Allah. Kuma ga Allah
sai muminai su dogara.
'A&C'&.Ar^At'
Uyu bUylij ^-^V 't5>-fi J>i' b- 3 ^ 3
^ '\' S'\ J?* " **. -Iff" 'S<\\
ojJ^y U^^. *Ij^ ogy L*^^— *
373
14 — Suratu Ibrahim
MK$&-u
12. "Kuma mene ne a gare mu,
ba za mu dogara ga Allah ba, alhali
kuwa hakika Ya shiryar da mu ga
hanyoyinmu? Kuma lalle ne muna
yin hakuri a kan abin da kuka cutar
da mu, kuma ga Allah sai masu
dogaro su dogara."
13. Kuma wadanda suka kafirta
suka ce wa Manzanninsu, "Lalle ne
muna fitar da ku daga kasarmu, ko
kuwa hakika, kuna komowa a cikin
addininmu." Sai Ubangijinsu Ya yi
wahayi zuwa gare su, "Lalle ne,
Muna halakar da azzalumai."
14. Kuma hakika, Muna zaunar
da ku ga Rasa a bayansu. Wancan
ne abin gargadi ga wanda ya ji
tsoron matsayiNa, kuma ya ji tso-
ron kyacewaTa.
75. Kuma suka yi addu'ar alfa-
nu. (1) Kuma kowane kangararre
mai tsaurin kai ya tabe.
16. Daga bayansa akwai Ja-
hannama, kuma ana shayar da shi
daga wani ruwa, surkin jini.
17. Yana kwankwadarsa, kuma
ba ya jin saukin hadiyarsa, kuma
mutuwa ta je masa daga kowane
wuri, kuma bai zama mai mutuwa
ba, kuma daga bayansa akwai aza-
ba mai kauri.
18. Misalin wadanda suka ka-
firta da Ubangijinsu, ayyukansu
sun yi kama da toka wadda iska ta
yi tsananin bugawa da ita a cikin
yini mai guguwa. Ba su iya amfani
s" "iir^.//
(1) Kowane 6angare ya yi addu'ar alfanu ga abin da yake gani gaskiyarsa. Annabawa
suka yi alfanu da Allah, kuma mutanensu suka yi da abin da suke zato alheri a gare su.
374
14 — Suratu Ibrahim
&£Sl!$&-ti
daga abin da suka yi tsirfa a kan
kome. Wancan ita ce Bata mai nisa.
19. Shin, ba ka gani ba cewa lalle
ne Allah Ya halicci sammai bakwai
da kasa da mallakarSa. (1) Idan Ya
so zai tafiyar da ku, kuma Ya zo da
wata halitta sabuwa.
20. Kuma wancan bai zama
mabuwayi ba ga Allah.
21. Kuma suka bayyana ga Al-
lah gaba daya, sai masu rauni suka
ce wa wadanda suka kangara, "Lal-
le ne mu, mun kasance masu bi a
gare ku, to, shin, ku masu karewa
ga barinmu ne daga azabar Allah
daga wani abu?" (2) Suka ce, "Da
Allah Ya shiryar da mu, da mun
shiryar da ku, daidai ne a kanmu,
mun yi raki ko mun yi hakuri ba
mu da wata mafaka."
22. Kuma Shaidan ya ce a loka-
cin da aka kare al'amarin, "Lalle ne
Allah Ya yi muku wa'adi, wa'adin
gaskiya, kuma na yi muku wa'adi,
sa'an nan na^saba muku. Kuma
babu wani dalTli a gare ni a kanku
face na kira ku, sa'an nan kun karBa
mini. Saboda haka kada ku zarge
ni, kuma ku zargi kanku. Ban zama
mai amfaninku ba, kuma ba ku
zama masu amfanlna ba. Lalle na
barranta da abin da kuka hada ni
da shi gabanin wannan (matsayi).
$ LS&SJ*
c * < ' < i y .
01 yj*^\&dfti\*j
( 1 ) Dalili ne a kan kafircin kafirai ba ya rage mulkin Allah da kome, domin ba su iya
fita daga halittar sammai da kasa, wacfanda Allah Ya halitta da abin da yake mallakarSa.
(2) Muhawarar 'yan wuta a tsakanin mabiya da shugabannin kafirci.
375
14 — Suratu Ibrahim
&r£K$&-ti
Lalle azzalumai suna da azaba mai
racfacfi. ,,(1)
23. Kuma aka shigar da wa-
cfanda suka yi Tmani, kuma suka
aikata ayyuka na kwarai, a gidajen
Aljanna, koramu suna gudana daga
karkashinsu, suna madawwama a
cikinsu da iznin Ubangijinsu, gaisu-
warsu a cikinta "Salam", (watau
Aminci).
24. Shin, ba ka gam ba, yadda
Allah Ya buga wani mlsali, kalma
mai kyau (2) kamar itaciya ce mai
kyau, asalinta yana tabbatacce,
kuma reshenta yana cikin sama?
25. Tana bayar da abincinta a
kowane lokaci da iznin Ubangijin-
ta! Kuma Allah Yana buga misali
ga mutane, mai yiwuwa ne, suna
tunawa.
26. Kuma misalin kalma mu-
mmuna (3) kamar itaciya mummuna
ce, an tum6uke ta daga bisa ga kasa,
ba ta da wata tabbata.
27. Allah Yana tabbatar da wa-
cfanda suka yi Tmani da magana
tabbatacciya a cikin rayuwar du-
niya, da cikin Lahira. Kuma Allah
Yana 6atar da azzalumai, kuma
Allah Yana aikata abin da Yake so.
^i^^^i^iiija^
*'*.<'» y\^\ A -'A -'s"f
( 1 ) Hucfubar Shaicfan ga mabiyansa, a cikin wuta, a bayan an yi muhawara a tsakanin
mabiya da shugabannin kafirci, sashe yana la'antar sashe har abu ya kai ga Shaicfan,
watau Iblis. Shi kuma ya tashi ya yi wannan hucfuba domin ya kara musu bakin ciki a kan
wani.
(2) Kalma mai kyau ta addini tana da asali, kamar itaciyar dablno ce.
(3) Kalma ta kafirci, ba ta da asali, kamar gunar shanu ce.
376
14 — Suratu Ibrahim
&£&$&- it
28. Shin, ba ka lura ba da wa-
cfanda suka musanya (1) ni'imar Al-
lah da kafirci, kuma suka saukar da
mutanensu a gidan halaka?
29. Suna konuwa a wutar Jaha-
nnama, kuma tir da matabbatarsu.
^30. Kuma suka sanya wa Allah
klshiyoyi, domin Batarwa daga ha-
nyarSa. Ka ce, "Ku ji dakfi, sa'an
nan, lalle ne, makomarku wutar
ce."
31. Ka ce wa bayiNa wacfanda
suka yi Tmani su tsayar da salla
kuma su ciyar daga abin da Muka
arziita su, a asirce da bayyane, daga
gabanin wani wuni ya zo, babu
ciniki a ciki, kuma babu abotaka.
32. Allah ne Wanda Ya halicci
sammai da kasa, kuma Ya saukar
da ruwa daga sama, sa'an nan Ya
fitar game da shi, daga 'ya'yan ita-
ce, arziki dominku, kuma Ya hore
jirgin ruwa domin ya yi gudu a cikin
teku da umurninSa, kuma Ya hore
muku koguna.
33. Kuma Ya hore muku rana da
wata suna madawwama biyu, kuma
Ya hore muku dare da wuni.
34. Kuma Ya ba ku dukan abin
da kuka roke Shi, kuma idan kun
kidaya, ni'imar Allah ba za ku lissa-
fe ta ba. Lalle ne mutum, haklka,
mai yawan zalunci ne, mai yawan
kafirci.
> ' < 11
*> &
H0 y-V* ' c^Aj->^J -At 4 ^r^icj
(jC-J ' 3j*Ju \j ^yn. A- ?t J 1 ^Uy-^-JJj
^^Z^
» * < < y / .
(1) Kuraishawa wacfanda Allah Ya yi musu ni'imar zama a cikin hurumin Allah da
aminci da Ya zuba a kansu da albarku, sun musanya godiya da kafirci a lokacin da suka
karyata Manzon Allah. Sun saukar da mutanensu a gidan halaka a Badar.
377
14 — Suratu Ibrahim
&^tjg£-U
35. Kuma a lokacin da Ibrahim
ya ce, "Ya Ubangijina! Ka sanya
wannan gari (1) amintacce, kuma
Ka nisanta ni, ni da cfiyana daga
bauta wa gumaka.
36. "Ya Ubangijina! Lalle ne su,
sun Batar da masu yawa daga muta-
ne, sa'an nan wanda ya bi ni, to,
lalle shi, yana daga gare ni, kuma
wanda ya saBa mini, to, lalle ne Kai
Mai gafara ne, Mai jin kai.
37. "Ya Ubangijinmu! Lalle ne
ni, na zaunar da zuriyyata ga rafi
wanda ba ma'abucin shuka ba, a
wurin T)akinka, mai alfarma. Ya
Ubangijinmu ! Domin su tsayar da
salla. Sai Ka sanya zukata daga
mutane suna gaggawar begen zuwa
gare su, kuma ka arzuta su daga
'ya'yan itace, mai yiwuwa ne suna
godewa.
38. "Ya Ubangijinmu! Lalle ne
Kai, Kana sanin abin da muke
Boyewa, da abin da muke bayyana-
wa. Kuma babu abin da yake Boye-
wa ga Allah, daga wani abu a cikin
kasa, kuma babu a cikin sama.
39. "Godiya ta tabbata ga Allah
Wanda Yake Ya ba ni, ina a cikin
tsufa, Isma'ila da Is'haka. Lalle ne
Ubangijina, hakika, Mai jin addu'a
ne.
40. "Ya Ubangijina ! Ka sanya ni
mai tsayar da salla. Kuma daga
zuriyyata. Ya Ubangijinmu ! Kuma
Ka karbi addu'ata.
^j
(1) Wannan gari watau Makka. Ana tunatar da Larabawa ga kakansu Ibrahim da
addifar da ya yi saboda garin Makka da mutanen garin da cfiyan Isma'ila domin su
wa'aztu.
378
14 - Suratu Ibrahim
&SKIJ&-H
41. "Ya Ubangijinmu! Ka yi ga-
fara gare ni, kuma ga mahaifana,
kuma da muminai, a ranar da hisabi
yake tsayawa.
42. "Kuma kada ka yi zaton Al-
lah Mai shagala ne daga abin da
azzalumai suke aikatawa. Abin sani
kawai, Yana jinkirta musu ne zuwa
ga wani wuni, wanda idanuwa suke
fita turu-turu a cikinsa.
43. "Suna masu gaggawa, masu
cfaukaka kawunansu zuwa sama,
kiftawar ganinsu ba ta komawa
gare su. Kuma zukatansu wofin-
tattu." (1)
44. Kuma ka yi gargacfi ga muta-
ne ga ranar da azaba take je musu,
sai wacfanda suka yi zalunci su ce,
"Ya Ubangijinmu! Ka yi mana jin-
kiri zuwa ga wani ajali makusanci,
mu kar6a wa kiranKa, kuma mu bi
Manzanni." (Allah Ya ce musu)
"Ashe, ba ku kasance kun yi rantsu-
wa ba daga gabani, cewa ba ku da
wata gushewa?
45. "Kuma kuka zauna a cikin
gidajen wacfanda suka zalunci kan-
su, kuma ya bayyana a gare ku
yadda Muka aikata game da su,
kuma Muka buga muku misalai."
46. Kuma lalle sun yi makirci
irin makircinsu, kuma a wurin Al-
lah makircinsu yake, kumajalle ne
makircinsu ya kasance, haklka, du-
watsu suna gushewa saboda shi.
\>'A
H\
4^3
(1) A nan ne iyakar maganar shugabanmu Ibrahim da addu'arsa.
379
14 — Suratu Ibrahim
smm-n
47. Saboda haka, kada ka kar-
fafa zaton Allah Mai saBa wa'adin-
Sa ne ga ManzanninSa. Lalle ne
Allah ne Mabuwayi, Ma'abucin
azabar ramuwa.
48. A ranar da ake musanya
kasa (1) , ba kasar nan ba, da sammai
kuma su bayyana ga Allah Maka-
daici, Mai tankwasawa.
49. Kuma kana ganin masu laifi,
a ranar nan, suna wadanda aka yi
wa ciri daidai a cikin maruruwa.
50. Rigunansu daga farar wuta
ne, kuma wuta ta rufe fuskokinsu.
51. Domin Allah Ya saka wa
kowane rai da abin da ya tsuwur-
wurta. Lalle ne, Allah Mai gag-
gawar hisabi ne.
52. Wannan iyarwa ce ga muta-
ne, kuma domin a yi musu gargacfi
da shi, kuma domin su sani cewa,
abin sani kawai, ShT ne abin bauta-
wa guda. Kuma domin masu han-
kali su rika tunawa.
Je.
(jy^jo
°i
^^&±h%&&&
( 1 ) A Ranar ICiyama Allah zai musanya kasa da sama a kawo wacfansu a lokacin da
mutane suke a kan siracfi kamar yadda ya zo a Hadisi.
380
15 - Suratul Hijr
-\o
Tana karantar da wa'azi da umurnin wa'azi da haicuri da
jarumtaka, saboda Allah Ya yi alkawarin halaka masu izgili ga
masu wa'azi na gaskiya, kuma masu gyara su ne tsayuwar aFumma;
dukan musun gaskiya izgili ne.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. A.L.R. Wacfancan ayoyin lit-
tafi ne da abin karantawa mai
bayyanawa.
2. Da yawa wadanda suka ka-
firta suke gurin da dai sun kasance
Musulmi. (1)
3. Ka bar su, su ci kuma su ji
dadi, kuma guri ya shagaltar da su,
sa'an nan da sannu za su sani.
4. Kuma ba Mu halakar da wata
alkarya ba face tana da littafi
sananne.
5. Wata aFumma ba ta gabatar
ajalinta, kuma ba za su jinkirta ba.
> s >
^^j\c^j^^z^\^y^J\
(1) Kowane kafiri yana gurin ya zama Musulmi domin abin da yake gani na shiriya
da ladubban Musulunci, wadanda ya tabbata babu zama lafiya ga mutum face idan ya
same su, amma Shaidan yana hana shi musulunta saboda wadansu dalTlai da yake sanyawa
a ganinsa.
381
15 - Suratul Hijr
rzrw&A.
mm-»
6. Suka ce, "Ya kai wanda aka
saukar da Ambato (Alkur'ani) a
kansa ! Lalle ne kai, hakika, mahau-
kaci ne.
7. "Domin me ba za ka zo mana
da mala'iku ba idan ka kasance
daga masu gaskiya?"
8. Ba Mu sassaukar da mala'iku
face da gaskiya, (1) ba za su kasance,
a wannan lokacin, wadanda ake yi
wa jinkiri ba.
9. Lalle Mu ne, Muka saukar da
Ambato JAlkur'ani), kuma lalle
Mu, hakika, Masu kiyayewa ne
gare shi.
10. Kuma lalle ne, hakika, Mun
aika manzanni a cikin kungiyoyin
farko, gabaninka.
11. Kuma wani Manzo ba ya
zuwa gare su face sun kasance suna
masu izgili a gare shi.
12. Kamar wancan ne Muke shi-
gar da shi (2) a cikin zukatan masu
laifi.
13. Ba^su yin Tmani da shi, (3)
kuma hakika, hanyar mutanen far-
ko ta shige.
14. Kuma da Mun burfe wata
kofa daga sama a kansu har suka
wuni a ciki suna takawa.
15. Lalle ne da sun ce, "Abin sani
kawai, an rufe idanuwanmu ne.
Qp ^j£&K~>Jb <4 >4$OLLi ^-A3
(1) Gaskiya a nan ana nufin azaba domin zuwanta tabbatacce ne. Dukan abin da yake
tabbatacce shT ne hakkun, watau gaskiya.
(2) Shirki da kafirci da karyatawa, su duka izgili ne da addini.
(3) Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Hanyar mutanen farko ta
karyata Manzanni har a lokacin da Allah zai halaka su da azabarSa.
382
15 - Siiratul Hijr
mm-*
AV mu mutane ne wacfanda aka
sihirce."
16. Kuma lalle ne, hakika, Mun
sanya wacfansu masaukai a cikin
sama, kuma Muka kawata ta ga
masu kallo.
17. Kuma Muka kiyaye ta daga
dukan shaidani wanda ake jlfa.
18. Face wanda ya sari saurare^
sai wutar yula bayyananniya ta bi
shi.
19. Kuma kasa Mun mike ta,
kuma Mun jefa duwatsu tabbatattu
a cikinta, kuma Mun tsirar, a cikin-
ta, daga dukan abu wanda ake
aunawa da sikeli.
20. Kuma Muka sanya muku, a
cikinta, abubuwan rayuwa (1) da
wanda ba ku zama masu ciyarwa
gare shi ba.
21. Kuma babu wani abu face, a
wurinMu, akwai taskokinsa, kuma
ba Mu saukar da shi ba face a kan
gwargwado sananne.
22. Kuma Muka aika iskoki
masu barbarar juna, sa'an nan
Muka saukar da ruwa daga sama,
sa'an nan Muka shayar da ku shi,
kuma ba ku zama masu taskacewa a
gare shi ba.
23. Kuma lalle ne Mu Muke
rayarwa, kuma Muke kashewa,
kuma Mu ne magada.
V$L^>jj ^rjyt ^u-— J ' <j& ^-1*^ ailj
^T> f^s^f
&^\&}A&Q£Q\\&>5
' '"\(&1
.j\j
y y
•. \ ^\^jC^Sy - J^U^J ^\j
( 1 ) Muka sanya muku abubuwan rayuwa a cikinta, kuma Muka mallaka muku bayi
wadanda suke ba ku ne kuke cij^ar da su ba, Mu ne ke ciyar da su game da ku duka. Watau
aza abubuwa a kan ma'auni shi ne maslaha rashin yarda da tsaron ma'aunin nan shi ne
izgili.
383
15 - Suratul Hijr
$££%&-**
24. Kuma lalle ne, hakTka, Mun
san masu gabata daga cikinku,
kuma Mun san masu jinkiri.
25. Kuma lalle ne Ubangijinka
Shine Yake tara su, lalle Shine Mai
hikima, Masani.
26. Kuma lalle ne, Mun halicci
mutum daga kekasasshiyar laka,
daga bakin yum6u wanda ya canja.
27. Kuma aljani, Mun halicce
shi daga gabani, daga wutar (1) iskar
zafl.
28. Kuma a lokacin da Ubangi-
jinka ya ce wa mala'iku "Lalle NT,
mai halittar wani jiki ne daga
kekasasshen yumBu wanda ya
canja.
29. "To, idan Na daidaita shi,
kuma Na hiira daga RuhTNa (2) a
cikinsa, to, ku facfi a gare shi, kuna
masu yin sujada."
30. Sai mala'iku suka yi sujada
dukansu gaba daya.
31. Face IblTs, ya ki kasancewa
daga masu yin sujadar.
32. Ya ce, "Ya IblTs, mene ne a
gare ka, ba ka kasance tare da masu
yin sujuda ba?"
fcj Oyt^l rt44^=» 4XIU I -W*-3
4 f^^ ^>^ -S
(1) Halittar Adamu daga yumBu £e£asasshe, ya fi daraja bisa halittar Shaidan daga
harshen wuta, domin wuta tana nuni ga sassabcin hankali da rashin natsuwa.
(2) Wannan ^a nuna Adamu an yi halittarsa ne da laka da Ruhi daga Allah kamar
yadda aka halitta Isa, amincin Allahjra tabbata a gare shi. Saboda haka halittar Adamu ta
fi zama abin mamaki daga halittar Isa, domin Isa asali guda kawai ya rasa daga halittar
cfiyan Adam ta al'ada, amma halittar Adamu ta rasa dukan asalan biyu na uwa da na uba.
Haka kuma halittar Hawwa'u, matar Adamu ta fi ta Isa ban mamaki domin rashin asalin
uwa da ta yi inda da yake daukar lokacin surantawa, ya fi ban mamaki daga rashin asalin
uba.
384
15 - Siiratul Hijr
:n m-"
33. Ya ce, "Ban kasance ina yin
sujada ba ga mutum wanda Ka
halicce shi daga busasshen yum-
6un laka wadda ta canja."
34. Ya ce, "To, ka fita daga gare
ta, domin lalle kai abin jlfa ne.
35. "Kuma lalle ne akwai la'ana
a kanka har ya zuwa ranar saka-
mako."
36. Ya ce, "Ya Ubangijlha! Sai
Ka yi mini jinkiri zuwa ranar da ake
tashe su."
37. Ya ce, "To, lalle ne kana daga
wadanda ake yi wa jinkiri.
38. "Zuwa ga yinin lokacin nan
sananne."
39. Ya ce, "Ya Ubangijina! Ina
rantsuwa da abin da Ka batar da ni
da shi, haioka, ina kawata musu
(rayuwa) a cikin kasa kuma hakika
ina batar da su gaba daya.
40. "Face bayinKa daga gare su,
wadanda Ka tsarkake."
41. Ya ce, "Wannan tafarki ne a
gare Ni, madaidaici.
42. "Lalle ne bayiNa, ba ka da
Tko a kansu, face wanda ya bl ka
daga batattu."
43. Kuma lalle Jahannama ce,
hakika, ma'alkawartarsu gaba
daya.
44. Tana da kofofi bakwai, (1) ga
kowace kofa akwai wani juz'i daga
gare su rababbe.
jjO^i^^;^^
>*f" "* '
© ^^^f^nj^^
© ##jk$^^$'Qy
^J
Jli
^JSXV^&\^yi
(1) Kofofin Jahannama bakwai ne, watau dabakokinta, ta farko ita ce Jahannama,
sa'an nan Lazza, sa'an nan Alhudama, sa'an nan Assa'Tra, sa'an nan Sakar, sa'an nan
385
15 - Suratul Hijr
AQU^-*
45. Lalle masu takawa suna a
cikin gidajen Aljanna mai idan-
dunan ruwa.
46. "Ku shige ta da aminci, kuna
amintattu."
47. Kuma Muka debe abin da ke
a cikin zukatansu na daga kullin
zuci, suka zama 'yan'uwa a kan
gadaje, suna masu fuskantar juna.
48. Wata wahala ba za ta shafe
su ba a cikinta, kuma ba su zama
masu fita daga cikinta ba.
49. Ka bai wa baylNa labari
cewa lalle ne Ni, Mai gafara ne, Mai
jin kai.
50. Kuma azabaTa ita ce azaba
mai ratfacfi.
J/._Kuma ka ba su labarin bakin
Ibrahim.
52. A lokacin da suka shiga gun-
sa, sai suka ce, "Sallama." Ya ce,
"Lalle mu, daga gare ku, masu
flrgita ne."
53. Suka ce, "Kada ka flrgita.
Lalle ne mu, muna yi maka bushara
game da wani yaro masani."
54. Ya ce, "Shin, kun ba ni bu-
shara (1) ne a kan tsufa ya shafe ni?
To, da me kuke ba ni bushara?"
IP <>_i^s-^4oM^Cl4
*^ ' \ '
E|04^-1aI>--3
Aljahim, sa'an nan Alhawiya. Kowace tfabaka tana da juz'i sananne, watau kofa ga
Yahudu, wata ga Nasara, wata Saba'awa, wata ga Majusawa, wata ga Mushirikai, wata ga
munafukai, wata ga Musulmi wadanda aka yi musu hushi (mummunan aiki). Ana fatan fita
ga masu tauhTdi daga gare ta. Ba a fatan kome ga sauran, suna dawwama a cikinta har
abada.
(1) Ibrahim yana yi musu tambaya ne domin yana ganin kamar suna yi masa
magana ta izgili ne a kan samun da a bayan tsufansa da na matarsa. Saboda haka suka
gaya masa cewa su masu gaskiya ne.
386
15 - Sfiratul Hijr
«#j8£-w
55. Suka ce, "Muna yi maka
bushara da gaskiya ne, saboda
haka, kada da kasance daga masu
yanke tsammani."
56. Ya ce, "Kuma wane ne yake
yanke tsammani daga rahamar
Ubangijinsa, face 6atattu?"
57. Ya ce, "To, mene ne babban
aPamarinku? Ya ku manzanni!"
58. Suka ce, "Lalle ne mu, an
aika mu zuwa ga wasu mutane
masu laifi.
59. "Face mutanen Ludu, lalle
ne mu, hakTka, masu tsTrar da su
ne gaba daya.
60. "Face matarsa^ mun kaddara
cewa lalle ne ita, haklka, tana daga
masu halaka."
61. To, a lokacin da manzannin
suka je wa mutanen Ludu,
62. Ya ce, "Lalle ne ku mutane
ne wadanda ba a sani ba."
63. Suka ce, "A'a, mun zo maka
saboda abin da suka kasance suna
shakka a cikinsa.
64. "Kuma mun zo maka^da
gaskiya. Kuma lalle ne mu, hakika,
masu gaskiya ne.
65. "Sai ka yi tafiya da iyalinka,
a wani yanki na dare, kuma ka bi
bayansu, kuma kada wani daga
cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi
ta inda aka aumurce ku."
66. Kuma Muka hukunta wan-
can al'amarin zuwa gare shi cewa
lalle ne karshen wadancan abin
yankewa ne a lokacin da suke masu
shiga asuba.
/<,<. •-'x-rr ''Sts
lid
*>"£» Its I 1f/„
387
15 - Suratul Hijr
&M&-V
67. Kuma mutanen alkaryar
suka je suna masu bushara.
68. Ya ce, "Lalle ne wacfannan
baklna ne, saboda haka kada ku
kunyata ni.
69. "Kuma ku bi Allah da ta-
kawa, kuma kada ku sanya ni a
bakin ciki."
70. Suka ce, "Ashe ba mu hana
ka daga talikai ba?"
71. Ya ce, "Ga wadannan 'ya'ya-
na (1) idan kun kasance masu aika-
tawa ne."
72. Rantsuwa da (2) rayuwarka!
Lalle ne su a cikin mayensu suna ta
cfimuwa.
73. Sa'an nan tsawa ta kama su,
suna masu shiga lokacin hudowar
rana.
74. Sa'an nan Muka sanya sa-
manta ya koma kasanta, kuma
Muka yi ruwan duwatsu na lakar
wuta a kansu.
75. Lalle ne a cikin wancan ak-
wai ayoyi ga masu tsokaci da
hankali.
76. Kuma lalle ne ita, hakika,
suna a gefen wata hanya tabba-
tacciya. (3)
77. Lalle ne a cikin wancan ak-
wai aya ga masu imani.
(jjp OJ^Cli A^t JJ* JJ* iU,
* *w^*u *-*•('
©pJLH^^J^ 1 \>&j
frftAj^
Ep>^ Jrv^ W^>
$ u&£$$^* &i
(1) Yana nufin matan garin, domin Annabin mutane shi ne ubansu.
(2) Allah Ya yi rantsuwa da rayuwar Annabi Muhammadu, tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi. Wannan shT ne matuicar girmamawa wadda Allah Yake yi wa mutum.
Kuma yana nuna cewa rayuwar Annabi tana da muhimmanci Rwarai.
(3) Hanya tabbatacciya ta mutanen Makka zuwa Syria (Sham).
388
15 - Suratul Hijr
mm-\>
78. Kuma lalle ne ma'abuta Al'-
aika (1) sun kasance, hakSca, masu
zalunci !
79. Sai Muka yi azabar ramuwa
a gare su, kuma lalle su biyun,
haklka, suna a gefen wani tafarki
mabayyani.
80. Kuma lalle ne, hakTka,
ma'abuta Hijiri (2) sun karyata
Manzanni.
81. Kuma Muka kai musu
ayoyinMu, sai suka kasance masu
bijirewa daga gare su.
82. Kuma sun kasance suna sas-
saka gidaje daga duwatsu, alhali
suna amintattu.
83. Sai tsawa ta kama su, suna
masu shiga asuba.
84. Sa'an nan abin da suka ka-
sance suna tsirfantawa bai wadatar
ga barinsu ba.
85. Kuma ba M u halicci sammai
da Rasa da abin da yake a tsaka-
ninsu ba face da gaskiya. Kuma
lalle^ ne Sa'a (Ranar Alkiyama)
hakTka, mai zuwa ce. Saboda haka
ka yi rangwame, rangwame mai
kyau.
86. Lalle ne Ubangijinka, Shi ne
Mai yawan halitta, Masani.
87. Kuma lalle ne, haloka, Mun
ba ka bakwai watfanda ake karan-
tawa (3) da Alkur'ani mai girma.
m c*^&$\£&&&
f\p o^?*>£U u^lj l^u Llii;li
' ^'^'<
&cjC£\JS\^\^X&;
Gp ^-^^^4^.4^ ^ly^y^y^y^J
69 Ojy*£^\?vUft^^\\J
[«j.vJsU«L^J\
t& > r&sri£Z&
(1) Ma'abuta Al'aika, su ne mutanen Shu'aibu.
(2) Ma'abuta Hijiri, su ne Samudawa.
(3) Bakwai wadanda ake karantawa su ne Fatiha mai ayoyi bakwai. Ana karanta su a
cikin kowace raka'a ta salla.
389
15 - Suratul Hijr
^^->°
88. Kada lalle ka mika idanunka
biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da
su dacfi game da shi, nau'i-nau'i a
gare su, kuma kada ka yi bakin ciki
a kansu, kuma sassauta fikafikanka
ga masu imani.
89. Kuma ka ce, "Lalle nl, ni ne
mai gargacfi bayyananne."
90. Kamar yadda Muka saukar
a kan masu yin rantsuwa, (1)
91. Wacfanda suka sanya Alku-
r'ani tatsuniyoyi.
92. To, rantsuwa da Ubangi-
jinka! (2) HakTka, Muna tambayar
su gaba cfaya.
93. Daga abin da suka kasance
suna aikatawa.
94. Sai ka tsage gaskiya game da
abin da ake umurnin ka, kuma ka
kau da kai daga masu shirki.
95. Lalle ne Mu, Mun isar maka
daga masu (3) izgili.
96. Wacfanda suke sanyawar
wani abin bautawa na dabam tare
m *A~9rjj\ ^LiL»U J^JCl^ o ji£ *
6P ui-^o^^^!y*-^ui•^
u*
(1) Masu rantsuwa a kan saba wa Annabawa, watau kamar sun yi rantsuwa cewa ba
za su bi abin da Annabawa suka zo da shi ba. Watau su ne masu tsananin izgili da addini.
(2) Allah Ya yi rantsuwa da ZatinSa a kan Shi ne Ubangijin Annabi Muhammadu
tsTra da aminci su tabbata a gare shi, domin Ya natsar da ransa daga tsoron masu yi masa
izgili, kuma domin Ya karfafa shi ga zartar da aikin da Ya sanya shi na iyar da Manzanci,
ba da wata fargaba ba.
(3) Masu tsananin izgili ga Annabi wacfanda Allah Ya isar masa daga gare su. Su
biyar ne, daga Bani Asad bn Abdul'uzza bn Kusayyi akwai Aswadu bn el Muttalib, Abu
Zamah, kuma daga Bani Zuhrah akwai el Aswad bn Abdu Yaguth. Daga Bani Makhzumi
akwai el Walid bn Mugira. Daga Bani Sahmi akwai el As bn Wa'il. Daga Ban! Khuza'a
akwai el Harith bn el Tulatilah. Su ne masu darajar mutanensu. A lokacin da suka doge da
sharri, Allah Ya hutar da Annabi daga^sharrinsu da nau'i-nau'i na masifu, suka halaka.
Dubi karin bayani daga tafsirin bn Kathir. Tsare Annabi daga gare su tun yana shi kacfai a
Makka ya isa ya sanya shi ya dogara ga Allah bayan abubuwa sun kara yawa da sauki.
390
15 - Suratul Hijr
SOTS£-N
da Allah, sa'an nan da sannu za su
sani.
97. Kuma lalle ne, hakika, Muna
sanin cewa lalle kai, kirjinka yana
yin kunci game da abin da suke facfa
(na izgili).
98. Saboda haka ka yi tasbihi
game da gode wa Ubangijinka,
kuma ka kasance daga masu
sujada.
99. Kuma ka bauta wa Ubangi-
jinka, har mutuwa ta zo maka.
>-r»^ y *o"
lip OW ' ^V ^l^^J -M^b
Tana karantar da ni'imomin da Allah Ya bai wa mutum daga
halittarsa, da abincinsa da shiryarwar da Ya yi masa, da hankalin da
Ya ba shi, domin ya kacfaita Shi da bautarSa, har zuwa ga ni'imomin
Lahira ga wanda ya shiryu.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Umurnin Allah ya zo, saboda
haka kada ku nemi hanzartawarsa.
Tsarkin Allah ya tabbata, kuma Ya
daukaka daga abin da suke yi na
shirka.
ZS£j&*
391
16 - Suratun Nahl
Wti&-n
2. Yana sassaukar da mala'iku
da Ruhi (1) daga umurninSa a kan
wanda Yake so daga bayinSa, cewa
ku yi gargacfi cewa: Lalle ne shT,
babu abin bautawa face Ni, saboda
haka ku bl Ni da takawa.
3. Ya halicci sammai da kasa da
gaskiya. Ya cfaukaka daga abin da
suke yi na shirka.
4. Ya halicci mutum daga ma-
niyyi, sai ga shi yana mai husuma
bayyananniya.
5. Da dabbobin ni'ima, Ya halio
ce su dominku. A cikinsu akwai
abin yin cfimi da wacfansu amfano-
ni, kuma daga gare su kuke ci.
6. Kuma kuna da kyau a cikinsu
a lokacin da suke komowa daga
kiwo da maraice da lokacin da suke
sakuwa.
7. Kuma suna cfaukar kayanku
masu nauyi zuwa ga wani gari, ba
ku kasance masu isa gare shi ba,
face da tsananin wahalar rayuka.
Lalle ne Ubangijinka ne, haklka,
Mai tausayi, Mai jin kai.
8. Kuma da dawaki (2) da alfa-
darai da jakuna, domin ku hau su,
iOjj Ubj : fr-'=^_ > ^uI>JV^ J uJ)^ <j4=M-?
(1) Saukar da mala'iku da Ruhi watau Alkur'ani a zamanin Annabci ko kuma
fahimta da karfin zuciya wacfanda Allah kesanyawa ga wanda Ya nufa da jaddada addini a
kan kowane karni. Aiko masu gargacfi shi ne mail girman ni'imar Allah a kan mutane.
(2) Hada dawaki da alfadarai zuwa ga jakuna kuma aka ce domin "hawansu da yin
kawa" yana nuna cewa ba a cin dawaki da alfadarai, domin an san cewa an hana cin
jakuna a lokacin yakin Khaibara, kuma ayoyin da ke gaba da wannan aya sun nuna ana
cin dabbobin ni'ima kuma ana hawansu, kuma cin nama ya fi hawa zama ni'ima, saboda
haka, shi ne ya kamata a ambata inda ya halatta. Wannan ne mazhabar Maliki da Abu
HariTfa, kuma shi ne maganar Abdullah bn Abbas, Allah Ya yarda da su. Wasu sun ce ana
cin dawaki da alfadarai domin cewa ana "hawansu domin kawa" ba ya hana a yi wani abu
da su, wato cin namansu, domin a cikin Bukhari da Muslim an ruwaito halaccin cin
392
16 - Suratun Nahl
«&-n
kuma da kawa. Kuma Yana halitta
abin da ba ku sani ba.
9. Kuma ga Allah madaidaiciyar
hanya take kuma daga gare ta ak-
wai mai karkacewa. Kuma da Ya
so, da Ya shiryar da ku gaba daya.
10. Shi ne Wanda Ya saukar da
ruwa daga sama dominku, daga
gare shi akwai abin sha, kuma daga
gare shi itace yake, a cikinsa kuke
yin kiwo.
1 1 . Yana tsirar da shuka game da
shi, dominku, zaituni da dablnai da
inabai, kuma daga dukan 'ya'yan
itace. Lalle ne a cikin wancan, hakl-
ka, akwai aya ga mutane wadanda
suke yin tunani.
12. Kuma Ya hore muku dare da
wuni, da rana da wata, kuma tau-
rari horarru ne da umurninSa. Lalle
ne a cikin wancan, hakika, akwai
ayoyi ga mutane wadanda suke
hankalta.
13. Kuma abin da Ya halitta
muku a cikin kasa, yana mai sa-
6anin launukansa. Lalle ne a cikin
wancan, hakika, akwai aya ga mu-
tane wadanda suke tunawa.
*" ^ ' s»± -*
iijClifc <&1&<<j* &\zs$y>
dawaki. Wannan shi ne maganar Al-Hasan da Shuraih da ' Acfa'a da Sa'id bn Jubair. Kuma
shT ne mazhabar^Shafi'i da Is'haic. Sun yi hujja da halaccin naman dawaki da abin da
Asma'u bint Abi Bakar As-Siddik ta ce, "Mun soke wata gocfiya, muka ci, a zamanin
Manzon Allah, a Madina." Kuma a cikin Bukhari da Muslim daga Jabir, Allah Ya yarda
da shi, "Mun ci dawaki da jakunan jeji a Khaibara, kuma Annabi, tsira da aminci sun
tabbata a gare shi, ya hana jakunan gida". A cikin AbT Dawud, "Mun yanke dawaki da
alfadarai da jakuna alhali yunwa ta kama mu, amma sai Annabi ya hana mu cin jakuna da
alfadarai, bai hana mu cin dawaki ba". NT, a ganina, ra'ayin cin dawaki ya fi karfi, domin
surar ta sauka a Makka, amma hadisin yankan gocfiyar, a Madina aka yi shi. Saboda haka
surar ba ta shafe shi ba. Dubi Radd Al-Azhan.
393
16 - Suratun Nahl
mm-*
14. Kuma Shi ne Ya hore teku
domin ku ci wani nama sabo daga
gare shi, kuma kuna fitarwa, daga
gare shi, kawa wadda kuke yin ado
da ita. Kuma kuna ganin jirage
suna yankan ruwa a cikinsa kuma
domin ku yi neman (fatauci) daga
falalarSa. Kuma mai yiwuwa ne
kuna godewa.
15. Kuma Ya jefa, a cikin kasa,
tabbatattun duwatsu domin kada ta
karkata da ku, da koguna da hany-
yoyi, cfammaninku kuna shiryuwa.
16. Kuma da wacfansu alamomi,
kuma da taurari suna masu neman
shiryuwa (ga tafiyarsu ta fatauci).
1 7. Shin, Wanda Yake yin halitta
yana yin kama da wanda ba ya yin
halitta? Shin fa, ba ku tunawa?
18. Kuma idan kun kidaya
ni'imar Allah, ba ku iya lissafa ta.
Lalle ne Allah, haklka, Mai gafara
ne, Mai jin kai.
19. Kuma Allah Yana sanin abin
da kuke asirtawa da abin da kuke
bayyanawa.
20. Kuma wacfanda suke kira,
baicin Allah, ba su halicci kome ba,
kuma su ne ake halittawa.
21. Matattu ne, ba su da rai,
kuma ba su san a wane lokaci ake
tayar da su ba.
22. Abin bautawarku, abin bau-
tawa ne guda, to, wacfanda ba su yin
imani da Lahira, zukatansu masu
musu ne, kuma su makangara ne.
23. HakTka, lalle ne, Allah Yana
sanin abin da suke asirtawa da abin
>» 1 >l K <t'i y ->'*■?'
fc^ffi
-~—£j-h
f^l >' S 9 * *^\\ ' c ' '\"
lo^
iu** ]
* ft ^ ft
394
16 - Suratun Nahl
m\m-n
da suke bayyanawa. Lalle ne Shi, ba
Ya son masu girman kai.
24. Idan aka ce musu "Mene ne
Ubangijinku Ya saukar?" Sai su ce,
"Tatsuniyoyin mutanen farko."
25. Domin su cfauki zunubansu
cikakku a Ranar Kiyama, kuma
daga zunuban wacfanda suke 6atar-
wa ba da wani ilmi ba. To, abin da
suke cfauka na zunubi ya munana.
26. Lalle ne wacfanda suke a
gabaninsu sun yi makirci, sai Allah
Ya je wa gininsu daga harsa-
shensa, (1) sai rufi ya facfa a kansu
daga bisansu, kuma azaba ta je
musu daga inda ba su sani ba.
27. Sa'an nan a Ranar Kiyama
(Allah) Yana kunyata su, kuma
Yana cewa, "Ina abokan taray-
yaTa, wacfanda kuka kasance kuna
gaba a cikin cfaukaka sha'aninsu?"
Wacfanda aka bai wa ilmi suka ce,
"Lalle ne wulakanci a yau da cuta
sun tabbata a kan kafirai."
28. Wacfanda mala'iku suke kar-
6ar rayukansu suna masu zalun-
tar kansu. Sai suka jefa neman sul-
hu (suka ce) "Ba mu kasance muna
aikata wani mummunan aiki ba."
Kayya! Lalle Allah ne Masani ga
abin da kuka kasance kuna aika-
ta wa.
29. Sai ku shiga kofofin Jahan-
nama, kuna madawwama a cikinta.
Sa'an nan tir da mazaunin masu
girman kai.
>r 'iM&\
\yj \i lf~Ju\ ^yJ U* 4>j^i^^iy^ o^
</ c
>/ »^,s>
yj .^-^ o^ <J**-*j u«^=^ L« ^LnJ »
iilol
*»/->> i
"^ II ^^* " ^ X »| I M * I*
<JLr*
(1) Kamar yadda Allah Ya halaka Bukht Nasar. Aka halaka shi da ginin gidansa.
Allah Yana halaka kafirai da abin da suke tanada wa kansu domin neman rayuwarsu.
395
16 - Suratun Nahl
«&-n
30. Kuma aka ce wa wacfanda
suka yi takawa, "Mene ne Ubangi-
jinku Ya saukar?" Suka ce, "Alheri
Ya saukar, ga wacfanda suka kyau-
tata a cikin wannan duniya akwai
wani abu mai kyau, kuma hakika,
Lahira ce mafi allien." Kuma haki-
ka, madalla da gidan masu takawa.
31. Gidajen Aljannar zama, suna
shigarsu, koramu suna gudana
daga karkashinsu, suna da abin da
suke so a cikinsu. Kamar haka Al-
lah ke saka wa masu takawa.
32. Wacfanda mala'iku suke
karBar rayukansu suna masu jin
dacfin rai, mala'ikun suna cewa.
"Aminci ya tabbata a kanku. Ku
shiga Aljanna saboda abin da kuka
kasance kuna aikata wa."
33. Shin, suna jiran wani abu?
Face mala'iku su je musu ko kuwa
umurnin Ubangijinka. Kamar
wancan ne wacfanda suke a gaba-
ninsu, suka aikata. Kuma Allah
bai zalunce su ba, kuma amma
kansu suka kasance suna zalunta.
34. Sai munanan abubuwan da
suka aikata ya same su, kuma abin
da suka kasance suna yi na izgili ya
wajaba a kansu.
35. Kuma wacfanda suka yi shir-
ki suka ce, "Da Allah Ya so, da ba
mu bauta wa kome ba, baicinSa, mu,
ko ubannimmu kuma da ba mu
haramta kome ba, baicin abin da Ya
haramta." Kamar wancan ne wa-
cfanda suke a gabaninsu suka aika-
ta. To, shin, akwai wani abu a kan
Manzanni, face iyarwa bayya-
nanniya?
\> '\
► C " >>
pL^4^ I ^-ot^S/P- ^rJ^ ■*£-** ci*.
i^\ '. ^ < ~* fa\" - * ' ut \* *vfa 'S
|*p ojLSti^^a Lo aL>JI \yiol ScSc
396
16 - Suratun Nahl
m\m-*
36. Kuma lalle ne, haklka, Mun
aika a cikin kowace al'umma da
wani Manzo (ya ce), "Ku bauta wa
Allah, kuma ku msanci T)agutu."
To, daga gare su akwai wanda Al-
lah Ya shiryar, kuma daga cikinsu
akwai wanda 6ata ta wajaba a kan-
sa. Sai ku yi tafiya a cikin kasa,
sa'an nan ku duba yadda akibar
masu karyatawa ta kasance.
37. Idan ka yi kwacfayi a kan
shiryuwarsu, to, lalle ne, Allah ba
Ya shiryar da wanda yake batarwa,
kuma ba su da wadansu matai-
maka.
38. Kuma suka rantse da Allah
iyakar rantsuwarsu (cewa) Allah ba
ya tayar da wanda yake mutuwa!
Na'am, Yana tayarwa. Wa'adi ne
(Allah) Ya yi a kanSa tabbatacce,
kuma amma mafi yawan mutane ba
su sani ba.
39. Domin Ya bayyana musu
abin da suke saBa wa juna a cikinsa,
kuma domin wacfanda suka kafirta
su sani cewa lalle su ne suka kasance
makaryata.
40. Abin sani kawai, Maganar-
Mu ga wani abu idan Mun nufe shi,
Mu ce masa, "Ka kasance," sai
yana kasancewa.
41. Kuma wacfanda suka yi hiji-
ra a cikin sha'anin Allah daga
bayan an zalunce su, haklka Muna
zaunar da su a cikin duniya da
alheri, kuma lalle ladar Lahira ce
mafi girma, da sun kasance suna
sani.
\^\^^y^^^^x^j
Oj U>- 4^P \ J&J ^> CjJ^i 4>*
i^\ ' • >*> \*. & 'SACK'S
E3 c££^-=*)yb tt"jj&
j>'u^^%0^^^l
>^
X
■&a
397
16 - Suratun Nahl
mm-*
42. Wacfanda suka yi hakuri,
kuma ga Ubangijinsu suke dogara.
43. Kuma ba Mu aika daga
gabaninka ba, face wacfansu mazaje
Muna yin wahayi zuwa gare su. Sai
ku tambayi mutanen Ambato idan
kun kasance ba ku sani ba.
44. Da hujjoji bayyanannu da
littattafai, kuma Mun saukar da
Ambato zuwa gare ka, domin ka
bayyana wa mutane abin da aka
sassaukar zuwa gare su, kuma don
dammaninsu su yi tunani.
45. Shin fa, wadanda suka yi
makircin munanan ayyuka sun
amince da Allah, ba zai shafe kasa
dominsu ba, ko kuwa azaba ba za ta
je musu daga inda ba su sani ba?
46. Ko kuwa Ya kama su a cikin
jujjuyawarsu? Saboda haka ba su
zama masu buwaya ba.
47. Ko kuwa Ya kama su & kan
nakasa? To, lalle ne Ubangijinka
haioka Mai tausayi ne, Mai jin kai.
48. Shin, ba su lura ba da abin da
Allah Ya halitta, ko mene ne, inu-
woyinsu suna karkata daga dama
da wajajen hagu, suna masu sujada
ga Allah, alhali suna masu £as-
kantar da kai?
49. Kuma ga Allah, abin da yake
a cikin sammai da kasa na dabba da
mala'iku, suke yin sujada, kuma ba
su kangara.
50. Suna tsoron Ubangijinsu
daga bisansu, kuma suna aikata
abin da ake umurnin su.
398
16 - Suratun Nahl
&-v\
51. Kuma Allah Yace, "Kadaku
ri£i abubuwan bautawa biyu. Abin
sani kawai, Wanda ake bautawa
guda ne, sa'an nan sai ku ji tsoroNa,
Ni kawai."
52. Kuma Yana da abin da yake
a ci k i n sammai da £asa, kuma Yana
da addini wanda yake dawwa-
mamme. Shin fa, wanin Allah kuke
bT da takawa?
53. Kumaabindayakeagareku
na ni'ima, to, daga Allah ne. Sa'an
nan kuma idan cuta ta shafe ku, to,
zuwa gare Shi kuke hargowa.
54. Sa'an nan idan Ya kuranye
cutar daga gare ku, sai ga wani
bangare daga gare ku game da
Ubangijinsu suna shirki.
55. Domin su kafirta da abin da
Muka ba su. To, ku ji dadi, sa'an
nan da sannu za ku sani.
56. Kuma suna sanya rabo (l) ga
abin da ba su sani ba daga abin da
Muka arzuta su. Ranstuwa da Al-
lah! Lalle ne za a tambaye ku daga
abin da kuka kasance kuna kir-
kirawa.
57. Kuma suna danganta ^ya'ya
mata ga Allah. TsarkinSa ya tabba-
ta! Kuma su ne da abin da suke
sha'awa.
**.'>!
&*}&&
( 1 ) Suna sanya war rabo daga dabbobi da hatsi ga gumaka ko aljannu, alhali ba su san
amfanin da gumakan ko aljannun suke iya jawo musu ba ko suke tunkudewa daga gare su.
Akwai daga cikin nTimomin Allah, Ya shiryar da mutane ga gane cewa wadannan gumaka
da aljannu ko wani mahaluki ba ya iya cuta ko jawo wani amfani face da iznin Allah.
Saboda haka babu wanda ya cancanci a bauta masa face Allah, Mai tum6uke cuta kuma
Mai jawo amfani. Watau wannan bayar da nfimar 'yancin dan Adam kamilan, su duka
bayi ne, babu daraja ga kowa sai da takawa. Sanin haka wata nfima ce daga Allah.
399
16 - Suratun Nahl
mm-*
58. Kuma idan aka yi wa cfa-
yansu bushara da mace (1) sai fus-
karsa ta wuni baka kirin, alhali
kuwa yana mai cike da bakin ciki.
59. Yana 66yewa daga mutane
domin munin abin da aka yi masa
bushara da shi. Shin, zai rike shi a
kan wulakanci, ko zai turBude shi a
cikin turbaya? To, abin da suke
hukuntawa ya munana.
60. Ga wadanda ba su yi ima-
ni (2) da Lahira ba akwai sifar cuta,
kuma ga Allah akwai sifa mafi dau-
kaka. Kuma Shi ne Mabuwayi, Mai
hikima.
61. Kuma da Allah Yana kama
mutane da zaluncinsu, (3) da bai
bar wata dabba ba a kan kasa.
Kuma amma Yana jinkirta musu
zuwa ga ajali ambatacce. Sa'an nan
idan ajalinsu ya zo, ba za a yi musu
jinkiri ba ko da sa'a guda, kuma ba
za su gabata ba.
62. Kuma suna sanya wa Allah
abin da suke ki, kuma harsunansu
na siffanta karya cewa lalle ne suna
da abubuwa masu kyau. Babu
shakka, lalle ne suna da wuta, kuma
lalle su, wadanda ake kyalewa ne (a
cikinta).
63. Rantsuwar Allah! Lalle ne
hakika Mun aika zuwa ga al'um-
s."s *>
j*\J iU3^ JL-J JJj} I j^^-jj Jhdj
s.wf **
JpOyl»yli »f^_*^l2H Jl^t
( 1 ) Fahintar cewa da namiji da 'ya mace duka daya suke, da hana kashe su ko turbude
su, wata ni'ima ce babba da 'yancin mata babba, a cikin rayuwar dan Adam.
(2) Karin bayani ne ga abin da ya gabata kuma na bay a da shi ya ratayu da shi.
Shiryarwa zuwa ga halaye madaukaka ni'ima ce babba.
(3) Rashin halaka duniya saboda laifin mutane da rashin kama su da dukan laifinsu,
ni'ima ce babba.
400
16 - Suratun Nahl
mm-*
momi daga gabaninka, sai Shairfan
ya kawacejnusu ayyukansu, sabo-
da haka shi ne majibincinsu, a yau,
kuma suna da azaba mai radacfi.
64. Lalle ba Mu saukar da Littafi
ba a kanka, face domin ka bayyana
musu abin da suka saba wa juna a
cikinsa, kuma domin shiriya da
rahama ga mutane warfanda suke
yin Tmani.
65. Kuma Allah Ya saukar da
ruwa daga sama, sa'an nan Ya rayar
da kasa da shi a bayan mutuwarta.
Lalle ne a cikin wannan, haklka
akwai aya ga mutane warfanda suke
saurare.
66. Kuma lalle ne, kuna da abin
lura a cikin dabbobin ni'ima ; Muna
shayar da ku daga abin da yake a
cikin cikunansu, daga tsakanin tu-
kar tumbi da jini, nono tsantsan,
mai saukin hacfiya ga masu sha.
67. Kuma daga 'ya'yan itacen
dabmo da inabai. Kuna samu daga
gare shi, abin maye (1) da abinci mai
kyau. Lalle a cikin wannan, hakika,
akwai aya ga mutane warfanda suke
hankalta.
68. Kuma Ubangijinka Ya yi
wahayi (2) zuwa ga kudan zuma
: V M
±&ja>, j l>^ili *jsj&j£jqx IciyOob
^.^O-^cJj^U^^J
(1) Ya ambaci abin maye a cikin abubuwan ni'ima a gabanin a haramta giya. Kuma
haramta ta ba ya hana ta zama a cikin ni'imomin Allah ga mutane domin an haramta ne
saboda tsaron hankalinmu a kan neman wacfansu ni'imomin da suka fi ta a Aljanna a inda
ba za a hana ta ba saboda karewar taklifi a can. Saboda haka ne ya kare ayar da cewa ;
"Akwai aya ga mutane wadanda suke hankalta."
(2) Wahayi na ilhama, watau Allah Ya cusa wa kudan zama ilmin yin sa kar gidan
zuma da gane hanyoyin tafiya ta koma gidanta, da cin kowane iri furen itace domin a fitar
da ni'imar abin sha mai dacfi ga mutane, kuma wanda ya kunsa dukan magani ga
ciwarwatansu. Wannan ni'ima ce babba.
401
16 - Suratun Nahl
mm-*
cewa; "Ki riki gidaje daga duwatsu,
kuma daga itace, kuma daga abin
da suke ginawa.
69. "Sa'an nan ki ci daga dukan
'ya'yan itace, saboda haka ki shiga
hanyoyin Ubangijinki, suna
horarru." Wani abin sha yana fita
daga cikunanta, mai sa6awar
launukansa, a cikinsa akwai wata
warkewa ga mutane. Lalle ne, a
cikin wannan, hakika, akwai ayoyi
ga mutane wadanda suke yin
tunani.
70. Kuma Allah ne Ya halicce
ku, sa'an nan Yana karbar rayu-
kanku, kuma daga gare ku akwai
wanda ake mayarwa zuwa ga mafi
RasRancin rayuwa, domin kada ya
san kome a bayan da ya zama mai
ilmi. Lalle Allah ne Masani, Mai
Tkon yi.
71. Kuma Allah Ya fifita sashen-
ku (1) a kan sashejaarziki. Sa'an nan
wadanda aka fifita, ba su zama
masu mayar da arzikinsu a kan abin
da hannayensu na dama suka mal-
laka ba, har su zama daidai a cikin-
sa. Shin fa, da ni'imar Allah suke
musu?
72. Kuma Allah Ya sanya muku
matan aure daga kawunanku,
kuma Ya sanya muku daga matan
aurenku diya da jTkoki, kuma Ya
arzuta ku daga abubuwa masu
(1) Arziki daga Allah yake, yana fifita wacfansu bayinSa da arziki a kan wadansu,
Sa'an nan wanda aka bai wa arziki daga cikinsu ba ya iya mayar da arzikin a tsakaninsa da
wani bawa nasa har su zama daidai a kan arzikin. To, idan haka ne, yaya kuke sanya
wadansu bayin Allah daidai da Allah wajen bautarku gare su?
402
16 - Suratun Nahl
mm-*
dacfi. Shin fa, da karya suke yin
imani, kuma da ni'imar Allah su,
suke kafirta?
73. Kuma suna bauta wa, baicin
Allah, abin da yake ba ya mallakar
wani arziki dominsu, daga sammai
da kasa game da kome, kuma ba su
iyawa (ga aikata kome).
74. Sa'an nan kada ku bayar da
wacfansu misalai ga Allah. Lalle ne
Allah Yana sani, kuma ku, ba ku
sani ba.
75. Allah Ya buga wani misali da
wani bawa wanda ba ya iya samun
iko a kan yin kome, da (wani bawa)
wanda Muka arzuta shi daga gare
Mu da arziki mai kyau. Sa'an nan
shT yana ciyarwa daga arzikin, a
asirce da bayyane. Shin suna dai-
daita? Godiya ta tabbata ga Allah.
A'a mafi yawansu ba su sani ba.
76. Kuma Allah Ya buga wani
misali, maza biyu, cfayansu bebe ne,
ba ya i^a samun ikon yin kome,
kuma shTnauyi ne a kan mai malla-
karsa, inda duk ya fuskantar da shi,
ba ya zuwa da wani alheri. Shin,
yana daidaita, shi da (namiji na
biyu) wanda yake umurni da a yi
adalci kuma yana a kan tafarki
madaidaici?
77. Kuma ga Allah gaibin (1)
sammai da kasa yake, kuma
aFamarin Sa'a bai zama ba face
kamar walkawar gani, ko kuwa shT
ne mafi kusa!
>£SZfr\j *^°
(1) *B6ye lokacin Kiyama a bayan bayanin tabbatar aukuwarta yana daga cikin
ni'imomin Allah, domin mai hankali ya yi tattali saboda ita.
403
16 - Suratun Nahl
-n
Lalle Allah, a kan dukan kome, Mai
ikon yi ne.
78. Kuma Allah neYafitar da ku
daga cikunan iyayenku, ba da kuna
sanin kome ba, kuma Ya sanya
muku ji da gannai da zukata, tsam-
maninku za ku gode.
79. Shin ba su ga tsuntsaye m ba
suna horarru a cikin sararin sama,
babu abin da yake rike su face
Allah? Lalle ne a cikin wancan,
hakika, akwai ayoyi ga mutane wa-
danda suke yin Tmani.
80. Kuma Allah ne Ya sanya
muku daga gidajenku wurin natsu-
wa, kuma Ya sanya muku daga
fatun dabbobin nfima wasu gidaje
kuna daukar su da sauki a ranar
tafiyarku da ranar zamanku, kuma
daga sufinsu (2) da gashinsu da ge-
zarsu (Allah) Ya sanya muku
kayan daki da na jin dadi zuwa ga
wani lokaci.
81. Kuma Allah ne Ya sanya
muku inuwa daga abin da Ya hali t-
ta, kuma Ya sanya muku dakuna
daga duwatsu, kuma Ya sanya
? " »?\\'tt\»"
J^tftt*
>Ui^j3
(1) Tsuntsaye horarru a cikin sararin sama, ana nufi da su, a ganina, Allah ne Ya san
haluka, su ne jiragen sama, saboda ambaton horewa tare da su a cikin sararin samaniya,
domin abin da aka hore, ana horonsa ne domin a ci amfaninsa a lokaci da wurin horon.
Tsuntsayen al'ada ba su da wani amfani a gare mu a lokacin da suke a cikin sararin sama.
Saboda haka babu wani abu, sai jirgin sama. Ba za a ce ana nufm shaho ba a lokacin
farauta, domin wannan amfani ya yi kadan bisa ga abin da Surar take kidayawa na
nf imomin Allah a kan mutane gaba daya. Farauta ke5a66iya ce ga mutanen kauye kawai.
(2) Sufi, shi ne gashin tumaki mai kama da auduga, wabar shi ne gashin rakumi mai
laushi, sha'ar, shi ne gashin awaki da gezar dawaki. Bai ambaci auduga da kattani ba,
domin a wajen shuka suke.
404
16 - Suratun Nahl
mm-*
muku wadansu riguna (1 ^suna tsare
muku zafi, da wadansu riguna suna
tsare muku makaminku. Kamar
wancan ne (Allah) Yake cika ni'im-
arSa a kanku,dsammanin ku, kuna
sallamawa.
82. To, idan sun juya, to, abin da
ya wajaba a kanka, shi ne iyarwa
kawai, bayyananniya.
83. Suna sanin ni'imar Allah,
sa'an nan kuma suna musunta,
kuma mafi yawansu kafirai ne.
84. Kuma a ranar da Muke tayar
da mai shaida daga kowace al'um-
ma, sa'an nan kuma ba za a yi izni
ba ga wadanda suka kafirta, kuma
ba su zama ana neman komawarsu
ba.
85. Kuma idan wadanda suka yi
zalunci suka ga azaba, sa'an nan ba
za a saukake ta daga gare su ba,
kuma ba su zama ana yi musu jin-
kiri ba.
86. Kuma idan wadanda suka yi
shirka suka ga abubuwan shirkarsu
sai su ce, "Ya Ubangijinmu!
Wadiannan ne abubuwan shirkar-
mu wadanda muka kasance muna
kira baicinKa". Sai su jefa magana
zuwa gare su, "Lalle ne ku, hakika,
makaryata ne."
87. Kuma su shiga neman sulhu
zuwa ga Allah a ranar nan, kuma
abin da suka kasance suna kir-
kirawa ya Bace daga gare su.
-" :r>v
@ skills jSU3
* > \i* ■
■s '' '<.' °
\" * f *'*\ 1 i ' ' ». ' *> "
>'~s ,>,>
IgJ C&m^f*X> V
V' 9 \ 3
>oOJJ
>i>'> " / s ' \i° *' '\ ' \i " ' s
°, > "r^ Six'*?' ^> -r^> '!'<.'
( 1 ) Riga domin zafi da sanyi daga sufi da wabar da gashi da auduga da kattani da rlga
domin makami shi ne sulke, domin makami daga bakin karfe yake kamar takobi, mashi
da kibiya.
405
16 - Suratun Nahl
mm-*
88. Wacfanda suka kafirta, kuma
suka kange daga hanyar Allah,
Mun kara musu wata azaba bisa ga
azabar, saboda abin da suka kasan-
ce suna yi na fasadi.
89. Kuma a ranar da Muke tayar
da shaidu a cikin kowace al'umma,
a kansu daga kawunansu, kuma
Muka zo da kai kana mai bayar da
shaida a kan wadannan, kuma Mun
saussaukar da Littafi a kanka do-
min yin bayani ga dukan kome da
shiriya da rahama da bushara ga
masu mika wuya (Musulmi).
90. Lalle Allah na yin umurni da
adalci da kyautatawa, da bai wa
ma'abucin zumunta, kuma yana
hani ga alfasha da abin da aka ki da
rarrabe jama'a. Yana yi muku gar-
gadi, cfammanin ku, kuna tunawa.
91. Kuma ku cika da alka-
warin (1) Allah idan kun yi alkawari,
kuma kada ku warware rantsu-
woyinku a bayan karfafa su, alhali
kuma hakika kun sanya Allah Mai
lamuncewa a kanku. Kuma lalle
Allah ne Yake sanin abin da kuke
aikatawa.
92. Kuma kada ku kasance ka-
mar wadda ta warware zarenta a
|3p OU-L-^eSy^j "k^-^jj
*>sS.
(1) Wanda yake rantsuwar alkawari da wani, sa'an nan ya warware rantsuwar domin
neman ya kulla jvata rantsuwa da wani mutum saboda wani amfaninsa, ko jama'arsa a
cikin wata kabila wadda ta fi ta mutanen farko icarfi, to, sifarsa kamar mace ce
mahaukaciya, mai yin zare, a bayan ta tukka shi, ya yi karfi, sa'an nan ta warware shi.
Saboda haka idan ta so mayar da shi wani zare, to, ba zai yi kyau ba kamar zaren farko da
ta yi kuma mutane sun gane haukarta, ba za su yi wata ma'mala da ita ba. Wanda ya yi
rantsuwa da Allah a kan abu, to, ya sanya Allah lamuni ke nan. Ba ya halatta ga wanda ya
shugabantar da Allah ga wani abu, sa'an nan ya koma baya ya ki cika wannan alkawarin,
domin bai kiyaye girman Allah ba, Wanda ya sanya a tsakaninsa da abokin ma'amalarsa.
Tsaron alkawari ni'ima ne.
406
16 - Sura tun Nahl
mm-*
bayan tukka, ya zama warwararku,
kuna rikon rantsuwoyinku domin
yaudara a tsakaninku, domin ka-
sance war wata al'umma ta fi riba
daga wata al'umma! Abin sani ka-
wai Allah Yana jarrabar ku da shi,
kuma lalle ne yana bayyana muku,
a Ranar Kiyama, abin da kuka ka-
sance, a cikinsa, kuna saBa wa juna.
93. Kuma da Allah Ya so, haki-
ka, da Ya sanya ku al'umma guda,
kuma Yana Batar da wanda Ya so,
kuma Yana shiryar da wanda Ya so.
Lalle ne ana tambayarku abin da
kuka kasance kuna aikatawa.
94. Kada ku riki rantsuwoyinku
domin yaudara a tsakaninku, har
kafa ta yi sulBi a bayan tabbatarta,
kuma ku dandani azaba saboda
abin da kuka kange daga hanyar
Allah. Kuma kuna da wata azaba
mai girma. (1)
95. Kada ku sayi 'yan kudi ka-
dan da alkawarin Allah. Lalle ne
abin da yake a wurin Allah shi ne
mafi alheri a gare ku, idan kun
kasance kuna sani.
96. Abin da yake a wurinku yana
karewa, kuma abin da yake a wurin
Allah ne mai wanzuwa. Kuma lalle
ne, Muna saka wa wadanda suka yi
hakuri da ladarsu da mafi kyawun
abin da suka kasance suna aika-
tawa.
>> vr^^t* "V M ^ & \
a&~»J *-^<y <^^M-f J *L-^i o* S^9i
JjaXjM.
>> >.
^- it ^* 4 .,
(1) Wanda yake yin rantsuwa da Allah domin ya yaudari wani, to, yana rusa kansa ne
da kansa, kuma Allah Yana debe jarumci da natsuwa daga zuciyarsa, sa'an nan kuma yana
da wata azaba mai girma a Lahira idan Allah bai gafarta masa ba, da tuba ko da wani
sababi. Sanin haka nfima ne.
407
16 - Suratun Nahl
«&-n
97. Wanda ya aikata aiki na
kwarai daga namiji ko kuwa mace,
alhali yana mumini, to, haklka,
Muna rayar da shi, rayuwa mai
dacfi. Kuma haklka, Muna saka
musu ladarsu da mafi kyawun abin
da suka kasance suna aikatawa.
98. Sa'an nan idan ka karanta (1)
Alkur'ani, sai ka nemi tsari ga Allah
daga Shaidan jefaffe.
99. Lalle ne shi, ba shi da wani
karfi a kan wadanda suka yi imani,
kuma suna dogara ga Ubangijinsu.
100. Abin sani kawai, karfinsa
yana a kan wadanda suke ji6intar
sa, kuma wadanda suke su, game da
shi, fiiasu shirki ne.
101. Kuma idan Muka musanya
wata aya a matsayin wata aya,
kuma Allah ne Mafi sani ga abin da
Yake saukarwa, sai su ce, "Abin
sani kawai, kai makirkiri ne." A'a
mafi yawansu ba swa sani.
102. Ka ce, Ruhul Kudusi (2) ne
ya sassaukar da shi, daga Ubangi-
jinka da gaskiya, domin ya tabbatar
da wadanda suka yi imani, kuma
(domin) shiriya da bushara ga
Musulmi.
103. Kuma lalle ne, hakika,
Muna sanin (cewa) lalle ne su, suna
fp oyu>^s)y l^=»U o~^»\ (vA^.\
^^i5^V&\3&fy
' ?\i' >' ?\ '" ^ ?\\ V >> 1 \ * 1^1 1
JUL* O^ UJll ¥ 15— JLa» u*-> >JL-^i
^ t-s - - >
g3 u)JUlJu
$\3J&
» <^ »to
!iA>Aj t $^u^\^^j^_j^\*X^ •XJabj
(1) An yi sabani ga zaman Isti'aza a gabanin karatu ko a bayansa. Malik ya zabi a yi
Isti'aza a bayan^karatu, ko a bayan an kare yin salla, domin kada Shaicfan ya rinjayi
mutum a bayan Tmaninsa da salla. Saboda haka ya karhanta shi a cikin salla. Wasu kuma
suna isti'aza a gabanin karatu ko a gabanin salla.
(2) Ruhul FCudusi, watau rai mai tsarki, ana nufln Jibrilu, amincin Allah ya tabbata a
gare shi.
408
16 - Suratun Nahl
m\m-*
cewa, "Abin sani kawai, wani mu-
tum ne yake karantar da shi." Hars-
hen wanda suke karkatar da maga-
nar zuwa gare shi, Ba'ajame (1) ne,
kuma wannan (Alkur'ani) harshe
ne Balarabe bayyananne.
104. Lalle ne wacfanda ba su yin
imani da ayoyin Allah, Allah ba zai
shiryar da su ba, kuma suna da
azaba mai racfacfi.
105. Abin sani kawai, wacfanda
ba su yin Imani da ayoyin Allah, su
ne suke kirkira karya. Kuma
wacfannan su ne makaryata.
106. Wanda ya kafirta da Allah
daga bayanTmaninsa, (2) face wan-
da aka tilasta alhali kuwa zuciyarsa
tana natse da imani, kuma wanda
ya yi farin ciki da kafirci, to, akwai
fushi a kansa daga Allah, kuma
suna da wata azaba mai girma.
107.^ Wadancan ne kafirai domin
sun fifita son duniya a kan Lahira,
kuma lalle ne Allah ba Ya shiryar da
mutane kafirai.
108. Wadancan ne wadanda Al-
lah Ya bice hasken zukatansu da
<oLJ\l2Jbj
(1) A'ajami ga asali, wanda ba ya iya magana da Larabci ko da ga asalin jini shi
Balarabe ne. Asalin maganar akwai wani Bawa Barume Nasarani, watau mabiyin addinin
Tsa yana karatun littattafansa kuma yana zuwa yana sauraron Annabi, sai makiya suka ce
wai shi ne yake gaya wa Annabi Alkur'ani. Domin haka Allah ya yi raddin maganarsu da
rashin sanin Larabcin wannan mutumin. Sunansa Kainu ko Jabra.
(2) Ridda ita ce komawa ga kafirci a bayan shiga Musuhinci. Ba a yin hukunci da
ridda ga Musulmi, sai idan ya kafirta da kansa, babu wata ttlastawa, kuma ya nuna ya
yarda da kafircin, kuma_yana farin cikin da shi. To, hukuncinsa kisa ne, domin ya zama
dan tawaye. Wannan shT ne ma'anar cewa akwai fushi a kansa daga Allah. Kuma ba a
kashe shi sai an neme shi da tuba a cikin kwana uku, babu yunwa, babu kishirwa. Kuma a
yi munazara da shi ko zai komo. Bayan kwana uku a kashe shi idan ya ki tuba.
409
16 - Suratun Nahl
mm-*
jinsu da gannansu. Kuma wacfan-
can sii ne gafalallu.
109. Babu shakka, lalle ne, a
Lahira su ne masu hasara.
110. Sa'an nan kuma lalle ne
Ubangijinka ga wacfanda suka yi
hijira daga bayan an fitine su, sa'an
nan kuma suka yi jihadi, kuma
suka yi hakuri, lalle ne Ubangi-
jinka, daga bayanta (1) haklka Mai
gafara ne, Mai jin kai.
111. Aranardakowaneraizaije
yana jayayyar tunkudewa daga
kansa, kuma a cika wa kowane rai
(sakamakon) abin da ya aikata,
kuma su ba za a zalunce su ba.
112. Kuma Allah Ya buga misa-
li, (2) wata alkarya ta kasance amin-
tacciya, natsattsiya, arzikinta yana
je mata a wadace daga kowane
wuri, sai ta kafirta da ni'imomin
Allah, saboda haka Allah ya cfancfa-
na mata tufafin yunwa da tsoro,
saboda abin da suka kasance suna
sana'antawa.
1 13. Kuma lalle ne, hakika, wani
Manzo daga gare su, ya je musu, sai
suka karyata shi, saboda haka aza-
ba ta kama su, alhali kuwa su ne
masu zalunci.
<k^ *-7v —
*c / * />
v>-
(1) Bayan fitina, yana nufin wanda ya shiga Musulunci, sa'an nan fitinar ridda ta
same shi, kuma Allah Ya sanya shi ya koma cikin Musulunci, ya yi abin da Musulunci yake
nema daga gare shi, na ayyukan Rwarai gwargwadon halinsa, to, Allah Yana gafarta masa
laifuffukansa na ridda, kuma Yana jin kansa da rahamarSa.
(2) Kamar Makka. Annabi Muhammadu ya je musu sun karyata shi, sai Allah Ya
musanya amincinsu da tsoro, kuma wadatarsu da yunwa. Wannan shine sakamakon ridda
a kowane lokaci.
410
16 - Suratun Nahl
OBHJ&-n
114. Sa'annankucidaga (1) abin
da Allah Ya arzuta ku da shi, halas,
kuma mai dacfi, kuma ku gode wa
ni'imar Allah idan kun kasance Shi
kuke bautawa.
115. Abin sani kawai (Allah) Ya
haramta (2) muku mussai da jini da
naman alade da abin da aka ambaci
sunan wanin Allah game da shi.
Sa'an nan wanda aka tTlasta a kan
jama'a, kuma baicin mai zalunci,
to, lalle Allah ne Mai gafara, Mai
jin kai.
116. Kuma kada ku ce, domin
abin da harsunanku suke siffanta-
wa da karya, "Wannan halas ne,
kuma wannan haramun ne." Do-
min ku kirkira karya ga Allah. Lalle
ne, wacfanda suke kirkira karya ga
Allah ba za su ci nasara ba.
117. Jin dacfi ne kacfan. Kuma
suna da wata azaba mai racfacfi.
118. Kuma kan wacfanda suka
tuba (Yahudu) Mun haramta abin
da Muka bayar da labari a gare ka
daga gabani, (3) kuma ba Mu zalun-
E3 OJJ^^ju
' ' / *S'' '
'XtyK- <"<. /
(1) Bayan bayani a kan hukuncin ridda saboda sanyawar sashen ni'imomin Allah ga
wasu gumaka ko aljannu ko wadansu mutane salihai, sa'an nan Ya yi umurni da cin abin
da Allah Ya arzuta mutum duka amma da sharudcfa uku, watau ya zama halas ga shari'a
kuma mai dadln ci, wani haicici na wani mutum bai rataya ba a kansa ga shari'a, kuma a bi
shari'a wajen aikatar da shi kamar yadda Allah Ya ce wajen yanka da mai kama da shi, shi
ne gode wa Allah. Saboda haka banda kamar giya da kayan wani mutum sai fa a bisa
yardarsa.
(2) Bayanin abubuwan da aka haramta, idan babu larura. Ana cin abin da shari'a ta
hana a ci a kan larura, sai idan larurar ta sami mutum ne a cikin halin sa6on Allah, kamar
mai fita daga da'ar Sarkin Musulunci ya yi tasa icungiya dabam, ko wanda ya fita domin
wani zalunci kamar sata ga misali, to, ba su cin haram domin su ci gaba da aikinsu.
(3) Gabanin wancan Sura, kamar a cikin Suratul An 'am aya ta 146. Saboda haka ba a
biyar da Yahudu a wajen haramcin abin da Allah Ya haramta musu, su kadai saboda
zaluncinsu.
411
16 - Suratun Nahl
mm-*
ce su ba, amma sun kasance kansu
suke zalunta.
119. Sa'an nan kuma lalle ne
Ubangijinka ga wacfanda suka ai-
kata mummunan aiki (1) da jahilci,
sa'an nan suka tuba daga bayan
wancan, kuma suka gyara, lallejie
Ubangijinka, daga bayanta hakika
Mai gafara ne, Mai jin kai.
120. Lalle ne Ibrahim (2) ya ka-
sance Shugaba, mai kaskantar da
kai ga Allah, mai karkata zuwa ga
gaskiya, kuma bai kasance daga
masu shirki ba.
121. Mai godiya (3) ga ni'imo-
minSa (Allah), Ya zaBe shi, kuma
Ya shiryar da shi zuwa ga tafarki
madaidaici.
122. Kuma Muka ba shi alheri a
cikin duniya. Kuma lalle shi, a La-
hira, yana daga salihai.
123. Sa'an nan kuma Muka yi
wahaja zuwa garejca (cewa), "Ka (4)
bi akldar Ibrahim, mai karkata
zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance
daga masu shirki ba."
" ^-> tt?^ ^
M :iQ*lJ\i t
he
(1) Wanda ya yi wani abu da Allah Ya hana wajen ni'imomi, ko wajen wani abu
dabam na sa6on Allah, to, idan ya tuba a gabanin ya kai ga gargara, Allah zai gafarta
masa. Wannan ni'ima ce.
(2) Akwai daga ni'imomin Allah, Ya sanya mutum madaukaki saboda addininsa da
imaninsa ga Ubangijinsa, kuma Ya ba shi ikon binSa da takawa kamar yadda Ya yi wa
Ibrahim. Kuma akwai daga ni'imomin Allah Ya sanya mutum a cikin zuriyyar mutumin
kirki kamar yadda Ya yi wa Annabi Muhammadu Ya sanya shi a cikin zuriyyar Ibrahim.
(3) An ambaci Ibrahim saboda ya gode wa ni'imonin Allah domin Musulmi su yi
koyi da shi wajen gode wa Allah ga ni'imomin da Ya yi ishara zuwa gare su a cikin wannan
Sura da watanta. Gode wa ni'ima wata ni'ima ce.
(4) Yana cikin ni'ima ga Ibrahim da kammalarta a gare shi a umurci mafificin talikai,
Muhammadu, tslra da amincin Allah su tabbata a gare shi, da bin akldar Ibrahim.
412
16 - Suratun Nahl
mm-*
124. Abin sani kawai, an sanya
Asabar a kan wacfanda suka sa6a
wa juna a cikin sha'aninsa/ 1 * Kuma
lalle ne Ubangijinka, hakTka, Yana
yin hukunci a tsakaninsu a Ranar
Kiyama a cikin abin da suka kasan-
ce a cikinsa suna sa6a wa juna.
125. Ka yi kira zuwa ga hanyar
Ubangijinka da hikima (2) da wa'azi
mai kyau kuma ka yi jayayya da su
da magana wadda take mafi kyau.
Lalle ne Ubangijinka Shi ne Mafi
sani ga wanda ya 6ace daga han-
yarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga
masu shiryuwa.
126. Kuma idan kuka saka (3) wa
ukuba, to, ku saka wa ukuba da
misalin abin da aka yi muku ukubar
da shi. Kuma idan kun yi hakuri,
lalle shi ne mafi alheri ga masu
hakuri.
127. Kuma ka yi hakuri, kuma
hakurinka ba zai zama ba face do-
min Allah, kuma kada ka yi bakin
u > »- > I
f >- 1 '< »> *<.\
> Z^4^53^VJ ^Wi^^^JJv^
(1) Wacfanda suka sa6a wa juna a cikin sha'anin Ibrahim wanda yake ya kasance
yana girmama Juma]a domin ita ce ranar cikon ni'imomin Allah a kan bayinSa. Yahudu
suka sa6a wa Ibrahim suka girmama Asabar domin a ranar nan ne babu wani aiki.
Wannan ya doge har a bayan cfauke Tsa. Nasara suka juya domin kin Yahudu zuwa ga
Lahadi, domin su yi daidai da Kaisara, Kustantayin, mai girmama Lahadi, ranar bauta wa
rana. Kafirce wa ni'ima azaba ce.
(2) Kira zuwa ga hanyar Ubangiji, Allah, yana daga cikin abubuwan koyo daga
Ibrahim kuma kira zuwa ga Allah na daga cikin ni'imomin Allah ga mai kiran da wanda
ake kiran, sa'an nan zaman kiran da hikima da wa'azi mai kyau, ni'ima ce ga mai yi da
wacfanda ake kira zuwa ga shiriyar duka. Abin da ake cewa Hikima shi ne a yi magana a
kan hujja wadda abokin husuma ba zai iya kauce mata ba.
(3) Kuma mai kiran mutane zuwa ga Allah lalle ne sai ya hadu da cutarwa daga
mutanen da ba su son gaskiya. To, Allah ba Ya son zalunci ko da a kan makiyanSa, saboda
haka Ya yi umurni da yin kisasi da misalin ukuba, ko a yi hakuri, amma yin hakuri ya fi
ramawa domin neman ni'imar Allah ta kara kammala.
413
17 — Suratul Isra'
imm-"
ciki sabo da su, kuma kada ka
kasance a cikin kuncin rai daga abin
da suke yi na makirci.
128. Lalle Allah Yana tare da
wacfanda suka yi takawa da wacfan-
da suke su masu kyautatawa ne.
Tana karantar da daidaitawa a tsakanin abubuwa masu
dangantaka da juna.
-» j 9 ^.** ^ <*
Y&&
J?
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
1. Tsarki ya tabbata ga Wanda
Ya yi tafiyar dare (1 } da bawanSa, da
dare daga Masallaci mai alfarma
zuwa ga Masallaci mafi nlsa, (2)
wanda Muka sanya albarka a ge-
fensa domin Mu nuna masa daga
ayoyinMu. Lalle ne Shi, Shi ne Mai
ji, Mai gani.
(1) Isra'i, shi ne tafiyar dare da Allah Ya yi da Annabi daga Makka zuwa Baitil
Makadis. Sa'an nan Mi'iraji zuwa sama inda aka ba shi salloli.
(2) Mukarana a tsakanin Masjidil Haram watau tsararre daga a yaki mutanensa da
Masjidil Aksa wanda J)a tsararre ba. Isra'i da Mi'iraji sun fi Mikatin Musa da ganawarsa
da Ubangiji a T)ur Slna'a.
414
17 - Suratul lsra'
MIM-w
2. Kuma Mun bai wa Musa (1)
littafi, kuma Mun sanya shi shiriya
ga BanT Isra'ila, cewa kada ku riki
wani wakili baiciNa.
3. Zuriyar wadanda Muka dau-
ka tare da Nuhu. Lalle ne shi ya
kasance wani bawa mai godiya.
4. Kuma Mun hukunta zuwa ga
Bam Tsra'ila a cikin Littafi, cewa
lalle ne, kuna yin 6arna a cikin kasa
sau biyu, kuma lalle ne kuna zalun-
ci, zalunci mai girma.
5. To idan wa'adin na farkonsu
ya je, za Mu aika, a kanku wadansu
bayi (2) Namu, ma'abuta yaki mai
tsanani, har su yi yawo a tsakanin
gidajenku, kuma ya zama wa'adi
abin aikatawa.
6. Sa'an nan kuma Mu mayar da
dauki a gare ku a kansu, kuma Mu
taimake ku da dukiyoyi da cfiya
kuma Mu sanya ku mafiya yawan
masu fita yaki.
7. Idan kun kyautata, kun kyau-
tata domin kanku, kuma idan kun
munana, to, dominsu. Sa'an nan
idan wa'adin na karshe (3) ya je, (za
Xj?4 t |c$JUb ^Sjotj v^£^ Wl** £}^*j
(1) Tsakanin Bawan Allah Muhammadu da Musa, kuma an aiko Musa ga Bani
Isra'ila kawai, kuma Nuhu an ce masa bawa amma ba a jingina shi kamar yadda aka jingina
Bawansa ba. Sa'an nan kuma jingina Yahudu ga Nuhu ya daidaita su da sauran mutane
wajen da'awar daukaka da nasaba.
(2) Sun yi fasadi da barin aiki da Taurati, saboda haka aka aika Jaluta a kansu. Ya
kashe su kuma ya kama zuriyarsu.
(3) Suka yi fasadi marra ta biyu da kashe Zakariyya da Yahaya, sai aka aika musu da
Bukht Nasar daga Babila ya karkashe su, kuma ya. kama zuriyarsu, kuma ya rushe Baitil
Makadis. Wadannan labaru biyu na 6arnar BanT Isra'ila suna cikin bayar da labaru ga
gaibi. Idan an daidaita su da labarun gaibi wadanda Alkur'ani ya fada, wadansu suka auku
kuma wadansu suna ta aukuwa, za a san falalar Alkur'ani a kan Taurati kamar yadda ya
bayyana cewa Attaura ta yi kira zuwa ga tauhidi da shiriya, sa'an nan ya bayyana
abubuwan da Alkur'ani yake karantarwa daga aya ta 9 zuwa ga aya ta 38 inda ya tara
halayen kwarai kuma ya kore munana.
415
17 — Suratul Isra'
imm-"
su je) domin su bakanta fusko-
kinku, kuma su shiga masallaci ka-
mar yadda suka shige shi a farkon
lokaci, kuma domin su halakar da
abin da suka rinjaya a kansa, hala-
karwa.
8. Akwai tsammanin Uban-
gijinku Ya yi muku rahama. Kuma
idan kun sake, Mu sake. Kuma
Mun sanya Jahannama matsara ga
kafirai.
9. Lalle ne wannan Alkur'ani
yana shiryarwa ga (halayen) wa-
cfanda suke mafi daidaita, (1) kuma
yana bayar da bushara ga muminai
wacfanda suke aikata ayyuka na
kwarai (cewa) "Lalle ne suna da
wata ijara mai girma."
10. Kuma lalle ne wacfanda ba su
yin Tmani da Lahira, Mun yi musu
tattalin wata azaba mai radadi.
11. Kuma mutum yana (2) yin
addu'a da sharri kamar addu'arsa
da alheri, kuma mutum ya kasance
mai gaggawa.
12. Kuma Mun sanya dare da
rana, ayoyi biyu, sa'an nan Muka
shafe ayar dare, kuma Muka sanya
ayar rana mai sanyawa a yi gani,
domin ku nemi falala daga Ubangi-
jinku, kuma domin ku san kidayar
shekara da lissafi. Kuma dukan
s vS*' s '»*
( 1 ) Bayan ya facfi abubuwan da Attaura ta karantar, ya ce, "Alioir'ani yana shiryarwa
zuwa ga halayen da suka fi daidaita daga abin da Attaura ta karantar." Sa'an nan ya ci
gaba da bayanin abubuwan da Al£ur'ani yake karantarwa.
(2) Alioir'ani yana shiryar da mutum har ga yadda yake yin addu'a domin kada ya yi
wa kansa addu'a ta sharri alhali kuwa yana nufin ya yi alheri domin an halicci mutum da
son gaggawa.
416
17 - Suratul Isra'
^Oi^->v
kome Mun bayyana shi daki-dakin
bayyanawa.
13. Kuma kowane mutum Mun
lazimta masa abin rekodinsa a cikin
wuyansa, kuma Mu fitar masa a
Ranar Kiyama da littafi wanda zai
hadu da shi bucfacfcfe.
14. "Karanta Littafinka. Ranka
ya isa ya zama mai hisabi a kanka a
yau."
15. Wanda ya nemi shiryuwa, to,
ya nemi shiryuwa ne domin kansa
kawai kuma wanda ya 6ace, to, ya
6ace ne a kansa kawai, kuma rai
mai cfaukar nauyi ba ya cfaukar
nauyin wani ran, kuma ba Mu zama
masu yin azaba ba, sai Mun aika
wani Manzo.
16. Kuma idan Mun yi nufin Mu
halakar da wata alkarya, sai Mu
umurci mawadatanta, har su yi fa-
sicci a cikinta, sa'an nan maganar
azaba ta wajaba a kanta, sa'an nan
Mu darkake ta, darkakewa.
17. Kuma da yawa Muka hala-
kar da aFummomi a bayan Nuhu.
Kuma Ubangijinka Ya isa ya zama
Mai Rididdigewa ga zunubban
bayinSa, Mai gani.
18. Wanda ya kasance yana nu-
fin mai gaggawa, (1) sai Mu gag-
gauta masa a cikinta, abin da Muke
so ga wanda Muke nufi, sa'an nan
kuma Mu sanya masa Jahannama,
ya konu da ita, yana abin zargi
kuma abin tunkucfewa.
%^lS&t&$3
^^loL^^oLiiS \J\
\'4 X ' " •+
>' / '..
™j j_yj*
(1) Duniya. Ana kwatanta duniya da mai son ta, da Lahira da mai son ta.
417
17 - Suratul Isra'
«&-W
19. Kuma wanda ya nufi Lahira,
kuma ya yi aiki saboda ita irin
aikinta alhali kuwa yana mumini,
to, wacfannan aikinsu ya kasance
godadde.
20. Dukansu Muna taimakon
wacfannan da wacfancan daga kyau-
tar Ubangijinka, kuma kyautar
Ubangijinka ba ta kasance hananna
ba.
21. Ka duba yadda Muka fifitar
da sashensu a kan sashe ! Kuma lalle
ne Lahira ce mafi girman darajoji,
kuma mafi girman fifitawa.
22. Kada ka sanya wani abin
bauta wa na dabam tare da Allah,
har ka zauna kana abin zargi, yar-
BaBBe.
23. Kuma Ubangijinka Ya hu-
kunta kada ku bauta wa kowa face
Shi, kuma game da mahaifa biyu ku
kyautata kyautatawa, ko dai
cfayansu ya kai ga tsufa a wurinka
ko dukansu biyu, to, kada ka ce
musu 'tir' kuma kada ka tsawace su,
kuma ka facfa musu magana mai
karimci.
24. Kuma ka sassauta musu fi-
kafikan tausasawa na rahama.
Kuma ka ce "Ya Ubangijina ! Ka yi
musu rahama, kamar yadda suka yi
renona, ina karami."
25. Ubangijinku ne Mafi sani ga
abin da yake a cikin rayukanku.
Idan kun kasance salihai, to, lalle ne
Shi, Ya kasance ga masu komawa
gare Shi, Mai gafara.
^k s . *->'?%' y " fir*'*
418
17 — Suratul Isra'
33&li£*-w
26. Kuma ka bai wa ma'abuein
zumunta hakkinsa, (1) da miskTna
da dan hanya. Kuma kada ka baz-
zara dukiyarka, bazzarawa.
27. Lalle ne mubazzarai sun ka-
sance 'yan'uwan Shaidanu. Kuma
Shaidan ya kasance ga Ubangijinsa,
mai yawan kafirci.
28. Ko dai ka kau da kai daga
gare su domin neman rahama daga
Ubangijinka, wadda kake fatanta,
to sai ka gaya musu magana mai
laushi.
29. Kuma kada ka sanya han-
nunka kukuntacce zuwa ga
wuyanka, kuma kada ka shimfitfa
shi dukan shimfidawa, har ka zama
abin zargi, wanda ake yanke wa. (2)
30. Lalle ne Ubangijinka Yana
shimfida arziki ga wanda Yake so,
kuma Yana kukuntawa. Lalle Shi,
Ya kasance Masani ga bayinSa, Mai
gani.
31. Kuma kada ku kashe
'ya'yanku domin tsoron talauci.
Mu ne ke arzuta su, su da ku. Lalle
ne kashe su ya kasance kuskure
babba.
32. Kuma kada ku kusanci zina.
Lalle ne ita ta kasance alfasha ce
kuma ta munana ga zama hanya.
33. Kuma kada ku kashe rai
wanda Allah Ya haramta face da
> *-Z S 9 ' ,>-£ >y
^l^WJ^
^ 9 *»y yy y >> y *' > 9 s y^y 9 y~C <•
(1) Hakkin zumu shi ne alheri da sadar da zumunta. Hakkin miskini da dan hanya
zakka da sadakar tacfawwa'i da liyafar kwana uku ga bako bisa al'ada da alheri, ba bisa
6arna da kallafawa ba.
(2) Kada ka zama marowaci a zarge ka, kuma kada ka zama almubazzari ka rasa
mutane, su yanke daga gare ka.
419
17 - Suratul Isra'
m\m-*
hakki, kuma wanda aka kashe, yana
wanda aka zalunta, to, hakika,
Mun sanya hujja ga waliyyinsa, sai
dai kada ya ketare haddi a cikin
kashewar. Lalle shi ya kasance wan-
da ake taimako.
34. Kuma kada ku kusanci du-
kiyar maraya face dai da sifa wadda
take ita ce mafi kyau, har ya isa ga
mafi karfinsa. Kuma ku cika alka-
wari. Lalle alkawari ya kasance
abin tambayawa ne.
35. Kuma ku cika mudu idan
kun yi a wo, kuma ku auna nauyi da
sikeli madaidaici. Wancan ne mafi
alheri, kuma mafi kyau ga fassara.
36. Kuma kada ka bi abin da ba
ka da ilmi game da shi. Lalle ne jTda
gani da zuciya, dukan wadancan,
(mutum) ya kasance daga gare shi
wanda ake tambaya.
37. Kuma kada ka yi tafiya a
cikin kasa da alfahari. Lalle kai, ba
za ka huda kasa ba, kuma ba za ka
kai ga duwatsu ba ga tsawo.
38. Dukan wancan, mai mu-
ninsa ya kasance abin kyama a
wurin Ubangijinka.
39. Wancan yana daga abin da
Ubangijinka Ya yi wahayi zuwa
gare ka na hikima. Kuma kada ka
sanya wani abin bautawa na dabam
tare da Allah, har a jefa ka a cikin
Jahannama kana wanda ake zargi,
wanda ake tunkudewa. (1)
, E *r
»-
&&#
( 1 ) Wannan shi ne Karshen muicarana tsakanin shiryarwar da AlRur'ani ya kawo wa
duniya da abin da Attaura ta kawo wa Bani Isra'ila. Kuma akwai daidatawa a cikinsu a
tsakanin halaye masu kyau da kishiyoyinsu, watau halaye masu muni.
420
17 - Suratul Isra'
^.Uj^-w
«o£
40. Shin fa, Ubangijinku Ya
zaBe ku da cfiya maza ne, kuma Ya
riki 'ya'ya mata daga mala'iku? (1)
Lalle ne ku, hakTka, kuna facfar
magana mai girma!
41. Kuma lalle ne hakTka, Mun
sarrafa bayani a cikin wannan Al-
kur'ani domin su yi tunani, kuma
ba ya kara musu kome face gudu.
42. Ka ce, "Da akwai wadansu
abubuwan bautawa tare da Shi,
kamar yadda suka facfa, a lokacin,
da (abubuwan bautawar) sun nemi
wata hanya (2) zuwa ga Ma'abucin
ATarshi."
43. TsarkinSa ya tabbata kuma
Ya daukaka daga abin da suke facfa,
daukaka mai girma.
44. Sammai bakwai da kasa da
wanda yake a cikinsu suna yi Masa
tasbihi. Kuma babu wani abu face
yana tasbihi game da gode Masa,
kuma amma ba ku fahimtar tasbi-
hinsu. Lalle ne Shi, Ya kasance Mai
hakuri ne, Mai gafara.
45. Kuma idan ka karanta Alku-
r'ani/ 3 * sai Mu sanya a tsakaninka
da tsakanin wadanda ba su yin
'».
®b>^
j^ii LS 4-i I * t4a* o oy J5
o ss *'* /
Op ^ffl**&&£* %
'*S< t I'S*' <,'">v>
CfJ& 'crjfj <^4> U^>- <j\ *y& \ ^\A ty J
(1) Farkon mukarana a tsakanin al'adun mushirikai da shiryarwar Alkur'ani domin
gyara tunaninsu ga karBar Tmanin TauhTdi.
(2) Da su abokan tarayyar sun nemi hanya zuwa ga Allah domin su yake Shi saboda
Ya ce ATarshi tasa ce, Shi kacfai, domin su sami nasu rabon, saboda ATarshi ta hadiye
kome, har da su.
(3) Mushirikai jahilai ne, ba su iya daukar jayayyar magana, saboda sun fi kusanta
zuwa ga dabbobi ga tunaninsu, bisa gare su zuwa ga mutane, ko da yake sauran jikinsu na
mutane ne. Saboda haka a koyaushe suna kusa ga fadan tayar da hankali da doke-doke.
Saboda haka Allah Ya sanya tsari ga AnnabinSa da wanda ya bi hanyar Annabin, wajen
shiryar da mutane game da karanta Alkur'ani. Ba za su iya fada mai karanta Alkur'ani da
duka ba, kuma tsoronsa suke ji domin kwarjinin Alkur'ani.
421
17 - Suratul Isra'
&#X
ftji-w
imani da Lahira wani shamaki mai
suturcewa.
46. Kuma Mu sanya marufai a
kan zukatansu, domin kada su fa-
himce shi, da wani nauyi a cikin
kunnuwansu, kuma idan ka ambati
Ubangijinka, a cikin Alkur'ani, ShT
kacfai, sai su juya a kan baya-
yyakinsu domin gudu.
47. Mu ne Mafi sani game da
abin da suke saurare da shi, a loka-
cin da suke yin sauraren zuwa gare
ka, kuma a lokacin da suke masu
ganawa a tsakaninsu, a lokacin da
azzalumai suke cewa, "Ba ku biyar
kowa face wani namiji sihirtacce."
48. Ka duba yadda suka buga
maka misalai, sai suka Bace, ba su
iya samun hanya.
49. Kuma suka ce, "Shin, idan
mun kasance kasusuwa da nika-
kkun gaBaBuwa, ashe, lalle ne mu,
hakTka, wacfanda ake tayarwa ne a
wata halitta sabuwa?"
50. Ka ce, "Ku kasance duwatsu
ko kuwa bakin karfe.
57. "Ko kuwa wata halitta daga
abin da yake da girma a cikin kira-
zanku." To, za su ce, "Wane ne zai
mayar da mu?" Ka ce, "Wanda Ya
kaga halittarku a farkon lokaci."
To, za su gyacfa kansu zuwa gare ka,
kuma suna cewa, "A yaushe ne
shi?" Ka ce, "Akwai tsammaninsa
ya kasance kusa.
52. "A ranar da Yake kiran ku,
sa'an nan ku rika karBawa game da
gode Masa, kuma kuna zaton ba ku
zauna ba face kacfan."
> ' 9 ' * *"Z
» ss '*,
^^Ud^I \j>^b\by-&j
All
17 - Suratul Isra'
$*ili£~-W
53. Kuma ka ce wa BayiNa, su
facfi kalma (1) wadda take mafi
kyau. Lalle ne Shaicfan yana sanya
6arna a tsakaninsu. Lalle ne Shai-
cfan ya kasance ga mutum, makiyi
bayyananne.
54. Ubangijinku ne Mafi sani
game da ku. Idan Ya so, zai yi muku
rahama, ko kuwa idan Ya so zai
azabta ku. Kuma ba Mu aika ka
kana wakili a kansu ba.
55. Kuma Ubangijinka ne
Mafi sani game da wanda yake a
cikin sammai dajcasa. Kuma lalle
ne, haklka, Mun fifita sashen Anna-
bawa a kan sashe kuma Mun bai wa
Dawuda Zabura. (2)
56. Ka ce, "Ku kirayi wadanda
kuka riya, baicinSa. To, ba su mal-
lakar kuranyewar cuta daga gare
ku, kuma haka juyarwa." (3)
57. Wadancan, wadanda suke
kiran, (4) suna neman tsani zuwa ga
Ubangijinsu. Wadanne ne suke ma-
fifita a kusanta? Kuma suna fa tan
samun rahamarSa, kuma suna tso-
ron azabarSa. Lalle ne azabar
Ubangijinka ta kasance abar tsoro
ce.
.<.'<£>
a*< "j\' & *ir^ "<\t • - ^A't"
» *" s 9 *
(1) Ka ce wa bayiNa, mutane, idan suna magana su auna kalmomin da suke zance da
su, sa'an nan su rika amfani da kalma mafi kyawo domin kada Shaidan ya sami mashiga
daga maganarsu zuwa ga zukatansu, ya sanya barna a tsakaninsu.
(2) Mukarana a tsakanin Annabawa. Allah Ya fifita wadansu a kan wadansu. Falalar
Dawuda a kan^wadansu Annabawa da Zabura ne, to, ina fifikon wanda aka bai wa
Alkur'ani mafificin littafi da sauran Annabawa?
(3) Ba za su iya juyar da cuta daga gare ku zuwa ga wani ko kuwa daga wani zuwa
gare ku ba.
(4) Wadanda kafirai ke neman tawassuli da su zuwa ga Allah, su ma suna neman abin
da zai sadar da su zuwa ga Allah, saboda haka babu bambanci a tsakanin mai tawassuli da
wanda ake tawassulin da shi ga kusanta zuwa ga Allah. Babu mai kusanta zuwa ga Allah
sai da takawa ga ibadarSa kawai.
423
17 — Suratul Isra'
«&-w
58. Kuma babu wata alkarya
face, Mu ne masu halaka ta a gaba-
nin Ranar Kiyama k5 kuwa Mu
masu azabta ta ne da azaba mai
tsanani. Wancan ya kasance a cikin
littafi rubutacce.
59. Kuma babu abin da ya hana
Mu, Mu aika da ayoyi face saboda
mutanen farko sun karyata game da
su. Kuma Mun bai wa Samudawa
taguwa, aya bayyananna, sai suka
yi zalunci game da ita. Kuma ba Mu
aikatawa da ayoyi face domin
tsoratarwa.
60. Kuma a lokacin da Muka ce
maka, "Lalle ne Ubangijinka Ya
kewaye mutane". Kuma ba Mu
sanya Mafarki wanda (1) Muka
nuna maka ba, face domin fitina ga
mutane, da itaciya wadda aka la'an-
ta a cikin Alkur'ani. Kuma Muna
tsoratar da su, sa'an nan (tsora-
tarwar) ba ta kara su face da kanga-
ra mai girma.
61. Kuma a lokacin (2) da Muka
ce wa mala'iku, "Ku yi sujada ga
Adamu" sai suka yi sujada, face
IbilTsa, ya ce, "Shin, zan yi sujada ga
wanda ka (3) halitta shi yana laka?"
•» 'CSS ' A< i ^ > t x > »i • ^ 7?
til
c^> at — => jl *)l I cJ-i |S/ \* S^/j o^ Li^ uj
3 bo G^iW]
(1) Abubuwan da Annabi ya gani a daren Isra'i da Mi'iraji, watau tafiyarsa zuwa
sama wadda aka yi ishara da ita a farkon surar. Itaciyar da aka la'anta, ita ce Zakkum,
abincin mutanen wuta. Akwai mukarana, a cikin wannan, cewa ayoyin da aka bai wa wani
Annabi sun fi wadanda aka bai wa wasu Annabawa girma.
(2) Mukarana a tsakanin jinsin mutum da mala'iku da aljannu. An fifitar da jinsin
mutum da sanya wa sauran jinsoshi biyu su yi masa sujada, sa'an nan aka daukaka jinsin
mala'ika saboda da'a, kuma aka la'anci jinsin IblTsa da sabo.
(3) Rubuta "ka" da karamin "ka" ne ko da yake lamTrin Allah ne, domin ya nuna
halin maganar Shaidan zuwa ga Allah Mai girma. Yana yin maganar da hushi, ba da
girmamawa ba.
424
17 - Suratul Isra'
9g^li^-w
62. Ya ce, "Shin, ka gan ka (1) ... !
Wannan wanda ka girmama a kai-
na, lalle ne idan ka jinkirta mini
zuwa ga Ranar Kiyama lalle ne, zan
tumBuke zuriyarsa, face katfan."
63. Ya ce^ "Ka tafi. Sa'an nan
wanda ya bl ka daga gare su, to,
Jahannama ce sakamakonku, (Mu
ba ku shi) sakamako cikakke.
64. "Kuma ka rikitar da wanda
ka sami iko a kansa, daga gare su,
da sautinka, kuma ka yi hari a
kansu da dawakinka da dakarunka,
kuma ka yi tarewa da su a cikin
dukiyoyi da cfiya, kuma ka yi musu
wa'adi. " Alhali kuwa Shaidan ba ya
yi musu wa'adin kome face da rucfi.
65. "Lalle ne bayiNa, ba ka da
wani karfi a kansu. Kuma Ubangi-
jinka Ya isa Ya zama WakTii."
66. Ubangijinku ne Yake gu-
danar da jirgi a cikin teku, domin ku
nema daga falalarSa. Lalle ne Shi,
Ya kasance a gare ku Mai jin kai.
67. Kuma idan cuta ta shafe ku,
a cikin teku, sai wanda kuke kira ya
6ace, face Shi. To, a lokacin da Ya
tsirar da ku zuwa ga tudu sai kuka
bijire. Kuma mutum ya kasance
mai yawan butulci.
68. Shin fa, kun amince cewa
(Allah) ba Ya shafe gefen kasa game
da ku, ko kuwa Ya aika da iska mai
tsakuwa a kanku, sa'an nan kuma
• y s s y, 9 y s ** yy y ^ 9 y ^ fr y y
^kS^\££j*
'*" is. 9 * 9 V- '< •^rfti-
j^^r o^a>^fU ^Xx^ i y<^ ^Jt j I J Is
Jy Vi j ^SlSj ^%-Ij d£h?$*
M-'M^l^
C »> > y 1*± Tf'
* y** y* »>»-*>> < »> ^>>-i^> <
^ — ' <: ,
(1) Mai sa66 saboda hassada ba ya ganin girman Ubangijinsa. A cikin maganar IblTs
akwai rashin ladabi da nuna kiyayya ga Adamu, har zuwa ga zuriyarsa, wadda ba a haifa
ba tukuna.
425
17 — Suratul Isra'
«c£
s'TVV
->Y
ba za ku sami wani wakili ba
dominku?
69. Ko kun amince ga Ya mayar
da ku a cikin tekun, a wani lokaci na
dabam, sa'an nan Ya aika wata
guguwa mai karya abubuwa daga
iska, har ya nutsar da ku saboda
abin da kuka yi na kafirci? Sa'an
nan kuma ba ku samun mai bin
hakki saboda ku, a kanMu, game
da Shi.
70. Kuma lalle ne Mun gir-
mama 'yan Adam, (1) kuma Muka
cfauke su a cikin kasa da teku, kuma
Muka arzuta su daga abubuwa
masu dadi, kuma Muka fTfita su a
kan masu yawa daga wadanda
Muka halitta, fifitawa.
71. A ranar da Muke kiran (2)
kowane mutane da limaminsu, to,
wanda aka bai wa littafinsa a da-
mansa, to, wadannan suna karatun
littafinsu, kuma ba a zaluntar su da
zaren bakin gurtsin dabino.
72. Kuma wanda ya kasance ma-
kaho (3) a cikin wannan, saboda
haka shi a Lahira makaho ne, ku-
ma mafi Bata ga hanya.
73. Kuma lalle ne sun yi kusa,
haklka, su fitine ka daga abin da
Muka yi wahayi zuwa gare ka, do-
min ka kirkira waninsa a gare Mu, a
lokacin, hakika, da sun rike ka
masoyi.
LU
< »*s s** > * *ss s
(1) Mukarana a tsakanin jinsin mutum da sauran halittar Allah.
(2) Mukarana a Lahira a tsakanin al'ummdmi kuma da tsakanin muminai da
kafirai.
(3) Mukarana a tsakanin makantar basTra da makantar ganin ido.
426
17 — Suratul Isra'
fMli&~--w
74. Kuma ba domin (1) Mun
tabbatar da kai ba, lalle ne, hakika,
da ka yi kusa ka karkata zuwa gare
su ta wani abu kacfan.
75. A lokacin, lalle ne, da
Mun cfancfana maka ninkin azabar
rayuwa da ninkin azabar mutuwa,
sa'an nan kuma ba za ka sami
mataimaki ba a kanMu.
76. Kuma lalle ne, sun (2) yi kusa,
hakika, su tayar da hankalinka
daga kasar, domin su fitar da kai
daga gare ta. Kuma a lokacin, ba za
su zauna ba a kan sa6aninka face
kacfan.
77. Hanyar wacfanda, hakika,
Muka aika a gabaninka, daga Man-
zanninMu, kuma ba za ka sami
juyarwa ba ga hanyarMu.
78. Ka tsayar da salla (3) a kar-
katar rana zuwa ga duhun dare da
lokacin fitar alfijir, lalle ne karatun
fitar alfijir (4) ya kasance wanda ake
halarta.
^\&X£\c£=~?
(1) Mukarana a tsakanin sarauta da Manzancin Allah. Sarkin duniya yana canja
manufarsa domin neman yardar mutanensa. Amman Manzon Allah ba ya sake abin da
Allah Ya umurce shi da shi domin neman yardar mutane.
(2) Mukarana a tsakanin mai aiki domin Allah, ba a iya juyar da shi daga aikinsa
domin neman wata kamala, amma mai aikin duniya ana iya canja shi domin haka. Kuma
bambancin hijira da kora, wacfanda suka kori Annabinsu sai a halaka su, amma wacfanda
Annabinsu ya yi hijira gabanin azaba, to, ba za a halaka su ba.
(3) Tsayar da salla a cikin lokutanta, shi ne yake hana a yaudari mutum da magana
har a sanya shi ya yi abin da bai kamata ba, ko kuma ya yi abin da shari'a ta hana.
(4) Karatun fitar alfijir, ana nufin sallar asuba. Saboda haka ana son dogon karatu a
cikinta, gwargwadon fara ta a duhun dare a bayan fitar alfijir.
427
17 — Sura tul Isra'
^Ji£~--w
J9. Kuma da dare, sai ka yi
hlra (1) da shi (Alkur'ani) a kan kari
gare ka. Akwai tsammanin Ubangi-
jinka Ya tayar da kai a wani matsayi
godadde.
80. Kuma ka ce, "Ya Uban-
gijina! (2) Ka shigar da ni shigar
gaskiya, kuma Ka fitar da ni fitar
gaskiya. Kuma Ka sanya mini,
daga gunKa, wani karfi mai taima-
ko."
81. Kuma ka ce, "Gaskiya ta zo,
kuma karya ta lalace. Lalle ne karya
ta kasance lalatacciya."
82. Kuma Muna sassaukarwa,
daga Alkur'ani, abin da yake wara-
ka ne da rahama ga muminai.
Kuma ba ya kara wa azzalumai
(kome) face hasara.
83. Kuma idan Muka yi ni'ima a
kan mutum, (3) sai ya hinjire, kuma
ya nlsanta da gefensa, kuma idan
sharri ya shafe shi, sai ya kasance
mai yanke kauna.
84. Ka ce, "Kowa ya yi aiki a
kan hanyarsa. Sa'an nan Ubangi-
jinka ne Mafi sani ga wanda yake
mafl shiryuwa ga hanya."
85. Suna tambayar ka ga ruhi.
Ka ce, "Ruhi daga aramarin
^-^(ii! ^lib^Aj XJ^^ ^\^jtj
j HiLL- est jJ & J S**\) 4 -*-»?
\j\^^\cyJ^\j,y^j
J >
p^Lu-t^JUblykJlj
(1) Hira da Alicur'ani, watau a yi sallolin nafila na dare, Shafa'i, bibbiyu, a kare da
Wutri. Ga Annabi tahajjudi da Wutrin wajibi ne, kari a kan abin da aka cfora wa sauran
mutane, a lokacin da yake zaune a gida. Ga sauran mutane, Wutri sunna ce, kamar sallolin
Tdi da rokon ruwa da husufin rana da na wata. A nan akwai bambanci a tsakanin Annabi
da jama'arsa a wajen Wutri.
(2) Kuma ka yi addu'a a cikin sallarka da bayanta da wannnan addu'a domin ta nuna
sallamawarka ga Ubangijinka Allah.
(3) Mukarana a tsakanin halaye biyu na mutum , halin tsanani da halin cuta.
428
17 — Suratul Isra'
raifc&-w
tteex
Ubangijina ne, kuma ba a ba ku
(kome) ba daga ilmi face kacfan."
86. Kuma lalle ne idan Mun so,
haklka, Muna tafiya da abin da
Muka yi wahayi zuwa gare ka.
Sa'an nan kuma ba za ka sami wani
wakili ba dominka game da shi a
kanMu.
87. Face da rahama daga
Ubangijinka. Lalle ne falalarSa ta
kasance mai girma a kanka.
88. Ka ce, "Lalle ne idan mutane
da aljannu sun taru a kan su zo da
misalin wannan Alkur'ani, ba za su
zo da misalinsa ba, kuma ko da
sashinsu ya kasance mataimaki ga
sashi."
89. Kuma lalle ne, haklka, Mun
caccanza domin mutane, a cikin
wannan Alkur'ani, daga kowane
misali, sai mafi yawan mutane suka
ki (kome) face kafirci.
90. Kuma suka ce, "Ba za mu yi
Tmani ba dominka sai ka bubbu-
gar (1) da idan ruwa daga kasa.
9L "Ko kuma wata gona daga
dablnai da inabi ta kasance a gare
ka. Sa'an nan ka bubbugar da kora-
mu a tsakaninta bubbugarwa.
92. "Ko kuwa ka kayar da sama
a kanmu, kabukka, ko kuwa ka zo
da Allah, da mala'iku banga-
banga.
Q^LiVj^
l Jy? 'l>^>— i>J' U J
y ' — v 9S 1 ' -* "£ y y »" y » y y
y^jC&^^^^'f
' '' ^y '/*.' * ' ' ^y^ " '
^—^Zj d^rOt ^>-^ o£oj \
<£$^r .* »y ss s s y , * X'" * '*"'
Ul-S Lib- c^j^j LS *L-2J1 Jailijl
^5fc> ^ -^ y *s**s y\ * y *-y *
f5p *i^i^==^lLJb^^L^"J^
(1) Kaflri ba ya iya hangen abin da ba a iya taba shi daj*abobin ji na jiki, domin haka
suka nemi cfayan wacfannan abubuwa ya auku kamin su yi imani. Mumini yana kange da
ganin baslra, domin haka ya wadatu da zaman Aliair'ani aya mai isa ga ya yi Tmani da shi.
429
17 - Suratul Isra'
il^Bj^-W
93. "Ko kuwa wani gida na zina-
riya ya kasance a gare ka, ko kuwa
ka taka a cikin sama. Kuma ba za
mu yi Imani ba ga takawarka, sai ka
sassauko da wani littafi a kanmu,
muna karanta shi." Ka ce, "Tsarki
ya tabbata ga Ubangijlna ! Ban ka-
sance ba face mutum, Manzo."
94. Kuma babu abin da ya hana
mutane su yi imani, a lokacin da
shiriya ta je musu, face sun ce,
"Shin, Allah zai aiko mutum ya
zamo yana Manzo."
95. Ka ce, "Da mala'iku sun
kasance a cikin kasa, kuma suna
tafiya, suna masu natsuwa, lalle ne
da mun saukar da mala'ika daga
sama ya zama manzo a kansu."
96. Ka ce, "Allah Ya isa zama
Shaida a tsakanina da ku. Lalle ShT
Ya kasance ga bayinSa, mai kidid-
digewa Mai gani."
97. Kuma wanda Allah Ya shi-
ryar, to, shT ne shiryayye, kuma
wanda Ya Batar, to, ba za ka sami
wacfansu masoya a gare su ba bai-
cinSa. Kuma Muna tara su a Ranar
Kiyama a kan fuskokinsu, suna
makafi, kuma bebaye da kurame.
Matattararsu Jahannama ce, ko da
yaushe ta bice, sai Mu kara musu
wata wuta mai tsanani.
98. Wancan ne sakamakonsu,
saboda lalle su, sun kafirta da ayo-
yinMu, kuma suka ce, "Shin idan
muka kasance kasusuwa da nlkak-
kun ga6uBuwa, shin lalle mu, haki-
ka, wacfanda ake tayarwa ne a cikin
wata halitta sabuwa?"
+ •'»<.
a^ji^tU
„> •.•• ** {.
(^= == ^ jl^. 1 ^^ ^u^cy^^J 5
430
17 - Suratul IsraT
»&4-w
5^
99. Shin, kuma ba su ganT (1) ba
(cewa) lalle ne Allah, Wanda Ya
halicci sammai da Rasa, Mai ikon yi
ne a kan Ya halicci misalinsu?
Kuma Ya sanya wani ajali wanda
babu kokwanto a cikinsa? Sai azza-
lumai suka ki face kafirci.
100. Ka ce, "Da dai ku, kuna
mallakar (2) taskokin rahamar
Ubangijina, a lokacin, haklka, da
kun kame, domin tsoron karewar
taskokin. Kuma mutum ya kasance
mai kwauro ne."
101. Kuma lalle ne, haklka, Mun
bai wa Musa ayoyi (3) guda tara
bayyanannu, sai ka tambayi Bam
Isra'ila, a lokacin da ya je musu, sai
Fir'auna ya ce masa, "Lalle ni, ina
zaton ka, ya Musa, sihirtacce."
102. Ya ce, "Lalle ne, hakika, ka
sani babu wanda ya saukar da
warfannan, face Ubangijin sammai
da Rasa, domin su zama abubuwan
lura. Kuma lalle ne ni, haklka, ina
zaton ka, ya Fir'auna, halakakke."
103. Sai ya yi nufin fitar da su
daga kasar, sai Muka nutsar da shi,
shi da wanda yake tare da shi gaba
cfaya.
104. Kuma^Muka ce, daga ba-
yansa ga Bam Isra'Tla, "Ku zauni
3**-J M^t Cy^zo ] &j^J*j* j
/ + y / * y y ~?y s y >x* » x »> "* * -*
y*' y *y<s
^ >-> ,^ y >,'/;*{ If* .
a> jT-" - > * ^ »^ "+y "i.y
' **■ +**>Ky *y ' 9 y. *y f C**'
(1) Mukarana a tsakanin farkon halitta da mayarwa da ita, idan farawa ba ta
buwaya ba, mayarwa ba za ta buwaya ba.
(2) Muka ran a a tsakanin kyautar mutum da rowarsa ga dukiyar da ya mallaka.
(3) Mukarana a tsakanin maganar makangari Fir'auna da Manzon Allah, Musa
domin niina ayar Annabawa ba su tsoron kowa wajen iyar da Manzancin Allah, kuma ba
su ganin wani karfi a gabansu face na Allah.
431
17 — Siiratul Isra'
«&-w
kasar. Sa'an nan idan wa'adin
karshe ya zo, za Mu je da ku
jama'a-jama'a. " (1 }
105. Kuma da gaskiya Muka
saukar da shi, kuma da gaskiya ya
sauka. Kuma ba Mu aike ka ba face
kana mai bayar da bushara, kuma
mai gargacfi.
106. Kuma yana abin karatu,
Mun rarraba shi, domin ka karanta
shi ga mutane a kan jinkiri, kuma
Mun sassaukar da shi sassau-
karwa. (2)
107. Ka ce, "Ku yi miani (3) da
shi, ko kuwa kada ku yi imani, lalle
ne wacfanda aka bai wa ilmi daga
gabaninsa, idan ana karatunsa a
kansu, suna facfuwa ga ha666insu,
suna masu sujada.
108. "Kuma suna cewa: Tsarki
ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle
ne wa'adin Ubangijinmu ya kasan-
ce, hakika, abin aikatawa."
109. Kuma suna facfuwa ga
ha666insu suna kuka, kuma yana
kara musu tsoro.
' %.'*<.,
@5LjJa5^iJ>j
(1) Wannan magana tana kama da da'awar Yahudu cewa yana rubuce a cikin
littafinsu za su koma haduwa bayan rarraba a nan duniya, kuma Hadisin komawar
Yahudu a FalasdTnu, har Musulmi su yi yaki da su, suna a kan ga6ar gabas, kuma su
Yahudawa suna a kan ga6ar yamma daga Kogin Urdun yana karfafa wannan ra'ayi.
Kuma an ruwaito cewa daga cikin alamomin Tashin FCiyama akwai komawar Yahudu a
Falasdinu. Allah ne Mafi sani.
(2) Saukar da Alkur'ani a cikin shekaru ashirin ko ashirin da uku ya yi kama da
saukar ayoyin Musa tara a lokacin da yake kiran Fir'auna zuwa ga addini.
(3) Mukaranar yin Tmani da rashin !manin_ mutane ga Alkur'ani ba zai rage
gaskiyarsa da kome ba, sai dai wadanda suka ki imanin ne za su cutu. Sa'an nan da
bambanci a tsakanin mai ilmi da jahili. Mai ilmi yana da saukin jawuwa zuwa ga gaskiya
har ya rasa abin da zai aikata face ya facfi rikice, a kan ha6arsa, yana mayar da al'amari ga
Allah kuma yana tawali'u.
432
17 - Suratul Isra'
^JM-w
110. Ka ce, "Ku kirayi Al-
lah (1) ko kuwa ku kirayi Mai raha-
ma. Kowane kuka kira, to, Yana da
sunaye mafi kyau. Kuma kada ka
bayyana (2) ga sallarka, kuma kada
ka 66ye ta. Ka nemi hanya a tsaka-
nin wancan."
111. Kuma ka ce, "G6diya (3) ta
tabbata ga Allah Wanda bai riki da
ba, kuma abokin tarayya bai kasan-
ce a gare Shi ba a cikin mulkinSa,
kuma wani masoyi saboda wula-
kancin bai kasance a gare Shi ba."
Kuma ka girmama Shi, girma-
mawa.
>"f >~1\lf'\
Tana karantar da ladubban ibada zuwa ga Allah da yin aiki da
zahirin shari'a da barin dukan abin da ya sa6a wa shari'a.
* j* y , * ^ *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Godiya ta tabbata ga Allah
wanda Ya saukar da Littafi a kan
bawanSa kuma bai sanya karkata
ba a gare shi.
(1) Mukarana a tsakanin sunayen Allah wadanda ake kiran Sa da su wajen roko da
wadanda ba a yin rako da su. Sunayen mafiya kyau da ake kiran Allah da su Hadisi ya
kawo su sai a nema daga Jalalaini.
(2) Kuma tsakaitawa wajen karatun salla ko addu'a kamar yadda aikin Annabi ya
nuna yadda ake yi, kada a bayyana kada a Boye. Sai dai tsaka.
(3) Ka ce, "Allah ba shi da abokin mukarna a kowace jiha. Shi kadai Ya cancanci
girmamawa." Saboda haka ka girmama ShT, girmama war da ta dace da Shi.
433
18 - Suratul Kahf
i<*
-^mm-^
2. Madaidaici, domin Ya yi gar-
gadi da azaba mai tsanani daga gare
Shi, kuma Ya yi bushara ga mumi-
nai, wacfanda suke aikata ayyuka
na kwarai da (cewa) suna da wata
lada mai kyau.
3. Suna masu zama a cikinta har
abada.
4. Kuma Ya yi gargadi ga wa-
cfanda (1) suka ce, "Allah yana da
(fa."
5. Ba su da wani ilmi game da
wannan magana, kuma iyayensu ba
su da shi, abin da ke fita daga
bakunansu ya girma ga ya zama
kalmar facfa ! Ba su facfan kome face
karya.
6. To, ka yi kusa ka halaka ranka
a gurabbansu, wai domin ba su yi
Tmani da wannan labari ba, saboda
bakin ciki.
7. Lalle ne Mu, Mun sanya abin
da ke kan £asa, wata £awa (2) ce
gare ta, domin Mu jarraba su ; wan-
ne daga cikinsu zai zama mafi kyau
ga aiki.
8. Kuma lalle Mu, Masu sanya
abin da ke a kanta (ya zama) tur-
6aya kekasasshiya ne.
• 'i.
$5^ f ,S >S»\ 9 »&
.'»
<'x' ' t *",
U li^lJu-^l^Uo^U^JlSlj
(1) Larabawajsun ce mala'iku 'ya'yan Allah ne. Yahudawa sun ce Uzairu dan Allah
ne, Nasara sun ce Tsa dan Allah ne. Babu ladabi ga fadin wannan magana. Saboda haka
Annabi Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ^a gaya musu, cewa
wannan magana karya ce kuma rashin ladabi ne ga Allah, da ba su yi imani ba, ya ji tsoro
kada ya zama shT ne ya yi kwauron baki ga fada musu gaskiya. Sai Allah Ya gaya masa,
cewa kada ya halakar da ransa domin bakin cikin haka.
(2) Saboda haka kawar kasa, kamar furen itacenta ne, ba su rudin mai hankali ga
tsarewar ladabi tare da Ubangijinsa, da bin shan'ar littafin da aka saukar wa Annabi,
kuma ba a sanya masa karkata ba.
434
18 - SuratulKahf
ij&^-NA
9. Ko kuwa ka yi zaton cewa
ma'abuta kogo (1) da alio sun ka-
sance abin mamaki daga ayoyin
Allah?
10. A lokacin da samarin suka
tattara zuwa ga kogon, sai suka ce,
"Ya Ubangijinmu! (2) Ka ba mu
wata rahama daga gare Ka, kuma
Ka saukake mana (samun) shiriya
daga aramarinmu."
11. Sai Muka yi duka a kan kun-
nunwansu, (3) a cikin kogon, she-
karu masu yawa.
12. Sa'an nan Muka tayar da su,
domin Mu san wane dayan kungi-
yoyin biyu suka fi lissafi ga abin da
suka zauna na lokacin.
13. Mu ne ke jeranta maka la-
barinsu da gaskiya. Lalle ne su,
wacfansu samari ne. Sun yi Imani da
Ubangijinsu, kuma Muka kara
musu wata shiriya.
14. Kuma Muka daure a kan
zukatansu, a lokacin da suka tsayu,
sa'an nan suka ce, "Ubangijinmu
Shi ne Ubangijin sammai da kasa.
Ba za mu kirayi waninSa abin bau-
tawa ba. (Idan mun yi haka) lalle
ne, haklka, mun fadi abin da ya
ketare haddi a sa'an nan."
cJ^>J \J| *^>1 ^^ iSJ^ai
" 9 l\*\A m '\~ > Cl"" : *
JpJL r»-*U <i^ u !*ii t ^i:
4* f .^ l*^
Pa\ . > t^*? i .-Iff" ^^Ctr
(1) Lokacin da Allah Ya ce, kada Annabi ya wahalar da kansa domin bakin cikin ba a
kar6i maganarsa ba, sai Ya ba shi labarin ma'abuta kogo, yadda suka yi gudun hijira da
addininsu, Allah Ya tsare su daga wahala, a cikin halin abin al'ajabi. Sa'an nan kissar ta
tattara a kan ladubba wadanda ake neman mutun ya tsare su tare da Ubangijinsa a cikin
dukan motsinsa, kamar yadda bayani zai nuna.
(2) Sun fara da addu'a ta neman shiriya daga Allah, Ubangijinsu. Addu'a tun farko
ga kome ladabi ne. Kuma farawa da nuna bautarsu ga Ubangiji, ladabi ne. Hijira da
addini, ladabi ne, kuma amincewa da samun rahamar Allah, ladabi ne ga Allah, saboda
haka Allah ya ji6inci tsaron kogon ya zame musu mail kyawun wurin zama.
(3) Duka a cikin kunnuwa, shT ne sanya musu barci.
435
18 - Suratul Kahf
&m-*
15. "Ga wacfannanmutanenmu,
sun riki waninSa abin bautawa!
Don me ba su zuwa da wata hujja
bayyananna a kansu (wacfanda ake
bautawar) ? To, wane ne mafi zalunci
daga wanda ya kaga karya ga
Allah?
16. "Kuma idan kun nisance su,
su da abin da suke bautawa, face
Allah, to, ku tattara zuwa ga kogon,
sai Ubangijinku Ya watsa muku
daga rahamarSa, kuma Ya saukake
muku madogara daga al'ama-
rinku."
17. Kuma kana ganin rana idan
ta fito tana karkata daga kogonsu
wajen dama, kuma idan ta fadi,
tana gurgurar su wajen hagu, kuma
su, suna a cikin wani fili daga gare
shi. Wannan abu yana daga ayoyin
Allah. Wanda Allah Ya shiryar, to,
shi ne mai shiryuwa, kuma wanda
Allah Ya batar, to, ba za ka samar
masa wani majibinci mai shiryarwa
ba.
18. Kuma kana zaton su far-
kakku ne, alhali kuwa su masu barci
ne. Muna juya su wajen dama da
wajen hagu, kuma karensu yana
shimfide da zira'o'in kafafuwansa
ga farfajiya (ta kogon). Da ka leka
(a kan) su (da) lalle ne, ka juya daga
gare su a guje kuma (da) lalle ne ka
cika da tsoro daga gare su.
19. Kuma kamar wannan ne,
Muka tayar da su, domin (1) su
<4UX-\>j Ja~*L> A^Jbi juJJ\cl>taj cfl*±j\
(1) Mahawarar muminai a bayan barcin shekara cfari uku, amma duk da haka suna
cikin hankalinsu suna mayar da al'amari ga Allah.
436
18 - Suratul Kahf
\i<*
%** — lA
tambayi juna a tsakaninsu. Wani
mai magana daga cikinsu ya ce,
"Mene ne lokacin da kuka zauna?"
Suka ce, "Mun zauna yini cfaya ko
sashen yini." Suka ce, "Ubangi-
jinku ne Mafi sani ga abin da kuka
zauna. To, ku aika da cfayanku,
game da azurfarku wannan, zuwa
ga birnin. (1) Sai ya duba wanne ne
mafi tsarki ga abin dafawa, sai ya zo
muku da abinci daga gare shi.
Kuma sai ya yi da hankali, kada ya
sanar da ku ga wani mutum.
20. "Lalle ne su, idan sun kama
ku, za su jefe ku, ko kuwa su mayar
da ku a cikin addininsu, kuma ba za
ku sami babban rabo ba, a sa'an
nan har abada."
21. Kuma kamar wancan ne,
Muka nuna su (gare su) domin su
san lalle wa'adin Allah gaskiya ne,
kuma lalle ne Sa'a babu shakka a
cikinta. A lokacin da suke jayayyar
aFamarinsu a tsakaninsu, (2) sai
suka ce, "Ku gina wani gini a kansu,
Ubangijinsu ne Mafi sani game da
su." Wacfanda suka rinjaya a kan
aFamarinsu suka ce, "Lalle mu riki
masallaci a kansu."
22. Za su ce, "Uku ne da na
hucfunsu, karensu." Kuma suna
cewa, "Biyar ne^da na shidansu
karensu," a kan jTfa a cikin duhu.
Kuma suna cewa, "Bakwai ne da
^* <f -$i^ »> T <
f^rt
CyyjL$\}\ij^^
h\ykj»J„o**>j\
(1) Birnin shi ne Tarasus. Sunan sarkinsu Dalcayanus.
(2) Muhawarar muminai da kafirai, da yadda kafirai ke zartar da al'amari ba da
ambaton yardar Allah Ubangijinsu ba. Da yadda suke yin sari-fadi ga matsalolin ilmi da ya
kamata a mayar da saninsu ga Allah.
437
18 - Suratul Kahf
itfA
•*x» — NA
na takwas cfinsu karensu." Ka ce,
"Ubangijlna (1) ne Mafi sani ga
kidayarsu, babu wanda ya san su
face kacfan." Kada ka yi jayayya
bayyananna. Kuma kada ka yi
fatawa (2) ga kowa daga gare su a
cikin al'amarinsu.
23. Kuma kada lalle ka ce ga
wani abu, "Lalle ni, mai aikatawa
ne ga wancan a gobe."
24. Face idan Allah Ya so. Kuma
ka ambaci Ubangijinka idan ka
manta, kuma ka ce, "T)ammani ga
UbangijTna, Ya shiryar da ni ga abin
da yake shi ne mafi kusa ga wannan
na shiriya."
25. Kuma suka zauna a cikin
kogonsu shekaru cfari uku, kuma
suka dacfa tara.
26. Ka ce, Allah ne Mafi sani ga
abin da suka zauna. Shi ne da (sa-
nin) gaibin sammai da kasa. Mene
ne ya yi ganinSa da jinSa ! Ba su da
wani majiBinci baicinSa, kuma ba
Ya tarayya da kowa a cikin hukun-
cinSa.
27. Ka karanta abin da aka yi
wahayi zuwa gare ka, na littafin
Ubangijinka. Babu mai musan-
yawa ga kalmominSa, kuma ba za
ka sami wata madogara ba daga
waninSa.
rt
>i:i ^ r K1 -^lL^^\ijX^
j^iP;*^
\%djy> de&iiii&Q&J&^j
( 1 ) Bayanin ladubban magana ga matsalolin ilmi da na aiki. Babu wanda ya san gaibu
sai Allah. Ba a tambayar malaman 6ata da son zuciya, domin sari-facfi suke yi ga jawabin
mai tambaya.
(2) Domin haka ba a yin fatawa a wurin malamin bidi'a ko jahili domin zai facfi abin
da yake so, ko kuma ya yi kaddari facfi, jTfa a cikin duhu.
438
18 - Suratul Kahf
gttSflt&M
Yif — M
28. Ka hakurtar da ranka tare da
wacfanda ke kiran Ubangijinsu, safe
da maraice, suna nufin yardarSa.
Kuma kada idanunka su juya daga
barinsu, kana nufin kawar rayuwar
duniya. (1) Kuma kada ka bi wanda
Muka shagaltar da zuciyarsa daga
hukuncinMu, kuma ya bi son zuci-
yarsa, alhali kuwa al'amarinsa ya
kasance yin Barna.
29. Kuma ka ce, "Gaskiya daga
Ubangijinku take." Saboda haka
wanda ya so, to, ya yi Tmani, kuma
wanda ya so, to, ya kafirta. Lalle ne
Mu, Mun yi tattali domin azza-
lumai, wata wuta wadda shama-
kunta sun kewaye da su. Kuma idan
sun nemi taimako sai a taimake su
da wani ruwa kamar dabzar mai,
yana soye fuskoki. Tir da abin shan-
su, kuma wutar ta yi munin zama
mahutarsu.
30. Lalle ne wacfanda suka yi
Tmani kuma suka aikata ayyukan
kwarai, lalle ne Mu, ba Mu tozartar
da ladar wanda ya kyautata aiki.
31. Wacfannan suna da gidajen
Aljannar zama, koramu na gudana
daga karkashinsu, ana sanya musu
kawa, a cikinsu, daga mundaye na
zinariya, kuma suna tufantar wa-
cfansu tufafi kore, na alharini rakiki
da alharini mai kauri, suna kishin-
gicfe a cikinsu, a kan karagu. Ma-
JJqxj**4*-j OjJ^ji ^fb *JXJA v
(1) Ayoyi na ashirin da bakwai da ashirin da takwas suna umurni da bin shari'a ta
AUoir'ani, kuma suna hani daga bin son zuciya domin neman kawar rayuwar duniya
wadda aka yi domin a jarrabi wawa da ita, sa'an nan ta koma turbaya kekasasshiya. Dubi
aya kuma, ta takwas da ta tara. Mun dai sani, cewa umurni da bin shari'a bayyananna shi
ne kan labarin surar.
439
18 - Suratul Kahf
\i<*
-\A
dalla da sakamakonsu. Kuma Al-
janna ta kyautatu da zama wurin
hutawa.
32. Kuma ka buga musu misa-
li (1) da wadansu maza biyu. Mun
sanya wa dayansu gonaki biyu na
inabSbi, kuma Muka kewaye su da
itacen dablnai, kuma Muka sanya
shuka a tsakaninsu (su gonakin).
33. Kowace gona daga biyun, ta
bayar da amfaninta, kuma ba ta yi
zaluncin kome ba daga gare shi.
Kuma Muka BuBBugar da koramu
a tsakaninsu.
34. Kuma dan itace ya kasance
gare shi. Sai ya ce wa abokinsa,
alhali kuwa ^ana muhawara da shi,
"Nine mafTfici daga gare ka a wajen
dukiya, kuma mafi izza a wajen
jama'a."
35. Kuma ya shiga gonarsa, al-
hali yana mai zalunci ga kansa, ya
ce, "Ba ni zaton wannan za ta hala-
ka har abada.
36. "Kuma ba ni zaton Sa'a
mai tsayuwa ce, kuma lalle ne, idan
an mayar da ni zuwa ga Ubangijina,
to, lalle ne, zan sami abin da yake
mafi alheri daga gare ta ya zama
makoma."
37. Abokinsa ya ce masa, alhali
kuwa yana muhawara da shi, "Ashe
ka kafirta da Wanda Ya halitta ka
daga tur6aya, sa'an nan daga cfigon
maniyi, sa'an nan Ya daidaita ka, ka
zama mutum?"
<£$*/" 9 > " y" > Cut"- i \ vTi 1 X K-
Q3 LJLiu \^jk\j^oJ^i
ffrv
(1) Misali ga mai shagala da duniya da kawarta, mai saurin komawa turBaya
kekasasshiya, da mai bin umurnin Allah, mai ladabi da bin sharT'a. Yadda akibar
kowanensu za ta kasance.
440
18 - SuratulKahf
\6<[A.
-NA
38. "Amma ni, ShT ne Allah
Ubangijlna, kuma ba zan tara kowa
da Ubangijina ba.
39. "Kuma don me, a lokacin da
ka shiga gonarka, ka ce, fc Abin da
Allah ya so (shi ke tabbata) babu
wani karfi face game da Allah. ' Idan
ka gan ni, ni ne mafi Jcaranci daga
gare ka a wajen dukiya da cfiya.
40. "To, akwai fatan Ubangijlna
Ya ba ni abin da yake mafi alheri
daga gonarka, kuma ya aika azaba
a kanta (ita gonarka) daga sama, sai
ta wayi gari tur6aya mai santsi.
41. "K6 kuma ruwanta ya wayi
gari fakakke, saboda haka, ba za ka
iya nemo shi ba dominta."
42. Kuma aka halaka dukan
'ya'yan itacensa, sai ya wayi gari
yana juyar da tafunansa biyu, sabo-
da abin da ya kashe a cikinta, alhali
kuwa ita tana kwance a kan rassan-
ta, kuma yana cewa, "Kaitona, da
dai ban tara (1) wani da Ubangijina
bar
43. Kuma wata jama'a ba ta ka-
sance a gare shi ba, wacfanda ke
taimakon sa, baicin Allah, kuma
bai kasance mai taimakon kansa
ba.
44. A can taimako da ji6inta ga
Allah yake^ ShT ne kawai Gaskiya,
Shi ne Mafifici ga lada kuma Mafi-
fici ga akiba.
»*~
p OlJe£ l&ji^ij ijj *x\yt> 12&J
\$\0&>&'f})^
l^iJiilU^
>~V"'-\*
TZ~y0\&*£
■'^^Jj
•*>"
(j£*ivyA>3 v3x^<> 4^l£j
(1) Ya yi nadamar halakar gonar kawai, amma bai yi nadamar kafircin shirkin da ya
yi ba, saboda haka Allah bai mayar masa da badalinta ba. Daga nan kuma ana fahimtar
cewa rashin mai da al'amari ga Allah shirku ne, kuma girman kai saboda dukiya, shirku ne
wanda kawar duniya ke sanya wawaye a ciki.
441
18 - Suratul Kahf
it*.
-\A
45. Ka buga musu misalin ra-
yuwar duniya, kamar ruwa ne wan-
da Muka saukar da shi daga sama
sa'an nan tsirin kasa ya garwaya da
shi, sa'an nanya wayi gari dudduga,
iska tana shikar sa. Kuma Allah
Ya kasance Mai ya wan Ikon yi ne a
kan dukan kome.
46. Dukiya da cfiya, (1) su ne ka-
war rayuwar duniya, kuma ayyuka
masu wanzuwa na kwarai sun fi
zama alheri a wurin Ubangijinka ga
lada kuma sun fi alheri ga buri.
47. Kuma a ranar da Muke ta-
fiyar da duwatsu, kuma ka ga kasa
bayyane, kuma Mu tara su har ba
Mu bar kowa ba daga gare su.
48. Kuma a gitta (2) suga Uban-
gijinka suna sahu guda, (Mu ce
musu), "Lalle ne, hakTka, kun zo
Mana kamar yadda Muka halitta
ku a farkon lokaci. A'a, kun riya
cewa ba za Mu sanya muku wani
lokacin hacfuwa ba."
49. Kuma aka aza littafin ayyu-
ka, sai ka ga masu laifi suna masu
jin tsoro daga abin da ke cikinsa,
kuma suna cewa, "Kaitonmu!
Mene ne ga wannan littafl, ba ya
barin karama, kuma ba ya barin
babba, face ya kididdige ta ?" Kuma
suka sami abin da suka aikata ha-
larce. Kuma Ubangijinka ba Ya
zaluntar kowa.
(1) Dukiya da diya, kawar duniya ne, idan suka zama abin alfahari ga mai su, amma
idan an ciyar da dukiya ga tafarkin Allah, kuma aka karantar da diya ga bisa tafarkin
hanyar shari'a suka tashi Musulmin kwarai, to, sun zama aikin shari'a na Lahira ke nan.
(2) Ba^anin abubuwan da ke aukuwa a wurin hisabi ke nan ga masu bin son zuciya,
su bar shari'a.
442
18 - Suratul Kahf
'&?A
-\A
50. Kuma a lokacin da Muka ce
wa mala'iku, "Ku yi sujada ga
Adamu." Sai suka yi sujada, face
Ibllsa, ya kasance daga aljannu sai
ya yi fSsikanci ga barin umurnin
Ubangijinsa. To fa, ashe, kuna ri-
kon sa, shi da zuriyarsa, su zama
maji6inta, baicin Ni, alhali kuwa su
makiya ne a gare ku? Tir da ya
zama musanya ga azzalumai. (l)
51. Ban shaida musu halittar
sammai da kasa ba, kuma ban
(shaida musu) halittar rayukansu
ba, kuma ban kasance mai rikon
masu Batarwa (da wani) su zama
mataimaka ba.
52. Kuma da ranar da Allah
Yake cewa, "Ku kirayi abokan ta-
rayyaTa, wacfanda kuka riya." Sai
su kiraye su, sai ba za su karba
musu ba, kuma Mu sanya Mau-
bika (2) (Mahalaka) a tsakaninsu.
53. Kuma masu laifi suka ga
Wuta, suka tabbata lalle ne, su
masu auka mata ne, kuma ba su
sami majuya ba daga gare ta.
54. Kuma lalle ne, haklka, Mun
jujjuya, a cikin wannan Alkur'ani,
" ' **» ?
'' * *•"'.
(1) Allah Shi ne Ya halitta jiutane, kuma Ya daukaka darajarsu, domin Ya sanya
mala'iku su yi sujada ga ubansu Adamu. Saboda wannan sdyayyar kuma Ya ba su shan'ar
da za su bi su shiryu har su shiga Aljanna, amma sai suka £i, suka koma wa Shaidan wanda
yake shi ne farkon makiyin ubansu, Adamu, wanda ya £i yi wa sujada, har aka la'ane shi,
suna bin sa, shi da cfiyansa, alhali kuwa babu wani abin da za su iya yi musu na alheri ko na
sharri, domin su ma halitta ne kamarsu. Ba su san kome ba a sama ko a kasa, kuma Allah
ba Ya yin ma'amalar kome da su. Wanda ya bi Shaidan ya bar Allah, to, ya yi mugunyar
musanya, kuma ya zalunci kansa kwarai.
(2) Maubika sunan wani rafi ne na wuta, asalinsa daga 'Wabika, watau ya halaka. Za
a sanya wannan rafi a tsakanin masu bin Shaidan da surorin gumaka, da wanda ya shirya
musu gumakan, suna bauta musu.
443
18 - Suratul Kahf
&mm-s*
daga kowane irin misali ga mutane
(domin su gane, su bi sharT'a), kuma
mutum ya kasance mafi yawan abu
ga jidali. (1)
55. Kuma babu abin da ya hana
mutane su yi Tmani a lokacin da
shiriya ta zo musu, kuma su nemi
gafara daga Ubangijinsu, face han-
yar farko (2) ta je musu ko kuma
azaba ta je musu nau'i-nau'i.
56. Kuma ba Mu aika Manzanni
ba face suna masu bayar da bushara
kuma masu gargacfi, kuma wacfan-
da suka kafirta suna jidali da karya
domin su bata gaskiya da ita, kuma
suka riki ayoyiNa da abin da aka yi
musu gargacfi da shi abin izgili.
57. Kuma wane ne mafi zalunci
daga wanda aka tunatar game da
ayoyin Ubangijinsa, sai ya bijire
daga barinsu, kuma ya manta abin
da hannayensa suka gabatar? Lalle
ne Mu, Mun sanya abubuwan rufi a
kan zukatansu domin kada su fa-
himce shi, kuma a cikin kunnu-
wansu (Mun sanya) wani nauyi,
kuma idan ka klraye su zuwa ga
shiriya, to, ba za su shiryu ba, a
sa'an nan, har abada.
58. Kuma Ubangijinka Mai ga-
fara ne, Ma'abucin rahama. Da
Yana kama su saboda abin da suka
sana'anta, lalle ne, da Ya gaggauta
*$Z. p&j^\&y\&j£
>t?>>^ T\ \-> \>
/»? >
0/-"> "Z */ ^^
> > ,'>
> > >^rr <£'
(1) Jidali, shT ne jayayya, alhali kuwa mutum ya san yana kan karya.
(2) Hanyar farko ita ce Allah Ya halaka su saboda laifinsu, ko kuma azaba ta je musu
nau'i-nau'i, domin su Musulunta, sai karshe idan sun ki, a halaka su. Wadansu sun fassara
'kubala' ko'kibala' da ta fuskance su bayyane, bisa ga karatun kalmar 'kibala' da wasalin
kasa, da ma'anar azaba.
444
18 - Suratul Kahf
i^li^-NA
azaba a gare su. A'a, suna da loka-
cin alkawari, (wanda) ba za su sami
wata makoma ba, baicinsa. (1)
59. Kuma wacfancan alkaryu (2)
Mun halaka su, a lokacin da suka yi
zalunci, kuma Muka sanya lokacin
alkawarin, ga halaka (3) su.
60. Kuma a lokacin da Musa (4)
ya ce wa yaronsa, "Ba zan gushe ba
sai na isa mahatfar teku biyu, ko in
shucfe da tafiya shekara da
shekaru."
61. To, a lokacin da suka isa
mahatfar tsakaninsu, sai suka man-
ta kTfinsu, sai ya kama tafarkinsa a
cikin teku kamar blga.
62. To, a lokacin da suka wuce,
ya ce wa yaronsa, "Ka kawo mana
kalacinmu. Lalle ne halaka, mun
hatfu da wahala daga tafiyarmu
wannan."
63. (Yaron) ya ce, "Ka gani! A
lokacin da muka tattara zuwa ga
falalen nan, to, lalle m, na manta
kTfin, kuma babu abin da ya mantar
da mshi, face Shaidan, domin kada
j> ' * & *'+
^^^&jio*\)-X^^J&y
\jAbO $&&^^\Jl)&
IpU-j^^
$Z
*j
,^> >
'Z'^s * ' '
3 Li^-^^^lji^jt^^ijt-^-^x^ »u
b A J£> LiU ^LSJ^jS IS \jj U. Hid
(1) Watau ba su da wata makoma su bar wannan lokacin alkawarin saukar azabar.
(2) Alkaryun Adawa da Samudawa da wacfansunsu.
(3) Kome Allah zai yi, sai Ya sanya masa lokacin aukuwarsa, kuma ba zai aukun ba
sai ajalin nan da Ya ambata masa ya zo.
(4) Shi ne Musa bn Imran Manzon Bani Isra'ila. Sababin wannan kissa, an tambaye
shine, "Wane ne ya fi ilmi a saninsa?" Sai ya ce, shine ya fi. Wannan jawabi nasa gaskiya
ne, domin shine Manzon zamaninsa, shine aka bai wa Attaura, kuma Allah Ya yi magana
da shi, sai dai ya mance bai ce Allah Ya fi sani ba, domin haka aka ce masa ya tafi neman
ilmi ga warn" mutum a magamar teku biyu. Wannan bawan Allah Haliru ne An ce yana
nan da rai har Ranar Tashin Kiyama. Yaron Musa kuwa, shi ne Yusha'u bn Nunin,
Manzon Allah a bayan Musa. Kifin kuma na guzurinsu ne wanda Allah Ya umurce shi ya
cfauka, soyayye, kuma aka ce musu duka inda yai rai, to, a nan ne Bawan Allah yake, mai
shirin kara wa Musa ilmi. Mayar da ilmi ga Allah, shi ne ladabin shari'a.
445
18 - Suratul Kahf
i<*
«£->A
in tuna shi, sai ya kama tafarkinsa a
cikin teku, da mamaki!"
64. Ya ce, "Wancan ne abin da
muka kasance muna bida." Sai
suka koma a kan gurabunsu, suna
bTbiya.
65. Sai suka sami wani bawa
daga bayinMu, Mun ba shi wata
rahama (1) daga wurinMu, kuma
Mun sanar da shi wani ilmi daga
gunMu.
66. Musa ya ce masa, "Ko in bT
ka a kan ka sanar da ni daga abin da
aka sanar da kai na shiriya?"
67. Ya ce, "Lalle ne kai, ba za ka
iya yin hakuri tare da m ba.
68. "Kuma yaya za ka yi hakuri
a kan abin da ba ka kewaye da shi
ba ga jarrabawa?"
69. Ya ce, "Za ka same ni, in
Allah Ya so, mai hakuri, kuma ba
zan sa6a maka ba ga wani umurni."
70. Ya ce, "To, idan ka blni, to,
kada ka tambaye ni daga kome sai
na labarta maka ambato (2) daga
gare shi."
71. Sai suka tafi, har a lokacin da
suka hau a cikin jirgi, ya huje shi, ya
ce, "Ka huje shi domin yajiutsar da
mutanensa? Lalle ne, haklka, ka zo
da wani babban abu!"
l>jbC^JuJli^lSCl4'iJU
* s * ' >
(1) Rahama a nan ita ce Annabci saboda cewa kuma an ba shi ilmi daga gun Allah,
kuma ya yi hukunci da shi. Ilmin ilhama ba a yin hukunci da shi domin Annabawa kawai
Allah Ya tsare daga kuskure game da wahayi. Wannan ne bambanci bayyananne a
tsakanin wahayin Annabci da wahayin walicci. Haka mu'ijiza da karama, su duka sabawar
al'ada ne, amma mu'ujizar Annabi an san za ta zo daga bakin wanda aka yi dominsa,
amma karama babu mai saninta, sai ta auku. Saboda waliyyi ba ya iya yin takara, amma
annabi yana iya yin takara a kan makiyansa.
(2) Watau sai na gaya maka hukuncinsa da kaina, kuma na ambace shi da kaina.
446
18 - Suratul Kahf
\i<*
-\A
72. Ya ce, "Ashe, ban ce, lalle
kai, ba za ka iya yin hakuri tare da
m ba?"
73. Ya ce, "Kada ka kama ni da
abin da na manta, kuma kada ka
kallafa mini tsanani ga aFamarlna."
74. Sai suka tafi, har suka hacfu
da wani yaro, sai ya kashe shi. Ya ce,
"Ashe, ka kashe rai tsarkakakke, ba
da wani rai ba? Lalle ne, hakika, ka
zo da wani abu na kyama."
75. Ya ce, "Shin, ban ce maka ba,
lalle ne kai ba za ka iya yin hakuri
tare da nlba?"
76. Ya ce, "Idan na tambaye (1)
ka daga wani abu a bayanta, to,
kada ka abuce ni. Lalle ne, ka isa ga
iyakar uzuri daga gare ni."
77. Sai suka tafi, har a lokacin da
suka je wa mutanen wata alkarya,
suka nemi mutanenta da su ba su
abinci, sai suka £i su yi musu liyafa.
Sai suka sami wani bango a cikinta
yana nufin ya karye, sai (Haliru) ya
tayar da shi mike. (Musa) ya ce,
"Da ka so, lalle ne da ka karbi ijara
a kansa."
78. Ya ce, "Wannan shi ne rabu-
war tsakanina da tsakaninka. Za ni
gaya maka fassarar abin da ba ka
iya yin hakuri ba a kansa.
£ +*1 "is '
I.I 1«* I *\\ \\ —
59 ft
» ^ y
-' ' st, "* y+
J^^o^WWe ♦
^. '>
S ' •'+'', ' f
OJ^ol^Jte^^ol^feoiaijo'
(&)lj>Uj&
(1 ) Musa ya kasa yin ha£uri a bayan ya yi alkawura cewa zai yi ha£uri, saboda ba ya
halatta ga mutum ya ga abin da ya saba wa sharTa, sa'an nan ya yi shiru. Da zai halatta a yi
shim, da Musa bai yi magana ba ga aikin malamin da Allah Ya umurce shi da ya tafi ya
karbo ilmi daga gare shi, a bayan Ya gaya masa cewa, Ya ba shi wani ilmi daga gare Shi.
Domin sharadin da ya sa6a wa shari'a warwararre ne. Saboda haka Allah bai zargi Musa
ba a bayan sun rabu. Sake munkar wajibi ne a cikin ladubban shari'a gwargwadon hali,
kamar yadda yake a cikin HadTsi. Ana gabatar da hukuncin da ya fi tsanani.
447
18 - Suratul Kahf
fi^ii^-u
79. "Amma jirgin, to, ya zama
na wadansu matalauta ne, suna
aiki (1) a cikin teku, sai na yi niyyar
in aibanta shi, alhali kuwa wani
Sarki ya kasance a gaba gare su,
yana karBewar kowane jirgi (lafi-
yayye) da kwace.
80. "Kuma amma yaron, to,
uwayensa sun kasance muminai, to,
sai muka ji tsoron ya kallafa musu
kangara da kafirci.
81. "Sai muka yi nufin Ubangi-
jinsu Ya musanya musu mafl alheri
daga gare shi ga tsarkakuwa, kuma
mafl kusantar tausayi.
82. "Kuma amma bangon, to, ya
kasance na wacfansu yara biyu ne,
marayu a cikin birnin, kuma akwai
wata taska tasu a karkashinsa,
kuma ubansu ya kasance sahlhin
mutum (2) ne, domin haka Ubangi-
jinka Ya yi nufin su isa iyakar kar-
finsu, kuma su, su fitar da taskarsu,
saboda rahama ne daga Ubangi-
jinka. JCuma ban yi shi ba daga
umurnlna. Wancan shT ne fassarar
abin da ba ka iya yin hakuri ba a
kansa."
^-~^ cfirlj* *[?) o& >lu) \wj
(1) Watau wani kamfani ne na matalauta, suna sana'ar cfaukar kaya a cikin teku.
Sharika watau kamfani a ciniki ya halatta da sharudtfansa.
(2) Wannan ya nuna cewa kirkin uba yana amfanin cfiyansa, haka gari na daraja
saboda samun mutanen kirki a cikinsa, kamar yadda yake kaskanta da kaskancin
mazaunansa bisa dalilin da farko an kira garin 'alkarya' saboda rowar mazauna, kuma aka
kira shi Madina saboda darajar yaranjian biyu da ubansu da taskarsu. Alkarya ita ce
karamin gari watau kauye, kuma Madina ita ce babban gari.
448
18 - Suratul Kahf
i<*
-\A
83. Kuma suna tambayar ka
daga Zulkarnaini, (1) ka ce, "Zan
karanta muku ambato daga gare
shi."
84. Lalle ne Mu, Mun ba shi
mulki a cikin kasa, kuma Muka ba
shi daga kowane abu, hanya (zuwa
ga muradinsa).
85. Sai ya bi hanya.
86. Har a lokacin da ya isa ga
mafacfar rana, kuma ya same ta
tana Bacewa a cikin wani ruwa mai
bakar laka, kuma ya sami wadansu
mutane a wurinta. Muka ce, "Ya
Zulkarnaini, imma dai ka azabtar,
kuma imma ka riki kyautatawa a
cikinsu."
87. Ya ce, "Amma wanda ya yi
zalunci, to, za mu azabta shi, sa'an
nan a mayar da shi zuwa ga Ubangi-
jinsa, sai kuma Ya yi masa azaba,
azaba abar kyama.
88. "Kuma amma wanda ya yi
Tmani kuma ya aikata aikin kwarai,
to, za mu yi sakamako a gare shi
(watau kyauta) mai kyau, (2) kuma
za mu gaya masa sauki daga umur-
ninmu."
89. Sa'an nan kuma ya bi hanya.
^f> • >"- ¥ A'
►^ . >>»^i^y^^
^k x +" 'SX'
Wl \ >jU J&Jo JauB
x "' 'ffi
cr
(1) Zulkarnaini an ce Sarki ne yana bin shari'ar Ibrahim, ga hannunsa ya musulunta,
sunansa Askandar. Haliru Wazirinsa ne yana tafiya a gaban yakinsa, kuma dan innarsa,
watau (fan Khalarsa ne. Shi ne ya gina Askandariyya. Sai dai ga maganar akwai warware
juna. Allah Ya sani. Abin dajce a gabaninmu a nan, shi ne sanin cewa Allah Ya ba shi
mulki, ya ko yi shi bisa sharl'a, ya yi karfi, da karfin Allah.
(2) Kyauta mai kyau a nan ba Aljanna ba ce, domin maganar ta Zulkarnaini ce, idan
ya ci kasa, yana iya sanya masu Imaninta a cikin hali mai kyau. Amma idan an cfauki
maganar, ta Allah ce, a cikin maganar Zulkarnaini ga kafiri, to, a nan 'mai kyau' sai ta
zama Aljanna ke nan.
449
18 - Suratul Kahf
a#3ij&->A
90. Har a lokacin da ya isa ga
mafitar rana, ya same ta tana fita a
kan wacfansu mutane (wacfanda) ba
Mu sanya musu wata kariya ba
daga barinta.
9L Kamar wancan, alhali kuwa,
haklica, Mun kewaye da jarrabawa
ga abin da ke gunsa.
92. Sa'an nan kuma ya bi hanya.
93. Har a lokacin da ya isa a
tsakanin duwatsu biyu, ya sami
wadansu mutane daga gabaninsu.
Ba su yi kusa su fahimci magana ba.
94. Suka ce, "Ya Zulkarnaini!
Lalle ne Yajuja da Majuja masu
6arna ne a cikin kasa. To, ko za mu
sanya haraji saboda kai, a kan ka
sanya wani danni a tsakaninmu da
tsakaninsu?"
95. Ya ce, "Abin da Ubangijlna
Ya mallaka mini, a cikinsa ya fi
zama alheri. Sai ku taimake ni da
karfi, in sanya babbar katanga a
tsakaninku da tsakaninsu.
96. "Ku kawo mini guntayen ba-
kin karfe". (Suka kai masa) har a
lokacin da ya daidaita a tsakanin
duwatsun biyu (ya sanya wuta a
cikin karfen) ya ce, "Ku hura (da
zugazugai)." Har a lokacin da ya
mayar da shi wuta, ya ce, "Ku kawo
mini gaci (narkakke) in zuba a
kansa."
97. Domin haka ba za su iya
hawansa ba, kuma ba za su iya
hujewa gare shi ba.
98. Ya ce, "Wannan wata raha-
ma ce daga Ubangijina. Sai idan
l^ (ill JoJf J^^jV l^oj juJu
,J ->pr^J
ft ±*
"Tv* ** yy + y > * y "^y ** y * ^ & s »s s * y s
450
18 - Suratul Kahf
FXftlfca.
-NA
wa'adin (1) Ubangijina ya zo, ya
mayar da shi nikakke. Kuma
wa'adin Ubangijina ya kasance
tabbatacce."
99. Kuma Muka bar sashensu a
ranar nan, yana garwaya a cikin
sashe, kuma aka busa a cikin kaho,
sai muka tara su, tarawa. (2)
100. Kuma Muka gitta Jahan-
nama, a ranar nan ga kafirai git-
tawa.
101. Wacfanda idanunsu suka
kasance a cikin rufi daga tuna (3) Ni,
kuma sun kasance ba su iya saura-
rawa.
102. Shin fa, wacfanda suka ka-
firta sun yi zaton (daidai ne) su riki
wadansu bayiNa, (4) maji6inta bai-
ciNa? Lalle ne, Mun yi tattalin
Jahannama ta zama liyafa ga ka-
firai.
103. Ka ce^'Ko mu gaya muku
game da mafifita hasara ga ayyuka?
Cp U>- <J*l) -tejovj
(1) Wa'adin Ubangiji da fitdwar Yajuj da Majuj. A yanzu babu wanda ya san inda
suke zaune, sai Allah.
(2) Allah Ya nuna yadda halin da Zulkarnaini ya bar Yajuj da Majuj, watau sun
garwaya a cikin junansu, sa'an nan kuma wannan ma'anar aka bayar da ita ga mutane
wacfanda ke bin son ransu, ba su bin shari'ar Allah, suna hargitse a tsakaninsu, har a yi
busar farko, su mutu, kuma a yi busa ta biyu su tashi a cikin hargitsinsu, sai kuma a gitta
Jahannama gaba gare su.
(3) Zikr — tunawa — shi ne Alkur'ani da abin da ya tara na ibada da sauran
ma'amaloli, dukansu ibada ne, matukar an blabin da Allah Ya ajiye a cikinsu na hukunce-
hukunce.
(4) Wacfanda suka riki wasu bayin Allah, suna bauta musu, kamar Yahudu masu
bauta wa Uzairu da Nasara masu bauta wa Tsa da wasu Musulmi masu bauta wa wasu
salihai, sun zama kafirai. Ma'anar bautawar shi ne su kirkira wasu hukunce-hukunce ko
wasu sifofi wadanda suka sa6a wa maganar Alkur'ani da Hacfisi, sa'an nan su jingina su
zuwa ga wacfannan bayin Allah, su bi su da su.
451
18 - Suratul Kahf
w&\m-^
104. "Wacfanda aikinsu ya Bace
a cikin rayuwar duniya, alhali kuwa
suna zaton lalle ne su, suna kyau-
tata (abin da suke gani) aikin kwa-
rai?"
105. Wacfancan ne wacfanda
suka kafirta da ayoyin Ubangijinsu,
da kuma hatfuwa da Shi, sai ayyu-
kansu suka 6aci. Saboda haka ba za
Mu tsayar musu da awo (1) ba a
Ranar Kiyama.
106. Wancan ne, sakamakonsu
shT ne Jahannama, saboda kafir-
cinsu, kuma suka riki ayoyiNa da
ManzanniNa abin izgili.
107. Lalle ne, wadanda suka yi
imani kuma suka aikata ayyuka na
kwarai, Aljannar Firdausi ta ka-
sance ita ce liyafa a gare su.
108. Suna madawwama a ci-
kinta, ba su neman makarkata daga
barinta.
109. Ka ce, "Da teku (2) ta kasan-
ce tawada ga (rubutun) kalmomin
Ubangijina, lalle ne da tekun ta
kare a gabanin kalmomin Ubangi-
jina su kare, kuma ko da mun je da
misalinsa domin kari."
110. Ka ce, "Nl, mutum ne ka-
wai kamarku, ana yin wahayi zuwa
gare ni cewa: Lalle ne, Abin bauta-
warku, Abin bautawa Guda ne,
5P ^^^yjp(^#c?^(»4^»oiw*-
(1) Watau ko aunawa ba za a yi ba balle a daidaita ma'auni.
(2) Ma'anar ayar nan ita ce Allah ne Mafi sani. Ilmin Allah ba shi da iyaka, ko kalmomin
da suka tfauki ma'anoninsa, ba za a iya rubuta su ba, balle ma'anonin da ke cikinsu.
Saboda haka abin da ke hankali ga mutum, shT ne ya yi aiki da dan ilmin da Allah Ya
umurce shi da aiki da shi. Idan ya nemi ya wuce nan, to, ya halakar da kansa domin bai san
inda zai fada ba. Wannan ilmin shi ne shari'a da aiki da ita.
452
19 — Suratu Maryam
vmm-*
saboda haka wanda ya kasance
yana fatan harfuwa da Ubangijinsa,
to, sai ya yi aiki na kwarai. Kuma
kada ya hatfa kowa ga bauta wa
Ubangijinsa." (1)
^ ijJi^J oi^ii^Vj
Tana karantar da hikimar samun diya da 'ya'ya ga mutane da
tsarkake Allah daga haka.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L K.H.Y.'I.S.
2. Ambaton rahamar Ubangijin-
ka ne ga BawanSa Zakariyya.
3. A lokacin da ya kirayi
Ubangijinsa, kira Boyayye.
4. Ya ce, "Ya Ubangijina! Lalle
ne m, Rashi na daga gare ni ya yi
rauni, kuma kaina ya kunnu da
furfura, kuma ban kasance maras-
hin arziki ba game da kiranKa, ya
Ubangiji !
(1) Wannan aya, a dun£ule, ta tara dukan abin da ke cikin siirar. Allah Ya shiryar da
mu, ga kadaita Shi ga ibada, da yin ibadar, kuma yadda Allah Ya ce a yi ta, ga mai tsammanin
rabo a Lahira. Wanda ba ya tsammanin rabon Lahira, ya tsaya ga duniya mai gushewa da
sauri, to, shT ba a shiga batunsa ba.
453
19 — Suratu Maryam
fiS^?i&-u
5. "Kuma lalle ni, na ji tsoron (1)
dangi a bayana, kuma matata ta
kasance bakarariya! Sai ka ba ni
wani mataimaki daga wajenKa.
6. "Ya gaje ni, kuma ya yi gado
daga gidan Yakuba. Kuma Ka
sanya shi yardajje, ya Ubangiji!"
7. (Allah Ya karba) "Ya
Zakariyya! Lalle ne Mu, Muna yi
maka bushara da wani yaro, sunan-
sa Yahaya. Ba Mu sanya masa wani
takwara ba a gabani."
8. Ya ce, "Ya UbangijTna! Yaya
wani yaro zai kasance a gare ni,
alhali kuwa matata ta kasance ba-
karariya, kuma ga shi na kai ga
matuka ta tsufa?"
9. Ya ce, "Kamar wancan Uban-
gijinka Ya ce. Shi a gare Ni mai
sauki ne, kuma haklka Na halitta
ka a gabanin haka, alhali ba ka
kasance kome ba."
10. Ya ce, "Ya Ubangijina! Ka
sanya mini alama." Ya ce, "Ala-
marka ita ce ka kasa yi wa mutane
magana a daruruwa uku daidai."
77. Sai ya fita a kan mutanensa
daga masallaci, sa'an nan ya yi
ishara zuwa gare su da cewa, "Ku yi
tasblhi safe da yamma."
12. Ya Yahaya! Ka kama littafi
da karfi. Kuma Muka ba shi hu-
kunci yana yaro. (2)
•V'l- fi-^i' 1
► -» .- s <.'
(1 ) Amfanin samun da ga mutumin kirki shi ne domin ya gaji kirkin kuma ya taimaki
sauran danginsa, ya rayar da gida. Kuma wanda ba mutumin kirki ba yana yiwuwa ya
sami dan kirki mai shiryar da shi zuwa ga hanyar icwarai.
(2) Yahaya dan Zakariyya, shi ne Annabi da aka bai wa hukunci tun yana yaro.
Kuma shi ne mai bayar da bushara da Tsa, amincin Allah ya tabbata a gare su.
454
19 — Suratu Maryam
05§g?i&-«
13. Kuma (Muka sanya shi) abin
girmamawa daga gunMu, kuma
mai albarka, kuma ya kasance mai
cfa'a da takawa.
14. Kuma mai biyayya ga
mahaifansa biyu, kuma bai kasance
mai girman kai mai sa6o ba.
15. Kuma aminci ya tabbata a
gare shi a ranar da aka haife shi da
ranar da yake mutuwa da ranar da
ake tayar da shi yana mai rai.
16. Kuma ka ambaci Mar-
yamu (1) a cikin Littafi, a lokacin da
ta tsallake daga mutanenta a wani
wuri, a gefen gabas.
77. Sa'an nan ta riki wani sha-
maki daga barinsu. Sai Muka aika
ruhinMu zuwa gare ta. Sai ya bay-
yana a gare ta da siffar mutum
madaidaci.
18. Ta ce, "Lalle ni, ina neman
tsari ga Mai rahama daga gare ka,
idan ka kasance mai tsaron
addini!"
19. Ya ce, "Abin sani kawai, ni
Manzon Ubangijinki ne domin in
bayar da wani yaro tsarkakke gare
ki."
20. Ta ce, "A ina yaro zai kasan-
ce a gare ni alhali kuwa wani mutum
bai shafe ni ba, kuma ban kasance
karuwa ba?"
21. Ya ce, "Kamar wancan
Ubangijinki Ya ce, 'Shi a gare Ni
5p iW*£^J^j^>)J^
"*/ *Y. Sx ' » . >
~'\"
S> s ^ .
>i *s*iS+f'<, <.'
^^^%^Jjv&^>l^
^=F=t>
opj^^o^sj^ollS
V^&J*^j$>^J&i JS
(1) An fara da kissar Maryamu domin a nuna sakamakon da aka yi mata da samun
dan kirki saboda kasancewarta mutumiyar kirki, kuma da nuna cewa Annabi Tsa ba cfan
Allah ba ne.
455
19 — Suratu Maryam
&®®k-\\
mai sauki (1) ne. Kuma domin Mu
sanya shi wata alama ga mutane,
kuma wata rahama ce daga gare
Mu.' Kuma abin ya kasance wani
al'amari hukuntacce."
22. Sai ta yi cikinsa, sai ta tsalla-
ke da shi ga wani wuri mai msa.
23. Sai nakuda ta kai ta zuwa ga
wani kututturun dablniya, ta ce,
"Kaitona, da dai na mutu a gabanin
wannan kuma na kasance wani abu
wulakantacce wanda aka manta!"
24. Sai (yaron da ta haifa) ya (2)
kira ta daga karkashinta, "Kada ki
yi bakin ciki! Haklka Ubangijinki
Ya sanya wani marmaro a karka-
shinki.
25. "Kuma ki girgiza zuwa gare
ki game da kututturun dabinon ya
zuba a kanki yana 'ya'yan dabino,
rucfabi nunannu.
26. "Sai ki ci, kuma ki sha, kuma
ki ji sanyi ga idanunki. (3) To, idan
kin ga wani cfaya daga mutane, sai
ki ce, 'Lalle nT, na yi alwashin azumi
domin Mai rahama, saboda haka
ba zan yi wa wani mutum magana
baV
-t^r^D
(1) ^/fala'ikin da ya je ga Maryama a cikin surar mutum Jibnlu ne, Ya hura a cikin
wuyan rigarta, sai ta yi ciki da Tsa.
(2) Annabi Tsa, amincin Allah ya tabbata a gare shi, ya fara magana ga uwarsa tun a
lokacin da aka haife shi yana a karkashin uwarsa. Gudanar ruwan marmaro a karkashinta
da fitar da 'ya'yan dabino daga kututturun dabino, alamu ne masu nuna cewa Allah na iya
halitta jariri ba da uba ba, kuma Yana tayar da matattu daga kabarinsu ba da wata wahala
ba.
(3) Jin sanyi ga idanu shi ne farin cikin saboda samun haihuwa. Ga ibadar BanI
Isra'ila, mai azumi ba ya yin magana, amma ga Musulunci Allah Ya shafe wannan
hukunci. Mai azumi yana magana sai dai ana son ya kama bakinsa daga maganar da ba ta
ibada ba.
456
19 — Suratu Maryam
£^?i$&-«
27. Sai ta je wa mutanenta tana
cfauke da shi. Suka ce, "Ya Marya-
mu ! Lalle ne, haklka, kin zo da wani
abu mai girma!
28. "Ya 'yar'uwar Haruna!
Ubanki bai kasance mutumin alfa-
sha ba, kuma uwarki ba ta kasance
karuwa ba."
29. Sai ta yi ishara zuwa gare shi,
suka ce, "Yaya za mu yi magana da
wanda ya kasance a cikin shimficfar
tsumma yana janri?"
30. Ya ce, "Lalle ne, nl bawan
Allah ne, Allah Ya ba ni Littafi
kuma Ya sanya ni Annabi. (1)
31. "Kuma Ya sanya ni mai al-
barka a inda duk na kasance, kuma
Ya umurce ni da yin salla da zakka
matukar ina da rai.
32. "Kuma mai biyayya ga uwa-
ta, kuma bai sanya ni mai kaushin
zuciya ba marashin alheri.
33. "Kuma aminci ya tabbata a
gare ni a ranar da aka haife ni da
ranar da nake mutuwa da ranar da
ake tayar da ni ina mai rai."
34. Wancan ne Tsa dan Marya-
mu, maganar gaskiya wadda suke
shakka a cikinta.
35. Ba ya kasancewa ga Allah Ya
riki wani cfa. (2) Tsarki ya tabbata a
>e>i
*JlS]
\' \*> ' 7 y
' y .
|p ll^)S^(^-^^Jc^^^)Jri?
S'S> «. ' >
r-*->
•.^»^>»f ^
^^^l^J^r^^l^-J^^jj
t>x ^ ^
(1) Wannan ita ce maganar da Tsa ya yi wa mutanen uwarsa domin ya barrantar da ita
daga tuhuma, kuma ya nuna matsayinsa ga Allah da mukaminsa na Annabci.
(2) Ba ya kasancewa ga Allah Ya riki cfa, domin ba Ya mutuwa balle Ya yi bukatar
mai gado ga tsaron dukiya. Shi kacfai ne, ba Ya bukatar wani cfa mai tsaron dangi domin
kada su bar hanya.
457
19 — Suratu Maryam
«^l^-«
gare shi! Idan Ya hukunta wani
aramari, sai kawai Ya ce masa,
"Kasance." Sai ya dinga kasan-
cewa.
36. u Kuma lalle Allah ne Uban-
gijina (1) kuma Ubangijinku, sai ku
bauta Masa. Wannan shi ne tafarki
madaidaici."
37. Sai icungiy6yin (2) suka saBa
wa juna a tsakaninsu. To, bone ya
tabbata ga wacfanda suka kafirta
daga halartar yini mai girma.
38. Mene ne ya yi jinsu, (3) kuma
mene ne ya yi ganinsu a ranar da
suke zo Mana! Amma azzalumai
suna a cikin Bata bayyananna.
39. Kuma ka yi musu gargacfi da
ranar nadama a lokacin da aka
hukunta al'amari, alhali kuwa suna
a cikin Bata, kuma su ba su yin
Tmani.
40. Lalle ne Mu, Mu ne ke ga-
don kasa (4) da wanda yake a kanta,
kuma zuwa gare Mu ake mayar da
su.
\^o]fe{£& Oj^V^^^ai \*\
ftp pk^^ j^ii &
> c>.?,
P <^*^^b ^cs*jJ6^ \&J><y* %
(1) Tana a cikin maganar Tsa a lokacin da ya girma yana wa'azi ga mutanensa.
Saboda haka aka raba ta da maganar farko a lokacin da yake janri.
(2) Bayan dauke Annabin Allah Tsa dan Maryama kungiyoyin mutane sun saba wa
junansu a cikin sha'aninsa. Yahudu suna sukar sa, Nasara suka kasu uku : Nasturiyya suka
ce, "Shi dan Allah ne", Malakaniyya suka ce, "Shi ne na uku din uku," Ya'akubiyya, suka
ce, "Shi ne Allah." Saboda haka Nasara suka haihaye kuma suka zurfafa, sa'an nan Yahudu
suka takaita kuma suka yi suka gare shi.
(3) A ranar Lahira a lokacin da ake yi musu hisabi a gaban Allah ganinsu da jinsu
suna da kyau kwarai, amma a nan duniya suna a cikin makanta da kurumci saboda batar
da suka yi, suka karyata Tsa, aminci ya tabbata a gare shi.
(4) Tun da yake Mu ke gadon kasa da wanda yake a cikinta, ba za Mu yi bukatar
samun wani magaji ba.
458
19 — Suratu Maryam
(%&>ji&-\\
41. Kuma ambaci Ibrahim (1) a
cikin Littafi. Lalle shi ya kasance
mai yawan gaskatawa, Annabi.
42. A lokacin da ya ce wa uban-
sa, "Ya baba! Don me kake bauta
wa abin da ba ya ji, kuma ba ya ga
ni, kuma ba ya wadatar da kome
daga barinka?
43. "Ya baba! Lalle ni, hakika,
abin da bai je maka ba na ilmi ya zo
mini, saboda haka ka bi ni in shiryar
da kai wani tafarki madaidaici.
44. "Ya baba ! Kada ka bauta wa
Shaicfan. Lalle Shaicfan ya kasance
mai sa6awa ga Mai rahama.
45. "Ya baba! Lalle ne ni ina
tsoron wata azaba daga Mai raha-
ma ta shafe ka, har ka zama masoyi
ga Shaicfan."
46. Ya ce, "Ashe, mai gudu^ne
kai daga gumakana? Ya Ibrahlrn !
Lalle ne, idan ba ka hanu ba, haki-
ka, zan jefe ka. Kuma ka kaurace
mini tun kana mai mutunci."
47. Ya ce, "Aminci (2) ya tabbata
a gare ka! Zan nemi Ubangijina Ya
gafarta maka. Lalle Shi Ya kasance
Mai girmamawa gare ni.
48. "Kuma ina nisantar ku da
abin da kuke kira, baicin Allah,
kuma ina kiran Ubangijina,
+ * ' y * *<*
l^^J4iBo|ci
(1) Ibrahim ya yi kokarin shiryar da ubansa, sai dai Allah bai nufi shiryuwarsa ba.
Daga cikin amfanin haihuwa akwai abin haihuwa ya shiryar da mahaiflnsa, ya yi masa
nasiha gwargwadon hali.
(2) Ibrahim ya mayar da magana mai kyau da laushi da aminci ga maganar ubansa
mai muni da gautsi da tsoratarwa. Wannan yana koyar da yadda ake kira zuwa ga Allah da
kuma yadda ya kamata a tausasa wa uba ko da shi kafiri ne.
459
19 — Suratu Maryam
£&%&-*
tsammanin kada in zama marashin
arziki game da kiran Ubangijina."
49. To, sa'ad da ya nisance su
da abin da suke bautawa, baicin
Allah, Muka ba shi Is'haka da
Ya'akuba, alhali kuwa kowanensu
Mun mayar da shi annabi.
50. Kuma Muka yi musu kyauta
daga RahamarMu, kuma Muka
sanya musu harshen gaskiya (1)
macfaukaki.
51. Kuma ka ambaciMusa a ci-
kin Littafi. Lalle ne shi, ya kasance
za6a66e, kuma ya kasance Manzo,
Annabi.
52. Kuma Muka kira shi daga
gefen dutse na dama, kuma Muka
kusanta shi yana abokin ganawa.
53. Kuma Muka yi masa kyauta
daga RahamarMu da cfan'uwansa
Haruna, ya zama Annabi.
54. Kuma ka ambaci Isma'ila a
cikin Littafi. Lalle shi, ya kasance
mai gaskiyar alkawari, kuma ya
kasance Manzo, Annabi.
55. Kuma ya kasance yana
umurnin mutanensa (2) da salla da
zakka. Kuma ya kasance yardajje
a wurin Ubangijinsa.
56. Kuma ka ambaci Idrisa a
cikin Littafi. Lalle shi, ya kasance
mai yawan gaskatawa, Annabi.
m\^
f&S^ V? ' K ^ y / //
\J^&%^^
(1) Harshen gaskiya, shi ne yabo mai kyau daga Allah da mutane. Wanda ya yanke
wa mutanensa domin Allah, to, zai saka masa da wacfansu mutanen kirki, domin su debe
masa kewa.
(2) Matarsa da 'ya'yansa da Jurhum, yana umurninsu da salla da zakka. Yana
wajaba ga mutum ya umurci iyalinsa da tsare hakkokin Allah.
460
19 — Suratu Maryam
fi^J&-W
57. Muka cfaukaka shi a wuri
macfaukaki.
58. Wacfancan su ne wacfanda
Allah Ya yi wa ni'ima daga Anna-
bawa daga zuriyar Adamu, kuma
daga wacfanda muka cfauka tare da
Nuhu, kuma daga zuriyar Ibrahim
da Isra'ila, kuma daga wacfanda
Muka shiryar kuma Muka zabe su.
Idan ana karatun ayoyin Mai raha-
ma a kansu, sai su facfi suna masu
sujada kuma masu kuka.
59. Sai wacfansu 'yan baya (1)
suka maye a bayansu suka tozarta
salla, kuma suka bi sha'awowinsu.
To, da sannu za su hacfu da wani
sharri.
60.^ Face wanda ya tuba, kuma
ya yi imani, kuma ya aikata aiki na
kwarai. To, wacfannan suna shiga
Aljanna, kuma ba a zaluntar su da
kome.
61. Gidajen Aljannar zama wad-
da Mai rahama ya yi alkawarin
bayarwa ga bayinSa (masu aikin
Imani) a fake. Lalle ne Shi, alka-
warin ya kasance abin riskuwa.
62. Ba su jin yasassar magana a
cikinta, face sallama. Kuma suna da
abinci, a cikinta, safe da maraice.
63. Wancan Aljannar ce wadda
Muke gadar da wanda ya kasance
mai aiki da takawa daga bayiNa.
p t (gji^i^^\c4\;
j'./ f'^rfy
<,*
»>^. a
(1) An ruwaito cewa wannan zai auku a lokacin Tashin BCiyama ne a bayan tafiyar
salihan wannan al'umma ta Muhammadu. Za su dinga barbarar junansu a cikin hanyoyi.
Su tozarta salla, su gina manyan gidaje su hau dukan abin da aka hana su, su tufanci abin
da aka hana su. Kurcfabi.
461
19 — Suratu Maryam
&m%&-\\
64. (Suna masu cewa) "Kuwa ba
mu sauka (1) face da umurnin
Ubangijinka (Muhammad). ShT ne
da mulkin abin da ke a gaba gare
mu da abin da ke a bayanmu da
abin da ke a tsakanin wannan."
Kuma (2) Ubangijinka bai kasance
Wanda ake mantawa ba.
65. Shi ne Ubangijin sammai da
kasa da abin da yake a tsakaninsu.
Sai ka bauta Masa, kuma ka yi
hakuri ga bautarSa. Shin, ka san
wani takwara a gare Shi?
66. Kuma mutum yana cewa,
"Shin, idan na mutu, lalle ne, hakl-
ka, da sannu za a fitar da ni ina mai
rai?"
67. Shin, kuma mutum ba zai
tuna ba cewa lalle ne Mun halitta
shi a gabani, alhali kuwa bai kasan-
ce kome ba?
68. To, Muna rantsuwa da
Ubangijinka, lalle ne, Muna tayar
da su da kuma shaidanun, sa'an
nan, kuma, lalle Muna halartar da
su da kuma shaidanun, sa'an nan,
kuma, lalle Muna halartar da su a
gefen Jahannama suna gurfane.
69. Sa'an nan kuma, lalle, Muna
fizge wanda yake mafi tsananin
girman kai ga Mai rahama daga
kowace kungiya.
y »♦ y »^ s }' / + ' £*■ ' }/+'" sy
> '.^Y\ \ t'
'*'**"* s?t
£""t»> > * "£/ ^y" '"S
(1) 'Yan Aljanna suna cewa ba mu sauka a wadannan gidaje ba sai da umurnin
Ubangijinka, kai mai karatu, Allah Mai mallakar kome, kuma kome aya ne mai nuni zuwa
gare Shi, saboda haka ba a mantawa da Shi.
(2) Maganar Allah ce a bayan maganar 'yan Aljanna domin ta'aklbi da karin bayani
ga maganarsu.
462
19 — Suratu Maryam
e@m-n
70. Sa'an nan kuma, lalle Mu ne
Mafi sani ga wacfanda suke su ne
mafiya cancantar konuwa da ita.
71. Kuma babu kowa daga gare
ku sai mai tuzga mata. (1) Ya ka-
sance wajibi ga Ubangijinka,
hukuntacce.
72. Sa'an nan kuma, Mu tserar
da wacfanda suka yi aiki da takawa,
kuma Mu bar azzalumai a cikinta
gurfane.
73. Kuma idan ana karatun ayo-
yinMu, bayyanannu a kansu, sai
wacfanda suka kafirta su ce wa wa-
cfanda suka yi imani, "Wane daga
kungiyoyin biyu ya zama mafi alhe-
ri ga matsayi, kuma mafi kyaun
majalisa?"
74. Kuma da yawa daga muta-
nen karni Muka halakar a gaba-
ninsu, su (wadanda Muka halakar)
din ne mafi kyaun kayan daki da
magana (2) .
75. Ka ce, "Wanda ya kasance a
cikin 6ata, sai Mai rahama Ya yal-
wata masa yalwatawa, har idan sun
ga abin da ake yi musu wa'adi,
imma azaba ko Sa'a, to, za su sani,
wane ne yake shT ne mafi sharri ga
wuri, kuma mafi rauni ga runduna !"
z? i'*'* > »^~>
ti&\]>j&&^
*l>
(1) Idan an tara mutane domin hisabi, ana ajiye wuta a tsakanin mutane da Aljanna,
sa'an nan a gitta siracfi a kan wutar domin mutane su bi a kansa su £etare wutar zuwa
Aljanna, kuma wacfansu su facfa a cikin wutar domin azaba dawwamamma ko kuma ta
dan lokaci gwargwadon laifi.
(2) Kayan daki na jin dacfi kamar gadaje da kujeri da kayan cin abin ci. Magana kuwa
ita ce wurin da ake gani ga mutum kamar tufafinsa da surar jikinsa da dukan abin gani
daga gare shi.
463
19 — Suratu Maryam
tim%&-\\
76. Kuma Allah na kara wa wa-
cfanda suka nemi shiryuwa da shir-
iya. Kuma ayyuka masu wanzuwa
na kwarai ne mafi alheri a wurin
Ubangijinka ga lada, kuma mafi
alheri ga makoma.
77. Shin, ka ga wanda ya kafirta
da ayoyinMu, kuma ya ce, "Lalle ne
za a ba ni dukiya da cfiya?"
78. Shin, ya tsinkayi gaibi ne, ko
kuwa ya cfauki wani alkawari daga
Mai rahama ne?
79. A'aha ! Za mu rubuta abin da
yake facfa, kuma Mu yalwata masa,
daga azaba, yalwatawa.
80. Kuma Mu gade shi ga abin
da yake facfa, kuma ya zo Mana
yana shi kacfai.
81. Kuma suka riki gumaka, (1)
baicin Allah, domin su kasance
mataimaka a gare su.
82. A'aha ! Za su kafirta da iba-
darsu, kuma su kasance makiya a
kansu.
83. Shin, ba ka gani ba cewa
Mun saki shaicfanu (2) a kan kafirai
suna shushuta su ga zunubi shushu-
ta wa?
84. Saboda haka kada ka yi gag-
gawa a kansu, Muna yi musu ki-
dayar ajali ne kawai, kidayawa.
jDSj tsx* \jxJk\ <dU^^^y?j
,>£>'
(1) Gunki, shi ne dukan abin bautawa wanda ba Allah ba. Wanda ya riki wani salihi
ko mala'iki ko aljani, yana bauta masa, to, ya rike shi gunki ke nan. Bauta, ita ce bin
umurni da barin hani. Wanda ya bi umurnin da ba na Allah ba, ko ya bar abin hanin da ba
na Allah ba, to, ya bauta wa mai umurnin ko mai hanin, ya rike shi gunki baicin Allah.
(2) Idan shaidanu sun ga mai wa'azin gaskiya, sai su dinga shushuta mabiyansu
domin su yi facfa da mai wa'azin, domin kada su saurare shi har su gane batarsu. Shaicfan
shi ne mai 6atar da wani, mutum ne ko aljani.
464
19 — Suratu Maryam
tmm-s\
85. A ranar da Muka tara masu
takawa zuwa ga Mai rahama suna
bakin girma.
86. Kuma Muna kora masu laifi
zuwa Jahannama, gargadawa.
87. Ba su mallakar ceto, face
wanda ya riki alkawari a wurin Mai
rahama.
88. Kuma suka ce, "Mai rahama
Ya riki da!"
89. Lalle ne, hakika, kun zo da
wani abu mai girman muni.
90. Sammai suna kusa su tsat-
tsage saboda shi, kuma kasa ta
kece, kuma duwatsu su facfi, suna
karyayyu.
91. Domin sun yi da'awar da ga
Mai rahama.
92. Alhali ba ya kamata ga Mai
rahama ya riki wani da.
93. Dukan wanda yake a cikin
sammai da kasa bai zama ba face
mai je wa Mai rahama ne yana
bawa.
94. Lalle ne, hakika, Ya lissafe
su, kuma ya kidaye su kidaya.
95. Kuma dukan kowanensu
mai je Masa ne a Ranar Kiyama
yana shi kadai.
96. Lalle ne wadanda suka yi
imani, kuma suka aikata ayyuka na
kwarai, Mai rahama zai sanya
musu so. (1)
<£$± K <Cs »*^"S 'A*'?\
Bub
■f-*
^)*(t4JG
> >^*-»r > >t \' ~ ' '
( 1 ) Wanda ya bi Allah da gaskiya, Allah zai sanya zukatan mutane su so shi, kamar
yadda yake a cikin Hadisi wanda Imam Tirmizi ya ruwaito daga Sa'ad da Abu Huraira.
465
20 - Suratu T>.H.
W&A
-*•
97. Sa'an nan abin sani kawai,
Mun saukakar da shi (Alkur'ani) a
harshenka, domin ka yi bushara da
shi ga masu aiki da takawa, kuma
ka yi gargadi da shi ga mutane masu
tsananin husuma.
98. Kuma da yawa Muka ha-
lakar da mutanen karnoni a gaba-
ninsu. Shin, kana jin motsin wani
guda daga gare su, ko kuwa kana jin
wata tfuriya tasu?
' ' . >
59 Vj&A^AijXZy
Tana karantar da cewa Alkur'ani ko Musulunci, abu ne mai
sauki domin shiryar da mutane zuwa ga sauki, babu wahala a
-cikinsa.
* j* s . *
W3»«».
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. T>.H.
2. Ba Mu saukar da Alkur'ani a
gare ka domin ka wahala ba.
3. Face domin tunatarwa ga
wanda ke tsoron Allah.
4. (An saukar da shi) saukarwa
daga Wanda Ya halitta kasa da
sammai madaukaka.
466
20 - Suratu T>.H.
l/slt?!^ 1 —f*
5. Mai rahama, Ya daidaita (1) a
kan Al'arshi.
6. Abin da yake a cikin sammai
Nasa, ne, da abin da yake a cikin
kasa da abin da yake a tsakaninsu
da abin da ke karkashin tur6aya.
7. Kuma idan ka bayyana da
magana, to, lalle Shi, Yana sanin
asTri da mafi boyuwa.
8. Allah, babu abin bautawa face
Shi. Yana da sunaye mafiya kyau.
9. Kuma shin, labarin Musa ya je
maka?
10. A lokacin da ya ga wata
wuta, sai ya ce wa iyalinsa, "Ku
dakata. Lalle ne nl, na tsinkayi wata
wuta, tsammanma in zo muku da
makamashi daga gare ta, ko kuwa
in sami wata shiriya a kan wutar."
11. Sa'an nan a lokacin da ya je
mata, aka kira shi, "Ya Musa!
12. "Lalle ne, NT ne Ubangi-
jinka, sai ka debe takalmanka. (2)
Lalle ne kana a rafin nan abin
tsarkakewa, T)uwa.
13. "Kuma Nl,Naza6eka. Sai ka
saurara ga abin da ake yin wahayi.
14. "Lalle NT, Nine Allah. Babu
abin bautawa face Ni. Sai ka bauta
Mini, kuma ka tsayar da salla do-
min tuna Ni.
/*** < 9 \"* '\'\>\ 9 ' >'.\' \G& 9 "i \'
2? c^ty Qf^^^&J*^ 1*13
(1) Allah Ya daidaitu a kan Al'arshi daidaita wadda ta dace da Shi. Watau bayani ne
ga cewa Allah Ya mallake kome, kuma kome yana a gaban idanunSa, babu abin da ya
66yu a gare Shi, tun da Ya daidaitu a kan Al'arshi wanda ya hadiye kome a cikinsa.
(2) An ce wa Musa ya debe takalmansa domin suna da najasa ko kuwa su kansu
najasa ne domin ya shiga wuri mai tsarki wanda ake kira TDuwa a cikin saharar Sinai a
tsakanin Masar da Madyana.
467
20 - Suratu T>.H.
t/^l&^-f*
75. "Lalle ne Sa'a mai zuwa ce,
Ina kusa da In 66ye ta domin a saka
wa dukan rai da abin da yake aika-
tawa.
16. "Saboda haka, kada wanda
ba ya yin Tmani da ita kuma ya bi
son zuciyarsa, ya taushe ka daga
gare ta har ka halaka.
17. "Kuma wace ce waccan ga
damanka ya Musa!"
18. Ya ce, "Ita sandata ce, ina
dogara a kanta, kuma ina kakka6ar
ganye da ita a kan kananan bisa-
shena, kuma ina da wadansu buka-
toci (1) na dabam a gare ta."
19. Ya ce "Ka yi jlfa da ita, ya
Musa!"
20. Sai ya jefa ta. Sai ga ta dab-
bar macyiya, tana tafiya da gag-
gawa.
21. Ya ce, "Ka kama ta, kuma
kada ka ji tsoro. Za Mu mayar da
ita ga halinta na farko.
22. "Kuma ka hada hannunka
zuwa ga damtsenka, ya fita yana
fari, babu sofane, wata aya ta da-
bam.
23. "Domin Mu nuna maka
daga ayoyinMu manya.
24. "Ka tafi zuwa ga Fir'auna.
Lalle shT, ya ketare haddi (da gir-
man kai)."
'•\
\s:> t-
iciiiV^U JU-JU
(1) Amfanonin sanda: ana rikon alkibla a cikin daji ta zama sitra, ana dogara a kanta
saboda gajiya ko rauni. Limamin Jumma'a na dogara a kanta a lokacin huduba, ana fita
da ita a cikin ruwan sama ana dogara a kanta, ana dukan iyali da ita domin ladabtarwa. A
cikin wani HadTsi Annabi ya ce, "Ka rataye sandarka inda iyalinka suke ganin ta." Rikon
sanda na sanya farkawa ga barin duniya, watau mai ita ya zama a cikin halin tafiya.
468
20 - Suratu T>.H.
-*•
25. Ya ce, "Ya Ubangiji! Ka
bucfa (1) mini kirjma.
26.^ "Kuma ka saukake mini al'-
amarina.
27. "Kuma Ka warware mini
wani kulli daga harshena.
28. "Su fahimci maganata.
29. "Kuma Ka sanya mini wani
mataimaki daga mutanena.
30. "Haruna cfan'uwana.
31. "Ka karfafa halittata da shi.
32. "Kuma Ka shigar da shi a
cikin al'amarina.
33. "Domin mu tsarkake Ka da
yawa.
34. "Kuma mu tuna Ka da
yawa.
35. "Lalle Kai, Ka kasarice Mai
gani gare mu."
36. Ya ce, "Lalle ne, an ba ka
rokonka, ya Musa!
37. "Kuma lalle ne, haklka, Mun
yi wata baiwa gare ka a wani loka-
cin na dabam.
38. "A lokacin da Muka yi wa-
hayin abin da aka yi wahayi zuwa
ga uwarka.
39. "Cewa, 'Ki jefa shi a cikin
akwatin nan, sa'an nan ki jefa shi a
cikin kogi, sa'an nan kogin ya jefa
shi a ga6a, wani makiyi Nawa kuma
makiyi nasa ya dauke shi.' Kuma
Na jefa wani so daga gare Ni a
kanka. Kuma domin a rike ka da
kyau a kan ganiNa.
-» ^^ <*<
^l^ju^(J^IJJJ13
l^d^S
KH^i!
">y,
Oij
E9 <!^U^ta^L^JuJ^
®&j&^&)&$\
(1) Ma'anar bucfa Rirji, shi ne a sanya masa ha£uri.
469
20 - Suratu T>.H.
-T-
40. "A sa'ad da 'yar'uwarka ke
tafiya har ta ce, 'Shin, in shiryar da
ku ga wanda ke renonsa?' Sai Muka
mayar da kai zuwa ga uwarka do-
min idonta ya yi sanyi (1 } kuma ba za
ta yi bakin ciki ba. Kuma ka kashe
wani rai, sa'an nan Muka tserar da
kai daga bakin ciki, kuma Muka
fitine ka da wacfansu fitinoni. Sa'an
nan ka zauna shekaru a cikin muta-
nen Madyana. Sa'an nan kuma ka
zo a kan wata kaddara, ya Musa!
41. "Kuma Na zaBe ka domin
Kaina.
42. "Ka tafi kai da cfan'uwanka
game da ayoyiNa, kuma kada ku yi
rauni ga ambatoNa.
43. "Ku tafi ku biyu zuwa ga
Fir'auna. Lalle shT, ya ketare haddi
(ga girman kai).
44. "Sai ku gaya masa magana
mai laushi, (2) tsammaninsa yana
tunawa ko kuwa ya ji tsoro."
45. Su biyu suka ce, "Ya
Ubangijinmu! Lalle ne muna tso-
ron ya yi gaggawa a kanmu, ko ya
ketare haddi."
46. Ya ce, "Kada ku ji tsoro.
Lalle NT, Ina tare da ku,Ina ji, kuma
Ina gani.
47. "Sai ku je masa, sa'an nan ku
ce, Lalle mu, Manzanni biyu ne na
Ubangijinka, sai ka saki BanI Is-
ra'Tla tare da mu. Kuma kada ka yi
<" l»s.s ,-v
/r 5 ^ • \ it *"r
>* ' »S 9 'ki'X" *
ra^^^oy^i <i ^W* i*
S^^JjI^jSu^olil^iGj^li
( 1 ) Idonta ya yi sanyi, watau ta ji dacfi saboda ganin cfanta.
(2) Wannan shT ne dalilin umurni da alheri da hani daga sharri, kuma a yi haka da
magana mai laushi ga wanda yake da iko da karfi. Ko da ga wanda Allah Ya tsare da
tsarinSa ne, balle ga wanda bai taki kome ba. Ta haka ne mai wa'azi ke cin nasara.
470
20 - Suratu T>.H.
musu azaba. Haklka, mun zo maka
da wata aya daga Ubangijinka.
Kuma aminci ya tabbata ga wanda
ya bi shiriya.
48. "'Lalle mu, haklka, an yi
wahayi zuwa gare mu, cewa azaba
tana a kan wanda ya karyata, kuma
ya juya baya.'"
49. Ya ce, "To, wane ne Ubangi-
jinku? Ya Musa!"
50. Ya ce, "Ubangijinmu Shi ne
Wanda Ya bai wa dukan kome ha-
littarsa, sa'an nan Ya shiryar."
57. Ya ce, "To, mene halin kar-
nonin farko?"
52. Ya ce, "Saninsu yana a wurin
Ubangijma, UbangijTna ba Ya 6ace-
wa kuma ba Ya mantuwa.
53. "Wanda Ya sanya muku
kasa shimficfa, kuma Ya shigar
muku da hanyoyi a cikinta, kuma
Ya saukar da ruwa daga sama."
Sa'an nan game da shi (1 } Muka fitar
da nau'i-nau'i daga tsiruruwa
dabam-dabam.
54. Ku ci kuma ku yi kiwon dab-
bobin ni'imarku. Lalle ne, a cikin
wannan akwai ayoyi ga masu
hankali.
55. Daga gare ta (2) Muka halitta
ku, kuma a cikinta Muke mayar da
ku, kuma daga gare ta Muke fitar
da ku a wani lokaci na dabam.
<&$^ 'tit's"'' ' ' ' * ' ' S' '\*' *
4&\ YC
(1) Ruwan.
(2) Kasa.
471
20 - Suratu T>.H.
ttMv&-^
56. Kuma lalle, haklka, Mun
nuna masa ayoyinMu dukansu, sai
ya karyata, kuma ya kiya!
57. Ya ce, "Shin, ka zo mana ne
domin ka fitar da mu daga kasarmu
game da sihirinka, ya Musa?
58. "To, lalle ne, muna zo maka
da wani sihiri irinsa. Sai ka sanya
wani wa'adi a tsakaninmu da tsaka-
ninka, ba mu sa6a masa mu, kai
kuma ba ka sa6awa, a wani wuri
mai dacewa."
59. Ya ce, "Wa'adinku shi ne
ranar kawa, kuma a tara mutane da
hantsi."
60. Sai Fir'auna ya juya, sa'an
nan ya tara mugunyar dibararsa,
sa'an nan kuma ya zo.
61. Musa ya ce musu, "Kai-
tonku! Kada ku kirkira karya ga
Allah, har Ya tum6uke ku da wata
azaba. Kuma wanda ya kirkira ka-
rya, ya ta6e."
62. Sai suka yi jayayya ga
aPamarinsu a tsakaninsu, kuma
suka asirta ganawa.
63. Suka^ce, "Lalle ne wacfannan
biyun, hakika, masihirta ne, suna
nufin su fitar da ku daga kasarku (1)
game da sihirinsu, kuma su tafi da
tabl'arku mafificiya.
64. "Sai ku hacfa dabararku, sa'-
an nan kuma ku tafi a sahu guda,
^-» ''"IS'
||p dSj c-a Joo l$JS bl^>\«. «cJ>! Jj&j
-t** >x "> "".>»'*. y
-art (>bJuL>^ (Mjj^y^^ JLi
yO <3>^ * Ij/^i? ^-^-^ (♦-^^r 4 ' \jf>^»*
(1) Ya fara da siyasa domin ya karkatar da hankalin mutane daga ayoyin Allah.
Cewarsa ya yi nufin ya fitar da ku daga kasarku, shT ne siyasa, domin idan mutane suka ji
maganar fitarwa daga kasa, sai su manta da kowace irin magana ta wani alheri.
472
20 - Suratu T>.H.
-V-
kuma hakika, wanda ya rinjaya, a
yau, ya rabbanta."
65. Suka ce, "Ya Musa ! Imma ka
jefa, ko kuma mu kasance farkon
mai jefawa."
66. Ya ce, "A'a, ku jefa." Sai ga
igiyoyinsu da sandunansu ana su-
ranta su a gare shi, daga sihirinsu,
lalle suna tafiya da sauri.
67. Sai Musa ya ji tsoro a cikin
ransa.
68. Muka ce, "Kada ka ji tsoro.
Lalle kai ne mafi daukaka.
69. "Kuma ka jefa abin da ke a
cikin hannun damanka, ta cafe abin
da suka aikata. Lalle ne abin da
suka aikata, makircin masihirci ne,
kuma masihirci ba ya cin nasara a
duk inda ya je."
70. Sai aka jefar da masihirtan
suna masu sujada, suka ce, "Mun yi
imani da Ubangijin Haruna da
Musa."
71. Ya ce, "Kun yiTmani saboda
sh[ a gabanin in yi muku izni? Lalle
shi, hakika, babbanku ne wanda ya
sanar da ku sihirin ! To, lalle ne zan
kakkatse hannayenku da kafa-
funku a tarnaki, kuma lalle zan tslre
ku a cikin kututturan itacen dabino,
kuma lalle za ku sani wanenmu ne
mafi tsananin azaba, kuma wane ne
mafi wanzuwar (azaba)."
72. Suka ce, "Ba za mu fifita ka
ba faufau a kan abin da ya zo mana
na hujjoji. Muna rantsuwa da Wan-
da Ya kaga halittarmu sai ka hu-
kunta abin da kake mai hukuntawa,
S ' »«• 9^y
A*
""SIS'* ^v >* *>^ X I'^'' ^ **» ^*^ ->^*^ '\''k'
473
20 - Suratu T>.H.
-r.
ai kana kare wannan rayuwar du-
niya kawai ne.
73. "Lalle mu, mun yi imani da
Ubangijinmu domin Ya gafarta
mana laifuffukanmu da abin da ka
tTlasta mu a kansa na sihiri. Kuma
Allah ne Mafi alheri, kuma Mafi
wanzuwa."
74. Lalle (1) shl, wanda ya je wa
Ubangijinsa yana mai laifi, to, lalle
ne yana da Jahannama, ba ya mutu-
wa a cikinta kuma ba ya rayuwa.
75. Kuma wanda ya je Masa
yana mai imani, alhali kuwa ya
aikata aikin kwarai, to, wacfannan
suna da darajoji macfaukaka.
76. Gidajen Aljannar zama, ko-
guna na gudana daga karkashinsu,
suna madawwama a cikinsu. Kuma
wannan ne sakamakon wanda ya
tsarkaku.
77. Kuma lalle ne, haklka, Mun
yi wahayi zuwa ga Musa cewa, "Ka
yi tafiyar dare da bayiNa. Sa'an nan
ka doka musu hanya a cikin teku
tana kekasasshiya, ba ka tsoron
riskuwa, kuma ba ka fargabar nut-
sewa."
78. Sai Fir'auna ya bi su game da
rundunarsa. Sai abin da ya rufe su
daga kogin ya rufe su.
79. Kuma Fir'auna ya Batar da
mutanensa, kuma bai shiryar (da
su) ba.
'>." ^.i" . ^
G3 i3>*y^l>r^J
*\ ' > liT 5 " *' »t *
(1) Aya ta 74 da ta 75 maganar Allah ce domin icarin bayani a kan maganar masihirta
a bayan sun musulunta.
474
20 - Suratu T).H.
Wi<tA.
-*•
80. Ya BanllsraTla! Lalle Mun
tserar da ku daga makiyinku, kuma
Mun yi muku wa'adi a gefen Dutsen
nan na dama, kuma Mun sassaukar
da dar6a da tattabaru dominku.
81. Ku ci daga masu dacfin abin
da Muka arzuta ku, kuma kada ku
ketare haddi a cikinsa har hushiNa
ya sauka a kanku. Kuma wanda
hushiNa ya sauka a kansa, to, lalle
ne, ya facfi.
82. Kuma lalle NT, haklka, Mai
gafara ne ga wanda ya tuba kuma
ya yi imani, kuma ya aikata aikin
kwarai, sa'an nan kuma ya nemi
shiryuwa.
83. "Kuma mene ne ya gag-
gautar (1) da kai ga barin muta-
nenka? Ya Musa!"
84. Ya ce, "Su ne wacfannan a
kan sawuna, kuma na yi gaggawa
zuwa gare Ka, ya Ubangiji ! Domin
Ka yarda."
85. Ya ce, "To, lalle ne, hakika,
Mun fitini mutanenka daga ba-
yanka, kuma Samiri ya 6atar da su. "
86. Sai Musa ya koma zuwa ga
mutanensa yana mai hushi, mai
bakin ciki, ya ce, "Ya mutanena!
Shin, Ubangijinku bai yi muku
wa'adi ba, wa'adi mai kyau? Shin,
lokacin ya yi tsawo a kanku ne, ko
> >
<&\£LSj^J& Stf,U Jvi
S^J
( 1 ) Musa ya za6i mutun saba'in daga Bani Isra'ila, domin su tafi wurin Mikati tare, su
ji maganar Ubangiji. A lokacin da ya yi kusa, sai ya yi gaggawa domin bege. K6 kuwa a
bayan azumin kwana arba'in ya tafi a wurin Mikatin, Allah Ya fara yi masa magana game
da mutanensa domin cfebe masa kewa. Sai ya karba da cewa, "Suna nan a kan sawuna."
Watau suna nan a kan abin da na cfora su a kansa na addini da aklda ta tauhldi. Sai Allah
Ya ce masa "A'aha! Sun musanya addininka da bautar maraki."
475
20 - Suratu T>.H.
WifA
-r-
kun yi nufi ne wani hushi ya sauka a
kanku daga Ubangijinku, saboda
haka kuka saBa wa alkawarina?"
87. Suka ce, "Ba mu saBa wa
alkawarinka (1) ba da Tkonmu,
kuma amma an dora mana wa-
dansu kaya masu nauyi daga abin
kawar mutanen ne, sai muka jefar
da su. Sa'an nan kamar haka ne
Samiri ya jefa.
88. "Sai ya fitar musu da wani
maraki, jikin mutane, yana ruri,
sa'an nan suka ce, 'Wannan ne
gunkinku kuma gunkin Musa, sai
ya mantaV
89. Shin, to, ba su ganin cewa, ba
ya mayar musu da magana, kuma
ba ya mallakar wata cuta a gare su,
kuma ba ya mallakar amfani?
90. Kuma, haklka, Haruna ya ce
musu daga gabani, "Ya mutanena!
Lalle an fitine ku da shi ne kawai.
Kuma lalle Ubangijinku Mai raha-
ma ne, saijcu bi ni, kuma ku yi da'a
ga umurnina."
91. Suka ce, "Ba za mu gushe ba
faufau a kansa muna masu la-
zimta, (2) sai Musa ya komo zuwa
gare mu."
' 's^ ^^* I" *' X^ ' * ' ' »"*
eiUliSi [£i Jii j£ju \ ±^jiy> [>\jj\
1 i3^&y k ^\*f S: ^v J *\y ^
( 1 ) Alokacin da Bani Isra'ila za su fita daga Masar sun yi aron mundayen mutanen
Masar domin su nuna cewa biki suke yi, ba gudu za su yi ba, domin kada a b! su da wuri.
Wadannan mundayen ne Samiri ya tara a bayan tafiyar Musa zuwa ga Mlkatin
Ubangijinsa ya kera musu maraki mai jiki irin na mutane da sauti irin na shanu, domin ya
yi masa magudanar iska a cikin cikinsa, idan iskar ta fito, sai a jT ta da sauti kamar sautin
kukan shanu. Kuma shi marakin ba ya da wani rai, ba ya motsi, sai dai kugin kawai.
(2) Lazimta a kan bauta wa marakin akwai wahala a cikinta, domin haka aka kawo
wannan kissa saboda a nuna cewa bautar Allah babu lazimta da wahala a cikinta, duk abin
da yake da wahala a cikinsa, ba addinin Allah ba ne. Akwai i'itikafi a cikin Musulunci
wanda mail yawansa kwana goma ne a cikin masallaci. Mutanen Samiri ne suka fara ibada
da kida da rawa da waka a cikin wurin ibadarsu.
476
20 - Suratu T>.H.
-r-
92. (Musa) ya ce, "Ya Haruna!
Me ya hane ka, sa'ad da ka gan su
sun Bace.
93. "Ba ka blni ba! Shin, to, ka
sa6a wa umurnina ne?"
94. (Haruna) ya ce, "Ya cfan'u-
wana! Kada ka yi kamu ga gemu-
na ko ga kaina. Lalle ni, na ji tso-
ronjta ce,JKa rarraba a tsakanin
BanT Isra'Tla, kuma ba ka tsare
maganata ba'."
95. (Musa) ya ce, "Mene ne bab-
ban al'amarinka? Ya Samiri!"
96. (Samiri) ya ce, "Na ga abin ( l }
da ba su gan shi ba shi, sai na yi
damka, damka guda daga kufan
sawun Manzon, sa'an nan na jefa
ta. Kuma haka dai raina ya kawata
mini."
97. (Musa) ya ce, "To, ka tafi,
saboda haka lalle ne kana da a cikin
rayuwarka, ka ce 'Babu shafa',
kuma kana da wani ma'alkawarta,
ba za a saBa maka gare ta ba. Kuma
ka duba zuwa ga gunkinka wanda
ka yini a kansa kana mai lazimta.
Lalle ne muna kone shi, (2) sa'an nan
kuma muna sheke shi, a cikin teku,
sheke wa."
•-"^ S **'A'*\ '\"'\' * * ' ' '\\~
^ \j9y »>',\'*. \'"S> >'?'*{-
l ' r s?i>\*< \".
^CSj*^C±
(1) Mai karya ba ya iya magana guda mikakkiya sai ya kara mata wata maganar da
ke nuna rashin gaskiyar maganar farko. Samiri ya ce ya ga abin da ba su gani ba, sa'an nan
ya nuna cewa akwai wani Manzo da ke zuwa gare shi ko ga wani, wanda mutane ba su gani
ba, shi kacfai ne ya gan shi. Bayan haka kuma ya rufe maganarsa da cewa haka dai ransa ya
kawata masa. Saboda haka ya karyata ganinsa da manzonsa, ya koma wa surantawar
ransa da ta Shaicfan.
(2) Musa, amincin Allah ya tabbata a gare shi, ya kone marakin ya sheke shi a cikin
ruwan teku ya nuna Tkon marakin ga kare kansa daga wata cuta kuma da karan-
cinsa a ciki teku wadda take cfaya ce daga cikin abubuwan Tkon Allah da suke iya
gani, da lalacewar ibadar masu bauta wa wanin Allah, a bayan wahalarsu mai yawa ta
lazimta a kansa.
477
20 - Suratu T>.H.
siHl5s4-r-
98. Abin sani kawai, abin bau-
tawarku Allah kawai ne, Wanda
babu wani abin bautawa face shi,
kuma Ya yalwaci (1) dukan kome da
ilmi.
99. Kamar wancan ne Muke la-
bartawa (2) a gare ka, daga labaran
abin da ya gabata, alhali kuwa
haiciica, Mun ba ka zikiri (Al£u-
r'ani) daga gunMu.
100. Wanda ya kau da kai daga
gare shi, to, lalle shT, yana cfaukar
wani nauyi a Ranar Kiyama.
101. Suna madawwama a cikin-
sa, kuma ya munana ya zama abin
cfauka, a Ranar Kiyama.
102. A Ranar da ake hurawa a
cikin £aho, kuma Muna tara masu
laifi, a ranar nan, suna masu jajayen
idanu.
103. Suna Boye magana a tsa-
kaninsu, (Suna ce wa juna) "Ba ku
zauna ba (a cikin duniya) face kwa-
na goma."
104. Mu ne mafi sani ga abin da
suke facfa a sa'ad da mafificinsu ga
hanya ke cewa, "Ba ku zauna ba
face a yini guda."
( 1 ) Allah Ya yalwaci dukan kome da sani, watau Yana aikata kome da ilminSa, kuma
Yana umurni da bauta Masa da ilmi, wanda Ya aiki ManzanninSa da shi.
(2) Ya kawo karin bayani game da wannan kissa a cikin ayoyin da ke tafe daga nan,
yadda bin addinin Allah yake da sauki a cikin lokaci gajere na duniya kawai, a cikin
takaitaccen lokaci, da kuma wuyar bauta wa wani ga cfaukar kaya masu nauyi a duniya da
Lahira, a cikin dogon lokaci.
478
20 - Suratu T>.H.
t^t34-f-
105. Kuma suna tambayar ka
daga duwatsu (1) , sai ka ce, "Uban-
gijina Yana sheke su shekewa,
106. Sa'an nan Yana barin (wu-
rinsu) fako mai santsi.
707. "Ba ka ganin karkata a ci-
kinsa, kuma ba ka ganin wani
tudu."
108. A ranar nan suna biyar mai
kira, babu karkata a gare shi, kuma
sautuka suka yi kawaici ga Mai
rahama, ba ka sauraren kome face
sautin tafiya.
109. A yinin nan ceto ba ya yin
amfani face wanda Mai rahama Ya
yi masa izni kuma Ya yarda da shi,
da magana. (2)
110. Yana sanin (3) abin da ke a
gaba gare su da abin da ke bayansu,
kuma ba su kewayewa da Shi ga
sani.
111. Kuma fuskoki suka kankan
da kai ga Rayayye, Tsayayye, alhali
kuwa wanda ya dauko wani zalunci
ya ta6e.
112. Kuma wanda ya aikata
wani abu daga ayyukan kwarai al-
hali kuwa yana mai imani, to, ba ya
^l^iVjiSefe^'
•<'*l'Zf^
(1) Ana siffanta duwatsu madaukaka da ayyukan duniya wadanda ba ibadar Allah
ba, watau al'adu da ibadodin da ba ibadar Allah ba, dukansu kome yawansu za su lalace a
ranar da Mai kira, watau Israfil, zai busa icaho na kiran mutane zuwa ga Tashin FCiyama,
kira wanda babu makarkata daga gare shi, watau ba kamar kiran da Annabawa suka yi ba,
wanda wadansu mutane suka karkace daga gare shi a nan duniya.
(2) Babu ceto ga kowa sai wanda Allah Mai rahama Ya yi masa iznin da yin ceton, ga
wanda aka yi iznin saboda shi, kuma izni ana yin sa ne da maganar Allah, ba da wata
ishara ba.
(3) Allah Ya san kome ga halittunSa, su kuwa ba su iya kewayewa da sanin kome game
da Shi.
479
20 - Suratu T>.H.
tsoron wani zalunci ko wata na-
kasa.
113. Kuma haka Muka saukar
da shi, Alkur'ani, yana abin karan-
tawa, da Larabci, kuma Muka juj-
juya misalai, a cikinsa, na tsoratar-
wa, tsammaninsu, suna yin takawa
ko ya sabbaba musu wata wa'az-
tuwa.
114. Sa'an nan Allah, Mamalla-
ki, Tabbatacce, Ya daukaka. Kuma
kada ka yi gaggawa (1) da Alkur'ani
a gabanin a kare wahayinsa zuwa
gare ka. Kuma ka ce, "Ya Ubangiji !
Ka kara mini ilmi."
115. Kuma lalle, haklka, Mun yi
alkawari zuwa ga Adamu a gabanin
wannan, sai ya manta, kuma ba Mu
sami karfin zuciya a gare shi ba.
116. Kuma sa'ad da Muka ce
wa mala'iku, "Ku yi sujada ga
Adamu." Sai suka yi sujada, face
IblTsa, ya kiya.
117. Sai Muka ce, "Ya Adamu!
Lalle ne wannan makiyi (2) ne gare
ka da kuma ga matarka, saboda
haka kada ya fitar da ku daga
Aljanna har ku wahala.
(^li^SfJuik
<> " f.f >**'*"* '*
M>
ff&sb '-*". -I'M' frl' 9 *^'
(1) Allah Ya umurci Annabi da ya bar gaggawar karatun Alkur'ani a lokacin da ake
yin wahayinsa zuwa gare shi, domin kada ya wahala, domin surar tana karantar da cewa
addinin Musulunci sauki ne, bai zo domin ya wahalar ba. Kuma tsoron yin kuskure yana
sanya yin kuskure mai jawo wahala kamar yadda Adamu ya yi gaggawar ga tsoron
umurnin Allah, sai ya yi mantuwa, ya yi abin da aka hana shi, har masifa ta samu, aka fitar
da shi daga Aljanna.
(2) Ana farkar da diyan Adamu ga makiyin ubansu wanda ya sabbaba musu wahalar
zuwa duniya da haduwa da taklTfi a cikinta. Kuma bin wannan takllfi yana zame musu
sauki idan sun blshi yadda Allah Ya ce, amma idan sun bi hanyar Shaidan, makiyinsu, to,
babu abin da zai samu a gare su face karin wahala daga duniya har Lahira.
480
20 - Suratu T>.H.
^w&-r.
118. "Lalle ne ka samu, ba za ka
ji yunwa ba a cikinta, kuma ba za ka
yi tsiraici ba.
119. "Lalle kai, ba za ka ji £ishir-
wa ba, kuma ba za ka shiga hantsi
ba."
120. Sai Shaidan ya sanya was-
wasi zuwa gare shi, ya ce, "Ya
Adamu ! Shin, in shiryar da kai ga
itaciyar dawwama da mulki wanda
ba ya Icarewa?"
121. Sai suka ci daga gare ta,
saboda haka al'aurunsu suka bay-
yana, kuma suka shiga suna lullu-
6a wa a kansu daga ganyen Aljanna.
Kuma Adamu ya sa6a wa Ubangi-
jinsa, saboda haka ya wahala.
122. Sa'an nan kuma Ubangijinsa
Ya zaBe shi, Ya kar6i tuba gare shi,
kuma Ya shiryar (da shi).
123. Ya ce, "Ku sauka ku biyu
daga gare ta gaba cfaya, sashenku
yana malciyi ga sashe. To, imma dai
wata shiriya ta je muku daga gare
Ni, to, wanda ya bi Shiryarwata, to,
ba ya 6acewa, kuma ba ya wahala.
124. "Kuma wanda ya bijire (1)
daga ambatoNa (Al£ur'ani), to,
lalle ne rayuwa mai £unci ta tabbata
a gare shi, kuma Muna tayar da shi
a Ranar Kiyama yana makaho."
125. Ya ce, "Ya Ubangiji! Don
me ne Ka tayar da ni makaho alhali
kuwa na kasance mai gani?"
i£s®%£'$&i
P CJx^^^\^£^^j
f * < <.** <
(1) Wanda ya bijire daga ayoyin Allah, shine kafirin da bai yarda da shiga Musulunci
ba.
481
20 - Suratu *D.H.
'}$>%&? — f*
126. Ya ce, "Kamar wancan ne
ayoyinMu suka je maka, sai ka
mance su, kuma kamar hakar a
yau ake mance ka."
127. Kuma kamar haka Muke
saka wa wanda ya yawaita, (1) kuma
bai yi Tmani da ayoyin Ubangijinsa
ba. Kuma lalle ne azabar Lahira ce
mafi tsanani, kuma mafi wanzuwa.
128. Shin,to,baishiryardasuba
cewa da yawa Muka halakar da
(kafirai) daga karnuka, a gaba-
ninsu, suna tafiya a cikin masau-
kansu? Lalle ne, a cikin wancan
akwai ayoyi ga masu hankula.
129. Kuma ba domin wata kal-
ma ba wadda ta gabata daga
Ubangijinka, da kuma ajali amba-
tacce, hakTka, da azabar ta kasance
mai lazimta.
130. Sai ka yi hakuri (2) a kan
abin^ da suke cewa, kuma ka yi
tasbThi da gode wa Ubangijinka a
gabanin fitowar rana da gabanin
6acewarta, kuma daga sa'o'in dare
sai ka yi tasbThi da sasannin yini,
tsammaninka za ka sami yarda.
131. Kuma kada ka mlkar da
idanunka zuwa ga abin da Muka
jiyar da su dadi da shi, nau'i-nau'i,
daga gare su, kamar huren rayuwar
duniya yake, domin Mu fitine su a
»}»'s ' ' £*'
'•>** sj:*
(1) Wanda ya yawaita, shi ne Musulmi fasiki ko mai bidi'a yana kara abin da ba a sani
ba a cikin addini, ya yawaita shi. Shi ma ya shiga a cikin wahalar duniya. Kuma ta Lahira
ta fi tsanani.
(2) Hakuri da rike ibada ta salloli da tasibThi a lokatanta, farilla da na nafila, shi ne
maganin izgilin masu izgili. TasbThi da gode wa Allah a gabanin fitowar rana ga sallar
Asuba T a gabanin Bacewarta ga La'asar, a sa'o'in dare ga Isha'i, da gefukan rana ga Azahar.
482
20 - Suratu T>.H.
(H?i^-^-
cikinsa, alhali kuwa arzikin Uban-
gijinka ne mafi alheri kuma mafi
wanzuwa.
132. Kuma ka umurci iyalanka
da salla, kuma ka yi hakuri a
kanta. Ba Mu tambayar ka wani
arziki, Mu ne Muke arzuta ka.
Kuma akiba mai kyau tana ga ta-
kawa.
133. Kuma suka ce, "Don me ba
ya zo mana da wata aya daga
Ubangijinsa?" Shin, kuwa hujjar
abin da ke a cikin littattafan farko,
ba ta je musu ba?
134. Kuma da dai Mun halaka
su da wata azaba daga gabaninsa,
lalle ne da sun ce, "Ya Ubangi-
jinmu ! Da Ka aiko da wani Manzo
zuwa gare mu har mu bibbiyi
ayoyinKa daga gabanin mu kaskas-
ta, kuma mu wulakantu!"
1 35. Ka ce, "Kowa mai tsumaye
ne. Sai ku yi tsumaye. Sa'an nan za
ku san su wa ne ma'abuta tafarki
madaidaici, kuma wane ne ya nemi
shiryuwa."
S* y*s ' IS''* t.' »*' ' y .* s'*****^
C „ ' „ • • y \s ' '• > yy
-ft V
p dJ^\^^\^C ^^Ispjt
.< x > / /<;
^ Ml
XL
^ *~>
483
21 - Suratul Anbiya'
aig&8&-n
Tana karantar da dokokin^ Allah masu hukunta haduwar
addinan Allah da hacfuwar akldodinsu a kan kacfaitar Allah
Makacfaici.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L Hisabin mutane ya kusanta
gare su, alhali kuwa suna a cikin
gafala, suna masu bijirewa.
2. Wani ambato daga Uban-
gijinsu sabo, ba ya zuwa gare su face
sun saurare shi, alhali kuwa suna
masu yin wasa.
3. Suna masu shagaltacin zuka-
tansu, kuma su asirta ganawa : wa-
danda suka yi zalunci, (suna cewa)
"Wannan ba kowa ba ne face mu-
tum misalinku. Shin, to, kuna je wa
sihiri, alhali kuwa ku, kuna fahim-
ta?"
4. Ya ce, "Ubangijina Yana sa-
nin magana a cikin sama da kasa,
kuma Shi ne Mai ji, Masani."
5. A'a, suka ce, "Yaye-yayen
mafarki ne. A'a, ya kirkira shi ne.
A'a, shi mawaki ne. Sai ya zo mana
da wata aya kamar yadda aka aiko
manzanni na farko."
• »i
Oyr**i A> oy^LJ ill
'Jtxrf^j^J.
484
21 — Suratul Anbiya'
aSg&tf&-n
6. Wata al£arya da Muka halaka
ta a gabaninsu, ba ta ^i imani ba.
Shin, to, su, suna yin imani?
7. Kuma ba Mu aika ba a gaba-
ninka face mazaje, Muna yin wa-
hayi zuwa gare su. Ku tambayi
ma'abuta ambato (1) idan kun ka-
sance ba ku sani ba.
8. KumabaMusanyasujiki, ba
su cin abin ci ba, kuma ba su kasan-
ce madawwama ba.
9. Sa'an nan kuma Muka gas-
kata musu alkawari; sai Muka tse-
rar da su da wanda Muke so, kuma
Muka halakar da masu yawai-
tawa. (2)
10. Lalle, haki£a, Mun saukar
da wani littafi zuwa gare ku, (3) a
cikinsa akwai ambatonku. Shin, to,
ba ku hankalta?
11. Kuma da yawa Muka karya
wata alicarya ta kasance mai zalun-
ci, kuma Muka £aga halittar wa-
rfansu mutane na dabam a bayanta.
12. Sai a lokacin da suka hangi
azabarMu, sai ga su suna gudu daga
gare ta.
13. "Kada ku yi gudu. Ku komo
zuwa ga abin da aka ni'imtar da ku
a cikinsa da gidajenku tsamma-
ninku ana tambayar ku."
^^
5^^e$-^3iP5s
jyj^
S s ' » s's ' *'
4-JLU C^ I^JL^^ b ^ - vj» ^Sj
(1) Ma'abuta ambato, watau mutanen da aka bai wa littattafan sama: Yahudu da
Nasara.
(2) Masu yawaitawa, su ne masu wuce haddodin Allah ga kdme, fasikai da masu
bidi'o'i.
(3) Al'ummar Muhammad, tsirar Allah da amincinSa su tabbata a gare shi. An
saukar musu da Alkur'ani, a cikinsa akwai daukakarsu da darajarsu, domin wanda aka
ambata, to, an cfaukaka shi.
485
21 — Sura tul Anbiya'
3£g&$&-n
14. Suka ce, "Kaitonmu! Lalle
mii ne muka kasance masu
zalunci."
15. Sa'an nan waccan ba ta gus-
he ba, ita ce da'awarsu har Muka
mayar da su girbabbu, bitattu.
16. Kuma ba Mu halitta sama da
kasa da abin da ke a tsakaninsu
Muna Masu wasa ba.
17. Da Mun yi nufin Mu riki
wani abin wasa da Mun (1) rike shi
daga gunMu, idan Mun kasance
masu aikatawa.
18. A'a, Muna jTfa da gaskiya a
kan karya, sai ta darkake ta, sai ga
ta halakakka. Kuma bone ya tabba-
ta a gare ku saboda abin da kuke
siffantawa.
19. Kuma ShT ne da mallakar
wanda yake a cikin sammai da kasa.
Kuma wacfanda suke wurinSa (wa-
tau mala'iku), ba su yin girman kai
ga ibadarSa, kuma ba su gajiya.
20. Suna tasbThi dare da rana, ba
su yin rauni.
21. K6 (kafirai) sun riki wa-
cfansu abubuwan bautawa ne ga
kasa, su ne masu tayarwa (gare su)?
22. Da wacfansu abubuwan bau-
tawa sun kasance a cikinsu (sama
da kasa) face Allah, hakika, da su
biyun sun 6aci. Saboda haka tsarki
ya tabbata ga Allah Ubangijin
Al'arshi daga abin da suke siffan-
tawa.
&&&^)^ffi
~>"Zf 1
(1) Abin wasa, shi ne mata, ko da, ko wani abin da ake shagaltuwa da shi.
486
21 — Suratul Anbiya'
aig^l^-n
23. Ba a tambayar Sa ga abin da
Yake aikatawa, alhali kuwa su ana
tambayar su.
24. Ko sun riki wacfansu abu-
buwan bautawa, baicinSa? Ka ce,
"Ku kawo hujjarku. Wannan shi ne
ambaton wanda yake tare da ni,
kuma shi ne ambaton wanda yake a
gabanlna." A'a, mafi yawansu ba
su sanin gaskiya, saboda haka su
masu bijirewa ne.
25. Kuma ba Mu aiki wani Man-
zo ba a gabaninka face Muna yin
wahayi zuwa gare shi, cewa "Lalle
ne shi, babu abin bautawa face NT,
sai ku bauta Mini."
26. Kuma suka ce, "Mai rahama
^a riki da." TsarkinSa ya tabbata!
A'a, (mala'iku) bayi ne masu daraja.
27. Ba su gabatarSa da magana,
kuma su da umurninSa suke aiki.
28. Yana sanin abin da yake
gaba gare su da abin da yake a
bayansu, kuma ba su yin ceto face
ga wanda Ya yarda, kuma su masu
sauna ne saboda tsoronSa.
29. Kuma wanda ya ce daga gare
su, "Lalle ni abin bautawa ne
baicinSa," to, wannan Muna saka
masa da Jahannama. Kamar haka
Muke saka wa azzalumai.
30. Shin, kuma wadanda suka
kafirta ba su gani da cewa lalle
sammai da kasa sun kasance din-
ke, (1) sai Muka bude su, kuma
>^»> *>^>/» x ,* x ^/»> k
^ >' *' 'i' 9* 'X' \" » *k '"' \' -^f *^
' > r> "
l5p S^J^iS^^^^l
(1) Sammai sun kasance cfinke, ruwa ba ya sauka daga gare su, kuma kasa ta kasance
cfinke, tsiro ba ya tsira daga gare ta. Sa'an nan Muka sanya kome mai rai daga ruwa mai
sauka daga sama ya jika kasa, ta yi tsiro, dabbobi su rayu.
487
21 - Suratul Anbiya'
3lig&l3&-n
Muka sanya dukan kome mai rai
daga ruwa? Shin, ba za su yi Tmani
ba?
31. Kuma Mun sanya tab-
batattun duwatsu a cikin kasa do-
min kada ta karkata da su, kuma
Mun sanya ranguna, hanyoyi, a
cikinsu (duwatsun), tsammaninsu
suna shiryuwa.
32. Kuma Mun sanya sama rufi
tsararre, alhali kuwa su daga ay 6-
yinta masu bijirewa ne.
33. Kuma Shine wandaYahalit-
ta dare da yini da rana da wata,
dukansu (1) a cikin wani sarari suke
iyo.
34. Kuma ba Mu sanya daw-
wama ga wani mutum ba, a gaba-
ninka. Shin, to, idan ka mutu, to, su
ne madawwama?
35. Kowane rai mai cfancfanar
mutuwa ne.Kuma Muna jarraba ku
da sharri da alheri domin fitina.
Kuma zuwa gare Mu ake mayar da
ku.
36. Kuma idan wacfanda suka
kafirta suka gan ka, ba su rikon ka
face da izgili (suna cewa) "Shin,
wannan ne ke ambatar guma-
kanku?" Alhali kuwa su, ga amba-
tar Mai rahama, masu kafirta (2) ne.
37. An halitta mutum daga gag-
gawa, zan nuna muku ayoyiNa.
1$ oj^jte*iS~%is* J 6 f^ ] ot
Tf . .'T^-'
^1 ojJC^jH-^^^V^^^i^
( 1 ) Wannan ya nuna cewa rana da wata a cikin sarari guda suke, ko da yake akwai
nisan gaske a tsakaninsu.
(2) Sun kasance suna aibanta wanda yake musun gumakansu, alhali kuwa su, suna
musun zaman Allah Mai rahama ya kasance abin bautawa guda. Wannan shi ne gayar
jahilci.
488
21 — Suratul Anbiya'
;UgvNJ^-n
Saboda haka kada ku nemi yin
gaggawa.
38. Kuma suna cewa, "A yaushe
wannan wa'adi zai tabbata, idan
kun kasance masu gaskiya?"
39. Da wacfanda suka kafirta
suna sanin lokacin da ba su kange
wuta daga fuskokinsu, kuma haka
daga bayayyakinsu, alhali kuwa ba
su zama ana taimakon su ba.
40. A'a, tana je musu bisa ga
auke, sai tacfimautar da su, sa'annan
ba su iya mayar da ita, kuma ba su
zama ana yi musu jinkiri ba.
41. Kuma lalle ne, haklka, an yi
izgili ga wacfansu Manzanni daga
gabaninka, sai abin da suka kasan-
ce suna izgili da shi ya auku ga
wacfanda suka yi izgilin daga gare
su.
42. Ka ce, "Wane ne yake tsare
ku a dare da yini daga Mai
rahama?" A'a, su masu bijirewa ne
daga ambaton Ubangijinsu.
43. Ko kuwa suna da wacfansu
abubuwan bautawa wacfanda ke
tsare su, daga gare Mu? Ba su iya
taimakon kansu, kuma ba su kasan-
ce ana abutar su (1) ba daga gare
Mu.
44. A'a, Mun yalwata wa
wacfannan da ubanninsu ni'imar-
Mu, har rayuwa ta yi tsawo a kansu.
Shin, to, ba su ganin cewa lalle Mu,
>^ > *•>
(1) Ba su iya samun wani aboki wanda zai tsare su daga azabarMu. Kuma wanda bai
tsare kansa ba yaya zai iya tsare wani?
489
21 — Suratul Anbiya'
aig^il^-n
Muna je wa kasarsu, Muna rage (1)
ta daga sasanninta? Shin, to, su ne
marinjaya?
45. Ka ce, "Abin sani, ina yi
muku gargacfi kawai da wahayi,"
kuma kurma ba ya jin kira a lokacin
da ake yi musu gargacfi.
46. Kuma haklka idan wata iska
daga azabar Ubangiji ta shafe su,
hakika suna cewa, "Ya kaitonmu !
Lalle mu ne muka kasance masu
zalunci."
47. Kuma Muna aza ma'aunan
adalci ga Ranar Kiyama, saboda
haka ba a zaluntar rai da kome.
Kuma ko da ya kasance nauyin
kwaya daga komayya ne Mun zo da
ita. Kuma Mun isa zama Masu
hisabi.
48. Kuma lalle, haklka, Mun
kawo wa Musa da Haruna Rarra-
bewa da haske da ambato ga masu
aiki da takawa.
49. Wacfanda suke tsoron Uban-
gijinsu a fake, alhali kuwa su, masu
sauna ne daga Sa'a.
50. Kuma wannan ambato ne
mai albarka, Mun saukar da shi.
Shin, to, ku masu musu ne gare shi ?
57. Kuma lalle, haklka, Mun
kawo wa Ibrahim shiryuwarsa
daga gabani, kuma Mun kasance
Masana gare shi.
52. Ya ce wa ubansa da muta-
nensa, "Mene ne wacfannan
Q^&a^ift&flJs
.<' ~»
^l>Jjf&j l^lSili J^>-6i
~.\\ *"' ^ •'?" .If
(1) Muna rage kasarsu daga sasanninta, watau mutanen da ke bin su ga 6atarsu
kullum suna raguwa, suna shiga Musulunci, Musulunci na karuwa.
490
21 — Suratul Anbiya'
;i^NJM-n
mutummutumai wacfanda kuke
masu lazimta a kansu?"
53. Suka ce, "Mun sami uban-
ninmu masu lazimta a kansu."
54. Ya ce, "Lalle, hakika, kun
kasance ku da ubanninku a cikin
bata bayyananna."
55. Suka ce, "Shin, ka zo mana
da gaskiya ne, ko kuwa kai kana
daga masu wasa ne?"
56. Ya ce, "A'a, Ubangijinku Shi
ne Ubangijin sammai da kasa,
Wanda Ya kaga halittarsu. Kuma ni
ina daga masu shaida a kan haka.
57. "Kuma ina rantsuwa da Al-
lah, lalle zan yi wani shiri ga guma-
kanku a bayan kun juya kuna masu
bayar da baya."
58. Sai ya sanya su guntu guntu
face wani babba gare su, tsamma-
ninsu suna komawa zuwa gare shi.
59. Suka ce, "Wane ne ya aikata
wannan ga gumakanmu? Lalle shT,
haklka, yana daga azzalumai."
60. Suka ce, "Mun ji wani sau-
rayi yana ambatar su. Ana ce masa
Ibrahim."
61. Suka ce, "To, ku zo da shi a
kan idanun mutane, tsammanin su
za su bayar da shaida."
62. Suka ce, "Shin, kai ne ka
aikata wannan ga gumakanmu? Ya
Ibrahim!"
63. Ya ce, "A'a, babbansu, wan-
nan, shT ya aikata shi. Sai ku tam-
baye su idan sun kasance suna yin
magana."
1?$\' >S' \\*>\
491
21 — Suratul Anbiya'
lli&W-n
64. Sai suka koma wa junansu
suka ce, "Lalle ne ku, ku ne azza-
lumai."
65. Sa'an nan kuma aka sun-
kuyar da su a kankawunansu (suka
ce,) "Lalle, hakika, ka sani ~
wacfannan ba su yin magana."
66. Ya ce, "Shin, to, kuna bauta
wa abin da ba ya amfanin ku da
kome kuma ba ya cutar da ku,
baicin Allah?
67. "Tir da ku, kuma da abin da
kuke bauta wa, baicin Allah ! Shin,
to, ba ku hankalta?"
68. Suka ce, "Ku kone shi, kuma
ku taimaki gumakanku, idan kun
kasance masu aikatawa."
69. Muka ce, "Ya wuta! Kijca-
sance sanyi da aminci ga Ibrahim.'
70. Kuma suka yi nufin wani
mugun shiri da shi, sai Muka sanya
su mafiya hasara.
71. Kuma Muka tserar da shi, da
Lucfu zuwa ga kasar nan wadda
Muka sanya albarka a cikinta ga
talikai.
72. Kuma Muka ba shi Is'haka
da Ya'akuba a kan dacfi, alhali
kuwa dukansu Mun sanya su
salihai.
73. Kuma Muka sanya su shuga-
banni, suna shiryarwa da umur-
ninMu. Kuma Muka yi wahayi
zuwa gare su da ayyukan alheri da
tsayar da salla da bayar da zakka.
Kuma sun kasance masu bauta
gare Mu.
>s* *l
''* ^ '">'
" m V\'> *\ y^ \*"-'\ 9> r\""
' <s +
492
21 - Suratul Anbiya'
aig^l^-n
74. Kuma Lucfu, Mun bashi hu-
kunci da ilmi. Kuma Mun tslrar da
shi daga alkaryar nan wadda ke
aikata munanan ayyuka. Lalle su,
sun kasance mutanen mugun aiki,
fasikai.
75. Kuma Muka shigar da shi a
cikin rahamarMu. Lalle ne shi,
yana daga salihai.
76. Kuma Nuhu, a sa'ad da ya yi
kira a gabani, sai Muka karba
masa, sa'an nan Muka tsirar da shi
da mutanensa daga bakin ciki mai
girma.
77. Kuma Muka taimake shi
daga mutanen nan wacfanda suka
karyata da ayoyinMu. Lalle ne su,
sun kasance mutanen mugun aiki.
Sai Muka nutsar da su gaba cfaya.
78. Kuma Dawuda da Sulaiman,
sa'ad da suke yin hukunci a cikin
sha'anin shuka, a lokacin da tuma-
kin mutane suka yi kiwon dare a
cikinsa. Kuma Mun kasance Masu
halarta ga hukuncinsu.
79. Sai Muka fahimtar da ita
(mas'alar (1) ) ga Sulaiman. Kuma
dukansu Mun ba su hukunci da
*>"-&. V i >- ?<0^ "\t '"At" >"".'
r*-
(1) Asalin mas 'alar, tumakin wani mutum suka yi kiwon 6arna a gonar wani a cikin
dare, alhali kuwa ana kallafa wa mai dabbobi ya kange dabbobinsa da dare kamar yadda
ake kallafa wa mai shuka da tsare shukarsa a cikin yini. Sai Dawudu ya yi hukunci da cewa
mai shukar ya mallaki tumakin, shi kuma mai tumaki ya mallaki shukar 6atacciya. Sai
Sulaiman ya gyara hukuncin da cewa mai gona ya riki tumakin ya rayu a kansu har a
lokacin da mai dabbobin ya gyara masa gonarsa har ta koma yadda take a farkon lokacin,
sa'an nan ya mayar da tumakin ya karfti gonarsa.
A cikin kissar akwai nunin cewa annabawa ba su saunar facfin gaskiya saboda wani
mutum duk yadda yake, kuma ana warware hukunci idan kuskure ya auku a ciki. Kuma
annabawa suna yin kuskure ga abin da bai shaft wahayi ba. Kuma komawa ga gaskiya idan
ta bayyana wajibi ne.
493
21 - Suratul Anbiya'
3ii^il^-n
ilmi, kuma Muka hore duwatsu tare
da Dawuda, suna tasblhi, da tsun-
tsaye. Kuma Mun kasance Masu
aikatawa.
80. Kuma Muka sanar da shi
sana'ar (1) wata tufa saboda ku,
domin ya tsare ku daga maka-
minku. To, shin, ku masu godewa
ne?
81. Kuma (Muka hore) wa
Sulaiman iska mai tsananin buga-
wa, tana gudana da umurninsa
zuwa ga Icasar nan wadda Muka
sanya albarka a cikinta. Kuma
Mun kasance Masana ga dukan
kome.
82. Kuma daga Shaicfannu
(Mun hore) wanda ke nutso saboda
shi. Kuma suna yin wani aiki baicin
wancan. Kuma Mun kasance Masu
tsaro a gare su.
83. Kuma da Ayyuba a sa'ad da
ya yi kiran Ubangijinsa, (ya ce,)
"Lalle m, cuta ta shafe ni, alhali
kuwa Kai ne Mafi rahamar masu
rahama."
84. Sai Muka karba masa, sa'an
nan Muka kuranye abin da ke a
gare shi na cuta, kuma Muka kawo
masa mutanesa da kwatankwacinsu
tare da su, saboda rahama daga
-V/. „/><./ 'u'tfu*? "
(1) Wannan yana nuna wajabcin yin sana'a wadda mutum ke rayuwa a kanta. Kuma
yana nuna wajabcin aiki da sabubba domin neman tsaron kai. Ba ya halatta ga mutum ya
yi kwance babu sana'ar da zai tsayu a kanta ko kuma ya gitta kansa ga halaka da tawTlin
tawakkali. Tawakkali shT ne mayar da a£ibar al'amura ga Allah a bayan mutum ya yi abin
da yake iya yi.
494
21 - Suratul Anbiya'
mhm-n
wurinMu da tunatarwa (1) ga masu
ibada.
85. Kuma da Isma'ila da Idrisa
da Zulkifli, dukansu suna daga
masu hakuri.
86. Kuma Muka shigar da su a
cikin rahamarMu. Lalle ne, suna
daga salihai.
87. Kuma mai kifi (2) , a sa'ad da
ya tafi yana mai hushi, sai ya yi
zaton cewa ba za Mu kukunta masa
ba. Sai ya yi kira a cikin duffai cewa,
"Babu abin bautawa face Kai.
Tsarki ya tabbata a gare Ka. Lalle
ne ni, na kasance daga azzalumai."
88. Sai Muka kar6a masa, kuma
Muka tslrar da shi daga bakin ciki.
Kamar haka ne Muke tsirar da
masu imani.
89. Kuma da Zakariyya a sa'ad
da ya kirayi Ubangijinsa cewa, "Ya
Ubangiji! Kada Ka bar ni maka-
daici alhali kuwa Kai ne Mafi alhe-
rin masu gado."
90. Sai Muka kar6a masa, kuma
Muka kyautata (3) masa matarsa.
Lalle ne su, sun kasance suna gudun
tsere zuwa ga ayyukan alheri.
EG Ci^^J^^}^^jt
^ .i r • *-* T ■
t
'•">\\' *"" >\\" "" *tr
( 1 ) Ayyuba Manzon Allah, an jarrabe shi da wahaloli ga jikinsa da halakar diyansa ya
yi hakuri da hukuncin Allah, sai Allah Ya mayar masa da abin da ya halaka, sa'an nan
kuma ya kara masa wani kamarsa, domin rahamarSa ga masu mayar da al'amari a gare
Shi, da kuma wa'azi ga masu ibada domin kada aukuwar wata masifa ta sanya su katsewa
da rashin daukar hakuri.
(2) ShT ne Yunus bn Matta. Ya yi hushi da mutanensa domin ba su kar6i addini ba,
sai ya bar su tun a gabanin a yi masa iznin barinsu. Sai Allah Ya jarrabe shi da fadawa cikin
ruwa har wani kifi ya hadlye shi, sa'an nan kuma ya amayo shi a bayan wahala, ya koma
wa mutanensa. Suka yi Tmani.
(3) Bayan matarsa ta tsufa ba ta haihu ba Allah Ya kyautata mahaifarta, ta sami cikin
Yahaya daga gare shi.
495
21 — Suratul Anbiya'
;i^Jl^-n
Kuma suna kiran Mu a kan kwa-
cfayi da fargaba. Kuma sun kasance
masu saunar (aikata saBo) gare Mu.
91. Kuma da wadda ta tsare far-
jinta daga alfasha. Sai Muka hura a
cikinta daga ruhinMu. (1) Kuma
Muka sanya ta ita da danta wata
aya ga duniya.
92. Lalle ne wannan (2) ita ce
al'ummarku, J;a zama al'umma
guda, kuma Ni ne Ubangijinku. Sai
ku bauta Mini.
93. Kuma suka kakkatse al 'ama-
rinsu a tsakaninsu. Dukan kowa-
nensu masu komowa zuwa gare Ni
ne.
94. Domin wandaya aikata daga
ayyukan kwarai alhali kuwa yana
mai imani, to, babu musu ga ai-
kinsa, kuma Mu Masu rubutawa
gare shi ne.
95. Kuma hananne ne a kan
wata alkarya da Muka halakar
cewa lalle su, ba su komowa.
96. Har sa'ad da aka burfe Ya-
juju da Majuju, alhali kuwa suna
gaggawa daga kowane tudun kasa.
^t >> "\< »>s t'V'Y
^J~?J
(1) Ruhin Allah a nan, shi ne Mala'ika Jibnla. ShTne ya hura a cikin wuyan ngarta.
sai ta yi ciki da Tsa. Maryamu ba Annabiya ba ce, an ambace ta ne domin shimfida ga
maganar Tsa, amincin Allah ya tabbata a gare shi. Zamanta aya shi ne ta sami da ba da
namiji ba, kuma wanda ya yi hakuri ga tsaren haddodin Allah, Allah zai daukaka shi da
ni'imar duniya da ta Lahira. Danta ya zama aya saboda magana yana yaro, da Annabci,
da daukar hakuri ga zartar da umurnin Allah.
(2) Al'ummar Musulmi duka guda ce ko da yake Annabawansu sun zo dabam-
dabam, a cikin lokuta masu nlsa tsakaninsu da harsuna dabam-dabam, domin duk
akidarsu guda ce a kan Ubangiji guda ne. Sa'an nan daga baya wacfanda suka fita daga
wannan akidar suka rarrabu kungiya-kungiya.
496
21 - Suratul Anbiya'
ag&fi&-n
97. Kuma wa'adin nan tabbatac-
ce ya kusanto, sai ga ta idanun
wadanda suka kafirta suna bay-
yanannu,j(suna cewa), "Ya kaiton-
mu! Hakika, mun kasance a cikin
gafala daga wannan! A'a, mun ka-
sance dai masu zalunci!"
98. (A ce musu) "Lalle ne, ku da
abin (1) da kuke bautawa, baicin
Allah, makamashin Jahannama ne.
Ku masu tusgawa gare ta ne."
99. Da wadannan (abubuwan
bautawar) sun kasance abubuwan
bautawar gaskiya ne, da ba su tusga
mata ba, alhali kuwa dukansu
madawwama a cikinta ne.
100. Suna da wata hargdwa a
cikinta, alhali kuwa su, a cikinta, ba
su sauraren kome.
101. Lalle ne wadanda kalmar
yabo ta gabata a gare su dagaj*are
Mu, wadannan wadanda ake nisan-
tarwa daga barinta ne.
102. Ba su jin sautin motsinta
alhali kuwa su madawwama ne a
cikin abin da rayukansu suka yi
marmarinsa.
103. Firgitar nan mafi girma, ba
za ta bakanta musu rai ba. Kuma
mala'iku na yi musu maraba (suna
cewa), "Wannan yininku ne wanda
kuka kasance ana yi muku wa'adi
da shi."
'*>>'+ '4"
-A
>".<-:
.' ~*<> ' ^ .<*<
Jiij;pyT&
O^L^tUcjpJ^l ^ ..-I ^ ^jyu^i
'*>K/'* ' ' y > ' "■**
(1) Bayin Allah salihai da mala'iku wadanda wadansu mutane suka bauta musu da
tsammanin cewa za su cece su daja Allah, ba za a sanya su wuta ba saboda ibadar da aka yi
musu, domin yabon Allah ya rigayi hushinSa zuwa gare su. Bayansu da mai bautar da
wanda ake bautawar kamar gumaka da wadansunsu, wuta za su shiga.
497
21 — Suratul Anbiya'
*M&m-t\
104. A ranar da Muke nacfe
sama kamar nadewar takarda ga
abubuwan rubutawa, kamar yadda
Muka fSra a farkon (1) halitta Muke
mayar da ita. Wa'adi ne a Kanmu.
Lalle ne Mun kasance Masu aika-
tawa.
105. Kuma lalle, haklka, Mun
rubuta a cikin Littafi baicin Amba-
to (2 ^ (Lauhul Mahfuz) cewa kasa,
bayiNa salihai, suna gadonta.
106. Lalle ne^a cikin wannan
(Al£ur'ani), haklka, akwai iyarwa
(ga maganar da ta gabata (3) ) ga
wacfansu mutane masu ibada.
707. Kuma ba Mu aike ka ba
face domin wata rahama ga talikai.
108. ICa ce, "Abin sani kawai,
ana yin wahayi zuwa gare ni ne,
cewa 4 Lalle ne, Abin bautawarku,
Abin bautawa ne Guda. To, shin, ku
masu mika wuya ne?"
109. Sa'an nan idan suka juya,
to, ka ce, "Na sanar da ku, a kan
daidaita, kuma ban sani ba, shin,
abin da ake yi muku wa'adi maku-
sanci ne ko kuwa mamsanci?
110. "Lalle ne ShT (Allah) Yana
sanin bayyane daga magana, kuma
Yana sanin abin da kuke Boyewa.
111. "Kuma ban sani ba, tsam-
maninsa ya zama fitina a gare ku,
.<#%
pJ^S^y
* *' \\>\ *' * *.
£*\ S> >> > <i'
(1) Tim da farawa bai buwaye Mu ba mayarwa ba za ta buwaye Mu ba. A Ranar
ICiyama ake nacfe sama a kan abin da yake a cikinta kamar yadda ake nade takarda a kan
abin da ta kunsa na rubutun mala'iku a kan bayin Allah.
(2) Allah Yana mallakar da kasa bayinSa salihai, ba za ta fita daga gare su ba sai idan
sun musanya addininsu na kwarai da wani mugu.
(3) Ita ce cewa, bayin Allah salihai suna gadon kasa.
498
22 - Suratul Hajj
mm-v
ko kuma don jin dadi, zuwa ga wani
dan lokaci."
112. Ya ce, "Ya Ubangiji! Ka yi
hukunci da gaskiya. Kuma Ubangi-
jinmu Mai rahama ne Wanda ake
neman taimako a kan abin da kuke
siffantawa."
Tana karantar da yadda ake tsarkake aklda daga aFadu, kuma
a tsare ta daga gare su, kada a cucfanya ta da su.
Da si/raw ^4//a/*, Ma/ rahama, Mai jin kai.
1. Ya ku mutane ! Ku bi Ubangi-
jinku da takawa. Lalle ne girgizar (1)
kasa ta tsayuwar Sa'a wata aba ce
mai girma.
2. A ranar da kuke ganin ta du-
kan mai shayar da mama tana sha-
gala daga abin da ta shayar, kuma
dukan mai ciki tana haihuwar cikin-
ta, kuma kana ganin mutane suna
masu maye alhali kuwa su ba masu
maye ba, amma azabar Allah ce mai
tsanani.
I . \ * .111 ^ J
( 1 ) AddTni tsantsa shT ne ke sanya kafa ta yi tsayi da kyau. Idan an cucfanya addini da
wasu abubuwa na bidi'a ko al'adu, to, kafa ba ta iya tsayi balle ma a lokacin girgizar kasa
ta tsayin Sa'a.
499
22 - Suratul Hajj
4-rr
3. Akwai daga mutane (1) wanda
yake yin musu ga sha'anin Allah ba
da wani ilmi ba, kuma yana biyar
kowane Shaidan mai taurin kai.
4. An wajabta masa cewa wanda
ya jiBince shi, to, lalle ne sai ya Batar
da shi, kuma jra shiryar da shi zuwa
ga azabar sa'ir.
5. Ya ku mutane! Idan kun ka-
sance a cikin shakka a Tashin JCiya-
ma, to, lalle ne Mu, Mun halitta ku
daga turbaya, sa'an nan kuma daga
gudajin jini, sa'an nan kuma daga
tsoka wadda ake halittawa, da
wadda ba a halittawa domin Mu
bayyana muku. Kuma Muna tab-
batar da abin da Muke so a cikin
mahaifa zuwa ga wani ajali amba-
tacce, sa'an nan kuma Muna fitar
da ku kuna jariri, sa'an nan kuma
domin ku kai ga cikar karfinku.
Kuma daga gare ku akwai wanda
ke mutuwa, kuma daga gare ku
akwai wanda ake mayarwa zuwa
ga mafi kaskancin rayuwa domin
kada ya san kome a bayan ya sani.
Kuma kana ganin kasa shiru, sa'an
nan idan Muka saukar da ruwa a
kanta, sai ta girgiza kuma ta kum-
bura, kuma ta tsirar da tsiri daga
kowane nau'i mai ban sha'awa.
6. Wancan ne, domin lalle Allah
Shi ne Gaskiya, kuma lalle ne Shi
Yake rayar da matattu, kuma lalle
Shi Mai ikon yi ne a kan kome.
A
( 1 ) An raba mutane a game da addlni kashi hucfu, sa'an nan ya fara da kashi na farko,
mafi yawa daga cikin sauran kasusuwan, watau kashin wawaye masu biyar Shaicfan ga
al'adu da son zuciyoyi su bar hukunce-hukuncen Allah.
500
22 — Suratul Hajj
-rr
7. Kuma lalle ne Sa'ar Tashin
Kiyama mai zuwa ce, babu shakka
a cikinta, kuma lalle ne Allah Yana
tayar da wacfanda suke a cikin
kaburbura.
8. Kuma daga mutane akwai
mai yin musu (1 } ga Allah ba da wani
ilmi ba, kuma ba da wata shiriya ba,
kuma ba da wani littafi mai haska-
kawa ba.
9. Yana mai karkatar da sashen-
sa domin ya Batar (da wasu) daga
tafarkin Allah ! Yana da wani wula-
kanci a duniya, kuma Muna cfanda-
na masa azabar gobara a Ranar
Kiyama.
10. (A ce masa) "Wancan azaba
saboda abin da hannayenka biyu
suka gabatar ne, kuma lalle ne Al-
lah bai zama Mai zalunci ga bayin-
Sa ba."
11. Kuma daga mutane akwai
mai bauta (2) wa Allah a kan wani
gefe. Sa'an nan idan wani alheri ya
same shi, sai ya natsu da shi, kuma
idan wata fitina ta same shi, sai ya
juya baya a kan fuskarsa. Ya yi
hasarar duniya da Lahira. Waccan
ita ce hasara bayyananna.
12. Yana kiran, baicin Allah,
abin da ba ya cutarsa da abin da ba
ya amfaninsa! Waccan ita ce Bata
mai nlsa.
13. Yana kiran wanda yake lalle
cutarwarsa ce mafi kusa daga amfa-
£J£$j
V&,
(1) Kashi na biyu shi ne mugun malami ko Shaidan mai kolcarin 6atar da mabiyansa
wawaye.
(2) Kashi na uku shi ne munafuki mai shiga addTni da biyu.
501
22 - Suratul Hajj
-K
ninsa ! Lalle ne, tir da shi ya zama
majiBinci, kuma tir da ya zama
abokin zama !
14. Lalle ne Allah Yana shigar da
wacfanda suka yi Tmani (1) kuma
suka aikata ayyukan kwarai a cikin
gidajen Aljanna, koramu na gudana
daga karkashinsu. Lalle ne Allah
Yana aikata abin da Yake nufi.
15. Wanda ya kasance yana za-
ton cewa Allah ba zai taimake shi (2)
ba a cikin duniya da Lahira, to, sai
ya mlka wata igiya zuwa sama,
sa'an nan kuma ya yanke ta, sa'an
nan ya duba. Shin, ko lalle kaidinsa
zai gusar da abin da yake ji na
takaici?
16. Kuma kamar haka Muka
saukar da shi (Alkur'ani) yana
ayoyi bayyanannu. Kuma lalle ne,
Allah Yana shiryar da wanda Yake
nufi.
^17. Lalle ne wacfanda suka yi
Tmani da wacfanda suka tuba (3) (Ya-
hudu) da wacfanda suka karkace
(Saba'awa) da Nasara da Maju-
sawa da wacfanda suka yi shirka,
S + S S '
s s y
2^ 0*1>U AlJ^I^ lX£=».
(1) Kashi na hucfu su ne muminai wacfanda suke tsoron Allah, su tsaya a inda Ya
tsayar da su. Su ne mafi karancin kashi ga uku na farko.
(2) Wanda yake zaton Allah ba zai taimaki AnnabinSa ba, kuma yana jin hushin
Allah Ya za6i Muhammadu da Annabci, to, sai ya mutu da hushinsa, kuma ya yi dukan
kaidin da yake so ya yi, Allah ba zai rasa abin da Ya yi nufi ba a game da AnnabinSa, tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi.
(3) Ana ce wa Yahudawa "wadanda suka tuba" domin sun sa6a wa maganar
Annabinsu, Musa, wanda ya ce wa Allah, "Mun tuba zuwa gare Ka." Saba'awa, su ne
masu bauta wa mala'iku daga cikin Larabawa ko Yahudawa. Nasara, su ne wadanda suka
bi Annabi TsaT)an Maryamu, amincin Allah ya tabbata a gare shi. Majusawa, su ne masu
bauta wa wuta da irin addinin Farisa. Masu shirki, su ne masu bauta wa gumaka ko
aljannu ko wadansu mutane, watau irin addinin Larabawa na lokacin Jahiliyya da irin
bautar da wadansu Musulmi ke yi wa waliyyai a yanzu.
502
22 - Suratul Hajj
W$&-rr
lalle ne Allah Yana yin hukunci a
tsakaninsu a Ranar Kryama. Lalle
ne Allah Mahalarci ne a kan dukan
kome.
18. Ashe, ba ka gani ba, lalle
Allah, wanda yake a cikin sammai
da wanda yake a cikin kasa yana yin
sujada a gare Shi, da kuma rana da
wata da taurari da duwatsu da itace
da dabbobi, da kuma masu yawa
daga mutane? Kuma wacfansu
masu yawa azaba ta tabbata a kan-
su. Kuma wanda Allah Ya wula-
kantar, to, ba ya da wani mai girma-
mawa. Kuma Lalle ne Allah Yana
aikata abin da Yake so.
19. Wacfannan kungiyoyi biyu (1)
ne masu husuma, sun yi husuma ga
sha'anin Ubangijinsu. To, wacfanda
suka kafirta an yanka musu wacfan-
su tufafi daga wata irin wuta, ana
zuba tafasasshen ruwa daga bisa
kawunansu.
20. Da shl ake narkar da abin da
yake a cikin cikunansu da fatun
jikinsu.
21. Kuma suna da wacfansu
gwalmomin duka na bakin karfe.
22. A koyaushe suka yi nufin fita
daga gare ta, daga bakin ciki, sai a
mayar da su a cikinta, (a ce musu)
"Ku cfancfani azabar gobara."
23. Lalle ne, Allah Jfana shigar
da wacfanda suka yi imani kuma
$> s s
^ ^" * ** - -^ — *
(1) Kuma ya kasa mutane kungiya biyu, kungiyar farko su ne masu bin addinin
gaskiya, kungiya ta biyu su ne masu karkace wa addinin gaskiya, kamar kasusuwa uku na
farko. A ko da yaushe akwai husuma a tsakanin kungiyoyin biyu. Sa'an ya ambaci
sakamakon kungiyar karya ta farkon,
503
22 - Suratul Hajj
-<r
suka aikata ayyukan kwarai a cikin
gidajen Aljanna, koramu suna gu-
dana daga karkashinsu, ana kawata
su, a^cikinsu, dawacfansumundaye
na zinari da lu'u-lu'u. Kuma tafa-
finsu a cikinsu alharini ne. (1)
24. Kuma an shiryar da su zu-
wa ga mai kyau na zance, kuma
an shiryar da su zuwa ga hanyar
Wanda ake gode wa.
25. Lalle ne wacfanda suka kafir-
ta kuma suka taushe (mutane) daga
hanyar Allah da masallaci mai al-
farma wanda Muka sanya shi ga
mutane alhali kuwa mazauni a ciki
da bakauye daidai suke, kuma wan-
da ya yi nufin karkatar (2) da gas-
kiya a cikinsa da zalunci, za Mu
dancfana masa daga wata azaba mai
racfacfi.
26. Kuma a lokacin da Muka
iyakance (3) wa Ibrahim wurin "Da-
kin (Muka ce masa), "Kada ka hacfa
kome da Ni ga bauta, kuma ka
tsarkake T)akiNa, domin masu da-
wafi da masu tsayuwa da masu
ruku'u da masu sujada.
27. "Kuma ka yi yekuwa ga mu-
tane da wajabcin Hajji, su je maka
suna masu tafiya da kafafu da kuma
a kan kowane madankwarin raku-
mi masu zuwa daga kowane rango
mai zurfi.
' if
^ y y
* > y y £ '^'y . > y* "" f"*
^ y ^ ' , s t ~* *
< *\'*'
^^ x y ^ s y -^y
(1) Sakamakon kungiya ta gaskiya, watau muminai.
(2) Ilhadi, shT ne yin ibada ba yadda Allah Ya yi umurni da a yi ta ba. Wanda ya yi
nufin karkatar da gaskiyar ibada a cikin hurumin Makka, Allah zai yi masa azaba mai
tsanani, balle fa a ce mutum ya aikata. Saboda haka yana wajaba ga mai nufin zuwa Hajji
ya koyi yadda ake yin ibada kafin ya tafi Makka domin kada ya jawo wa kansa halaka.
(3) Allah Ya nuna wa Ibrahim iyakar T)akin Ka'aba da iska, sa'an nan ya fara gina
shi, kuma Ya nuna masa iyakokin Hurumin Makka, ya sanya alamomi.
504
22 — Suratul Hajj
-rv
28. "Domin su halarci abubu-
wan amfani a gare su, kuma su
ambaci sunan Allah a cikin 'yan
kwanuka sanannu, saboda abin da
Ya azurta su da shi daga dabbobin
jin dadi. Sai ku ci daga gare su,
kuma ku ciyar da matsattse mata-
lauci.
29. "Sa'an nan kuma sai su kare
ibadarsu da gusar da kazanta,
kuma sai su cika alkawuransu,
kuma sai su yi dawafi (suna gewaya)
ga T)akin nan 'yantacce."
30. Wancan ne. Kuma wanda ya
girmama hukunce-hukuncen Allah,
to, shi ne mafifTci a gare shi, a wurin
Ubangijinsa. Kuma an halatta
muku dabbobin ni'ima, (1) face abin
da ake karantawa a kanku. Saboda
haka ku nTsanci kazanta daga gu-
maka, kuma ku nTsanci kazanta
daga shaidar zur.
31. Kuna masu tsayuwa ga gas-
kiya domin Allah, ba masu yin
shirka da Shi ba. Kuma wanda ya yi
shirka da Allah, to, yana kamar
abin da ya fado daga sama, sa'an
nan tsuntsaye su cafe shi, ko iska ta
fada da shi a cikin wani wuri mai
nlsa.
32. Wancan ne. Kuma wanda ya
girmama ibadodin Allah, to, lalle ne
ita (girmamawar) tana daga ayyu-
kan zukata na ibada.
1>*r*' 'S> . »>7 ' *> * 9 \ S" <" "it
*•&>
"> " '*'
(1) Dabbobin ni'ima, su ne rakumai da shanu da tumaki da awaki. An halatta cinsu
sai wacfanda suka mutu a gabanin a yanka. Kuma shaidar zur kamar bauta wa gumaka
take wajen sabbaba azaba, domin ana halattar da haram ko a haramtar da halat game da
ita.
505
22 - Suratul Hajj
•&&-rr
33. Kuna da wacfansu abubuwan
amfani (1) a cikinta (dabbar hadaya)
har ya zuwa ga wani ajali amba-
tacce, sa'an nan kuma wurin halatta
ta zuwa ga TDakin 'yantacce ne.
34. Kuma ga kowace aPumma
Mun sanya ibadar yanka, domin su
ambaci sunan Allah a kan abin da
Ya arzuta su da shi daga dabbobin
ni'ima. Sa'an nan kuma Abin bau-
tawarku Abin bautawa ne Gu-
da, sai ku sallama Masa. Kuma ka yi
bushara ga masu kankantar da kai.
35. Wadanda suke idan an am-
baci Allah sai zukatansu su firgita,
da masu hakuri a kan abin da ya
same su, da masu tsayar da salla,
kuma suna ciyarwa daga abin da
Muka arzuta su. (2)
36. Kuma rakuman, Mun sanya
su a gare ku, a ibadodin Allah.
Kuna da wani alheri babba a cikin-
su. Sai ku ambaci sunan Allah a
kansu suna tsaye (3) a kan kafafu
uku. Sa'an nan idan sasanninsu
suka fadi, to, ku ci daga gare su,
kuma ku ciyar da mai wadar zuci da
mai bara. Kamar haka Muka hore
muku su, tsammaninku, kuna
godewa.
-£ ^ i"1 h>. '■
^di^fe:
Li^p1j^=aj
( 1 ) Ana amfani da dabbar hadaya wajen hawa saboda larura da shan nono har a kai
ga wurin soke ta. Ana soke hadaya a cikin hurumin Makka.
(2) Wadannan su ne siffofin masu kaskantar da kai, watau masu tawali'u. Zukatansu
na firgita idan an ambaci Allah, su ga kamar suna ganin Sa, a gaba gare su, saboda haka sai
su ji saukin hakuri ga daukar masifa, kuma su tsayar da salla da sauran ibadodi na jiki,
kuma su bayar da zakka da sauran ibadodin dukiya.
(3) Wannan yana nuna yadda ake sukar rakuma suna tsaye a kan kafafu uku, a daure
guda bayan an lankwasa guiwarta an daure sama. Ana ambatar sunan Allah kuma a yi
kabbara a lokacin sukar a masokar zuciyarta. Ana sukar shanu kuma ana yankansu. Ana
yankan tumaki da awaki kawai. Ana yanka sauran dabbobi da tsuntsaye kawai.
506
22 - Suratul Hajj
\km-K
37. Namominsu baza su sami Al-
lah ba, haka jinainansu, amma ta-
kawa daga gare ku tana samun Sa.
Kamar haka Ya hore su saboda ku,
domin ku girmama Allah saboda
shiriyar da Ya yi muku. Kuma ka yi
bushara ga masu kyautata yi.
38. Lalle ne, Allah Yana yin
fada (1) saboda wacfanda suka yi
Imani. Lalle ne Allah ba Ya son
dukan mayaudari, mai yawan
kafirci.
39. An yi izni ga wacfanda ake
yakar su da cewa lalle an zalunce su,
kuma lalle ne Allah, haklka, Mai
Tkon yi ne a kan taimakonsu.
40. Wacfanda aka fitar daga
gidajensu ba da wani hakki ba face
suna cewa, "Ubangijinmu Allah
ne." Kuma ba domin tunkudewar
Allah ga mutane ba, sashensu da
sashe, haklka, da an rusa sau-
ma'o'in (Ruhbanawa) da maja-
mi'o'in Nasara da gidajen ibadar
Yahudu da masallatai wadanda ake
ambatar Allah a cikinsu da yawa.
Kuma lalle, haklka, Allah Yana
taimakon wanda yake taimakon Sa.
Lalle Allah ne, haklka, Mai karfi,
Mabuwayi.
41. ^Wacfanda suke idan Muka
ba su iko a cikin kasa, sai su tsai da
salla, kuma su bayar da zakka
kuma su yi umurni da abin da aka
2 \± m c£&j \£j£^j\&j&&\ ji^
y / \' " S+*
A S
(1) Allah Ya yi alkawarin kare wanda yake aiki da ta£awa dominSa. Yana tunkude
masa maiciyansa, Ya yi masa facfa.
507
22 - Suratul Hajj
-K
sani, (1) kuma su hana daga abin da
ba a sani ba. Kuma akibar al'amura
ga Allah take.
42. Kuma^idan sun karyata ka,
to, lalle, haklka, mutanen Nuhu da
Adawa da Samudawa, sun karyata
a gabaninsu.
43. Da mutanen Ibrahim da
mutanen Lucfu.
44. Da masu Madyana, kuma an
karyata Musa. Sai Na jinkirta wa
kafiran, sa'an nan kuma Na kama
su. To, yaya musuNa (gare su) ya
kasance?
45. Sa'an nan da yawa daga al-
karya, Muka halaka ta, alhali kuwa
tana mai zalunci, sai ta zama facfacf-
cfa a kan rassanta, da yawa daga
rijiya wadda aka wofintar, da kuma
gidajen sarauta macfaukaka.
46. Shin, to, ba su yi tafiya ba a
cikin kasa, domin zukata wacfanda
za su yi hankali da su da kunnuwa
da za su yi saurare da su su kasance
a gare su? Domin lalle ne idanun ba
su makanta, amma zukata wacfan-
da ke a cikin kiraza su ke makanta.
47. Kuma suna neman ka yi gag-
gawa da azaba, alhali kuwa Allah
ba zai sa6a wa'adinSa ba, kuma
lalle ne, yini (2) cfaya a wurin
^t >\3\t'- ' '* '^Z' *Y\ y \*'<
£*i X£=> JLA3 J±£^i dlj
Py^6ooL^=>
»^>.'
p jji^l^^J^L^^i
SS->* ss >
(1) Abin da aka sani daga shar'ia watau shine alheri, kuma abin da ba a sani ba ga
shari'a watau sharri wanda Allah ba Ya so, akasin alheri. Tsayar da ayyukan alheri ba zai
isa ba sai ana yin wa'azi ga mutane a umarce su da yin alheri kuma a hana su daga aikata
sharri.
(2) Allah ba Ya sa6a wa'adinSa. Dadewar rashin saukar azaba, ba sa6awar wa'adi ba
ne, ajalin azabar ne bai zo ba. Domin yini guda a wurin Allah daidai yake da shekara dubu
na shekarun duniya. Saboda haka kwana guda daidai yake da shekara dubu biyu. Saboda
haka Sa'a guda ta Allah na daidai da shekara tamanin da uku da wata hudu.
508
22 — Suratul Hajj
-rv
Ubangijinka kamar shekara dubu
yake daga abin da kuke kidayawa.
48. Kuma da yawa daga alkarya,
Na yi jinkirin azaba gare ta (da
laifinta) sa'an nan Na kama ta,
kuma zuwa gare Ni makoma take.
49. Ka ce, "Ya ku mutane! NT
wani mai gargacfi ne kawai zuwa
gare ku, mai bayyanawa."
50. To, wacfanda suka yi Tmani,
kuma suka aikata ayyuka na kwa-
rai, suna da gafara da arziki na
karimci.
51. Kuma wacfanda suka yi aikin
batawa a cikin ayoyinMu, suna
masu gajiyarwa, wacfancan 'yan Ja-
hTm ne.
52. Kuma ba Mu aika wani man-
zo ba a gabaninka, kuma ba Mu
umurci wani Annabi ba, face idan
ya yi buri, (1) sai Shaicfan ya jefa
(wani abu) a cikin burinsa, sa'an
nan Allah Ya shafe abin da Shaicfan
ke jefawa. Sa'an nan kuma Allah Ya
kyautata ayoyinSa. Kuma Allah
Masani ne, Mai hikima.
53. Domin Ya sanya abin da
Shaicfan ke jefawa ya zama fitina ga
wacfanda a cikin zukatansu akwai
cuta, da masu kekasassun zuka-
tansu. Kuma lalle ne azzalumai,
haklka, suna a cikin sabani mai
nlsa.
<^9l^ OiJr!^" ^^d^'ll ]>«— cJr^I^
s •' % s»
>'*>> i •'it -\\
m /,/>i^/ ***** 't • !»» -vr
( 1 ) Annabawa sukan yi wahami ga tunaninsu, su yi zaton wani abu daidai ne alhali
kuwa a wurin Allah ba haka Yake nufi ba. A kan wannan, sai shakka ta shiga wawa a
kansu, amma wanda ke da imani, to, ba zai rikice ba, saboda wannan kuskure, domin
Allah ba Ya barin su a kansa, sai Ya gyara abin da ke ciki na wahami. Misali kissar
Yunusu, da kissar Annabi a cikin Suratu Abasa, da kissar Ibrahim wajen jayayya da
mala'ikun da aka aika zuwa alkaryoyin mutanen Ludu.
509
22 - Suratul Hajj
-rv
54. Kuma domin wadanda aka
bai wa ilmi su sani lalle shi ne
gaskiya daga Ubangijinka domin su
yilmani da shi saboda zukatansu su
natsu gare Shi. Kuma lalle ne Allah,
hakika, Mai shiryar da wadanda
suka yi Tmani ne zuwa ga hanya
madaidaiciya.
55. Kuma wadanda suka kafirta
ba za su gushe ba suna a cikin
shakka daga gare Shi, har Sa'a ta je
musu bisa ga abke, ko kuwa azabar
wani yini bakarare ta je musu.
56. Mulki a ranar nan ga Allah
yake, Yana hukunci a^ tsakaninsu.
To, wadanda suka yi imani, kuma
suka aikata ayyukan kwarai, suna a
cikin gidajen Aljannar ni'ima.
57. Kuma wadanda suka kafirta,
kuma suka karyata, game da
ayoyinMu, to, wadannan suna da
azaba mai wulakantarwa.
58. Kuma wadanda suka yi hiji-
ra a cikin tafarkin Allah, sa'an nan
kuma aka kashe su, ko suka mutu,
lalle ne, Allah Yana arzuta su da
arziki mai^ kyau^ Kuma lalle ne
Allah, haklka, Shi ne Mafi alherin
masu arzutawa.
59. Lalle ne, Yana shigar da su a
wata mashiga wadda za su yardajda
ita. Kuma lalle ne Allah, hakika
Masani ne, Mai hakuri.
60. Wancan ! Kuma wanda ya
rama azaba da misalin abin da aka
yi masa, sa'an nan kuma aka zalun-
ce shi, lalle ne, Allah Yana taima-
kon sa. Lalle ne Allah, haklka, Mai
yafewa ne, Mai gafara.
i'Y\ >c $'\ tfi'1/ -If^f^t"
ty5*M££v&#'&
[( oo J| ju^^^K— Aa^/% 4 ?zJ>\ ASJO 4j>\jLi\
,>^^>>
S > r>rr
^&\*&&'&£&
4W QlJ>*-Jy^^yCj>~Ju»p.4 «U-JL-j
£ mL>^* J^^-J^ko^-^^Jte <
^
,>*?>^>
<>/ ><;>
510
22 - Suratul Hajj
IH8&-W
61. Wancan ! Saboda Allah Yana
shigar da dare a cikin yini, kuma
Yana shigar da yini a cikin dare,
kuma lalle, Allah Mai jT ne, Mai
gani.
62. Wancan ! Saboda lalle ne Al-
lah, Shi ne Gaskiya, kuma lalle ne,
abin da suke kira, waninSa, slti ne
karya. Kuma lalle ne Allah, Shi ne
Madaukaki, Mai girma.
63. Ashe, ba ka gani ba, lalle ne,
Allah Ya saukar da ruwa (1) daga
sama, sai kasa ta wayi gari koriya?
Lalle Allah Mai tausasawa ne,
Mai kididdigewa.
64. Abin da ke a cikin sammai,
da abin da ke a cikin kasa, Nasa ne,
kuma lalle ne Allah, hakika, Shi ne
Wadatacce, Godadde.
65. Shin ba ka gani ba, lalle ne
Allah Ya hore muku abin da yake a
cikin kasa, kuma jirage suna guda-
na a cikin teku, da umurninSa kuma
Yana rike sama domin kada ta fadi
a kan kasa face da izninSa? Lalle ne
Allah ga mutane hakTka, Mai tau-
sayi ne, Mai jin kai.
66. Kuma ShTne Wanda Ya ray a
ku, sa'an nan kuma Yana matar da
ku, sa'an nan kuma Yana rayar da
ku. Lalle mutum, hakTka, mai kafir-
ci ne.
67. Ga kowace al'umma Mun
sanya wurin yanka, su ne masu yin
baiko gare Shi, saboda haka, kada
t^j>^!fr^^*&
3>^£ J^Djy* *Ajfjc&
&3 ^omJlJJaw^i oj.
A „*;
\" s ' ^tf • \' >\
bljb&jli* UL*>-4jil jisJ
(1) Ya misalta Alkur'ani da ruwan girgije. Kamar yadda ruwa ke sauka daga sama ya
raya kasa haka Alkur'ani yake sauka ya raya zukata.
511
22 - Suratul Hajj
M^-w
su yi maka jayayya a cikin al'ama-
rin (hadaya). Kuma ka yi kira zuwa
ga Ubangijinka, lalle kai, kana a
kan shiriya madaidaiciya.
68. Kuma idan sun yimakajida-
li, sai ka ce, "Allah ne Mafi sani
game da abin da kuke aikatawa.
69. "Allah ne zai yi hukunci a
tsakaninku, a Ranar Kiyama, a
cikin abin da kuka kasance a cik insa
kuna saBa wa juna."
70. Ashe, ba ka sani ba, lalle ne
Allah Yana sanin abin da yake a
cikin sama da £asa? Lalle ne wan-
can yana cikin Littafi, lalle wancan
ga Allah mai sau£i ne.
71. Kuma suna bautawa, baicin
Allah, abin da (Allah) bai saukar da
wani dalili ba game da shi, kuma
abin da ba su da wani ilmi game da
shi, kuma babu wani mai taimako
ga azzalumai.
72. Kuma idan ana karanta ayo-
yinMu bayyanannu, a kansu, kana
sanin abin kyama a cikin fuskokin
wadanda suka kafirta, suna kusa su
yi danka ga wadanda ke karatun
ayoyinMu a kansu. Ka ce, "Shin to,
in gaya muku abin da yake mafi
sharri daga wannan? (Ita ce) Wuta.
Allah Ya yi alkawarinta ga wadan-
da suka kafirta. Kuma makomarsu
ta munana.
73. "Yakumutane! An buga wa-
ni misali, sai ku saurara zuwa gare
shi. Lalle ne wadanda kuke kira bai-
cin Allah, ba za su halitta £uda ba,
ko da sun taru gare shi, kuma
idan Ruda ya Rwace musu wani abu,
fo$A'ttJ&$ *''*'' "
\ o^lliuj^\4il^jJjJjOrO^
>y~ -*
3ft
\
A '4\"
512
22 — Suratul Hay
-tt
ba za su ku6utar da shi ba daga
gare shi. Mai nema da wanda ake
neman gare shi sun raunana."
74. Ba su kaddara wa Allah hak-
kin girmanSa ba. Lalle nc Allah,
hakika, Mai karfl ne, Mabuwayi.
75. Allah na za6en Manzanni
daga mala'iku kuma daga muta-
ne. Cl> Lalle Allah, Mai ji ne, Mai
ganL
76. Yana sanin abin da ke gaba
gare su da abin da ke bayansu,
kuma zuwa ga Allah ake mayar da
aTamura.
77. Ya ku wadanda suka yi ima-
ni ! Ku yi rukiTi, kuma ku yi sujada,
kuma ku bauta wa Ubangijinku,
kuma ku aikata alheri, tsam-
maninku, ku sami babban rabo.
78. Kuma ku yi jihadi a cikin
(aTamarin) Allah, hakkin jihadin-
Sa. ShT ne Ya za6e ku, alhali kuwa
bai sanya wani kunci (2) ba a kanku
a cikin addini. Bisa kudurcewar
ubanku Ibrahim, shine ya yi muku
suna Musulmi C3) daga gabanin
haka. Kuma a cikin wannan (Littafi
ya yi muku suna Musulmi), domin
Manzo ya kasance mai shaida a
fcAd^
©3ft£3#j£
(1) Allah na zaben Manzanni daga mutane da mala'iku kawai. Sabo da haka babu
wani manzo da jinsin aljannu ko wani jinsi, kuma ayar Suratul Ahzab ta 40 ta nuna za6en
nan ya £are daga Annabi Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Duk
wanda ya yi daawar Allah Ya ba shi wani hukumci a bayan Annabi Muhammadu, ko da
bai yi da'awar annabci ba, to, shT Dajjal ne, ba a bin sa.
(2) Babu kunci a cikin Musulunci, duk inda aka fadi tsanani kuma an fadi yadda
sauki zai samu a kowane hah.
(3) Sharadin Musulunci ya zama a kan akidar Ibrahim wanda ya yi wa wannan
aTumma suna da Musulmi tun a zamaninsa, kuma an ambaci wannan magana a cikin
wannan Littafi, watau Alkur'ani, a cikin Surar Bakara aya ta 128.
513
23 — Suratul Mifminun
^m&-xr
kanku, ku kuma ku kasance masu
shaida a kan mutane. Saboda haka
ku tsayar da salla kuma ku bayar
da zakka, kuma ku amince da Al-
lah, Shi ne Maji6incinku. Saboda
haka madalla da Shi Ya zama Maji-
6inci, madalla da Shi ya zama Mai
taimako.
Tana karantar da haklfeanin Tmani da ayyukan imani. Tmani ba
ya cika sai da aiki.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin fcai.
L. Lalle ne, Muminai ci> sun
sami babban rabo.
2. Wadanda suke a cikin sallarsu
masu tawali'u ne.
3. Kuma wadanda suke, su daga
barin yasasshiyar magana, masu
kau da kai ne.
4. Kuma wadanda suke ga zakka
masu aikatawa ne.
5. Kuma wadanda suke ga fa rjo-
jinsu masu tsarewa ne.
$&gxg&
<> ^
<^ * •* ' .tf
^oj^^^U^J
' &'
o**±
*-"&
(1) Muminai su ne wadanda suke da sifofin da aka jeranta a cikin ayoyin da ke hiye
daga ta 2 zuwa ga ta 9.
514
23 — Suratul Mu'minun
mmm-n
6. Face a kan matan aurensu, ko
kuwa abin da hannayen damansu
suka mallaka, to, lalle su, ba wacfan-
da ake zargi ba ne.
7. Saboda haka wanda ya nemi
abin da ke bayan wancan, to,
wadancan su ne masu ketarewar
haddi.
8. Kuma wadanda suke, su ga
amanoninsu da alkawarinsu masu
tsarewa ne.
9. Kuma da wadanda suke, su a
kan sallolinsu suna tsarewa.
10. Wadannan, su ne magada.
11. Wadanda suke gadon (Al-
jannar) Firdausi, (1) su a cikinta
madawwama ne.
12. Kuma lalle ne, halaka, Mun
halitta mutum daga wani tsantsa
daga laka.
13. Sa'an nan kuma Muka sanya
shi, digon maniyyi a cikin matab-
bata natsattsiya.
14. Sa'an nan kuma Muka halit-
ta shi gudan jini, sa'an nan Muka
halitta gudan jinin tsoka, sa'an nan
Muka halitta tsokar ta zama £asu-
suwa, sa'an nan Muka tufatar da
Rasusuwan da wani nama, sa'an
nan kuma Muka £aga shi wata
halitta dabam. Saboda haka albar-
kun Allah sun bayyana, Shi ne Mafi
kyaun masu halittawa.
15. Sa'an nan kuma ku, bayan
wannan, lalle ne masu mutuwa ne.
•».^.t •^<^i^
' >\'Yx»
t'*a < <& <*' *r*
ojsai^^judjj^^a^i
<*£*» ' >, y ,•. »-» y~-~ JSfy \ ' ^ it
ra/iiii3 ,> ^"
r
(1) Asalin firdausi fadama mai ruwa da itace da ni'ima. Aljannar firdausi ita ce mafi
daukakar Aljanna.
515
23 — Suratul Mu'minun
mm&-v
16. Sa'an nan kuma, lalle ne ku,
a Ranar Kiyama, za a tayar da ku.
17. Kuma lalle ne, hakika, Mun
halitta, a samanku, hanyoyi (1) bak-
wai, kuma ba Mu kasance, daga
barin halittar, Masu shagala ba.
18. Muka saukar da ruwa daga
sama bisa gwargwado, sa'an nan
Muka zaunar da shi a cikin kasa,
alhali, lalle ne Mu, a kan tafiyar da
shi, Masu iyawa ne.
19. Sai Muka Raga muku, game
da shi (ruwan), gonaki daga dabinai
da inabobi, kuna da, a cikinsu,
'ya'yan itacen marmari masu yawa,
kuma daga gare su kuke ci.
20. Da wata itaciya, (2) tana fita
daga dutsin Saina'a, tana tsira da
man shafawa, da man miya domin
masu cT.
21. Kuma lalle ne, kuna da abin
lura a cikin dabbobin ni'imomi,
Muna shayar da ku daga abin da
yake a cikinsu, kuma kuna da a
cikinsu, abubuwan amfani (3) masu
yawa, kuma daga gare su kuke cT.
22. Kuma a kansu da a kan jirgin
ruwa ake cfaukar ku.
23. Kuma lalle ne, hakika, Mun
aika Nuhu zuwa ga mutanensa, sai
>y< c\' 't'
(1) Hanyoyi bakwai a kan halittar mutum, su ne baki, da ido, da hand, da kunne, da
mama, da dubura da farji.
(2) Itaciyar Zaituni. Ita ce itaciyar farko da ta tsira a kan kasa a bayan T)ufana, tana
rayuwa mai dogon lokaci; an ce tana rayuwa kamar shekara dubu hucfu. Ana cin
'ya'yanta, ana man shafawa da su, kuma ana yin miya^da su. Asalin sibg, rini domin tana
rina lomar tuwo. Dutsen Sma'a mai albarka, cfur, shi ne dutse mai itace a kansa.
(3) Sufi da gashi domin tufafi da kayan cfaki, kasusuwa da fatu da kofatai domin yin
abubuwan amfani.
516
23 — Suratul Mu'minun
£&$%£- rr
ya ce, "Ya mutanena ! Ku bauta wa
Allah. Ba ku da wani abin bauta wa
waninSa. Shin, to, ba za ku yi taka-
wa ba?"
24. Sai mashawarta wadanda
suka kafirta daga mutanensa, suka
ce, "Wannan ba kowa ba ne, face
mutum misalinku, yana nufin ya
daukaka a kanku. Da Allah Ya so,
lalle ne da Ya saukar da mala'iku.
Ba mu ji (kome) ba, game da wan-
nan, a cikin ubanninmu na farko.
25. "Shi bai zamo kowa ba, face
wani namiji ne, a gare shi akwai
hauka, sai ku yi jinkiri da shi har
wani lokaci."
26. Ya ce, "Ya Ubangijlna! Ka
taimake ni saboda sun karyata ni."
27. Sai Muka yi wahayi zuwa
gare shi. "Ka sana'anta jirgin bisa
ga idonMu, da wahayinMu. To,
idan umurninMu ya je, kuma tanda
ta 6u66uga da ruwa, to, ka shigar a
cikinta daga kome, ma'aura biyu,
da iyalanka, sai wanda Magana ta
gabata a kansa, daga gare su, kuma
kada ka roke Ni (saboda wani) a
cikin wadanda suka yi zalunci, lalle
ne su wadanda ake nutsarwa ne.
28. "Sa'an nan idan ka daidaitu,
kai da wadanda ke tare da kai a kan
jirgin, sai ka ce, 'Godiya ta tabbata
ga Allah, Wanda Ya tsTrar da mu
daga mutane azzalumai.'
^ 29. "Kuma ka ce, 'Ya Ubangi-
jlna ! Ka saukar da ni, saukarwa mai
albarka. Kuma Kai ne Mafi alherin
masu saukarwa.'
U^M^i^hS$\
$ ^^^c!\M^^J3 VJ J5J
517
23 — Suratul Mu'minun
£A$^-cr
30. Lalle ne a cikin wancan
akwai ayoyi, ko da yake Mun ka-
sance, hakika, Masu jarrabawa.
31. Sa'an nan kuma Muka kaga
wani karni, na wadansu dabam,
daga bayansu.
32. Sai Muka aika a cikinsu,
Manzo daga gare su. "Ku bauta wa
Allah. Ba ku da wani abin bauta wa,
sai Shi. Shin to, ba za ku yi takawa
ba?"
33. Mashawarta daga muta-
nensa, wadanda suka kafirta kuma
suka karyata game da haduwa da
Lahira, kuma Muka ni'imtar da su
a cikin rayuwar duniya, suka ce,
"Wannan ba kowa ba, face wani
mutum ne kamarku, yana ci daga
abin da kuke cTdaga gare shi, kuma
yana sha daga abin da kuke sha.
34. "Kuma lalle ne idan kun yi
da'a ga mutum misalinku, lalle ne, a
lokacin nan, haklka, ku masu hasa-
ra ne.
35. "Shin, yana yi muku
wa'adin (cewa) lalle ku, idan kun
mutu kuma kuka kasance tur6aya
da kasusuwa, lalle ne ku, wadanda
ake fitarwa ne?
36. "Faufau faufau ga abin da
ake yi muku wa'adi da shi.
37. "Rayuwa ba ta zama ba face
rayuwarmu ta duniya, muna mutu-
wa kuma muna rayuwa, (1) kuma ba
mu zama wadanda ake tayarwa ba.
M hj^&yj^ij$^}
ftrf-^xl - *>'*'*&' -'.ill
&J&JZQ^k^^y&bl
(1) Muna mutuwa kuma muna rayuwa da haihuwar cfiya da 'ya'y a - A bayan wannan
babu wata rayuwa ta wata Lahira.
518
23 — Suratul Mu'minun
mm&-™
38. "Bai zama kowa ba face na-
miji, ya kirkira karya ga Allah,
kuma^ba mu zama, saboda shi,
masu Tmani ba."
39. Ya ce, "Ya Ubangijma! Ka
taimake ni saboda sun karyata ni."
40. Ya ce, "Daga abu kacfan,
lalle ne za su wayi gari suna masu
nadama."
41. Sai tsawa ta kama su da gas-
kiya, sai Muka ^anya su tunkuba.
Saboda haka nTsa ya tabbata ga
mutane azzalumai!
42. Sa'an kuma Muka kaga ha-
littar wasu karnoni dabam daga
bayansu.
43. Wata al'umma ba ta gabatar
ajalinta, kuma ba za su jinkirta ba.
44. Sa'an nan kuma Muka aika
da ManzanninMu jere, a ko da
yaushe Manzon wata al'umma ya je
mata, sai su karyata shi, saboda
haka Muka biyar da sashensu ga
sashe,_kuma Muka sanya su laba-
run hira. To, nTsa ya tabbata ga
mutane (wacfanda) ba su yin Tmani !
45. Sa'an nan kuma Muka aika
Musa da cfan'uwansa, Haruna,
game da ayoyinMu da dalili bay-
yananne.
46. Zuwa ga Fir'auna da majali-
sarsa, sai suka kangara, alhali sun
kasance mutane ne marinjaya.
47. Sai suka ce, "Shin, za mu yi
Tmani saboda wasu mutane biyu
misalinmu, alhali kuwa mutanensu,
a gare mu, masu bauta ne"
13 Qj^+vj/jfi^&u^*^
'•^-^•V
cr.^ * ^ *- r, -*
519
23 — Suratul Mifminun
<&&#££ -cr
48. Sai suka karyata su saboda
haka suka kasance halakakku.
49. Kuma lalle ne, haklka, Mun
bai wa Musa littafi tsammaninsu, (1)
za su shiryu.
50. Kuma Mun sanya T)an Ma-
ryama, shi da uwarsa wata aya. (2)
Kuma Muka tattara su zuwa ga
wani tsauni ma'abucin natsuwa da
maremari.
57. Ya ku Manzanni ! Ku ci daga
abubuwa masu dacfi, (3) kuma ku
aikata aikin kwarai. Lalle NT, ga
abin da kuke aikatawa, Masani ne.
52. Kuma lalle ne wannan arurn-
marku ce, al'umma guda, kuma NT,
Ubangijinku ne, sai ku bi Ni da
takawa. (4) .
53. Sai (al'ummar) suka yan-
yanke al'amarinsu a tsakaninsu
guntu-guntu, (5 } kowace kungiya
suna masu farin ciki da abin da yake
a gare su.
54. To, ka bar su a cikin 6atarsu
har a wani lokaci.
(1) Bani Isra'ila na yanzu idan sun tuna cewa Alkur'ani ba shTne farkon littafin sama
ba, an bai wa Musa wani littafi, su kuma suna alfahari da shi.
(2) Ayar Tsa da uwarsa ita ce an haife shi babu uba. Kuma a lokacin nan Yahudu
suka so sarkin zamanin nan ya kashe shi, sai uwarsa ta gudu da shi zuwa Baitil Makaddas,
ko Dimashka, ko FalascfTnu, inda suka zauna shekara goma sha biyar har sarkin nan ya
mutu.
(3) Allah Ya umurci ManzanninSa da cin halat, sa'an nan su aikata aikin kwarai.
Haka kuma Ya umurci Muminai. Saboda haka karbar aiki na kwarai an tsayar da shi ne a
kan cin halat.
(4) Takawa, ita ce bauta wa Allah da abin da Ya yi umurni a bauta Masa, a kan
harshen AnnabinSa na zamaninsa. Yanzu babu takawa sai a cikin Musulunci kawai.
(5) Kowa ya kama hanyarsa, al'ummar Musulmi ta zama kungiyoyi dabam-dabam,
kowanensu yana farin ciki da abin da ke gare shi, yana ganin shi ne mafifici.
520
23 — Suratul Mu'minun
^•^i^-rr
55. Shin, suna zaton cewa abin
da Muke taimakon su da shi daga
dukiya da cfiya,
56. Muna yi musu gaggawa ne a
cikin alherori?
57. Lalle ne, wacfanda suke masu
sauna sabo da tsoron Ubangijinsu,
58. Da wacfanda suke, jame da
ayoyin Ubangijinsu suna imani,
59. Da wacfanda suke game da
Ubangijinsu ba su yin shirki,
60. Da wacfanda ke bayar da
abin da suka bayar, alhali kuwa
zukatansu suna tsorace domin suna
komawa zuwa ga Ubangijinsu,
61. Wacfancan suna gaggawar
tsere a cikin ayyukan alheri, alhali
kuwa suna masu tserewa zuwa gare
su (ayyukan alheri).
62. Kuma ba Mu kallafa wa rai
face abin iyawarsa, kuma a wurin-
Mu akwai wani littafi wanda yake
magana da gakiya, kuma su ba a
zaluntar su.
63. A'a, zukatansu suna cikin
jahilci daga wannan (magana),
kuma suna da wacfansu ayyuka,
baicin wancan, su a gare su, masu
aikatawa ne.
64. Har idan Mun kama
mani'imtansu da azaba, sai ga su
suna hargowa.
65. Kada ku yi hargowa a yau,
lalle ne ku, daga gare Mu ba a
taimakon ku.
66. Lalle ne, ayoyiNa sun kasan-
ce ana karatun su a kanku, sai kuka
s£$± S »*' <•,*- ,*,** . , '> <*
"** '*>■' *"i^s l,s
^^^^^iv^krt^^^H^
521
23 — Suratul Mu'minun
m$m-n
kasance, a kan dugaduganku, kuna
komawa baya.
67. Kuna masu^girman kai gare
shi (Annabi), da hira kuna alfasha.
68. Shin fa, ba su yi ta'ammalin
maganar (Alkur'ani) ba, ko abin da
bai je wa ubanninsu na farko ba ne
ya je musu?
69. Ko ba su san Manzonsu ba
ne, domin haka suke masu musu a
gare shi?
70. Ko sunaj:ewa, "Akwai hau-
ka gare shi?" A'a, ya zo musu da
gaskiya, alhali kuwa mafi yawansu,
ga gaskiya, masu ki ne.
71. Kuma da gaskiya (Al-
kur'ani) ya bi son zuciyoyinsu, ha-
klka, da sammai da kasa da wanda
yake a cikinsu sun 6aci. A'a, Mun
tafo musu da ambaton (1) (darajar)
su, sa'an nan su daga barin amba-
tonsu masu bijirewa ne, bijirewa.
72. Ko kana tambayar su wani
haraji ne (a kan iyar da Manzanci a
gare su)? To, harajin Ubangijinka
ne mafi alheri, kuma ShT ne Mafi
alherin masu ciyarwa.
73. Kuma lalle ne, kai, haklka,
kana kiran su zuwa ga hanya
madaidaiciya.
74. Kuma lalle wacfanda ba su yi
Tmani da Lahira ba masu karka-
cewa daga hanya ne.
> >'>'*
»>K
1 -.*6>S'>'
^ ^
(1) Zikiri a nan, shi ne Alkur'ani wanda ya zo wa Larabawa, ko FCuraishawa da
abubuwa na cfaukakarsu, da ambaton sunansu, da shiryar da su, da gabatar da su a kan
sauran kabilu. Amma duk da haka suna bijirewa daga gare shi.
522
23 — Suratul Mu'minun
^m^-^
75. Kuma da Mun ji tausayinsu,
kuma Muka kuranye musu abin da
yake tare da su na cuta, lalle ne da
sun yi zurfi a cikin 6atarsu, suna
cfimuwa.
76. Kuma lalle ne, hakika, Muna
kama su da azaba, (1) sai dai ba su
saukar da kai ba ga Ubangijinsu,
kuma ba su yin tawali'u.
77. Har idan Mun bude, a kansu,
wata kofa mai azaba mai tsanani,
sai ga su a cikinta suna masu
mugi. (2)
78. Kuma Shi ne Wanda Ya kaga
halittar ji da gani da zukata domin-
ku. Kacfan kwarai kuke godewa.
79. Kuma Shi ne Ya halitta ku a
cikin kasa, kuma zuwa gare Shi ake
tayar da ku.
80. Kuma Shi ne Wanda Yake
rayarwa, kuma Yana matarwa,
kuma a gare Shi ne saBawar dare da
yini take. Shin, to, ba za ku han-
kalta ba?
81. A'a, sun fadi misalin abin da
na farko suka fada.
82. Suka ce, "Shin, idan mun
mutu kuma muka kasance turbaya
da kasusuwa, shin, lalle ne mu,
hakika wadanda ake tayarwa ne?
83. "Lalle ne, hakika, an yi mana
wa'adi, mu da ubanninmu ga wan-
nan a gabani. Wannan abu bai
zama kome ba, face tatsuniyoyin na
farko."
X • } S >* SS ** % ^ * ^ ♦ ^ ^ ^
(1) Azabar duniya kamar yunwa da ciwo da talauci da rashin kwanciyar hankali.
(2) Mugi, shi ne kasa yin magana saboda debe tsammani daga samun kowane alheri.
Asalin kalmar daga Fulatanci take.
523
23 — Suratul Mu'minun
mm&-™
84. Ka ce, "Wane ne da mulkin
Rasa da wanda ke a cikinta, idan
kun kasance kuna sani?"
85. Za su ce, "Ta Allah ce." Ka
ce, "Shin, to, ba za ku yi tunani
ba?"
86. Ka ce, "Wane ne Ubangijin
sammai bakwai kuma Ubangijin
Al'arshi mai girma?"
87. Za su ce, "Na Allahne." Ka
ce, "Shin, to, ba za ku b! Shi da
takawa ba?"
88. Ka ce, "Wane ne ga hannun-
sa mallakar kowane abu take, alhali
kuwa shi yana tsarewar wani, kuma
ba a tsare kowa daga gare shi, idan
kun kasance kuna sani?"
89. Za su ce, "Ga Allah yake."
Ka ce, "To, yaya ake sihirce ku?"
90. A'a, Mun zo musu da gas-
kiya, kuma lalle ne su, hakika,
makaryata ne.
91. Allah bai riki wani abin hai-
huwa ba, kuma babu wani abin
bautawa tare da Shi. Idan haka ne,
(akwai abin bautawa tare da Shi),
lalle ne, da kowane abin bautawar
ya tafi da abin da ya halitta, kuma
lalle ne, da wacfansu sun rinjaya a
kan wacfansu. Tsarki ya tabbata ga
Allah, daga abin da suke siffan-
tawa.
92. Masanin 66ye da bayyane.
Sa'an nan Ya cfaukaka daga barin
abin da suke yi na shirka.
93. Ka ce, "Ya Ubangijlna! Ko
dai Ka nuna mini abin da ake yi
musu wa'adi da shi,
> >'>' .i\$> * %"[' 'fit
524
23 — Suratul Mu'minun
mm&-™
94. "Ya Ubangijina, to, kada Ka
sanya ni a cikin mutane azzalumai."
95. Kuma lalle ne Mu, haklka,
masu iyawa ne a kan Mu nuna
maka abin da Muke yi musu wa'adi
da shi.
96. Ka tunkucfe cuta da wadda
take ita ce mafi kyau. Mu ne Mafi
sani game da abin da suke siffan-
tawa.
97. Ka ce, "Ya Ubangijina, ina
neman tsari da Kai daga fizge-
fizgen shaicfanu.
98. "Kuma ina neman tsari da
Kai, ya Ubangijina ! Domin kada su
halarto ni (1) ,"
99. Har idan mutuwa ta je wa
cfayansu, sai ya ce, "Ya Ubangijina,
Ku mayar da ni (duniya).
100. "Tsammanina in aikata aiki
na kwarai cikin abin da na bari."
Kayya ! Lalle ne ita kalma ce, shi ne
mafacfinta, alhali kuwa a baya gare
su akwai wani shamaki har ranar da
za a tayar da su.
101. Sa'an nan idan an yi busa a
cikin kaho, to, babu dangantakoki
a tsakaninsu a ranar nan, kuma ba
za su tambayi junansu ba.
102. To, wacfanda sikelinsu ya yi
nauyi, to, wacfannan su ne masu
babban rabo.
103. Kuma wadanda sikelinsu
ya yi sauki, to, wacfannan ne wa-
danda suka yi hasarar rayukansu
S* >*
J
:/ yVr^h'Ss*/?'^ .\S *s fA 1"\
/^.
(1) Ina neman tsari da Kai, ya Ubangijina! Kada shaicfanu su halarto ni a cikin
al'amurana duka, domin ba su halarta, face da sharri.
525
23 — Suratul Mu'minun
®m"£&-<r
suna madawwama a cikin Jahan-
nama.
104. Fuskokinsu suna balbalar
wuta, kuma su a cikinta masu
yagaggun le66a daga hakora ne.
105. "Shin, ayoyiNa ba su ka-
sance ana karanta su a kanku ba, sai
kuka kasance game da su kuna
karyatawa?"
106. Suka ce, "Ya Ubangijinmu,
shakawarmu ce ta rinjaya a kanmu,
kuma mun kasance mutane 6atattu.
107. "Ya Ubangijinmu! Ka fitar
da mu daga gare ta, sa'an nan idan
mun koma, to, lalle ne, mu ne masu
zalunci."
108. Ya ce, "Ku tafi (da wula-
kanci) a cikinta. Kada ku yi Mini
magana."
109. Lalle ne warfansu kungiyoyi
daga bayiNa sun kasance suna
cewa, "Ya Ubangijinmu! Mun yi
imani, sai Ka gafarta mana, kuma
Ka yi mana rahama, kuma Kai ne
Mafi alherin masu tausayi."
110. Sai kuka rike su leburori
har suka mantar da ku ambatoNa,
kuma kun kasance, daga gare su
kuke yin dariya.
111. Lalle ne Ni, Ina saka musu,
a yau, saboda abin da suka yi wa
hakuri. Domin lalle ne, su, su ne
masu samun babban rabo.
112. Ya ce, "Nawa kuka zauna a
cikin kasa na kidayar shekaru?"
113. Suka ce, "Mun zauna a yini
rfaya ko rabin yini, sai ka tambayi
masu kidayawa."
^<^^t^^==^j
>i *f ri^i"**-* *\^\^*
^<^J^^^i^Q^^J^^J
\$g£^\gg^i
3 ur^L^C-^V^^l^^lill*!*
S^^^y^>^^^^j^^j
j&*y y^ £tf • »*?<»y
526
23 — Suratul Mu'minun
®m&-™
114. Ya ce, "Ba ku zauna ba face
kadan, da dai kun kasance kuna
sani.
115. "Shin, to, kun yi zaton cewa
Mun halitta ku ne da wasa, kuma
lalle ku, zuwa gare Mu, ba za ku
komo ba?"
116. Allah, Mamallaki, Gas-
kiya, Ya daukaka. Babu abin bau-
tawa, face Shi. Shi ne Ubangijin
Al'arshi, mai daraja.
117. Kuma wanda ya kira, tare
da Allah, wadansu abubuwan bau-
tawa na dabam, ba yana da wani
dalili game da shl (kiran) ba, to,
hisabinsa yana wurin Ubangijinsa
kawai. Lalle ne, kafirai ba su cin
nasara.
118. Kuma ka ce, "Ya Ubangi-
jina! Ka yi gafara, Ka yi rahama,
kuma Kai ne Mafi alherin masu
rahama."
p\$u\i&^
*'»* ^
%s*\
.'<. * *'
t>w,
E3 ij^j\^c^j^jy^\C^^j
Tana karantar da hukunce-hukuncen zaman jama'a da ladub-
bansu.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
I.. (Wannan) sura ce. Mun sau-
kar da ita, kuma Mun wajabta ta,
<~» -"♦-'' <
X s »*"
T?"
^.^^l^^u^^jl^j>l vj*
527
24 - Suratul Nur
s^m-u
kuma Mun saukar da ayoyi bayya-
nannu a cikinta, domin ku zan
tunawa.
2.. Mazinaciya da mazinaci, (1)
to, ku yi bulala ga kowance daya
daga gare su, bulala dari. Kuma
kada tausayi ya kama ku game da
su a cikin addinin Allah, idan kun
kasance kuna yinlmani da Allah da
Ranar Lahira. Kuma wani yankin
jama'a daga muminai, su halarci
azabarsu.
3. Mazinaci ba ya aure (2) face da
mazinaciya ko mushirika, kuma
mazinaciya babu mai aurenta face
mazinaci ko mushiriki. Kuma an
haramta wannan a kan muminai.
4. Kuma wadanda ke jifar (3)
mata, masu kamun kai, sa'an nan
kuma ba su je da shaidu hudu ba,
to, ku yi musu bulala, bulala tama-
nin, kuma kada ku karbi wata shai-
da tasu, har abada. Wadancan su
ne fasikai.
5. Face wadanda suka tuba daga
bayan wannan, kuma suka gyaru,
to lalle ne Allah Mai gafara ne, Mai
jin kai.
6. Kuma wadanda ke jlfar ma-
tan (4) aurensu, kuma wadansu shai-
du ba su kasance a gare su ba, face
^qSSZ?'*
«1 «
*><
j^^i«SJ^>cOj<I^
^
^fapvj^
><
*'*
(1) Hukuncin wadanda ba su yi aure ba ne, amma wadanda suka yi aure, hukuncinsu
a jefe su har su mutu, bayan sharudtfa sun cika, kamar yadda yake ga sunna. Kuma
wannan ga hakkin 'ya'ya ne, amma bayi, hukuncinsu bulala hamsin kawai.
(2) Auren mazinaci ko mazinaciya makaruhi ne ga wanda ba hakanan yake ba, domin
tsaron mutunci da kore tuhuma.
(3) Haddin kazafi bulala tamanin ga da, ko arba'in ga bawa idan ya yi kazafi ga da.
(4) Hukuncin ranstuwar li'ani da yadda ake yin ta.
528
24 - Suratul Nur
-U
dai kansu, to, shaidar cfayansu,
shaida hucfu ce da Allah, 'Lalle shT,
haklka, yana daga magasganta'.
7. Kuma na biyar cewa 'La'anar
Allah ta tabbata a kansa, idan ya
kasance daga makaryata.'
8. Kuma yana tunkucfe mata
azaba ta yi shakia, shaida hucfu da
Allah, 'Lalle shi, hakika, yana daga
makaryata.'
9. Kuma ta biyar cewa 'Hushin
Allah ya tabbata a kanta idan ya
kasance daga magasganta.'
10. Kuma ba domin falalar Al-
lah ba a kanku, da rahamarSa,
kuma cewa Allah Mai kar6ar tuba
ne, Mai hikima!
11. Lalle ne, wacfanda (1) sukazo
da kiren karya wacfansu jama 'a ne
^ »
>*
A-^^ ^V \j^i$ty.
(1) Farko Hadisil Ifk ne wanda wadansu suka jefi A'isha, Ummul Muminina da zina
a cikinsa, Allah Ya barrantar da ita. Bai zama sharri ba ga Musulmi, sai dai ya zama alheri
domin ya zama sanadi ga sanin hukunce-hukunce masu yawa, na zaman jama 'a da kuma
darajar mutanen da abin ya shafa.
Yadda kissarjake, shi ne yadda A'ishatu, uwar muminai ta tada, ta ce, "Na kasance
tare da Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, a cikin wani yaki, a bayan an
saukar da Hijabi, watau kulle. Sai ya kare daga yakin ya koma, ya yi kusa da Madlna, sai
ya yi umurni da tashi ga tafiya a wani dare, sai ni kuma na tail na kare sha'anlna, na
fuskanta zuwa ga wurin rakumata, sai na ga abin wuyana ya yanke, sai na koma, na neme
shi, kuma su masu kula da ni suka dauki darbuka suka aza a kan rakuma suna zaton ina
ciki, alhali mata sun kasance saukaka, domin ba su cin kome sai kacfan na abinci.
"Na sami abin wuyana na komo a bayan sun tafi. Sai na zauna a masaukina wanda na
kasance a ciki. Kuma na yi zaton mutanen za su rasa ni su komo zuwa gare ni. Sai na ji
barci, na yi barcin. Shi kuma Safwanu ya yi rurumi daga bayan ayarin yaki, ya fita da
sauran dare, sai ya wayi gari a inda nake. Sai ya ga duhun mutum mai barci, sai ya gane ni a
lokacin da ya gan ni, da ma ya kasance yana ganl na a gabanin kulle, sai na farka da jin
sautinsa na istirja'i.
"A lokacin da ya gane ni, sai na rufe fuskata da mayafma. Wallahi bai yi mini
magana ba da kalma, ni kuma ban ji ko kalma ba daga gare shi, sai dai istirja'insa a
lokacin da ya gurfanar da rakumarsa, ya take kafarta ta gaba ni kuma na hau, ya shiga
yana jan rakumar da ni har muka isa ga uwar yakin, a bayan sun sauka, a cikin zafin rana.
Daga nan wanda ya halaka ya halaka, wanda ya jibinci girman abin, shi ne Abdullahi bn
Ubayyin bn Salul." Buhari da Muslimu sun ruwaito shi.
529
24 - Suratul Nur
&l)m-n
daga gare ku, kada ku yi zatonsa
sharri ne a gare ku. A'a, alheri ne
gare ku. Kowane mutum daga gare
su na da sakamakon abin da ya
sana'anta na zunubi, kuma wanda
ya jiBinci girmansa daga gare su,
yana da azaba mai girma.
12. Don me a lokacin da kuka ji
shi, muminai maza da muminai
mata ba su yi zaton alheri game da
kansu ba, kuma su ce, "Wannan
kiren karya ne bayyananne?"
13. Don me ba su zo da shaidu
hudu a kansa ba? To, idan ba su
kawo shaidun nan ba, to, watfan-
nan, a wurin Allah, su ne makar-
yata.
14. Kuma ba domin falalar Al-
lah ba a kanku da rahamarSa, a
cikin duniya da Lahira. Lalle ne, da
azaba mai girma ta shafe ku a cikin
abin da kuka kutsa da magana a
cikinsa.
15. A lokacin da kuke mara-
barsa da harsunanku kuma kuna
cewa da bakunanku abin da ba ku
da wani ilmi game da shi, kuma
kuna zaton sa mai sauki, alhali
kuwa, shi a wurin Allah, babba ne.
16. Kuma don me a lokacin da
kuka ji shi, ba ku ce ba, "Ba ya
yiwuwa a gare mu, mu yi magana a
game da wannan. Tsarki ya tabbata
a gare Ka, wannan kiren karya ne
mai girma"?
17. Allah Yana yi muku wa'azi,
kada ku koma ga irinsa, har abada,
idan kun kasance muminai.
.' *>s. C V^.
Ejr^K
\JC
y I**' f**S >r'»ss \y "v '*> *' y\<y
&&?*'*
530
24 - Suratul Nur
-a&U8&-ft
18. Kuma Allah Yana bayyana
muku ayoyinSa, kuma Allah Masa-
ni ne, Mai hikima.
19. Lalle ne wacfanda ke son al-
fasha ta watsu ga wacfanda suka yi
imani, suna da azaba mai racfacfi, a
cikin duniya da Lahira. Kuma Al-
lah, Shi ne Ya sani, alhali kuwa, ku
ba ku sani ba.
20. Kuma ba domin falalar Al-
lah ba a kanku da rahamarSa...
Kuma lalle ne Allah Mai tausayi ne,
Mai jin kai !
21. Ya ku wacfanda suka yi ima-
ni, kada ku bi hanyoyin Shaicfan.
Kuma wanda ke bin hanyoyin Shai-
cfan, to, lalle ne shi, yana umurni da
yin alfasha da abin da ba a sani ba,
kuma ba domin falalar Allah ba a
kanku da rahamarSa, babu wani
mutum daga gare ku da zai tsar-
kaka har abada, kuma amma Allah
Yana tsarkake wanda Yake so,
kuma Allah Mai ji ne, Masani.
22. Kuma kada (1) ma'abuta fa-
lala daga gare ku da mawadata su
rantse ga rashin su bayar da alheri
ga ma'abuta zumunta da miskinai
da muhajirai, a cikin hanyar Allah.
Kuma su yafe, kuma su kau da kai.
*^ £ <<■ £ ,^><r^ c '$\\>&"\ >*?-*-">'
EX < * ^i>> 4 ^X '•IS''' '+'/'** s A
j^J 4b\jkio &by£ 2 ' i^>tiL>^j l^Oj
( 1 ) Mai yin alheri domin Allah kada ya yanke shi daga wanda yake yi wa alherin nan,
saboda ya yi masa wani laifi, da ya shafe shi ga mutuncinsa ko dukiyarsa. Sai ya yafe, ya
kau da kai, ya ci gaba da alherinsa domin Allah, kamar yadda Mistahu, wanda yake a cikin
dangin Abubakar As-Siddik ya shiga a cikin HadTsil Ifk alhali kuwa Abubakar ke ciyar da
shi saboda shi miskini ne da zumunta kuma a tsakaninsu, sai Abubakar ya gafarta masa,
kuma ya ci gaba da ba shi abin da yake ba shi. Haka sauran wacfanda suka facfa a cikin
wannan masifa, an yafe musu a bayan an yi musu haddin £azafi, sai dai wanda ya cfauki
mai girmansa, watau Ibn Ubayyu, shi kam ba a yi masa haddi ba domin Allah Ya yi masa
alkawarin azaba mai tsanani a Lahira. Watau Musulmi ake yi wa haddi domin ya
tsarkaka.
531
24 - Suratul Nur
-^UJM-H
Shin, ba ku son Allah Ya gafarta
muku, alhali Allah Mai gafara ne,
Mai jin kai?
23. Lalle ne wacfannan da suke
jTfar mata masu kamun kai gafilai (1)
muminai, an la'ane su, a cikin du-
niya da Lahira, kuma suna da azaba
mai girma.
24. A ranar da harsunansu, da
hannayensu, da kafafunsu, suke
bayar da shaida a kansu, game da
abin da suka kasance suna aika-
tawa.
25. A ranar da Allah Yake cika
musu sakamakonsu tabbatacce,
kuma suna sanin (cewa) lalle Allah,
Shi ne Gaskiya bayyananna.
26. Miyagun mata domin miya-
gun (2) maza suke, kuma miyagun
maza domin miyagun mata suke,
kuma tsarkakan mata domin tsar-
kakan maza suke, kuma tsarkakan
maza domin tsarkakan mata suke.
Warfancan su ne wadanda ake
barrantawa daga abin da (masu
kazafi) suke facfa, kuma suna da
gafara da arziki na karimci.
27. Ya ku wadanda suka yi ima-
ni! Kada ku shiga gidaje wadan-
da ba gidajenku ba, sai kun sami
izni, kuma kun yi sallama (3) a kan
ma'abutansu. Wannan ne mafi al-
heri gare ku, tsammaninku, za ku
tuna.
f£\> *V\* '\?'> '*v\
(1) Gaflla, ita ce wadda ba ta jarrabi kome ba saboda Rurucciya.
(2) Haka miyagun kalmomi ba su dacewa sai daga mugun mutum. Kuma kalmomin
kwarai ba su fltowa sai daga mutanen kwarai.
(3) Hukuncin shiga gidaje da neman izni da sallama.
532
24 - Suratul Nur
^)m-u
28. To, idan ba ku sami kowa a
cikinsu ba, to, kada ku shige su, sai
an yi muku izni. Kuma idan an ce
muku, "Ku koma." Sai ku koma,
shi ne mafi tsarkaka a gare ku.
Kuma Allah game da abin da kuke
aikatawa, Masani ne.
29. Babu laifi a kanku, ga ku
shiga gidaje wadanda ba zaunannu
ba, a cikinsu akwai wadansu kaya
naku. Kuma Allah Yana sanin abin
da kuke nunawa, da abin da kuke
Boyewa.
30. Ka ce wa muminai maza su
runtse daga ganinsu, kuma su tsare
farjojinsu. (1) Wannan shi ne mafi
tsarki a gare su. Lalle ne, Allah,
Mai kididdigewa ne ga abin da
suke sana'antawa.
31. Kuma ka ce wa muminai
mata su runtse daga gannansu,
kuma su tsare farjojinsu, kuma
kada su bayyana kawarsu face abin
da ya bayyana daga gare ta, kuma
su doka da mayafansu a kan wuyan
rigunansu, kuma kada su nuna ka-
warsu face ga mazansu ko uban-
ninsu, ko ubannin mazansu, ko
cfiyansu, ko cfiyan mazansu, ko 'ya-
n'uwansu, ko cfiyan 'yan'uwansu
mata, ko matan (2) kungiyarsu, ko
abin da hannayensu na dama suka
ijj^u^A^ L3^j jyt- Jb 0' ^L^oj-^O^^^jlJ
J^>J^>
\>/<L»~
(1) Hukuncin tsare idanu da rufe al'aura ga maza da mata.
(2) Matansu, watau mata Musulmi banda mata kafirai, ba ya halatta ga mace kafira
ta ga al'aurar mace Musulma. Mabiya su ne masu neman bukata ga mata watau miskinai,
tsofaffi daga maza. Al'aurar mace, diya a cikin salla ko a tare da wani namiji ajnabi, to,
dukan jikinta ne sai fuska da tafuna, haka kuma a cikin salla. Amma a tare da mace
Musulma tsakanin cibiya da guiwoyi, shi ne al'aura, kuma tare da muharraminta, dukan
abin da ba sasanni ba. Baiwa kamar namiji take, al'aurarsu abin da ke tsakanin cibiya da
guiwa.
533
24 - Suratul Nur
s&UIISJ&-rt
mallaka, ko mabiya wasun masu
bukatar mata daga maza, ko jarirai
wacfanda ba su tsinkaya a kan al'au-
rar mata. Kuma kada su yi duka da
Rafafunsu, domin a san abin da
suke 66yewa daga kawarsu. Kuma
ku tuba zuwa ga Allah gaba cfaya,
ya ku muminai ! Tsammaninku, ku
sami babban rabo.
32. Kuma ku aurar da gwauraye
daga gare ku, da salihai daga bayin-
ku, da kuyanginku. Idan sun kasan-
ce matalauta, Allah zai wadatar da
su daga falalarsa. Kuma Allah Ma-
wadaci ne, Masani.
33. Kuma wacfannan da ba su
sami aure ba, su kame kansu, har
Allah Ya wadatar da su daga fala-
larsa. Kuma wacfanda ke neman
fansa daga abin da hannuwanku na
dama suka mallaka, to, ku cfaura
musu fansa idan kun san akwai
wani alheri a cikinsu, kuma ku ba su
wani abu daga dukiyar Allah wan-
nan da Ya ba ku. Kuma kada ku
tilasta kuyanginku a kan yin zina,
idan sun yi nufin tsaron kansu, (1)
domin ku nemi rayuwar duniya,
kuma wanda ya_ tilasta su, to, lalle
Allah, a bayan tilasta su, Mai gafa-
ra ne, Mai jin kai.
34. Kuma lalle ne, Mun saukar,
zuwa gare ku, ayoyi masu bay-
yanawa, da misali daga wacfanda
suka shige daga gabaninku, da
wa'azi ga masu takawa.
±^a&o* <W'j^Jot> ^j^yy^i o}p=*gylj
<£$*» •/£ s'**!'
( 1 ) Tsaron kai, shi ne su yi aure ; tllastawa a nan, shi ne a hana su aure domin su yi wa
ubangijinsu aiki.
534
24 — Suratul Nur
s^m-^
35. Allah ne Hasken sammai da
kasa, misalin HaskenSa, kamar
taga, a cikinta akwai fitila, fitilar a
cikin karau, karau cfin kamar shi
tauraro ne mai tsananin haske, ana
kunna shi daga wata itaciya mai
albarka, ta zaituni, ba bagabashiya
ba kuma ba bayammaciya ba, man-
ta na kusa ya yi haske, kuma ko
wuta ba ta shafe shi ba, haske a kan
haske, Allah na shiryar da wanda
Yake so zuwa ga HaskenSa. Kuma
Allah na buga misalai ga mutane,
kuma Allah game da dukan kome,
Masani ne.
36. A cikin wacfansu gidaje wa-
cfanda Allah Ya yi umurnin a dauka-
ka, kuma a ambaciJSunanSa a cikin-
su, suna yin tasblhi a gare Shi a
cikinsu, safe da maraice.
37. Wacfansu maza, wacfanda
wani fatauci ba ya shagaltar da su,
kuma sayarwa ba ta shagaltar da su
daga ambaton Allah, da tsai da
salla da bayar da zakka, suna
tsoron wani yini wanda zukata suna
bibbirkita a cikinsa, da gannai.
38. Domin Allah Ya saka musu
da mafi kyaun abin da suka aikata,
kuma Ya kara musu daga falalarSa.
Kuma Allah Yana arzuta wanda
Yake so, ba da lissafi ba.
39. Kuma wacfanda suka kafirta,
ayyukansu suna kamar kawa-
weniya ga fako, mai kishirwa yana
zaton sa ruwa, har idan ya je masa
bai iske shi kome ba, kuma ya
sami (1) Allah a wurinsa, sai Ya cika
&^t^3^^Jo^
>*i'*'\^ *'*.''>' S*i""
(1) Ya sami Allah a wurin da icawalwalniyar take, alhali Allah Ya gaya masa cewa
535
24 - Suratul Nur
^M&-h
44. Allah Yana juyar da dare da
yini. Lalle ne a cikin wannan akwai
abin kula ga ma'abuta gannai.
45. Kuma Allah ne Ya halitta
kowace dabba daga ruwa. To, daga
cikinsu akwai wacfanda ke tafiya a
kan cikinsu, kuma daga cikinsu
akwai wacfanda ke tafiya a kan
kafafu biyu, kuma daga cikinsu
akwai wacfanda ke tafiya a kan hudu.
Allah Yana halitta abin da Yake so,
lalle Allah, a kan kowane abu, Mai
ikon yi ne.
46. Lalle ne, haklka, Mun sau-
kar da ayoyi masu bayyanawa.
Kuma Allah Yana shiryar da wanda
Yake so zuwa ga hanya madaidai-
ciya.
47. Kuma suna cewa, "Mun yi
Tmani da Allah da kuma Manzo,
kuma mun yi cfa'a." Sa'an nan
kuma wata kungiya daga gare su, su
juya daga bay an wancan. Kuma
wacfancan ba muminai ba ne.
48. Kuma idan aka kira su zuwa
ga Allah da ManzonSa, domin Ya yi
hukunci (1) a tsakaninsu, sai ga wata
kungiya daga gare su suna masu
bijirewa.
49. Kuma idan hakki ya kasance
a gare su, za^su je zuwa gare shi,
suna masu mika wuya.
50. Shin, a cikin zukatansu ak-
wai cuta ne, ko kuwa suna tsoron
\" \" .•'<>>*'. y* "-*? Tr-T. >*T"
Dp O^^^l^u^^^^^^folj
(1 ) Wannan yana nuna cewa rashin yarda da hukuncin Allah kafirci ne. Wanda ya kai
kara ga kotun aFada alhali kuwa yana Musulmi kuma ya halatta haka, ba da wata lalura
ba, ya zama kafiri sai idan ya tuba. Ba ya halatta ga Musulmi su yarda da yin kotunan
al'ada a kasarsu.
537
24 - Suratul Nur
4&ai8i-ri
Allah Ya yi^zalunci a kansu, da
Manzonsa? A 'a, wadancan su ne
azzalumai.
57. Maganar muminai, idan aka
kira su zuwa ga Allah da ManzonSa
domin Ya yi hukunci a tsakaninsu,
takan kasance kawai su ce, "Mun ji,
kuma mun yi da'a." Kuma wadan-
nan su ne masu cin nasara.
52. Kuma wanda ya yi da'a ga
Allah da ManzonSa, kuma ya ji
tsoron Allah, ya kuma bl Shi da
takawa, to, wadannan su ne masu
babban rabo.
53. Kuma suka rantse da Allah
iyakar rantsuwarsu, 'Lalle ne, idan
ka umurce su, haklka, suna fita.' Ka
ce, "Kada ku rantse, da'a sananna
ce! Lalle ne, Allah Mai kididdige-
wa ne ga abin da kuke aikatawa."
54. Ka ce, "Ku yi cfa'a ga Allah,
kuma ku yi da'a ga Manzo. To, idan
kun juya, to, a kansa akwai abin da
aka aza masa kawai, kuma a kanku
akwai abin da aka aza muku kawai.
Kuma idan kun yi masa cfa'a za ku
shiryu. Kuma babu abin da yake a
kan Manzo face iyarwa bay-
yananna."
55. Allah Ya yi wa'adi ga wacfan-
da suka yi Tmani daga gare. ku,
kuma suka aikata ayyukan kwarai,
lalle zai shugabantar da su a cikin
kasa kamar yadda Ya shugabantar
da wacfanda suke daga gabaninsu,
kuma lalle ne zai tabbatar musu da
addininsu wanda Ya yardar musu,
kuma lalle ne Yana musanya musu
daga bayan tsoronsu da aminci,
A »s ^
^£\-^\%&J.\&Wj^
' \ <\t\\ /'*S \>'\" ?\\&i'"
'f •*- •f»'"> .•Irf • ^^irri
538
24 - Suratul Nur
-a&IIK&-ft
suna bauta Mini, ba su hacfa kome
da NT. Kuma wanda ya kafirta a
bayan wannan, to, wacfancan, su
ne fasikai.
56. Kuma ku tsayar da salla,
kuma ku bayar da zakka, kuma ku
yi cfa'a ga Manzo, tsammaninku a
yi muku rahama.
57. Kada lalle ka yi zaton
wacfanda suka kafirta za su bu-
waya a cikin kasa, kuma mako-
marsu wuta ce, kuma lalle ne ma-
komar ta munana.
58. Ya ku wacfanda suka yiTma-
ni! Wacfannan da hannuwanku na
dama suka mallaka da wacfanda ba
su isa mafarki ba daga cikinku, su
nemi izni (1) sau uku; daga gabanin
sallar alfijir, da lokacin da kuke
ajiye tufafinku saboda zafin rana,
kuma daga bayan sallar isha'i. Su
ne al'aurori uku a gare ku. Babu
laifi a kanku kuma babu a kansu a
bayansu. Su masu kewaya ne a
kanku, sashenku a kan sashe. Ka-
mar wannan ne Allah Yake bayya-
na ayoyinSa a gare ku. Kuma Allah
Masani ne, Mai hikima.
59. Kuma idan yara daga cikin-
ku suka isa mafarki, to, su nemi
izni, kamar yadda wacfanda suke a
gabaninsu suka nemi iznin. Kamar
wannan ne Allah Yake bayyana
ayoyinSa a gare ku, kuma Allah
Masani ne, Mai hikima.
( 1 ) Ladabin shiga gida shl ne dukan yaron da ya balaga, cfa ne ko bawa, kada ya shiga
gida ko cfaki a bayan sallama sai ya nemi izni da cewa "In shiga ?" Idan an karba masa da
izni, ya shiga, idan kuma yana zaton ba a ji shi ba, sai ya sake neman izni har sau uku.
Neman izni yana wajaba ko ga yaran gidan a cikin lokuta uku, watau a gabanin sallar
asuba da lokacin tsakar ranar na kailula da bayan sallar isha'i.
539
24 - Suratul Nur
4&M&-H
60. Kuma tsofaffi daga mata,
wacfanda ba su fatan wani aure, to,
babu laifi a kansu su ajiye tufafinsu,
ba suna masu fitar da kawaj)a,
kuma su tsare mutuncinsu, shl ne
mafi alheri a gare su. Kuma Allah
Mai ji ne, Masani.
61. Babu laifi a kan makaho,
kuma babu laifi a kan gurgu, kuma
babu laifi a kan majiyyaci, kuma
babu laifi a kan kowanenku, ga ku
ci (abinci) daga gidajenku, ko daga
gidajen ubanninku, ko daga gidajen
uwayenku, ko daga gidajen
'yan'uwanku maza, ko daga gidajen
'yan'uwanku mata, ko daga gidajen
baffanninku, ko daga gidajen gwag-
gwanninku, ko daga gidajen
kawunnanku, ko daga gidajen in-
noninku, ko abin da kuka mallaki
mabucfansa, ko abokinku, babu lai-
fi a gare ku ku ci gaba cfaya, ko
dabam-dabam. To, idan kun shiga
wasu gidaje, ku yi sallama a kan
kawunanku, (1) gaisuwa ta daga wu-
rin Allah mai albarka, mai dacfi.
Kamar wancan ne Allah Yake
bayyana muku ayoyinSa, tsam-
maninku ku yi hankali.
62. Wacfanda ke muminai sosai,
su ne wacfanda suka yi Tmani da
Allah da ManzonSa, kuma idan sun
kasance tare da shi, a kan wani
al'amari na aikin gayya, ba su tafiya
sai sun neme shi izni. Lalle ne wa-
( 1 ) Akwai daga ladubban zamantakewa har dai a tsakanin dangi a ci abincin juna, ko
a ci tare a makai gada, ko kuwa kowa ya ci dabam. Kuma idan an hadu a yi gaisuwa a
tsakanin juna, gaisuwa irin wadda Allah Ya ce Musulmi su yi wa junansu da cewa
"Assalamu alaikum". Ita ce gaisuwa mai kyau. Ana kara "wa rahmatul Lahi wa
barakatuh," domin ta kara dacfi.
540
24 - Suratul Nur
^miM-^
cfanda suke bicfar ka izni, wadancan
su ne suke yin Tmani da Allah da
ManzonSa. To, idan sun neme ka
izni saboda wani sha'aninsu, to, ka
yi izni ga wanda ka so daga gare su,
kuma ka nema musu gafara daga
Allah. Lalle Allah Mai gafara ne,
Mai jin kai (1) .
63. Kada ku sanya kiran Man-
zo (2) a tsakaninku kamar kiran
sashenku ga sashe. Lalle ne Allah
Yana sanin wacfanda ke sancewa
daga cikinku da sadade. To, wacfan-
da suke sabawa daga umurninSa, su
yi saunar wata fitina ta same su, ko
kuwa wata azaba mai radadi ta
same su.
64. To! Lalle Allah ne Yake da
mulkin abinjia ke a cikin sammai
da kasa, hakika, Yana sanin abin da
kuke a kansa, kuma a ranar da ake
mayar da su zuwa gare Shi, sai Yana
ba su labari game da abin da suka
aikata. Kuma Allah, ga dukan
kome, Masani ne.
**+ *'*' A\ ^ >">'*" *r * t .1t>
(1) Babban ladabin hacfuwar jama'a shi be Tmani da Allah kuma da ManzonSa. Sa'an
nan kuma biyayya ga shugaba wajen ayyukan gayya na rayuwa^hade, kamar ginin
masallaci da hanya da kasuwa da makabarta. Shugaba yana da ikon bayar da iznin
fakuwar mai uzuri, kuma yana da Ikon hanawa gwargwadon hali. Wannan kuma ya nuna
muhimmancin aikin gayya da tsayuwar shugaba a kansa, da wajabcin karba kira zuwa gare
shi. Kuma wannan yana nuna halaccin karbar haraji daga mutane domin a tsayu da
bukatocin hacfuwar jama'a gwargwadon hali.
(2) Wannan yana nuna ladabin yadda ake kiran Manzon Allah ta hanya mai ladabi.
Kada a kira shi da sunansa kamar yadda ake kiran sauran mutane da 'Ya Ali,' 'Ya Zaid,'
sai dai a ce Ya Manzon Allah! a cikin sauti mai laushi mai dacfi. Kuma wannan ladabi yana
shafar dukan Musulmi na kowane zamani game da Shu'abansu wanda yake shugabantar su
ga al'amurransu na zamantakewa. Kuma wannan yana nuna rashin kyawon masu cewa
suna zikiri da kiran sunan Allah kamar haka "Allah ! Allah ! Allah !" saboda rashin ladabin
da ke cikin yin haka ga Manzon Allah balle ga Allah. Ba a yin addini sai yadda Allah Yake
son a yi Masa, watau yadda AnnabinSa ya shiryar da mutane domin su bi shi, su yi aiki da
shi. Kuma saba wa umurnin Annabi yana sabbaba fitina ga mutane ko kuma ga kasa gaba
daya.
541
25 — Suratul Furican
£»Ji^-vo
Tana karantar da yin kira ga tauhidi da kore shubhohi daga
Alkur'ani Mai girma, da kuma Annabi, tslra da aminci su tabbata a
gare shi.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin RaL
1. Albarkata tabbata ga Wanda
Ya saukar da (Littafi) mai rar-
rabewa a kan BawanSa, domin ya
kasance mai gargadi ga halitta.
2. Wanda Yake da mulkin sam-
mai da kasa, kuma bai riki abin
haihuwa ba, kuma abokin tarayya
bai kasance a gare Shi ba a cikin
mulkinSa, kuma Ya halitta dukan
kowane abu, sa'an nan Ya kaddara
shi kaddarawa.
3. Kuma suka riki abubuwan
bautawa, baicin Shi, ba su yin halit-
tar kome, alhali su ne ake halitta wa,
kuma ba su mallakar wa kansu
wata cuta, ko wani amfani, kuma
ba su mallakar mutuwa, kuma ba su
mallakar rayarwa, kuma ba su mal-
lakar tayarwa.
4. Kuma warfanda suka kafirta
suka ce, "Wannan ba kome ba ne
face kiren karya da (Muhammadu)
~" <' ' s"**\
' '''A' •ire-' '^<t7 *»■*>» -It
rnr
>'C\'> -err ^r,-^,r< " •il" - *'^ .Irii^
542
25 — Suratul Fur£an
(WlS-w
ya kirkira shi, kuma wacfansu muta-
ne na dabam suka taimake shi a
kansa." To, lalle ne sun je wa zalun-
ci da karkacewar magana.
5. Kuma suka ce, "Tatsuniyoyi
ne na farko ya rurrubuta, sai su ake
shibtarsu a gare shi safe da yam-
ma."
6. Ka ce, "Wanda Yake sanin
asTri a cikin sammai da Rasa ne Ya
saukar da shi. Lalle ne, ShT Ya
kasance Mai gafara, Mai jin kai."
7. Kuma suka ce, "Mene ne ga
wannan Manzo, yana cin abinci,
kuma yana tafiya a cikin kasuwan-
ni ! Don me ba a saukar da mala'ika
zuwa gare shi ba, domin ya kasance
mai gargadi tare da shi?
8. "Ko kuwa a jefo wata taska
zuwa gare shi, ko kuwa wata gona
ta kasance a gare shi, yana ci daga
gare ta?" Kuma azzalumai suka ce,
"Ba ku bin kowa, face mutum sihir-
tacce."
9. Ka duba yadda suka buga
maka misalai, sai suka Bace, domin
haka ba su iya bin tafarki.
10. Albarka ta tabbata ga Wan-
da, idan Ya so, Ya sanya maka mafi
alheri daga wannan (abu): gonaki,
koramu na gudana daga karka-
shinsu, kuma Ya sanya maka ma-
nyan gidaje.
11. A 'a, sun karyata game da
Sa'a, alhali kuwa Mun yi tattalin
wuta mai tsanani ga wanda ya ka-
ryata (manzanni) game da Sa'a.
/&kS '*/>< ' m x's ><| C . •Iff'
Mi».' ' '
t)j>J^->,AjlAs
Wi^^Sil^y^di
• -s •
543
25 — Suratul Fur£an
&%&$$&-<>
12. Idan ta gan su daga wani
wuri mai nTsa, sai su ji sautin fushi
da wani ruri nata.
13. Kuma idan an jefa sua wani
wuri mai kunci daga gare ta, suna
wadanda aka daure, ciki daidai, sai
su kirayi halaka a can.
14. Kada ku kirayi halaka guda,
kuma ku kirayi halaka mai yawa.
15. Ka ce, "Shin, wancan ne mafi
alheri, ko kuwa Aljannar dawwama
wadda aka yi wa'adi ga masu taka-
wa? Ta zama, a gare su, sakamako
da makoma.
16. "Suna da abin da suke so, a
cikinta, suna madawwama. Wan-
nan ya kasance wa'adi abin tam-
baya a kan Ubangijinka."
17. Kuma ranar da Yake tara su
da abin da suke bauta wa, baicin
Allah, sai Ya ce, "Shin, ku ne kuka
Batar da bayiNa, wadannan, ko
kuwa su ne suka Bata daga hanya?"
18. Suka ce, "Tsarki ya tabbata a
gare Ka, ba ya kasancewa a gare
mu, mu riki wadansu majiBinta,
baicin Kai, kuma amma Ka jiyar da
su dacfi su da ubanninsu har suka
manta da Tunatarwa, kuma sun
kasance mutane ne halakakku."
19. To, lalle ne, sun karyata
game da abin da kuke cewa, saboda
haka ba ku iya karkatarwa ga
(maganarsu), kuma ba ku iya tai-
mako (ga hana azaba), kuma wan-
da ya yi zalunci a cikinku za Mu
dandana masa azaba mai girma.
20. Kuma ba Mu aika ba, a
gabaninka daga Manzanni, face
Uol*> ^ ]>*-£" -^r^t U^-* U^(*4^b ^i
LHj~*la
^i^^fJ^LjbV^,
' >\>"
>'*K<
|vp iyj^\\Jge*J>{\
9 £$\£j&^^
544
25 — Suratul Fur£an
OT$j&-fo
lalle su, haklka, suna cin abinci
kuma suna tafiya a cikin kasuwoyi.
Kuma Mun sanya sashen mutane
fitina ga sashe. Shin kuna yin haku-
ri? Kuma Ubangijinka Ya kasance
Mai gani.
21. Kuma wacfanda ba su fatan
haduwa da Mu, suka ce, "Don me
ba a saukar da mala'iku ba a kan-
mu, ko kuwa mu ga Ubangijinmu?"
Lalle ne sun kangara a cikin rayu-
kansu, kuma suka yi tsaurin kai,
tsaurin kai mai girma.
22. A ranar da suke ganin ma-
la'iku, babu bushara a yinin nan ga
masu laifi, kuma suna cewa, "Allah
Ya kiyashe (1) mu!"
23. Kuma Muka gabata zuwa ga
abin da suka aikata daga aiki, sai
Muka sanya shi kura watsattsiya.
24. Ma'abuta Aljanna a ranar
nan, su ne mafi alheri ga matab-
bata, kuma mafi kyaun wurin kai-
lula.
25. Kuma a ranar da sama take
tsattsagewa tare da gizagizai, kuma
a saukar da mala'iku, saukarwa.
26. Mulki a ranar nan, na gas-
kiya, yana ga Mai rahama, kuma ya
zama yini, a kan kafirai, mai tsa-
nani.
27. Kuma ranar da azzalumi
yake cTzo a kan hannayensa, yana
cewa, "Ya kaitona! (A ce dai) na
riki hanya tare da Manzo!
t^Vfa^^i^^jrU
E0 y^JLA{j~*>^J
(1) Asalin maganar shi ne "Tsari tsararre," watau muna neman tsari daga Allah, tsari
tabbatacce.
545
25 — Suratul Fur£an
ozmm-v
28. "Ya kaitona! (A ce dai) ban
riki wane masoyi ba!
29. "Lalle ne, haklka, ya 6atar
da ni daga Tunawa a bayan (Tuna-
war) ta je mini." Kuma Shaicfan ya
zama mai zum6ulewa ga mutum.
30. Kuma Manzo ya ce, "Ya
Ubangijlna! Lalle mutanena, sun
riki wannan Alkur'ani abin kaura-
cewa!"
31. Kuma kamar haka ne, Muka
sanya makiyi daga masu laifi ga
kowane annabi. Kuma Ubangi-
jinka Ya isa ga zama Mai shiryarwa,
kuma Mai taimako.
32. Kuma wacfanda suka kafirta
suka ce, "Don me ba a saukar da
Alkur'ani a kansa ba, jimla guda?"
Kamar wancan ! Domin Mu karfa-
fa zuciyarka game da shi, kuma
Mun jeranta karanta shi da hankali
jerantawa.
33. Kuma ba za su zo maka da
wani misali ba, face Mun je maka da
gaskiya da mafi kyau ga fassara.
34. Wacfanda ake tayarwa a kan
fuskokinsu, zuwa ga Jahannama,
wacfancan su ne mafi sharri ga wuri,
kuma mafi 6acewa ga hanya.
35. Kuma lalle ne, Mun bai wa
Musa Littafi, kuma Mun sanya
cfan'uwansa, Haruna, mataimaki
tare da shi.
36. Sai Muka ce, "Ku tafi, ku
biyu, zuwa ga mutanen nan wacfan-
da suka karyata game da ayo-
yinMu." Sai Muka darkake su,
darkakewa.
^ ^' >\" <'
Q\&^\^dx>jX&
546
25 — Suratul Fur£an
mm&-^
37. Kuma mutanen Nuhu, a 16-
kacin da suka karyata Manzanni,
Muka nutsar da su, kuma Muka
sanya su wata aya ga mutane, kuma
Muka yi tattalin azaba mai racfacfi
ga azzalumai.
38. Da Adawa da Samudawa, da
mutanen Rassi, da wacfansu al'um-
momi, a tsakanin wannan, masu
yawa.
39. Kuma kowannensu, Mun
buga masa misalai, kuma kowanne
Mun halakar da (shi), halakarwa.
40. Kuma lalle ne, haklka,
(Kuraishi) sun je a kan alkaryar nan
wadda aka yi wa ruwa, ruwan aza-
ba. Shin, ba su kasance sun gan ta
ba? A'a, sun kasance ba su kaunar
tayarwa (a Kiyama).
41. Kuma idan sun gan ka, ba su
rikon ka face da izgili, (suna cewa,)
"Shin, wannan ne wanda Allah Ya
aiko, Manzo?
42. "Lalle ne, ya yi kusa ya Batar
da mu daga Ubangijinmu, in ba
domin da muka yi hakuri a kansu
ba." Kuma za su sani, a lokacin da
suke ganin azaba, wane ne mafi
Bacewa ga hanya!
43. Shin, ka ga wanda ya riki
Ubangijinsa son zuciyarsa? Shin,
to, kai ne ke kasancewa mai tsaro a
kansa?
44. Ko kana zaton cewa, mafi
yawansu suna ji, ko kuwa suna
hankali? Su ba su zama ba face
dabbobin gida (1) suke. A'a, su ne
mafi 6acewa ga hanya.
$' >>' »4S
s'>*' '<>{\' f*Y\' >\'\'\"
((TAJ \j&S^sJ\\
><ia
$^53 ta ^* :: d^V^^'i^li^^ Jl ^
^ /*'. ^ > "vT
9^^/^
^ V^^^^^jJuIiaI
=»J<a
ll^i^
( I ) Dabbobin gida sun fi rashin hankali bisa ga na daji, domin na daji na gudun abin
547
25 — Suratul Furkan
Gmm-v>
45. Ashe, ba ka duba ba zuwa ga
Ubangijinka, yadda Ya mike inu-
wa? Kuma da Ya so da Ya bar ta
tsaye cif, sa'an nan Muka sanya
rana mai nuni a kanta.
46. Sa'an nan Muka karbe ta
(inuwa) zuwa gare Mu, karba mai
sauki.
47. Kuma ShT ne Wanda Ya sa-
nya muku dare ya zama tufa, da
barci ya zama hutawa, da yini ya
zama lokacin tashi (kamar Tashin
Kiyama).
48. Kuma Shi ne Ya aika iskokin
bushara gaba ga rahamarSa, kuma
Muka saukar da ruwa mai tsar-
kakewa daga sama.
49. Domin Mu rayar, game da
shi, gari matacce, kuma Mu shayar
da shi dabbobi da mutane masu
yawa daga abin da Muka halitta.
50. Kuma lalle ne, haklka, Mun
sarrafa (1) shi (Alkur'ani) a tsaka-
ninsu, domin su yi tunani, sai dai
mafi yawan mutanen sun ki face
kafirci.
51. Kuma da Mun so, haklka, da
Mun aika da mai gargadi (2) a cikin
kowace alkarya.
$&& &1$^&1^
M \yj* $->} ^s^L^J IjI^J]^
da zai cuce su su kuma dabbobin gida suna zama tare da masu cin su, su sha nononsu kuma
su kashe 'ya'yansu.
(1) Sarrafa Alkur'ani watau Mun sanya shi a cikin misalai dabam-dabam domin su
gani ko su ji, su yi tunani, amma sai suka lei sauraren, sai dai kafirci.
(2) Da Muna so da Mun aika wa kowane gari da Annabinsa mai yi musu gargadi,
amma ba Mu so haka ba, sai Muka aika ka kai daya zuwa ga dukan duniya domin Mu
daukaka darajarka.
548
25 — Suratul Furkan
vmm-v
52. Saboda haka kada ka yi cfa'a
ga kaflrai, ka yake su, da shi, yaki
mai girma.
53. Kuma ShT tie Ya garwaya
tekuna biyu, wannan mai dacfi, mai
saukin hacfiya, kuma wannan gishi-
ri gur6atacce, kuma Ya sanya wani
shamaki a tsakaninsu da kariya
mai shamakacewa.
54. Kuma Shi ne Ya halitta mu-
tum daga ruwa, sai Ya sanya shi
nasaba da surukuta, kuma Ubangi-
jinka Ya kasance Mai Tkon yi.
55. Kuma suna bauta wa, bai-
cin Allah, abin da ba ya amfanin su,
kuma ba ya cutar su, kuma kafiri ya
kasance mai taimakon (Shaicfan) a
kan Ubangijinsa.
56. Ba Mu aika ka ba sai kana
mai bayar da bushara, kuma mai
gargacfi.
57. Ka ce, "Ba ni tambayar ku
wata ijara a kansa face wanda ya so
ya riki wata hanya (1) zuwa ga
Ubangijinsa."
58. Kuma ka dogara a kan
Rayayye wanda^ba Ya mutuwa,
kuma ka yi tasblhi game da gode
Masa. KumaYa isa zama Mai ki-
diddigewa ga laifuffukan bayinSa.
59. Wanda Ya halitta sammai da
kasa da abin da yake a tsakaninsu, a
>< "". /" ?>
****'<{'•»< 'six' fa > ' *? 9 "
]j±J>-^bS^> ^r>y^*<j* £r-=>j±oX+^;
L j'^Jo^ji \j^jr+^ \ i^S^ \
(1) Ba na neman wata ijara saboda ina karanta muku Alkur'ani, ko, saboda ina
shiryar da ku, amma wanda ya so ya ciyar da dukiyarsa domin Allah, to, shT kam ba ni
hana shi, sai ya ciyar. Kuma mun sani Annabi ba ya cin sadaka. A kan haka ne wadansu
Malamai suka hana kar6ar ijara a kan karantar da Alkur'ani. Abin da yake Mu'utamadi
ya halatta saboda Hadisi, kuma da saukakewa ga aikin yacfa addinin Musulunci. Hukumci
yana canzawa da canzawar hali.
549
25 — Suratul Furkan
Q^lli^-vo
cikin kwanuka shida, sa'an nan Ya
daidaitu a kan Al'arshi, Mai raha-
ma, sai ka tambayi mai bayar da
labari game da (1) Shi.
60. Idan aka ce musu, "Ku yi
sujada ga Mai rahama." Sai su ce,
"Mene ne mai rahama? Ashe, za
mu yi sujada ga abin da kuke umur-
nin mu?" Kuma wannan (ma-
gana (2) ) ta kara musu gudu.
61. Albarka ta tabbata ga Wan-
da Ya sanya masaukai C3) (na tafiyar
wata) a cikin sama kuma Ya sanya
fitila da wata mai haskakewa a
cikinta.
62. Kuma Shi ne Wanda Ya sa-
nya dare da yini a kan mayewa, ga
wanda yake son ya yi tunani, ko
kuwa ya yi nufin ya gode.
63. Kuma bayin Mai rahama (4)
su ne wacfanda ke yin tafiya a kan
kasa da sauki, kuma idan jahilai sun
yi musu magana, sai su ce, "Sala-
ma" (a zama lafiya).
64. Kuma wacfanda suke kwana
suna masu sujada da tsayi a wurin
Ubangijinsu.
•/J,/*^ s I* s / y
(1) Idan kana son sanin siffofin Allah, sai ka tambayi Allah, domin babu wanda ya
san Shi, sani na gani balle ya iya gaya maka yadda Yake, saboda haka siffofin Allah da
sunayenSa duka ba a yin shisshigi a gare su, sai yadda aka ji su daga Manzon Allah.
Taukifiyyai ne.
(2) K6 sun san gaskiyar abin da aka kira su zuwa gare shi, ba za su yi dFa ba, domin
wai suna jin nauyi su kar6i umurni daga wani mutum.
(3) Taurari bakwai wacfanda ake ce wa matafa, su ne Mirrikh, da Zahra, da Ucfarid,
da Kamar watau wata, da rana, da Mushtari, da Zuhal, Kuma burjoji su goma sha biyu ne.
Su ne Himlu, da Saur, da Zauja'a, da Sirtan, da Asad, da Sunbula, da Mlzan, da Akrab, da
Kausu, da Jadyu, da Dalwu da Hut.
(4) Bay an da ya ambaci masu kin su yi sujada ga Mai rahama saboda kangararsu, sai
kuma ya fara ambaton siffofin masu son yin sujada gare Shi, Ya yi musu suna Bayin Mai
rahama.
550
25 — Suratul Furkan
m$m-v
65. Kuma wacfanda suke cewa,
"Ya Ubangijinmu ! Ka karkatar da
azabar Jahannama daga gare mu.
Lalle ne, azabarta ta zama tara. (1)
66. "Lalle ne ita ta munana ta
zama wurin tabbata da mazauni."
67. Kuma wacfanda suke, idan
sun ciyar, ba su yin barna, kuma ba
su yin kwauro, kuma (ciyarwarsu)
sai ta kasance a tsakanin wancan da
tsakaitawa.
68. Kuma wadanda ba su kiran
wani ubangiji tare da Allah, kuma
ba su kashe rai wanda Allah Ya
haramta face da hakki, kuma ba su
yin zina. Kuma wanda ya aikata
wancan, zai gamu da laifuffuka.
69. A ribanya masa azaba a Ra-
nar Kiyama. Kuma ya tabbata a
cikinta yana wulakantacce.
70. Sai wanda ya tuba, kuma ya
yi imani, kuma ya aikata aiki na
kwarai, to, wadancan Allah Yana
musanya miyagun ayyukansu da
masu kyau. Allah Ya kasance Mai
gafara Mai jin kai.
71. Kuma wanda ya tuba, (2)
kuma ya aikata aiki mai kyau, to,
lalle ne sai ya tuba zuwa ga Allah.
72. Kuma wadanda suke ba su
yin shaidar zur, kuma idan sun
ISP v^-^
(1) Garama, ita ce ukuba da dukiya mai lazimtar wanda aka aza wa ita. Da Hausa
ana cewa tara. Watau azaba da za ta fi karfin jiki har tana neman wani abu wanda ya
danganci jiki. K6 mene ne kamar dukiya.
(2) Wanda ya tuba daga kowane irin zunubi, wadanda aka ambata da wadanda ba a
ambata ba, ko da laifinsa kafirci ne, to, sai ya tuba zuwa ga Allah kawai, tuba ta gaskiya,
lalle ne Allah zai karbi tubarsa matukar ajalin mutuwa bai sauka a kansa ba.
551
25 — Suratul Furkan
mm&-^
shucfe ga yasassar magana sai su
shucfe suna masu mutumci.
73. Kuma wacfanda suke, idan
an tunatar da su da ayoyin Allah, ba
su saukar da kai, suna kurame (1) da
makafi.
74. Kuma wadanda suke cewa,
"Ya Ubangijinmu ! Ka ba mu sanyin
idanu daga matanmu da zuriyarmu,
kuma Ka sanya (2) mu shugabanni
ga masu takawa."
75. Wadannan ana saka musu da
bene, saboda hakurin da suka yi,
kuma a hada su, a cikinsa, da gaisu-
wa da aminci.
76. Suna madawwama a cikinsa.
Ya yi kyau ga zama matabbaci da
mazauni.
77. Ka ce, "Ubangijlna ba Ya
kula da ku in ba domin addu'ar-
ku (3) ba. To, lalle ne, kun karyata,
saboda haka al'amarin za ya zama
malizimci."
^c<j%=^y^
ftp ^Jioj=^^y^j^. JO -JUfl
(1) Idan an yi musu wa'azi za su saurare shi, kuma su yi aiki da shi. Ba za su zama
kurame ba ga kar6ar gaskiya, kuma ba za su zama makafi ba ga ganin hanyar shiryuwa.
(2) Ana son mutum ya roki Allah Ya daukaka shi, shi da zuriyarsa, daukakar
addini, kamar yadda Annabi Ibrahim ya yi rokon haka. Kuma wannan yana cikin sifofin
Bayin Mai rahama.
(3) Wannan yana nuna cewa Allah Yana son bayinSa masu rokonSa. Kuma Yana son
a roke Shi kwarai.
552
26 — Suratush Shu'ara'
mmm-K
Tana karantar da cewa addinin Allah abu guda ne kuma shi ne
gaskiya. Manzannin Allah ko da yake sun yi magana da harsuna
dabam-dabam a cikin lokutta masu nlsan gaske, amma duk da haka
ba su saba wa juna ga ma'anonin abin da suka facfa ba. Sauran
addinai duka karya ne, masu saba wa juna.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. T).S.M.
2. Wadancan ayoyin Littafi ne
bayyananne.
3. Tsammaninka kai mai hala-
kar (1) da ranka ne, domin ba su
kasance muminai ba !
4. Idan Mun so za Mu saukar, a
kansu, da wata aya daga sama, sai
wuyoyinsu su yini saboda ita suna
masu kaskantar da kai.
5. Kuma wata tunatarwa ba taje
musu ba, daga Mai rahama, sabu-
wa, face sun kasance daga barinta
suna masu bijirewa.
y '< +y* '»'*.
^»> '»■£ 'x-„ v- * .Vi^
»*>"\>
^Cf^S^A^l?
tfWl
(1) Wannan ya nuna cewa Annabi Muhammadu yana jin tsoron rashin Tmanin
mutanensa, kada ya zama shT ne ya gajarta daga abin da Allah Ya cfora a kansa, na iyar da
manzanci. Haka mumini yake, kullum girman Ubangijinsa yake dubi, saboda haka kome
ya yi na cfa'a, sai ya ga kasawar kansa ga tsayuwa da hakkin Ubangijinsa, a kansa, ya kara
jin tsoro da tawali'u.
553
26 — Suratush Shu'ara'
M&-n
6. To, lalle ne, sun karyata, to,
labaran abin da suka kasance suna
yi na izgili da shi za ya je musu.
7. Shin, ba su duba ba zuwa ga
kasa, da yawa Muka tsirar a cikin-
ta, daga dukan nau'i mai kyau?
8. Lalle ne, a cikin wancan ak-
wai aya, kuma mafi yawansu ba su
kasance muminai ba.
9.^ Kuma lalle ne, Ubangijinka,
haklka, ShT ne Mabuwayi, Mai ra-
hama.
10. Kuma a lokacin da Ubangi-
jinka Ya kirayi Musa, "Ka je wa
mutanen nan azzalumai.
11. "Mutanen Fir'auna, ba za su
yi takawa ba?"
12. Ya ce, "Ya Ubangijlna, nTina
tsoron su karyata ni.
13. "Kuma kirjlna ya yi kunci, (1)
kuma harshena ba zai saku ba,
saboda haka ka aika zuwa ga Ha-
runa.
14. "Kuma suna da wani laifi a
kaina, saboda haka ina tsoron kada
su kashe ni."
15. Ya ce, "Kayya! Ku tafi, ku
biyu, da AyoyinMu. Lalle ne ,
Muna tare da ku Muna Masu sau-
rare.
P cx^pJ^^ov^^^i^l
' '% y ys} < '' ^ 4
G3 Oyt^LLi JCt4 G^lS^l^Ciili^b JlJ
(1) Musa yana nuna cewa, shi yana jin tsoro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da
manzanci, domin shi mai saurin fushi ne, yana neman a taimake shi da cfan'uwansa,
Haruna. Wannan ya yi kama da farkon surar inda Annabi, tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi, ya nuna tsoron takaitawa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga
mutanensa domin haka ba su yilmani ba. Halin Annabawa duka cfaya ne ga tsoron takaita
aikin Ubangijinsu.
554
26 — Suratush Shu'ara'
mM&-n
16. "Sai ku je wa Fir'auna, sa'an
nan ku ce, 'Lalle ne, mu, Manzan-
nin Ubangijin halitta ne.
17. "'Ka saki Ban! Isra'ila tare
da mu'."
18. Ya ce, "Shin, ba muji renon-
ka ba a cikinmu, kana jariri, kuma
ka zauna a cikinmu shekaru daga
lokacin rayuwarka?
19. "Kuma ka aikata aikinka
wanda ka aikata alhali kai kana
daga butulai?"
20. Ya ce, "Na aikata shi a loka-
cin ina daga masu jahilcin hushi.
21. "Saboda haka na gudu daga
gare ku a lokacin da na ji tsoronku,
sai Ubangijlna Ya ba ni hukunci,
kuma Ya sanya ni daga Manzanni.
22. "Kuma waccan ni'ima ce,
kana gorinta a kaina, domin ka
bautar da Bani Isra'ila."
23. Fir'auna ya ce, "Kuma mene
ne Ubangijin halittu?"
24. Ya ce, "Ubangijin sammai da
Rasa, da abin da yake a tsakaninsu,
idan kun kasance masu Rarfinlmani.
25. Ya ce wa wadanda suke a
gefensa, "Ba za ku saurara ba?"
26. Ya ce, "Ubangijinku, kuma
Ubangijin ubanninku na farko."
27. Ya ce, "Lalle ne, Manzonku,
wanda aka aiko zuwa gare ku, haki-
Ra, mahaukaci ne."
28. Ya ce, "Ubangijin mafitar
rana da maBuyarta da abin da yake
a tsakaninsu, idan kun kasance
kuna hankalta."
■ »s^ ~f
X">'-'\" •iff ' ' '„ u £ "\C
555
26 — Suratush Shu'ara'
wm&-^
29. Ya ce, "Lalle ne idan ka jiki
wani abin bautawa wanlna, haklka,
ina sanya ka daga cfaurarru."
30. Ya ce, "Ashe, kuma ko da na
zo maka da wani abu mai bay-
yanawa?"
5/. Ya ce, "To, ka zo da shi, idan
ka kasance daga masu gaskiya."
32. Sai ya jefa sandarsa, sai ga ta
kumurci bayyananne.
33. Kuma ya fizge hannunsa, sai
ga shi fari ga masu kallo.
34. (Fir'auna) ya ce ga masha-
warta a gefensa, "Lalle ne, wannan
hakika, masihirci ne, mai ilmi!
35. "Yana son ya fitar da ku
daga kasarku game da sihirinsa. To,
mene ne kuke shawartawa?"
36. Suka ce, "Ka jinkirtar da shi,
shi da dan'uwansa, kuma ka aika
masu gayya a cikin birane.
37. "Za su zo maka da dukan
mai yawan sihiri masani."
38. Sai aka tara masihirta domin
ajalin yini sananne.
39. Kuma aka ce wa mutane,
"Ko ku masu taruwa ne?
40. "Tsammaninmu, mu bi ma-
sihirta, idan sun kasance su ne
marinjaya."
41. To, a lokacin da masihirta
suka je, suka ce wa Fir'auna, "Shin,
lalle ne, haklka muna da ijara, idan
mun kasance mu ne marinjaya?"
42. Ya ce, "Na'am! Kuma lalle
ne, ku ne a lokacin, hakika, mukar-
rabai."
a, / y »""!,*
b Ufl^>t^/» ^"= ^^?'o^ (t^^O'-i^
03 jAjj^^^^l^^^clJ^^Ld^
*£- . .*.
556
26 — Suratush Shu'ara'
mmm-^
43. Musa ya ce musu, "Ku jefa
abin da kuke masu jefawa."
44. Sai suka jefa igiyoyinsu, da
sandunansu, kuma suka ce, 'T)a
karfin Fir'auna lalle ne mu, hakika,
mu ne marinjaya."
45. Sai Musa ya jefa sandarsa,
sai ga ta tana harhacfe abin da suke
yi na karya.
46. Sai aka jefar da masihirta
suna masu sujada.
47. Suka ce, "Mun yi imani da
Ubangijin halitta.
48. "Ubangijin Musa da
Haruna."
49. Ya ce, "Ashe, kun yi Imani
saboda shl, a gabanin in yi muku
izni? Lalle ne shi, hakika babbanku
ne wanda ya koya muku sihirin, to,
za ku sani. Lalle ne, hakika, zan
kakkatse hannuwanku da kafa-
funku a tarnaki, kuma hakika, zan
tsire ku gaba cfaya."
50. Suka ce, "Babu wata cuta!
Lalle ne mu masu juyawa ne zuwa
ga Ubangijinmu.
57. "Lalle ne mu, muna kwa-
cfayin Ubangijinmu Ya gafarta
mana kurakuranmu, ^domin mun
kasance farkon masu imani."
52. Kuma Muka aika zuwa ga
Musa cewa ka yi tafiyar dare da
bayiNa, lalle ne ku wacfanda ake
biya (1) ne.
tQojjjtjtfJ'Z^
*$J
(1) Fir'auna da yakinsa za su bi ku domin su kama ku. Amma ba za su sami Ikon
kama ku ba.
557
26 — Suratush Shu'ara'
WSfflj^-n
53. Sai Fir'auna ya aika masu
gayya a cikin birane.
54. "Lalle ne, wacfannan, hakl-
ka, kungiya ce kacfan.
55. "Kuma lalle ne su, a gare mu,
masu fusatarwa ne.
56. "Kuma lalle ne mu, hakika,
gaba cfaya masu sauna ne."
57. Sai Muka fitar da su daga
gonaki da maremari.
58. Da taskoki da mazauni mai
kyau.
59. Kamar haka!^Kuma Muka
gadar da su ga Bani Isra'Tla.
60. Sai suka bl su suna masu fita
a lokacin hudowar rana.
61. Sa'an nan a lokacin da ja-
ma'a biyu suka ga juna, sai abokan
Musa suka ce, "Lalle ne mu, haki-
ka, wadanda ake riska ne."
62. Ya ce, "Kayya! Lalle ne,
Ubangijina Yana tare da ni, zai
shiryar da ni."
63. Sai Muka yi wahayi zuwa ga
Musa, cewa, "Ka doki teku da
sandarka."... Sai teku ta tsage, (1)
kowane tsagi ya kasance kamar
falalen dutse mai girma.
64. Kuma Muka kusantar da
wadansu mutane a can.
65. Kuma Muka tsTrar da Musa
da wadanda suke tare da shi gaba
daya.
»^ s^ -. >^»^»
(1) Teku ta tsage hanya goma sha biyu a kan adadin dangin BanT Isra'Tla. Suka bi,
suka wuce, sa'ilin nan aka nutsar da Fir'auna, shi da jama'arsa, a cikin hanyoyin ruwan.
558
26 — Suratush Shu'ara'
wmm-K
66. Sa'an nan kuma Muka nut-
sar da wacfansu mutanen.
67. Lalle ne, a cikin wannan ak-
wai aya, kumajnafi yawansu ba su
kasance masu Tmani ba.
68. Kuma lalle ne Ubangijinka,
hakika, Shi ne Mabuwayi, Mai jin
kai.
69. Kuma ka karanta, a kansu,
labarin Ibrahim.
70. A sa'ilin da ya ce wa ubansa
da mutanensa, "Mene ne kuke bau-
ta wa?"
71. Suka ce, "Muna bauta wa
gumaka, saboda haka muna yini
masu lazimta a gare su."
72. Ya ce, "Shin, suna jin ku, a
lokacin da kuke kira?
73. "K6 kuwa suna amfanin ku,
ko suna cutar ku?"
74. Suka ce, "A 'a, mun sami
ubanninmu, kamar haka ne suke
aikatawa."
75. Ya ce, "Shin to, kun ga abin
da kuka kasance kuna bauta wa?
76. "Ku da ubanninku mafi
dadewa?
77. "To, lalle ne su makiya ne a
gare ni, face Ubangijin halittu.
78. "Wanda Ya halitta ni, sa'an
nan Yana shiryar da ni.
79. "Kuma Wanda Yake Shi ne
Yake ciyar da ni, kuma Yana shayar
da ni.
80. "Kuma idan na yi jiyya, to,
Shi ne Yake warkar da ni.
* *.
%iJj^yj$b
559
26 - Suratush Shu'ara'
MSffl^-n
81. "Kuma Wanda Yake matar
da ni, sa'an nan Ya rayar da ni,
82. "Kuma Wanda Yake ina
kwacfayin Ya gafarta mini kuraku-
raina, a ranar sakamako.
83. "Ya UbangijTna! Ka ba ni
hukunci, kuma ka riskar da ni ga
salihai.
84. "Kuma Ka sanya mini hars-
hen gaskiya (1) a cikin mutanen
Rarshe.
85. "Kuma Ka sanya ni daga
magadan Aljannar ni'ima.
86. "Kuma Ka gafarta wa uba-
na, lalle ne shi, ya kasance daga
6atattu.
87. "Kuma kada Ka kunyata ni
a ranar da ake tayar da su.
88. "A ranar da dukiya ba ta
amfani, kuma cfiya ba su yi.
89. "Face wanda ya je wa Allah
da zuciya mai tsarki."
90. Kuma aka kusantar da Al-
janna ga masu takawa.
91. Kuma aka fitar da wuta bab-
ba domin halakakku.
92. Kuma aka ce musu, "Ina
abin da kuka kasance kuna bauta
wa?
93. "Baicin Allah? Shin, suna
taimakon ku ko kuwa suna tsare
kansu?"
p ^^<4«|-vSQ jj^
* ' s
'>'v1'**i'>'
(1 ) Harshen gaskiya shi ne yabo mai kyau. Mutanen karshe su ne Musulmi, arummar
Annabi Muhammadu, masu shaida ga annabawa da iyar da manzanci.
560
26 — Suratush Shu'anT
8KB3»-n
94. Sai aka kikkife su (1) a cikin-
ta, su da halakakkun.
95. Da rundunar Ibilisa gaba
daya.
96. Suka ce, alhali suna a cikinta
suna yin husuma,
97. "Rantsuwa da Allah! Lalle
ne mun kasance, haioka, a cikin
Bata bayyananna.
98. "A lokacin da muke daidaita
ku da Ubangijin halittu.
99. "Kuma babu abin da ya 6a-
tar da mu face masu laifi.
100. "Saboda haka ba mu da
wadansu maceta.
101. "Kuma ba mu da aboki,
masoyi.
102. "Saboda haka, da lalle
muna da (damar) komawa, domin
mu kasance daga muminai!"
103. Lalle ne, a cikin wancan
akwai aya, kuma mafi yawansu, ba
su kasance muminai ba.
104. Kuma lalle ne Ubangijinka,
Shi ne Mabuwayi, Mai jin kai.
105. MutanenNuhusunkaryata
Manzanni.
106. A lokacin da tfan'uwansu,
Nuhu, ya ce musu, "Shin, ba za ku
yi takawa ba?
707. "Lalle ne, zuwa gare ku, ni
Manzo ne amintacce.
108. "To,kubiAllahdatakawa,
kuma ku yi mini da'a.
^ - ^
<'> s\t'>< '(*"i\.
m^j\^9>&>l£
\' x' **\i *. >*-
<£%*** \% > y *y< m
(1) Gumakan, sii da halakakku tnabiyansu.
mai bin sa halakakke.
Dukan mai 6atar da wani shine gunki ga
561
26 — Suratush Shu'ara'
109. "Kuma ba ni tambayar ku
wata ijara a kansa. Ijarata ba ta
zama ba face daga Ubangijin halittu.
110. "Sabdda haka, ku bi Allah
da takawa, kuma ku yi mini da'a."
111. Suka ce, "Ashe, za mu yi
Tmani sabdda kai, alhali kuwa, ma-
fiya kaskanci sun bi ka?"
112. Ya ce, "Kuma ba ni da sani
ga abin da suka kasance suna aika-
tawa.
113. "Hisabinsu bai zama ba,
face ga Ubangijina, da kuna
sansancewa.
114. "Ban zama mai kore mumi-
nai ba.
115. "Nlba kowa ba ne, sai mai
gargacfi mai bayyanawa."
116. Suka ce, "Lalle ne, idan ba
ka hanu ba, ya Nuhu, (daga
maganarka,) hakTka, kana kasan-
cewa daga wacfanda ake jefewa."
117. Yace,"Ya Ubangijina! Lal-
le ne mutanena sun karyata ni.
118. "Sai ka yi hukunci, a tsaka-
nTna da tsakaninsu,^ tabbataccen
hukunci, kuma ka tslrar da ni, da
wacfanda suke tare da ni daga
muminai."
119. Sai Muka tslrar da shi, shi
da wadanda suke tare da shi, a cikin
jirgi wanda aka yi wa lodi.
120. Sa'an nan Muka nutsar, a
bayan haka, da sauran.
121. Lalle ne, a cikin wannan,
akwai aya, kuma mafi yawansu, ba
su kasance masu Tmani ba.
<^>
© ^J^*»)j ^-Jc^%^ J^
% %££$ cj jp^t^il
^ 9- >»' It
^'.s^ »>^-^ •"-^rfr
562
26 - Suratush Shu'ara'
mm-*
122. Kuma Lalle ne, Ubangijin-
ka, haklka, ShT ne Mabuwayi, Mai
rahama.
123. Adawa sun karyata Man-
zanni.
124. A lokacin da dan'uwansu,
Hudu ya ce musu, "Ba za ku yi
takawa ba?"
125. "Lalle ne ni, zuwa gare ku,
halaka, Manzo ne, amintacce.
126. "Saboda haka ku bi Allah
da takawa, kuma ku yi mini da'a.
127. "Kuma ba ni tambayar
wata ijara a kansa. Ijarata ba ta
zama ba, face daga Ubangijin halit-
tu.
128. "Shin, kuna yin ginin sita-
diyo (1) a kowane tsauni ne, kuna
yin wasa?
129. "Kuma kuna rikon matsa-
rar ruwa, tsammaninku, ku daw-
wama? (2)
130. "Kuma idan kun yi damka,
sai ku yi damkar kuna masu
tankwasawa.
131. "To, ku bi Allah da takawa,
kuma ku yi mini da'a.
132. "Ku ji tsoron Wanda Ya
taimake ku da abin da kuka sani.
133. "Ya taimake ku da dabbo-
bin ni'ima da diya.
134. "Da gonaki da maremari.
755. "Lalle ne ni, ina ji muku
tsoron azabar wani yini mai girma."
<£$*» t^>- Y'\*.\
*'"'$' » + » ^~'+ >> -r> */>' A?"
S S s»*
^auUl
I^Sl L&j^rj*** *»».>>* *« !•?> \ j)_j
oj^c^t^i^t;
p/UU^^l
(1) Sitadiyo shi ne gidan wasanni da Turanci, alama da Larabci.
(2) Ko kuma wuraren sana'o'i kamar masakoki irin na zamanin nan.
563
26 — Suratush Shu'ara'
8BDS»-n
136. Suka ce, "Daidai ne a kan-
mu : Ka yi wa'azi ko ba ka kasance
daga masu wa'azi ba.
137. "Wannan abu bai zamo ba
face halayen (1) mutanen farko.
138. "Kuma mu, ba mu zama
wacfanda ake yi wa azaba ba."
139. Saboda haka suka karyata
shi, sai Muka halakar da su. Lalle
ne a cikin wannan akwai aya, kuma
mafi yawansu ba su kasance masu
Tmani ba.
140. Kuma lalle ne, Ubangi-
jinka, hakika, Shi ne Mabuwayi,
Mai jin kai.
141. Samudawa sun karyata
Manzanni.
142. A lokacin da tfan'uwansu
Salihu ya ce, "Shin, ba za ku bi
Allah da takawa ba?
143. "Lalle ne ni, zuwa gare ku,
Manzo ne, amintacce.
144. "Saboda haka, ku bi Allah
da takawa, kuma ku yi mini da'a.
145. "Kuma ba ni tambayar ku
wata ijara, a kansa. Ijarata ba ta
zama ba face daga Ubangijin ha-
littu.
146. "Shin, ana barin ku (2) a
cikin abin da yake a nan, kuna
amintattu?
F3 <J&&& '
fun
1 ujJ 3^^4i
(1 ) Watau labarun mutane wacfanda ba su ci gaba ba, ba su son a yi rawa da nishadi.
Ana karantawar ma'anar icaryar ta farko, watau wai tatsuniya ce, a ce wai a hana aya a kan
tsaunuka domin wasanni. Suna nufi da aya ko alama gidajen rawa da na nashadi watau
stadiyam da kasTno.
(2) Kuna zaton za a bar ku a inn wannan ni'ima, Allah ba zai karfti rayukanku ba,
kuma Ya yi muku hisabi a kanta? Kayya ! Za a yi muku hisabi a bayan kun mutu an tsayar
da ku, domin hisabin ayyukan da kuka yi.
564
26 — Suratush Shu'ara'
«&&-n
147. "A cikin gonaki da mare-
mari.
148. "Da shuke-shuke da dab!-
nai, 'ya'yan itacensu hirtsi (1) masu
narkewa a ciki?
149. "Kuma kuna sassaka gidaje
daga duwatsu, kuna masu alfahari?
150. "Saboda haka ku bi Allah
da takawa, kuma ku yi mini da'a.
151. "Kada ku yi cfa'a ga umur-
nin ma6arnata.
152. "Wacfanda suke yin barna a
cikin kasa, kuma ba su kyauta-
tawa."
153. Suka ce, "Kai daga masu
sihiri kurum kake.
154. "Ba kowa kake ba, face
mutum kamarmu. To, ka zo da
wata aya idan ka kasance daga
masu gaskiya."
755. Ya ce, "Wannan rakuma ce
tana da shan C2) yini, kuma kuna da
shan yini sasanne.
156. "Kada ku shafe ta da cuta,
har azabar yini mai girma ta shafe
ku."
157. Sai suka soke ta, sa'an nan
suka wayi gari suna masu nadama.
158. Saboda haka azaba ta kama
su. Lalle ne a cikin wannan akwai
aya, kuma mafi yawansu, ba su
kasance masu imani ba.
$jL^l*^^Jg£&
±±ntj
a*
(1) Hirtsi shi ne 'ya'yan itace sababbi tun ba su nuna ba. Watau hirtsin gonakinsu
idan an ci shi narkewa yake yi a cikin ciki balle kuma 'ya'yan itace nunannu.
(2) Ranar da take da sha ita kadai za ta shanye ruwan njiyarsu, su kuma ranar da
suke da sha su kadai za su debi ruwan, ba za ta sha ba. Amma kuma tana ba su nono da
madara.
565
26 — Suratush Shu'ara'
8E»l&-n
759.^ Lalle ne Ubangijinka, haki-
ka, Shi ne Mabuwayi, Mai jin kai.
160. Mutanen Lucfu sun karyata
Manzanni.
161. A lokacin da cfan'uwan-
su, (1) Lucfu ya ce musu, "Ba za ku yi
takawa ba?
162. "Lalle ne nT, zuwa gare ku,
Manzo ne, amintacce.
163. "Saboda haka, ku bi Allah
da takawa, kuma ku yi mini da'a.
164. "Kuma ba ni tambayar ku
wata ijara. Ijarata ba ta zama ba
face daga Ubangijin halittu.
165. "Shin, kuna je wa maza
daga cikin talikai?
166. "Kuma kuna barin abin da
Ubangijinku Ya halitta muku daga
matanku? A 'a, ku mutane ne masu
ketarewa!'
167. Suka ce, "Lalle ne, hakika,
idan ba ka hanu ba, ya Ludu ! Tilas
ne kana kasancewa daga wadanda
ake fitarwa (daga gari)."
168. Ya ce, "Lalle ne ga aikinku,
hakika, ina daga masu kinsa.
169. " Ya Ubangijina ! Ka tslrar
da ni da iyallna daga abin da suke
aikatawa."
170. Saboda haka Muka tslrar
da shi, shi da mutanensa gaba daya.
171. Face wata tsohuwa a cikin
masu wanzuwa.
> -»ft '\\'*'\ 't'*\
h ?«'L*X'.J&r\ ftC -.vrl-ltils
' oj^^^^u^^^^^-^
%^jcp4p(s
^U^^Jy^l
(1) Lucfu cfan'uwansu ne na zaman gari da aure kawai. Asalinsa cfan baffan Ibrahim
ne, sun taso daga gabas, Icasar Babila suka yi hijira, har Ibrahim ya sauka Habruna a
Icasar Sham, Lucfu kuwa ya sauka a Sadum da allcaryunta.
566
26 — Suratush Shu'ara'
SBllj^-n
172. Sa'an nan kuma Muka dar-
kake wasu.
1 73. Kuma Muka yi ruwan sama
a kansu, ruwa. Sai dai ruwan wa-
cfanda ake yi wa gargadi ya muna-
na.
174. Lalle ne ga wannan, akwai
aya, kuma mafi yawansu ba su ka-
sance masu imani ba.
1 75. Kuma lalle ne Ubangijinka,
hakika, Shi ne Mabuwayi, Mai jin
kai.
176. Ma'abuta kunci sun karya-
ta Manzanni.
1 77. A lokacin da Shu'aibu ya ce
musu, "Ba za ku yi takawa ba?
178. "Lalle ne ni, zuwa gare ku,
Manzo ne, amintacce.
779. "Saboda haka, ku bi Allah
da takawa kuma ku yi mini da'a.
180. "Kuma ba ni tambayar ku
wata ijara a kansa. Ijarata ba ta
zama ba face daga Ubangijin hali-
ttu.
181. "Ku cika mudu, kuma kada
ku kasance daga masu sanyawar
hasara (ga mutane).
182. "Kuma ku yi awo da sikeli
daidaitacce.
183. "Kuma kada ku nakasa wa
mutane abubuwansu, kuma kada
ku yi fasadi a cikin kasa kuna masu
6arna.
184. "Kuma ku ji tsoron Allah
Wanda Ya halitta ku, ku da jama 'ar
farko."
%^.L& JC*}\j}a* <L*$\jla* Akb/Wj
' s *> '\t'/ K '£"£ *
567
26 - Suratush Shu'ara'
msti&-n
185. Suka ce, "Kai dai daga wa-
cfanda suke sihirtattu kawai ne.
186. "Kuma ba kowa kake ba,
face mutum kamarmu, kuma lalle
ne muna zaton ka, haklka, daga
makaryata.
187. "To, ka jefo wani 6a66ake
daga sama a kanmu, idan ka kasan-
ce daga masu gaskiya."
188. Ya ce, "Ubangijlna ne Mafi
sani ga abin da kuke aikatawa."
189. Sai suka karyata shi, sabo-
da haka, azabar ranar girgije (1) ta
kama su. Lalle ne ita ta kasance
azabar yini mai girma.
190. Lalle a cikin wancan, haki-
ka, akwai aya, amma mafi yawansu
ba su kasance masu imani ba.
191. Kuma lalle Ubangijlnka,
haklka, Shi ne Mabuwayi, Mai jin
kai.
192. Kuma lalle Shi (Alkur'ani),
haklka, saukarwar Ubangijin halit-
tu ne.
193. Ruhi (2) amintacce ne ya
sauka da shi.
194. A kan zuciyarka, domin ka
kasance daga masu gargadi.
195. Da harshe na Larabci mai
bayani.
ftp ^j^ ( »j^ioircy^<ii5:i(4o| i
( 1 ) An ruwaito cewa Allah Ya bucfe musu kofar Jahannama, zafi ya hana su zama a
ko'ina cikin gidajensu, sa'an nan aka sanya girgije ya yi musu inuwa mai sanyi-sanyi har
suka taru a ciki, sa'an nan aka sanya girgijen ya kama da wuta a kansu, suka kone kurmus
kamar an gasa fara. Suka koma toka kamar yadda suka nema daga Shu'aibu da a jefa
musu babbake daga sama idan ya zama daga masu gaskiya.
(2) Ruhul Kudus, shi ne Jibiril, amincin Allah ya tabbata a gare shi.
568
26 — Suratush Shu'ara'
wmm-^
196. Kuma lalle shin, hakika,
yana a cikin littattafan (Manzan-
nin) farko.
197. Ashe, bai kasance aya ba a
gare^su, ya zama Malaman Bam
Isra'ila sun san shi?
198. Kuma da mun saukar da shi
a kan sashen Ajamawa,
199. Ya karanta shi a kansu, ba
su kasance saboda shi masu imani
ba.
200. Kamar wancan ne! Muka
shigar da shi a cikin zukatan masu
laifi.
201. Ba za su yi imani da shi ba
sai sun ga azabar nan mai racfacfi.
202. Sai ta taho musu kwatsam,
alhali kuwa su, ba su sansance ba.
203. Sai su ce, "Shin, mu wacfan-
da ake yi wa jinkiri ne?"
204. Ashe, to, da azabarMu suke
neman gaggawa?
205. Ashe, to, ka gani, idan
Muka jishe su dacfi a shekaru,
206. Sa'an nan abin da suka ka-
sance ana yi musu wa'adi (da shi) ya
je musu,
_ 207. Abin da suka kasance ana
jTshe su dadin, ba zai tunkude azaba
ba daga gare (1) su.
208. Kuma ba Mu halakar da
wata alkarya ba face tana da masu
gargacfi.
" <^. ».* b^m
||p J^ Z^Zy^ VpJe jaXoJ^ typ<j®J>\
mK
yJ^^J*<&£' '
7?* ^ \' >W\'* >-7 -*
>''>\ > :&\'* >■
^ j^C^>j^>
jiyDU^v^^lU
O^^U^i^^^ls^* 1 ^
(1) Da an ba su lokaci mai tsawo suna jin dacfi da rayuwar duniya a cikinsa, to, ranar
da mutuwa ko azabar Allah ta je gare su, wannan lokacin ba zai tunkude mutuwar ko
azabar ba daga gare su.
569
26 — Suratush Shu'ara'
mmm-K
209. Domin tunatarwa, kuma ba
Mu kasance Masu zalunci ba.
210. Kuma (Alkur'ani) shaicfanu
ba su cfora sauka da shi ba.
211. Kuma ba ya kamata a gare
su (su shaicfanu su sauka da shi),
kuma ba su iyawa.
212. Lalle ne su, daga saurare,
hakika, wacfanda aka nisantar ne.
213. Saboda haka, kada ka kira
wani abin bautawa na dabam tare
da Allah, sai ka kasance daga wa-
cfanda ake yi wa azaba.
214. Kuma ka yi gargacfi ga dan-
ginka mafiya kusanci.
215. Kuma ka sassauta fikafi-
kanka (1) ga wanda ya bl ka daga
muminai.
216. Sa'an nan idan suka saba
maka, to, ka ce, "Lalle nl, bar-
rantacce ne daga abin da kuke aika-
tawa."
217. Kuma ka dogara ga Mabu-
wayi, Mai jin kai.
218. Wanda Yake ganin ka a
lokacin da kake tashi tsaye.
219. Da jujjuyawarka a cikin
masu yin sujada.
220. Lalle Shi (2) , Shi ne Mai ji,
Masani.
3 <Jy^^-^J^Jr^(^^J^J
> >*-"!
^»«. >* SSS s t
* s ' *
^XpyiQQ
(1) Ka zama mai tausayi ga muminai wacfanda suka blka, ka yi musu kamar yadda
kaza take yi wa 'ya'yanta kanana a lokacin sanyi, ko kuwa idan za su yi barci domin ta kare
su daga cuta.
(2) Allah Shi ne Mai ji, ji na gaskiya, kuma Masani, sani na gaskiya.
570
26 — Suratush Shu'ara'
»,$£-n
221. Shin, (kuna so) in gaya (1)
muku a kan wanda shaicfannu kan
sauka?
222. Sukan sauka a kan dukan
makaryaci, mai zunubi.
223. Suna jefa (abin da suka) ji,
alhali kuwa mafi yawansu makar-
yata ne.
224. Kuma mawaka (2) halakak-
ku ne ke bin su.
225. Shin, ba ku ga cewa, lalle ne
su, a cikin kowane rango suna yin
cfimuwa (su ketare haddi) ba?
226. Kuma lalle ne su, suna fadin
abin da ba su aikatawa?
227. Face wadanda suka yi Tma-
ni suka aikata ayyukan kwarai,
kuma suka ambaci Allah da yawa,
kuma suka rama zalunci, daga
bayan an zalunce su. Kuma wadan-
da suka yi zalunci, za su sani a wace
majuya suke juyawa.
*? .fA^"**
\< > »<n >>> -'>T
^3 0>A^^JL^(^^^JLis»
(1) Wannan domin raddi ne ga masu cewa aljannu ke gaya wa Muhammadu, tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi, Alkur'ani. Aljannu ba su sauka sai ga makaryaci, mai
zunubi, Muhammadu kuwa ba haka yake ba. Saboda haka shi ba mahaukaci ba, kuma ba
wanda aljannu suke gaya wa ba. Dukan abin da ya facfa, to, wahayi ne daga Allah.
(2) Siffofin mawaka sun nuna cewa Annabi Muhammadu ba mawaki ba ne, domin ba
shi da cfaya daga cikin siffofin mawaka. Kuma mabiyansa ba halakakku ba ne.
571
27 — Suratun Naml
d^OIIi^-rv
Tana karantar da cewa Allah Yana da asirrai, ba su da iyaka,
Yana nuna sashensu ta hannun wadansu mutane bayinSa da a cikin
littattafanSa, domin muminai su kara karfin Imani, kuma su yi aiki
da shari'ar da Ya aza su a kanta.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. T).S. Wacfancan ayoyin Al-
kur'ani ne da Littafi mai bay-
yanawa.
2. Shiriya ce da bushara ga
muminai.
3. Wadanda suke tsayar da sal-
la kuma su bayar da zakka, alhali
kuwa su, game da Lahira, to, su,
suna yin yaklni.
4.^ Lalle ne wadanda suke ba su
yin Tmani da Lahira, Mun kawata
musu ayyukansu, saboda haka suna
cfimuwa.
5. Wadannan ne wadanda suke
suna da mugunyar azaba (a du-
niya), kuma su, a Lahira, su ne
mafiya hasara.
*■"*■-'■$,
572
27 - Suratun Naml
^li&-rv
6. Kuma lalle ne kai, hakika, ana
hacfa (1) ka da Alkur'ani daga gun
Mai hikima, Masani.
7. A lokacin da Musa ya ce wa
iyalinsa, "Lalle ni, na tsinkayi wata
wuta, ni mai zo muku daga gare ta
ne, da wani labari, ko kuwa mai zo
muku ne da yula, makamashin,
tsammaninku, ku ji cfimi."
8. To, a lokacin da ya je mata, sai
aka kira shi cewa, "An tsarkake
wanda yake cikin (wurin) wutar da
wanda yake a gefenta, kuma tsarki
ya tabbata ga Allah Ubangijin ha-
littu.
9. "Ya Musa, lalle ne shi, NT ne
Allah, Mabuwayi, Mai hikima.
10. "Kuma ka jefa sandarka."
To, a lokacin da ya gan ta, tana
girgiza kamar dai ita karamin macT-
ji ne, sai ya juya yana mai bayar da
baya, kuma bai koma ba, "Ya
Musa! Kada ka ji tsoro, lalle Ni,
Manzanni ba su jin tsoro a wuriNa.
11. "Sai wanda ya yi zalunci,
sa'an nan ya musanya kyau a bayan
cuta, to, lalle NT, Mai gafara ne,
Mai jin kai.
12. "Kuma ka shigar da hannun-
ka a cikin wuyan rigarka, ya fita
fari, babu wata cuta, a cikin wasu
ayoyi tara zuwa ga Fir'auna da
mutanensa. Lalle ne su, sun kasance
mutane ne fasikai."
<«!%£*
~ /*' *>
(1) Lahira da Tmani da ita suna a cikin aslran Allah. Haka karbar Alicur'ani daga
Allah yana a cikin asiran Allah da Ya bayyana a Littafi. Ganin Musa ga wuta da abubuwan
da suka auku a wurin game da maganar Allah a gare shi da juyawar sanda macijiya da
komawarta sanda da juyawar hannunsa fari kal da juyawarsa zuwa ga asalinsa, duka suna
a cikin asiran Allah da Ya bayyana su ga wani mutum.
573
27 - Suratun Naml
mmm-™
13. To, a lokacin da ayoyinMu
suka je musu, suna masu wayar da
kai, suka ce, wannan sihiri ne,
bayyananne.
14. Kuma suka yi musunsu, al-
hali zukatansu, sun natsu da su,
domin zalunci da girman kai. To, ka
dubi yadda akibar mabarnata ta
kasance.
75. Kuma lalle ne, haloka, Mun
bai wa Dawuda da Sulaiman ilmi,
kuma suka ce, "Gddiya ( ^J;a tab-
bata ga Allah, Wanda Ya fifita mu a
kan masu yawa daga BayinSa
muminai."
16. Kuma Sulaiman ya gaji Da-
wuda ya ce, "Ya ku mutane! An
sanar da mu maganar tsuntsaye,
kuma an ba mu daga kowane abu.
Lalle ne, wannan, hakika, shi ne
falalar (Allah) bayyananna."
17. Kuma aka tattara, domin
Sulaiman, rundundninsa, daga al-
jannu da mutane da tsuntsaye, to,
su ana kange su (ga tafiya).
18. Har a lokacin da suka je a
kan rafin tururuwa, wata tururuwa
ta ce, " Ya ku jama'ar tururuwa ! Ku
shiga gidajenku, kada Sulaiman
da rundunoninsa su kakkarya ku,
alhali kuwa su, ba su sani ba."
19. Sai ya yi murmushi yana mai
dariya daga maganarta, kuma ya
^3 \^jy^y>x^f \ JCa ]y Is
\' m V >rtu"'f- 1i-~ >i'> '& * "
^ -**,
X^^^y&jQ<£c£r^£"s
(1) Abin da ke hakkin ni'imar Allah a kan mutum, ya gode Masa. Dawuda da
Sulaiman Allah Ya ba su ilmi na Annabci sun tsayu da godiyarsa a kan aiki da shi, da
kuma ikrari da cewa ni'ima ce daga Allah, ba da wani aiki nasu ba. Annabci da ilmi da
sanin maganar tsuntsu da ta aljannu da ta tururuwa duka suna cikin aslrin Allah da Yake
nunawa ta hanyar wadansu BayinSa, Annabawa.
574
27 — Suratun Naml
$3Hiljg~-rv
ce, "Ya UbangijTna ! Ka cusa mini
in gode wa ni'imarKa wadda Ka
ni'imta ta a gare ni da kuma ga
mahaifana biyu, kuma in aikata
aiki na kwarai, wanda Kake yarda
da shi, kuma Ka shigar da ni, sabo-
da rahamarKa, a cikin bayinKa
salihai."
20. Kuma ya binciki (1) tsunt-
saye, sai ya ce, "Me ya kare ni ba ni
ganin hudhudu, ko ya kasance daga
masu fakuwa ne?
21. "Lalle ne za ni azabta shi
azaba mai tsanani, ko kuwa lalle in
yanka^hi, ko kuwa lalle ya zo mini
da dafili bayyananne."
22. Sai ya zauna ba nesa ba,
sa'an nan ya ce, "Na san abin da ba
ka sani ba, kuma na zo maka daga
Saba da wani labari tabbatacce.
23. "Lalle ni, na sami wata mace
wadda tana mulkinsu, kuma an ba
ta daga dukan kome, kuma tana da
gadon sarauta mai girma.
24. "Na same ta, ita da mutanen-
ta, suna yin sujada ga rana, baicin
Allah, kuma Shaitfan ya kawace
musu ayyukansu, saboda haka ya
karkatar da su daga hanya, sa'an
nan su, ba su shiryuwa.
25. "Ga (2) su yi sujada ga Allah
Wanda Yake fitar da abin da yake a
Boye, a cikin sammai da kasa, kuma
-* - ' * * *"
(1) Wannan ya nuna tsayuwar Sulaiman da binciken kome da kowa a cikin daularsa.
Kuma da yadda yake yin tsanani a cikin sauki. Wannan ita ce hanyar mulki mai kyau.
(2) An kayar da harafin korewa domin barinsa, da Hausa, yana 6ata ma 'ana, domin
Shaitfan bai kange su daga rashin yin sujada ba.
575
27 - Suratun Naml
tU^li^-rv
Ya san abin da kuke 66yewa da
abin da kuke bayyanawa.
26. '\Allah, babu abin bautawa,
face Shi, Ubangijin (1) Al'arshi, mai
girma."
27. Ya ce, "Za mu duba, shin, ka
yi gaskiya ne, ko kuwa ka kasance
daga makaryata?
28. "Ka tafi da takardata wan-
nan, sa'an nan ka jefa ta zuwa gare
su, sa'an nan kuma ka juya daga
barinsu, sa'an nan ka ga mene ne
suke mayarwa."
29. Ta ce, "Ya ku mashawarta!
Lalle ne, an jefo, zuwa gare ni, wata
takarda mai girma.
30. "Lalle ita daga Sulaiman
take, kuma lalle ita, da sunan Al-
lah, Mai rahama, Mai jin kai ne.
31. "Kada ku yi girman kai a
gare ni, kuma ku zo mini kuna masu
sallamawa."
32. Ta ce, "Ya ku mashawar-
ta (2) ! Ku yi mini fatawa ga al'ama-
nna, ban kasance mai yanke wani
al'amari ba, sai kun halarta."
33. Suka ce, "Mu ma'abuta karfi
ne, kuma ma'abuta yaki mai tsana-
ni ne, kuma al'amari ya koma zuwa
gare ki, saboda haka ki duba, mene
ne za ki yi umurni (da shi)?"
rf^t ' -fit' ' 2"Vf ' f^ts*" n- .A.
0fj^nic£^v&$ $&&
^^s. S* S
J-lyS'S • >»'
iPf\ < , »> . > t" '.\ \ V -Nit
(1) Ya siffanta Allah da cewa babu abin bautawa face Shi, domin ya kore cancantar
rana ga ibada, da Ubangijin Al'arshi domin ya debe girman gadon Bilkisu daga zukata.
(2) Allah bai ke&ance hikima ga maza kawai ba, har mata akwai masu hikima a
cikinsu. Sai dai Musulunci ya hana shugabancin mata, saboda galibinsu adifarsu ta rinjayi
hankalinsu, saboda kyautata tarbiyyar yara. Ana fahimtar cewa iya mulki, shi ne rashin
fallewa da ra'ayi ga shugaba, sai a bayan ya shawarci mutanensa, kamar yadda Sarauniyar
Saba ta yi da Majalisarta.
576
27 — Suratun Naml
dJ^lli^-rv
34. Ta ce, "Lalle Sarakuna idan
sun shiga wata alkarya, sai su 6ata
ta, kuma su sanya masu darajar
mutanenta kaskantattu. Kuma ka-
mar wancan ne suke aikatawa.
35. "Kuma lalle m, mai aikawa
ce zuwa gare su da kyauta, sa'an
nan mai dubawa ce : da me manzan-
nin za su komo."
36. To, a lokacin da ya je wa
Sulaiman ya ce, "Shin, za ku kara
ni da dukiya ne? To, abin da Allah
Ya ba ni, shi ne mafi alheri daga
abin da Ya ba ku. A'a, ku ne kuke
yin farin tiki da kyautarku.
37. "Ka koma zuwa gare su.
Sa'an nan lalle muna je musu da
rundunoni, babu wata ta6ukawa
gare su game da su, kuma lalle
muna fitar da su daga gare ta, suna
mafi wulakantuwa, kuma suna
kaskantattu."
38. Ya ce, "Ya ku mashawarta!
Wannenk u zai zo mini da gadonta a
gabanin su zo, suna masu salla-
mawa?"
39. Wani mai karfi daga aljannu
ya ce, "NT, ina zo maka da shi a
gabanin ka tashi daga matsayinka.
Kuma lalle m 9 a gare shi, haklka,
mai karfi ne amintacce."
40. Wanda yake a wurinsa ak-
wai (1) wani ilmi daga Littafin ya ce,
*' S* «.
» >'*'*"' *
•k-&tiXrX\?*''"
I^u^jL J^Sl VjJLJl £li
' *» *
fe^^\*\$^j&
(1) Allah na bayar da asirai daga littattafai, ko da wahayi zuwa ga Annabawa, ko da
ilhama daga abin da aka bai wa Annabawa. Wadansu sun ce ilmin nan sunan Allah ne mafi
girma. Allah ne Mafi sani. Sai dai sharadin aiki da ilmi ga ibada, ya kasance daga
Annabawa kawai, a cikin lokacin aiwatar da shari'arsu. Ba a iya amfani da wani sunan
Allah wanda wani Annabi bai zo da shi ba a gabanin Musulunci, kuma a bayan Musulunci
577
27 - Siiratun Naml
$20!ti&-rv
"Ni ina zo maka da shi a gabanin
kyaftawar ganinka ta koma gare
ka." To, a lokacin da ya gan shi
matabbaci a wurinsa, ya ce, "Wan-
nan daga falalar Ubangijlna yake,
domin Ya jarraba ni : Shin, zan gode
ne, ko kuwa zan butulce! Kuma
wanda ya gode, to, yana godewa ne
domin kansa, kuma wanda ya kafir-
ta, to, lalle Ubangijina Wadatacce
ne, Karimi."
41. Ya ce, "Ku canza kamar ga-
donta gare ta, mu gani, shin za ta
shiryu, ko kuwa tana kasancewa
daga wacfanda ba su shiryuwa."
42. To, a lokacin da ta je, aka ce,
"Shin, kamar wannan gadon sarau-
tarki yake?" Ta ce, "Kamar dai shi
ne. Kuma an ba mu ilmi daga gaba-
ninta, kuma mun kasance masu
sallamawar (al'amari ga Allah)."
43. Kuma abin da ta kasance
tana bautawa, baicin Allah, ya kan-
ge ta. Lalle ita, ta kasance daga
mutane kafirai.
44. Aka ce mata, "Ki shiga a
gidan sarauta." To, a lokacin da ta
gan shi, ta yi zatonsa wai gurbi ne,
kuma ta kuranye (1) daga Icwau-
rinta. Ya ce, "Lalle ne shi, gidan
sarauta ne mai santsi daga ma-
dubai." Ta ce, "Ya Ubangijlna!
~e
r-
■J^4
&>d^CiPJ*CjtJ
' *"*■ »>?' \" *'\i i >
Z$J&\jMl\t^&
UTl ;y&fjH£
ba a rokon Allah sai da sunayenSa masu kyau, tis'in da taran nan, sai dai a dunkule kamar
a ce, "Ina rokon Allah da sunayenSa da na sani da wadanda ban sani ba."
Jl) Idan Tmani ya shiga a cikin zuciya, sai ginnan kai ya fita daga gare ta. Sarauniya
Bilkisu tana kuranye kafafunta da niyyarta ta shiga a cikin ruwa domin ta nuna da'arta ga
umurnin Annabin Allah Sulaiman, kuma ta yarda da shiga gulbin da ba ta san tsawon
zurfinsa ba, ko da za ta mutu a wurin da'a da takawa. Mace da sarauta iyakar ginnan kai
ke nan, babu abin da zai gusar da shi sai Imanin gaskiya.
578
27 — Suratun Naml
OM&-rv
Lalle ni, na zalunci kaina, kuma na
sallama al'amari tare da Sulaiman
ga Allah, Ubangijin halittu."
45. Kuma lalle ne, hakika, mun
aika zuwa Samudawa da cfan'u-
wansu, Salihu (ya ce), "Ku bauta
wa Allah." Sai ga su kungioyi biyu
suna ta husuma.
46. Ya ce, "Ya mutanena! Don
me kuke neman gaggawa game da
munanawa, a gabanin kyautatawa.
Don me ba ku neman Allah gafara,
tsammaninku, za a yi muku raha-
ma?"
47. Suka ce, "Muna shu'umci da
kai, kuma da wanda ke tare da kai."
Ya ce, "Shu'umcinku a wurin Allah
yake. A'a, ku mutane ne, ana fiti-
nar ku."
48. Kuma wacfansu jama'a
tara (1) sun kasance a cikin birnin,
suna yin 6arna, kuma ba su kyauta-
tawa.
49. Suka ce, "Ku yi rantsuwa da
Allah, lalle za mu kwanan masa, (2)
shi da mutanensa, sa'an nan mu ce
wa waliyyinsa. 'Ba mu halarci hala-
kar mutanensa ba, kuma mu, haki-
ka, masu gaskiya ne'."
50. Kuma suka kulla makirci,
kuma Muka kulla sakamakon ma-
kirci, alhali su ba su sani ba.
yp j±^\^^jL^>£<
i>ju^o> L>Ji^IjbU-\ ^^ciJ.Lll-31 xj&$
^ ^ ^<
.r> * '■■'*■
'< '< '
> »> * ~" t'~- -'
(1) Yawan masu 6arna ba ya hana gaskiya bayyana. Kuma mai makirci domin ya
halakar da mai gargadin addinin Allah, yana yi wa kansa sanadin halaka kawai ne.
Wadannan mutane tara sun yi niyyar kashe Salihu ne, ba da sanin danginsa ba, a wurin da
yake kwana yana salla a masallacinsa, a bayan gari. A can Allah ya halakar da su. Wannan
shi ne sakamakon makircin da suka kulla.
(2) Za mu kwanan masa, ai za mu kwana da niyyar kashe shi a cikin dare, a 66ye.
579
27 - Suratun Naml
$^lj££-rv
51. Ka duba yadda akibar ma-
kircinsu ta kasance, lalle Mu, Mun
darkake su da mutanensu gaba
daya.
52. Wadancan, gidajensu ne,
wofintattu, saboda zaluncin da
suka yi, lalle ne a wancan akwai aya
ga mutane wadanda suke sani.
53. Muka tsirar da wadanda
suka yi Imani, kuma sun kasance
suna takawa.
54. Da Ludu, a lokacin da ya ce
wa mutanensa, "Shin, kuna je wa
alfasha (1) ne alhali kuwa kuna
gani?
55. "Shin, lalle ku, haklka, kuna
je wa jnaza da sha'awa, baicin
mata? A 'a, ku, wasu irin mutane ne
kuna aikin jahilci."
56. Babu abin da ya kasance ja-
wabin mutanensa, face suka ce,
"Ku fitar da mutanen Ludu daga
alkaryarku, lalle su, wasu irin muta-
ne ne masu da'awar suna da tsarki."
57. Sai Muka tsirar da shi, shi da
mutanensa, (2) face matarsa, Mun
kaddara ta a cikin masu wanzuwa.
58. Kuma Muka yi ruwa a kansu
da wani irin ruwa. To, ruwan wa-
danda ake yi wa gargacfi ya mu-
nana.
'U^pf^pi^-
->T1 i" f-
\j^\*^U^\ \L1^X>
i^^&^tfjj
( 1 ) Alfashar mutanen Lucfu, ita ce luwacfi, namji ya bi namiji a duburarsa. Wannan
alfasha, ko dabbobi ba su yin ta.Ga mutanen Ludu ta fara bayyana. Allah Ya halakar da su
kamar yadda Ya ambata. Sa'an nan kuma ba a kara ganinta ba, sai ga wannan aFumma.
Asirin da ke ciki, shT ne yadda Allah Yake juyar da cfabi'ar mutum ta zama ba ta masu
hankali ba, tare da dogewar halittar jikinsa kamar yadda take ga zahiri.
(2) Mutanensa muminai. Imani da gaskiya idan gaskiya ta bayyana asiri ne daga
asTran Allah sai wanda Ya bai wa. Kusanci ga wani Annabi da aure ko zumunta, ba ya
bayar da shi. Ruwan azaba, shT ma asiri ne na Allah.
580
27 - Siiratun Naml
tm\%&~™
59. Ka ce, "Godiya ta tabbata ga
Allah, kuma aminci ya tabbata bisa
ga BayinSa, wacfanda Ya zaba."
Shin, Allah ne Mafi alheri, ko abin
da suke yin shirki da shi? (1)
60. K6 wane ne Ya halitta sam-
mai da Rasa, kuma Ya saukar
muku, daga sama, wani ruwa,
Muka tsirar, game da shi, gonaki
masu sha'awa, ba ya kasancewa
gare ku, ku tsirar da itacensu? Shin,
akwai abin bautawa tare da Allah?
A'a, su mutane ne suna daidaitawa
(Allah da wani).
61. K6 kuwa wane ne Ya sanya
kasa tabbatacciya, kuma Ya sanya
koguna a tsakaninta kuma Ya sa-
nya mata manyan duwatsu taba-
tattu, kuma Ya sanya wani sha-
maki a tsakanin tekuna biyu? Shin
akwai wani abin bautawa tare da
Allah. A 'a, mafi yawansu ba su sam
ba.
62. K6 wane ne yake karba wa
mai bukata idan ya kira Shi, kuma
ya sanya ku mamayan kasa? Shin
akwai wani abin bautawa tare da
Allah? Kacfan kwarai kuke yin
tunani.
63. K6 wane ne yake shiryarwa
a cikin duffan kasa da teku, kuma
wane ne Yake aikowar iskoki domin
bayar da bushara a gaba ga raha-
marSa? Ashe, akwai wani abin bau-
tawa tare da Allah? Tsarki ya tab-
• 'XI' *'Xt s'*'*
(1) Daga wannan aya ta 59 zuwa karshen sura, duka tambThi ne ga abubuwan fake na
ilmin Allah, wanda ya shafi jikunanmu, amma ba mu san yadda suke aukuwa a gare mu
ba. Sa'an nan kuma da tambihi ga abubuwan gaibi da suke zuwa domin mu yi imani da su.
581
27 — Suratun Naml
iflSOIIi^-fv
bata ga Allah daga barin abin da
suke shirki da shi.
64. K6 wane ne yake fara halit-
ta sa'an nan kuma ya mayar da ita,
kuma Wane ne Ya arzuta ku daga
sama da kasa? Ashe, akwai wani
abin bautawa tare da Allah? Ka ce,
"Ku kawo dalllinku, idan kun ka-
sance masu gaskiya."
65. Ka ce, "Babu wanda ya san
gaibi a cikin sammai da kasa face
Allah. Kuma ba su sansancewar a
yaushe ne ake tayar da su."
66. A^a, saninsu ya kai a cikin
Lahira. A'a, suna cikin shakka daga
gare ta. A'a, su da gare ta makafin
zuci ne.
67. Kuma wacfanda suka kafirta
suka ce, "Shin, idan mun kasance
turbaya, mu da ubanninmu, shin,
haklka, wacfanda ake fitarwa ne?
68. "Lalle ne, hakika, an yi mana
wa'adi ga wannan, mu da uban-
ninmu, daga gabanin haka. Wan-
nan ba kome ba ne face tatsuni-
yoyin farko."
69. Ka ce, "Ku yi tafiya a cikin
kasa, sa'an nan ku duba, yaya aki-
bar masu laifi take?"
70. Kuma kada ka yi bakin ciki a
kansu, kuma kada ka kasance a
cikin kuncin rai daga abin da suke
kullawa na makirci.
71. Kuma suna cewa, "A yaushe
wannan wa'adi (zai auku), idan kun
kasance masu gaskiya?"
72. Ka ce, "Akwai fatan sashen
abin da kuke neman gaggawarsa, ya
582
27 — Suratun Naml
$£2Ii&-rv
kasance ya kuturta (1) a gare ku."
73. Kuma lalle ne Ubangijinka,
hakika, Mai falala ne a kan mutane,
kuma amma mafi yawansu, ba su
godewa.
J74. Kuma lalle Ubangijinka, ha-
kika, Yana sanin abin da kirazansu
suke Boyewa, da abin da suke
bayyanawa.
75. Kuma babu wata (mas'ala)
mai 66yuwa, a cikin sama da kasa
face tana a cikin littafi bayyananne.
76. Lalle ne wannan Alkur'ani (2)
yana gaya wa Bani Isra'ila mafi
yawan abin da su suke sa6a wa
junansu a ciki.
77. Kuma lalle shi, hakika, shi-
riya ce da rahama ga muminai.
78. Lalle Ubangijinka Yana yin
hukunci a tsakaninsu da hukun-
cinSa, kuma Shi ne Mabuwayi,
Masani."
79. Saboda haka, ka dogara ga
Allah, lalle ne, kai ne a kan gaskiya
bayyananniya.
80. Lalle ne kai, ba ka jiyar da
matattu, kuma ba ka sa kurame su ji
kiranka, idan sun juya suna masu
bayar da baya.
:JU2
m {^\&\&*&l$Jpj&
&%p$^%&£\y!&&\
(1) Kuturi, shi ne a bayan wani ya hau dabba ya kuma aza wani a kanta daga baya
gare shi. Kinaya ce na cewa abin yana kusa gare su kwarai, kamar tsakanin cfan kuturi da
mahayin dabba.
(2) Idan wanna Alkur'ani ya kunsa ilmin asirai da yake iya gaya wa Bani Israila mafi
yawan abin da su da kansu, suke sa6a wa juna a kansu, tare da shahararsu da ilmi, da
yawan Annabawan da suka wuce a cikinsu, to, ga Larabawa jahilai hiyaka ke nan. Babu
abin da ya wajaba a gare su, sai sallamawa ga abin da yake kiran zuwa gare shi. In abin da
yake fada ba gaskiya ba ne, da Bani Isra'ila ne farkon masu nuna karyarsa. Amma ba su yi
ba. Saboda haka duka gaskiya ne. Sai kowa ya bi shi ya tsira.
583
27 — Suratun Naml
Ui^lj&i'-rv
81. Kuma kai ba ka zama mai
shiryar da cfimammu daga Bata ba.
Ba ka jiyarwa face wanda yake yin
imani da ayoyinMu. To, su ne masu
sallamawa (aramari zuwa ga
Allah).
82. Kuma idan magana ta auku
a kansu, Muna fitar musu da wata
dabba (1) daga kasa, tana yi musu
magana, cewa "Lalle mutane sun
kasance game da ayoyinMu, ba su
yin Tmanin yaklni."
83. Kuma a ranar da Muke tara-
wa daga kowace al'umma, wata
kungiya daga wacfanda suke kar-
yata ayoyinMu, sai ga su ana kange
su (ga kora).
84. Har idan sun zo, (Allah) zai
ce, "Ashe kun karyata ayoyinNa,
kuma ba ku kewaye su da sani ba?
To, mene ne kuka kasance kuna
aikatawa?"
85. Kuma magana ta auku a
kansu, saboda zaluncin da suka yi.
To, su ba su da ta cewa.
86. Shin, ba su gani ba, cewa,
lalle Mu, Mun sanya dare domin su
natsu a cikinsa, kuma da yini mai
sanya gani? Lalle a cikin wancan
akwai ayoyi^domin mutane wacfan-
da suka yi imani.
■ y > - >
(1) Wata dabba ce ana kiran ta Jassasa, an ce 'yar rakumar Salihu ce, a lokacin da aka
kashe uwarta, ta gudu, ta shiga cikin dutse, dutsen ya rufe da ita. Tana fitowa daga dutsen
Safa a Makka da hantsi. Bayan fitowarta, babu sauran wa'azi. Mumini ya tabbata mumini,
kafiri kuma ya tabbata haka. Tana rike da sandar Musa da Hatimin Sulaiman. Tana
fitowa a bayan fitowar rana daga yamma. Allah cfai Ya san gaskiyar yadda take.
584
27 - Suratun Naml
OJ^ii^-rv
87. Kuma da ranar (1) da ake
busa a cikin kaho, sai wanda yake a
cikin sammai da wadanda suke a
cikin kasa su firgita, face wanda
Allah Ya so, kuma dukansu, su je
Masa suna kaskantattu.
88. Kuma kana ganin duwatsu,
kana zaton su sandararru, alhali
kuwa su suna shucfewa, shucfewar
girgije, bisa sana'ar Allah Wanda
Ya kyautata kowane abu. Lalle Shi,
Mai labartawa ne game da abin da
kuke aikatawa.
89. Wanda ya zo da kyakkawan
aiki guda, to, yana da mafi alheri
daga gare shi. Kuma su daga wata
firgita, (2) a yinin nan, amintattu ne.
90. Kuma wanda ya zo da mu-
gun aiki, to, an kife fuskokinsu a
cikin wuta. Ko za a saka muku face
da abin da kuka kasance kuna aika-
tawa?
91. (Ka ce), "An umurce ni, in
bauta wa Ubangijin wannan
Gari (3) , Wanda ya mayar da shi
Hurumi, kuma Yana da dukan
kome. Kuma an umurce ni da in
kasance daga masu sallamawa.
92. "Kuma ina karanta Al-
kur'ani." To, wanda ya shiryu, ya
shiryu ne domin kansa kawai.
4 si • >< >'~
3o^>
<^<>^\y>j*><^j 5 xh\f~^- J \^<£yj
(1) Bayan fitowar dabba, kuma sai busar kaho na farko, sa'an nan na biyu sa'an nan
FCiyama.
(2) Firgita daga azabar Lahira, wannan firgita ba irin ta farko ba ce, wadda aka
ambata a cikin aya ta 87, domin wancan firgitar kwarjini ce a bayan tashi daga kaburbura.
(3) Wannan Gari shi ne Makka. Sanya Makka hurumi ba a iya shiga cikinsa da yaki
yana a cikin aslrai na Allah. Shiryuwa da 6ata duka asTrai ne na Allah. Tsarin Alkur'ani da
abubuwan da ya kunsa duka aslran Allah ne.
585
28 - Suratul Kasas
i^)r^-^
Kuma wanda ya Bace, to, ka ce, "Ni
daga masu gargacfi kawai nake."
93. Kuma ka ce, "Godiya ta tab-
bata ga Allah. Zai nuna muku ayo-
yinSa, har ku sansu." Kuma Uban-
gijinka bai zama Mai shagala daga
barin abin da kuke aikatawa ba.
Tana karantar da nuna falalar hijira domin addini, kuma tana
kwacfaitarwa ga yin hijira. Kada tsoron barin dukiya da cfiya, su
kange mumini daga yin hijira da addininsa zuwa ga wurin yardar
Allah Wanda Yake Shi ne Mai kome kuma Yana rike da kome Shi
kacfai. Kuma tana hana rarraba jama'ar Musulmi.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. T>. S. M.
2. Wacfancan ayoyin Littafi ne
bayyanannu.
3. Muna karantawa a kanka,
daga labarin Miisa da Fir'auna da
gaskiya domin mutane wacfanda
suke yin imani.
4. Lalle ne Fir'auna ya cfaukaka
a cikin kasa, kuma ya sanya muta-
nenta kungiya-kungiya, yana rau-
nanar da wata jama'a daga gare su;
yana yanyanka cfiyansu maza kuma
yana rayar da matan. Lalle shT, ya
kasance daga masu Barna.
^£§P ********
yj CfX^JmS^^ CiJ>v>K>\<*t> *u^<_|"i-_~J_j
586
28 — Suratul Kasas
ffigssarcji-fA
5. Kuma Muna nufin Mu yi fala-
la ga wacfanda aka raunanar a cikin
kasar, kuma Mu sanya su shuga-
banni, kuma Mu sanya su magada.
6. Kuma Mu tabbatar da su a
cikin kasar, kuma Mu nuna wa
Fir'auna da Hamana da rundu-
noninsu abin da suka kasance suna
sauna daga gare su.
7. Kuma Muka yi wahayi zuwa
ga uwar Musa, cewa ki shayar da
shi, sai idan kin ji tsoro game da shi,
to, ki jefa shi a cikin kogi, kuma
kada ki ji tsoro, kuma kada ki yi
bakin ciki. Lalle ne Mu, Masu
mayar da shi ne zuwa gare ki, kuma
Masu sanya shi ne a cikin Manzanni
8. Sai mutanen Fir'auna suka
tsince shi, domin ya kasance makiyi
da bakin ciki a gare su. Lalle ne
Fir'auna da Hamana da rundu-
noninsu, sun kasance masu aikin
ganganci.
9. Kuma matar (1) Fir'auna ta ce,
("Ka bar shi yana) sanyin ido a gare
ni da gare ka! Kada ka kashe shi,
akwai fatan ya amfane mu, ko mu
rike shi da," alhali kuwa su ba su
sansance ba.
10. Kuma zuciyar uwar Musa ta
wa^ gari yofintatta (2) . Lalle ne,
haklka, ta yi kusa ta bayyanar da
shi, ba domin Mun cfaure zuciyarta
V-^H* $^*r^& Zs*yj>) Ql^^y^
\jJ&J^Oj£====lJ >^Sy^jUya3?VJfe
-••<-!t-
''YM*
(1) Sunan matar Fir'auna A'siya, tana da zumunta da Musa. Ta ce ka yi masa suna
'Musha\ ma'anarsa an same shi tsakanin "mu" watau ruwa da "sha", watau itace, sa'an
nan ya zama Musa. Allah Yana tsare mutum gaba ga maiciyinsa.
(2) Zuciya yofintatta, ita ce wadda ba ta da wani tunani saboda abin da ya shagaltar
da ita na tunanin danta a hannun maiciyinsa.
587
28 - Suratul Kasas
(!»>&- *A
ba, domin ta kasance daga mumi-
nai.
11. Kuma ta ce wa 'yar'uwar-
sa, (1) "Ki bTshi." Saboda haka sai
ta leke shi daga gefe, alhali su ba su
sani ba.
12. Kuma Muka hana masa
masu shayar da mama, a gabanin
haka, sai ta ce, "Ko in nuna muku
mutanen wani gida, su yi muku
renonsa, alhali kuwa su masu nasT-
ha ne a gare shi?"
13. Sai Muka mayar da shi zuwa
ga uwarsa domin idanunta su yi
sanyi, kuma ba za ta yi bakin ciki
ba, kuma domin ta san cewa lalle
wa'adin Allah gaskiya ne, amma
kuma mafi yawansu ba su sani ba.
14. Kuma a lokacin da ya kai
karflnsa, kuma ya daidaita, Mun ba
shi hukunci (2) da ilmi, kuma kamar
haka Muke saka wa masu kyau-
tatawa.
75. Kuma sai ya shiga garin a
lokacin da mutanen garin suka sha-
gala, sai ya samu, a cikin garin,
wacfansu maza biyu suna facfa, wan-
nan daga kungiyarsa, kuma cfayan
daga makiyansa, sai wannann da
yake daga kungiyarsa ya nemi aga-
jinsa, sai Musa ya yi masa kulli,ya
■^r<j^ * A* C^jyAA \r*r<a& ^4j*>-j£ OJ \&j
(1) Sunan 'yar'uwar Musa Maryamu ko Kalsama ko Kalsumu. Sunan uwarsu
Yuhaniz cliyar Hamid cfan Lawaya cfan Yakubu.
(2) Wannan ya nuna, cewa Musa an ba shi Annabci a gabanin ya yi hijira zuwa
Madyana. Kuma yana kara karfafa wannan magana abin da ke cikin aya ta 1 6 inda ya roki
Allah gafara, Ya gafarta masa, da aya ta 1 7 wadda ta nuna ya san an yi masa gafarar har
yana neman tsari domin kada ya koma yin haka a gaba. Annabawa suna wahami ga abin
da ba wahayi ba, sa'an nan Allah Ya gyara kuskuren, Ya tabbatar da gaskiya.
588
28 — Suratul FCasas
(I^JI^-VA
kashe shi. Ya ce, "Wannan aikin
Shaicfan ne, domin shi makiyi ne
mai 6atarwa, bayyananne!"
16. Ya ce, "Ya Ubangijma! Lalle
na zalunci kaina, sai Ka yi mini
gafara/' Sai Ya gafarta masa, do-
min Shi ne Mai yawan gafara, Mai
jin kai.
17. Ya ce, "Ya UbangijTna! Do-
min abin da Ka ni'imta shi a kaina,
saboda haka ba zan kasance mai
taimako ga masu laifi ba."
18. Sai ya wayi gari a cikin birnin
yana mai tsoro, yana sauna. Sai ga
wanda ya nemi taimako daga gare
shi a jiya, yana neman agajinsa.
Musa ya ce masa, "Lalle kai 6atacce
ne, bayyananne."
19. To, a lokacin da Musa ya yi
nufin ya damki wanda yake makiyi
ne a gare su, (mai neman agajin) ya
ce, (1) "Ya Musa! Shin, kana nufin
ka kashe ni ne kamar yadda ka
kashe wani rai jiya? Ba ka son kome
face ka kasance mai tankwasawa (2)
a cikin Rasa, kuma ba ka nufin ka
kasance daga masu kyautatawa."
20. Kuma wani mutum ya zo
daga mafi nisan birnin yana tafiya
da gaggawa, ya ce, "Ya Musa ! Lalle
mashawarta suna shawara game da
kai domin su kashe ka, saboda haka
ka fita. Lalle nT, mai naslha ne a gare
ka."
^ y^t. »" "' y > s**-*" ^ * s <s '
o?
~' >S"\6 '*' -' 'Xkk' *<&***% *'j\"
( 1 ) Ya facfi haka zaton Musa zai kashe shi ne saboda gargadin da ya gabatar a gare
shi. Maganar ta nuna Musa ya shahara da son gyaran abubuwa domin islahi, haka ne ga
al'adar mutane wanda ya tashi yana gyara sai sun tuhumce shi da neman girma.
(2) Tankwasa ce sanya mutane su yi abin da ba su son yi. Kyautatawar islahi ba ta
samuwa sai da tankwasawa domin galibi mutane sun fi son barna a kan kyautatawa tare da
saninsu ga cewar kyautatawar ita ce daidai.
589
28 - Suratul Kasas
TS^UttV*
y» — ^A
21. Sai ya fita daga gare ta, (1)
yana mai jin tsoro yana sauna. Ya
ce, "Ya Ubangijina! Ka tserar da ni
daga mutane azzalumai."
22. Kuma a lokacin da ya fus-
kanci wajen Madyana, ya ce, "Ina
fatan Ubangijina Ya shiryar da ni a
kan madaidaiciyar hanya."
23. Kuma a lokacin da ya isa
mashayar Madyana, ya sami wata
jam'ar mutane suna shayarwa,
kuma a bayansu ya sami wacfansu
mata biyu suna korar (tumakinsu).
Ya ce, "Mene ne sha'aninku?" Suka
ce, "Ba za mu iya shayarwa ba sai
makiyaya sun fita, kuma ubanmu
tsoho ne (2) mai daraja."
24. Sai ya shayar musu, sa'an
nan kuma ya juya zuwa ga inuwa,
sa'an nan ya ce, "Ya Ubangijina!
Lalle ne, ga abin da Ka saukar zuwa
gare ni na alheri nlmai bukata ne."
25. Sai cfayansu ta je masa, tana
tafiya a kan jin kunya, ta ce, "Uba-
na yana kiran ka, domin ya saka
maka ijarar abin da ka shayar sabo-
da mu. " To, a lokacin da ya je masa,
ya gaya masa labarinsa^ ya ce,
"Kada ka ji tsoro, ka tsira daga
mutane azzalumai."
26. T)ayarsu ta ce, "Ya Baba!
Ka ba shi aikin ijara, lalle ne mafi
s s± *'" /r/ s» s"
os*' ~v y " . * ' '
(1) Ya fita daga alkaryar.
(2) Saboda girma ba ya zuwa ya shayar da tumakinsa, sai ya sanya mu, mu 'ya'yansa,
ko da muke mata. Wannan ya nuna mace tana yin aikin maza saboda larura. Kuma
saboda darajar ubansu ba su shiga a cikin makiyaya ba domin tsaron mutuncinsu^ don
haka ake son asali mai kyau. Nisantarsu daga maza nau'in kauracewa ne na shari'a.
590
28 - Suratul Kasas
g^JIj^-rA
alherin wanda ka bai wa aikin ijara
shi ne mai karfi (1) amintacce."
27. Ya ce, "Lalle ne ina nufin in
aurar da kai cfayan 'ya'yana biyu,
wadannan, a kan ka yi mini aikin
ijara shekara takwas, to, idan ka
cika goma, to, daga gare ka yake.
Ba ni so in tsananta maka, za ka
same ni, in Allah Ya so, daga sa-
lihai."
28. Ya ce, "Wannan yana a
tsakanina da tsakaninka, kowane
cfayan adadin biyun na kare, to,
babu wani zalunci a kaina. Kuma
Allah ne Wakili ga abin da muke
facfa."
29. To, a lokacin da Musa ya
kare adadin kuma yana tafiya da
iyalinsa, sai ya tsinkayi wata wuta
daga gefen dutse (T)ur). Ya ce wa
iyalinsa, "Ku dakata, lalle neni, na
tsinkayi wata wuta, tsammanlna ni,
mai zo muku ne daga gare ta da
wani labari, ko kuwa da guntun
makamashi daga wutar don ko ku ji
dimi."
30. To, a lokacin da ya je wurinta
(wutar) aka kira shi, daga gefen
rafin na dama, a cikin wurin nan
mai albarka, daga itaciyar (cewa)
"Ya Musa! Lalle NT ne Allah,
Ubangijin halittu.
31. "Kuma ka jefa sandarka."
To, a lokacin da ya gan ta, tana
girgiza kamar karamar macijiya, ya
juya yana mai bayar da baya, bai
koma ba. "Ya Musa ! Ka fuskanto,
*£$* > < ;^ 'X? ' -' •>' *i '
> s 'If
(1) Watau tana ishara ga ubanta da cewa Musa ya tara siffofin nan biyu na £arfi da
amana domin abin da ta jarraba daga gare shi kafin ya iso ga ubanta.
591
28 — Suratul Kasas
m$\M-u
kuma kada ka ji tsoro, lalle ne kana
daga wacfanda ke amintattu.
32. "Ka shigar da hannunka a
cikin wuyan rigarka, ya fita fari, ba
da wata cuta ba, kuma ka hacfa
hannuwanka ga kafadunka, domin
tsoro (ya gushe daga gare ka). To,
wacfannan abubuwa dalilai biyu ne
daga Ubangijinka zuwa ga Fir'auna
da 'yan Majalisarsa. Lalle sun ka-
sance mutane ne fasikai."
33. Ya ce, "Ya UbangijTna ! Lalle
na kashe wani rai daga gare su,
domin haka ina tsoron kada su
kashe ni.
34. "Kuma cfan'uwana Haruna
shT ne mafi fasaha daga gare ni, ga
harshe, saboda haka Ka aika shi
tare da ni, yana mai taimako, yana
gaskata ni, lalle ne ina tsoron su
karyata ni."
35. Ya ce, "Za Mu karfafa
damtsenka game da cfan'uwanka,
kuma Mu sanya muku wani dalili,
saboda haka ba za su sadu zuwa
gare ku ba, tare da ayoyinMu, ku da
wadanda suka btku ne marinjaya."
36. To, a lokacin da Musa ya je
musu da ayoyinMu bayyanannu,
suka ce, "Wannan ba kome ba, sai
sihiri, wanda aka kaga, kuma ba mu
ji wannan ba daga wajen uban-
ninmu na farko."
^ 37. Kuma Musa ya ce, "Ubangi-
jina ne Mafi sanin wanda ya zo da
shiriya daga gare Shi, da wanda
akibar gida take kasancewa a gare
shi. Lalle ne masu zalunci ba su cin
nasara."
U di^^St &&&&
>. V.
>^*f> > >.
l^jJ^JUii).
> " %*<'
5ojV fi^Cti
592
28 - Suratul Kasas
s&eax&A
-CA
38. Kuma Fir'auna ya ce, "Ya
ku mashawarta ! Ban san kuna da
wani abin bautawa baicina ba, sa-
boda haka ka hura mini wuta, ya
Hamanu! a kan laka (1) (domin a yi
tubali), sa'an nan ka sanya mini
bene, tsammanma zan ninkaya
zuwa ga Ubangijin Musa, kuma
lalle ne ni, hakTka, ina zaton sa daga
makaryata."
39. Kuma ya kangare, shi da
rundunoninsa a cikin Rasa, ba da
hakki ba, kuma suka hakkake cewa
su, ba za a mayar da su zuwa gare
Mu ba.
40. Sai Muka kama shi, shi da
rundunoninsa, sai Muka jefa su a
cikin kogi. Sai ka dubi yadda akibar
azzalumai ta kasance.
41. Kuma Muka sanya su shuga-
banni, suna kira zuwa ga wuta,
kuma a Ranar Kiyama ba za a
taimake su ba.
42. Kuma Muka biyar musu da
la'ana a cikin wannan duniya kuma
a Ranar Kiyama suna daga wacfan-
da aka munana halittarsu.
43. Kuma lalle ne, haklka, Mun
bai wa Musa Littafi daga bayan
Mun halakar da karnonin farko,
domin su zama abubuwan kula ga
mutane, da shiriya da rahama,
tsammaninsu suna tunawa.
(p<<jry*LJ^2ui:
(1) Fir'auna ya fara yin gasasshen tubali da ake cewa ajurru, aka gina masa dogon
bene, ya hau samansa, ya harba kibiya ta tafi sama, ta komo da jini. Sai ya ce, " ya kashe
Ubangijin Musa." Bayan haka sai benen ya karye guntu uku, guntu daya ya fada wa
sojansa, da yawa daga cikinsu suka mutu, guntu daya kuma ya fada a cikin ruwa, sauran
guntu daya ya fada wa magina, suka mutu. Kuma cewar Fir'auna, "Lalle ne ni, ina zaton
Musa daga ma£aryata," ya nuna girman kansa kawai ne ya hana shi imani, ba rashin
ganewa ba, sai dai kuma sun ga kamar babu Tashin Kiyama.
593
28 — Suratul Kasas
68&\?&-to
44. Kuma ba ka kasance ba ga
gefen rafi na yamma a lokacin da
Muka hukunta al'amaru zuwa ga
Musa, kuma ba ka kasance daga
halartattu ba.
45. Kuma amma Mu, Mun kaga
halittawar wasu karnoni har loka-
tan rayuwa suka yi tsawo a kansu.
Kuma ba ka kasance mazauni ba a
cikin mutanen Madyana, kana ka-
ranta musu ayoyinMu, amma Mu,
Mun kasance masu aikawa (da kai
game (1) da wacfancan labarai).
46. Kuma ba ka kasance ga ge-
fen dutse ba a lokacin da Muka yi
kira, kuma amma domin rahama
daga Ubangijinka, domin ka yi gar-
gacfi ga mutane wadanda suke wani
mai gargacfi a gabaninka bai je
musu ba, tsammaninsu suna
tunawa.
47. Kuma ba domin wata maslfa
ta same su ba saboda abin da
hannayensu suka gabatar, su ce,
"Ya Ubangijinmu! Don me ba Ka
aiko wani Manzo zuwa gare mu ba,
har mu dinga bin ayoyinKa, kuma
mu kasance daga muminai?"
48. Sa'an nan a lokacin da gas-
kiya ta je musu daga wurinMu,
suka ce, "Don me ba a ba shi kamar
abin da aka bai wa Musa ba?" Shin,
kuma ba su kafirta ba da abin da
aka bai wa Musa a gabanin (wan-
nan)? Suka ce, "Sihirori biyu ne
G9 Cj^J^\<^^<Z^j<^^>
\~"' "**L % * .'
(1) Sanin wacfannan abubuwa duka ga Ummiyyi a wuri mai nTsa daga wurin da abin
ya auku a ciki, da kuma nTsa daga wadanda abin ya fi shafuwa, ya nuna gaskiyar abin da
kake da'awa. Kuma yana natsar da zuciyarka da zuciyar wadanda suka yi Tmani, kuma
suka yi hijira tare da ku, cewa suna cikin tsaron Allah.
594
28 — Suratul Kasas
«&-VA
suka taimaki juna," kuma suka ce,
"Lalle ne mu, masu kafirta ne ga
dukansu?"
49. Ka ce, "To, ku zo da wani
littafi daga wurin Allah, wanda
yake shi ne^mafi shiryarwa daga
gare su, in b! shi, idan kun kasance
masu gaskiya."
50. To, idan ba su karba maka
ba, to, sai ka sani suna bin son
zuciyarsu ne kawai, kuma wane ne
mafi 6ata daga wanda ya bi son
zuciyarsa, ba tare da wata shiriya
daga Allah ba? Lalle ne, Allah ba ya
shiryar da mutane azzalumai.
57. Kuma lalle ne, hakSca, Mun
sadar (1) da magana saboda su,
tsammaninsu, suna tunani.
52. Wacfanda Muka ba su littafi
daga j*abaninsa (Alkur'ani), su
masu Tmani ne da shi. (2)
53. Kuma idan ana karanta shi a
kansu, sai su ce, "Mun yi Tmani da
shi, lalle shi ne gaskiya daga
Ubangijinmu. Lalle mu, mun ka-
sance a gabaninsa masu salla-
mawa."
54. Wacfancan ana ba su ladarsu
sau biyu, saboda hakurin da suka
yi, kuma da kyautatawa suna
tunkucfewar munanawa, kuma
daga abin da Muka arzuta su suna
ciyarwa.
> '/'*&' (* *~K\'
bUjlU,
_J^Jo Al^A *Jj \ ( j^ J-r^i <>°J *-* <- \jb\
3 u^^^^jt^^i
(1) Attaura da Alkur'ani. Ayyukan Annabawa sashensu sun sadu da sashe.
(2) Mun sadar da ilmin Taurata da ilmin Alkur'ani, kowane ya gaskata wani, ko
kuwa Mun sadar da maganar Alkur'ani, wata ta bi wata, babu bambanci ga fasaha da
abubuwan ban mamaki a cikinsu.
595
28 - Suratul Kasas
&zm\M-u
55. Kuma idan sun ji yasassar
magana sukan kau da kai daga
barinta, kuma sukan ce, "Ayyu-
kanmu suna a gare mu, kuma ayyu-
kanku suna a gare ku, aminci ya
tabbata a kanmu, ba mu neman
jahilai (da husuma)." (1)
56. Lalle ne kai ba ka shiryar (2)
da wanda ka so, amma kuma Allah
Yana shiryar da wanda Yake so,
kuma Shi ne Mafi sani daga masu
shiryuwa.
57. Kuma suka ce, "Idan mun bi
shiriya tare da kai ana fizge mu (3)
daga kasarmu." Shin, ba Mu tab-
batar musu da mallakar Hurumi ba,
ya zama amintacce, ana jawowa
zuwa gare shi, 'ya'yan itacen kowa-
ne iri, bisa ga arzutawa daga gare
Mu? Amma kuma mafi yawansu ba
su sani ba.
58. Kuma da yawa Muka hala-
kar da wata alkarya wadda ta yi
butulci ga rayuwarta. To, wadan-
can gidajensu ne, ba a zaune su ba, a
bayansu, face kadan. Kuma mun
kasance Mu ne Magada.
f$^J${M£==>j-xS\
(1) Wadanda aka bai wa littafi a gabanin Alkur'ani, su ne Yahudu da Nasara,
warfansu daga cikin Malamansu sun musulunta, kamar Abdullahi bn Salami daga Yahudu,
da Nasaran Najrana daga Nasara, sun musulunta. Idan ba'ali ya musulunta sai a ce
dukansu ke nan sun musulunta, sai wanda ya yi girman kai ya ki gaskiya. Ba za a kula da
shi ba.
(2) Annabi, tsira da aminci su tabbata a gare shi, ya kasance yana son mutanensa
ICuraishawa su shiryu har dai Amminsa Abu Talib, sai Allah Ya gaya masa cewa shiriya ga
hannunSa take, Shi kadai, kuma sai wanda Ya so, shi ne zai shiryu, amma kuma akwai
daga cikin dalTlai bayyanannu maganar hijira kamar yadda ayar da ke tafe ta bayyana.
(3) Wanda ya makkana musu Hurumi ya zama amintacce, yana iya tsare bawanSa
kuma Ya ba shi arziki a kd'ina yake a cikin kasa, saboda haka tsoron fita daga Hurumi da
tsoron wuyar abinci a wurin bakunci, ba zai hana mumini ya yi hijira da addininsa ba zuwa
wurin yardar Allah.
596
28 - Suratul Kasas
figSgll^-W
59. Kuma Ubangijinka bai ka-
sance Mai halaka alkaryu ba, sai Ya
aika a cikin hedkwatarsu da wani
Manzo yana karanta ayoyinMu a
kansu. Kuma ba Mu kasance Masu
halaka alkaryu ba, face mutanensu
sun kasance masu zalunci.
60. Kuma abin da aka ba su daga
kome, to, jin dacfin rayuwar duniya
ne da kawarta. Kuma abin da ke
wurin Allah, shl ne mafi alheri,
kuma mafi wanzuwa. Shin ba ku
hankalta?
61. Shin fa, wanda Muka yi wa
wa'adi, wa'adi mai kyau, sa'an nan
shl mai hacfuwa da shi ne, yana
zama kamar wanda Muka jiyar da
shi cfan dacfi, dacfin rayuwar duniya,
sa'an nan shi a Ranar Kiyama yana
daga masu shiga wuta?
62. Kuma ranar da (Allah) Ya
kira su, sa'an nan Ya ce, "Ina abo-
kan tarayyaTa, wacfanda kuka ka-
sance kuna riyawa?"
63. Wadanda magana ta wajaba
a kansu, su ce, "Ya Ubangijinmu !
Wacfannan su ne wadanda muka
halakar, mun halakar da su kamar
yadda muka halaka. Mun barranta
zuwa gare Ka, ba su kasance mu
suke bauta wa ba."
64. Kuma a ce, ku kirawo abo-
kan tarayyar cfinku, sai su kira su,
sai ba su amsa ba, kuma su ga
azabar. Da dai lalle su sun kasance
suna shiryuwa (1) !
Jm^ -4 L^==» \j>j bii^«. (*4*^ \y&*y*j
^-' *', ' '■>*, * y" ?-*> '"'. < «> > w .\"'^y
*\-~'-
3 oy^^'Q^JJ^- *& -*-^+j
^^ojX^yo^^\y^\j^\]j]jj^
( 1 ) An shafe jawabi. FCaddarawarsa ita ce "Da sun kasance suna shiryuwa a duniya,
da ba su gan ta ba a Lahira."
597
28 - Suratul Kasas
tt\\ l i?A
-TA
65. Kuma ranar da Ya kira su,
sa'an nan Ya ce, "Mene ne kuka
kar6a wa Manzanni?"
66. Sai labaru su 6ace musu a
ranar nan, sa'an nan ba za su tam-
bayi junansu ba.
67. To, amma wanda ya tuba,
kuma ya yi imani, ya aikata aiki na
kwarai, to, akwai fatan su kasance
daga masu cin nasara.
68. Kuma Ubangijinka Yana ha-
litta abin da Yake so kuma Yake
za6i. Za6i bai kasance a gare su ba.
Tsarki ya tabbata ga Allah, kuma
(Allah) Ya cfaukaka daga barin abin
da suke yi na shirka.
69. Kuma Ubangijinka Yana sa-
nin abin da zukatansu ke 66yewa,
da abin da suke bayyanawa.
70. Kuma Shi ne Allah, babu
abin bautawa face Shi. Kuma Shi ne
abin godiya a cikin ta farko (du-
niya), da ta Rarshe (Lahira). Kuma
Shi ne da hukunci, kuma zuwa gare
Shi ake mayar da ku.
71. Ka ce, "Shin, kun gani, idan
Allah Ya sanya dare tutur a kanku
har zuwa Ranar Kiyama, wane abin
bautawa wanin Allah zai zo muku
da haske? Shin, ba ku ji?"
72. Ka ce, "Shin, kun gani, idan
Allah Ya sanya yini a kanku tutur
zuwa Ranar Kiyama, wane abin
bautawa, wanin Allah, zai zo muku
da dare, wanda kuna natsuwa a
cikinsa? Shin fa, ba ku gani?
73. "Kuma daga rahamarSa Ya
sanya muku dare da yini domin ku
natsu a cikinsa, kuma domin ku
' ^" ' "" £ * v S — ft )■" ' <* a. Sl
598
28 — Suratul Kasas
&m\m-^
nema daga falalarSa, kuma tsam-
maninku za ku gode."
74. Kuma a ranar da Yake kiran
su ya ce, "Ina abokan tarayyaTa,
wacfanda kuka kasance kuna
riyawa? ,,(1)
75. Kuma Muka zare mai shaida
daga kowace al'umma, sa'an nan
Muka ce, "Ku kawo dalilinku." Sai
suka san cewa lalle gaskiya ga Allah
take. Kuma abin da suka kasance
suna kirkirawa na karya ya 6ace
daga barinsu.
76. Lalle ne Karuna ya kasance
daga mutanen Musa, sai ya fita (2)
daga tsarinsu alhali Mun ba shi
taskokin abin da yake mabudansa
suna nauyi ga jama'a (3) ma'abuta
karfi, a lokacin da mutanensa suka
ce masa, "Kada ka yi annashuwa,
lalle ne Allah ba Ya son masu anna-
shuwa.
77. "Kuma ka bida, a cikin abin
da Allah Ya ba ka, gidan Lahira,
kuma kada ka manta da rabonka
daga duniya. Kuma ka kyautata,
kamar yadda Allah Ya kyautata
zuwa gare ka, kuma kada ka nemi
6arna a cikin kasa, (4) lalle ne Allah
ba Ya son masu 6arna."
>/»/
&Lj*ll+
{3$ cy^^^4^ j^oio^^'ci
(1) Bayan Allah Ya tunatar da Musulmi rahamarSa da kadaita ga bayar da ni'ima ko
hana ta, da siffofi masu kwadaitar da mumini ga da 'a ga Allah da ManzonSa, daga cikin
da'a akwai yin hijira wanda yake shi ne kan labarin surar, sai kuma Ya tsoratar da mai bin
wanin Allah ga rashin yin hijira. Duka abin da ya hana muminai hijira idan shi abin nan ba
uzuri ne na shari'a ba, to, ya zama gunki, abin bautawa, wanin Allah. Umurnin da ya sa6a
wa umurnin Allah duka, umurnin abokin tarayya ne ga Allah ga wanda ya bi shi.
(2) Asalin baghy zalunci, amma ga izdilahi, shi ne fita daga da'ar Shugaban Musulmi.
(3) Yawansu saba'in, an ce arba'in, kuma an ce goma.
(4) *Barna a cikin kasa, shi ne fita daga tsarin jama'a, da raba su kungiya-kungiya, ko
barin hijira a bayan an yi umurni da yin ta.
599
28 - Suratul Kasas
m$\M-^
78. Ya ce, "An ba ni shi a kan
wani ilmi wanda yake gare ni ne
kawai." Shin, kuma bai sani ba
cewa lalle Allah, hakika, Ya halakar
a gabaninsa, daga karnoni, wanda
yake shi ne mafi tsananin karfi daga
gare shi, kuma mafi yawan tarawar
dukiya, kuma ba za a tambayi masu
laifi daga zunubansu ba? (1)
79. Sai (Karuna) ya fita a kan
mutanensa a cikin adonsa. Wa-
cfanda suke nufin rayuwar duniya
suka ce, "Ina dai muna da kwa-
tancin abin da^aka bai wa Karuna!
Lalle shi, haklka, ma'abucin rabo
babba ne."
80. Kuma wadanda aka bai wa
ilmi suka ce, "Kaitonku! Saka-
makon Allah ne mafi alheri ga wan-
da ya yi tunani, kuma ya aikata
aikin kwarai, (2) kuma babu wanda
ake hadawa da ita face mai ha
kuri."
81. SaiMukashafekasa (3) dashi
da kuma gidansa. To, wadansu ja-
A'sfA
yy y yy y
i^cj-^Jj^-
iLAJ^I^^l^iL^
^ / ^ y »*■ X y y y ■> ' .
(1) Yana ganin dukiyar da ya samu, ya same ta ne saboda ya san ilmin fatauci da
sana'a kuma yana da karfin neman dukiyar, saboda raddin irin tunaninsa, Allah Ya ce Ya
halaka wanda ya fi shi tsananin karfi da kdkarin tara dukiya, kuma idan Ya tashi halaka
mai laifi ba Ya tsayawa tambayarsa dalTlin da ya sa ya yi laifin, kafin Ya halakar da shi.
Wacfannan abubuwa uku sun isa ga mai dukiya ya yi tunani, domin kada annashuwa
ta shige shi ya ki gode wa Allah.
(2) Tmani da aikin kwarai wanda Allah Ya yi umurni da a yi shi, kuma yinsa kamar
yadda ManzonSa ya nuna. Akwai daga cikin aikin kwarai yin hijira da barin kula da
dukiya. Ba a samun sakamakon Allah sai da hakuri.
(3) An ce a bay an Karuna ya yanke kansa da nasa mutane daga Musa, sai ya shirya
da wata karuwa domin ta yi wa Musajcazafin cewa ya yi zinajla ita, a kan ya aure ta. Sai
Musa ya tashi yana wa'azi a cikin BanT Isra'Tla ya ce, "Ya BanllsraTla wanda ya yi sata za
mu yanke hannunsa, wanda ya yi kazafi mu yi masa bulala tamanin, wanda ya yi zina, ba
ya da mata, mu yi masa bulala dari, wanda ya yi zina yana da mata, mu jefe shi sai ya
mutu." Sai Karuna ya ce, "K6 da kai ne?" Ya ce, "K6 da ni ne." Sai Karuna ya ce "An ce
ka yi fajirci tare da wance, karuwa." Sai Musa ya ce, "A kira ta." Da tazo, ya gama ta da
600
28 — Suratul Kasas
tfZ\Vi<&
-TA
ma'a ba su kasance gare shi ba,
wacfanda suke taimakon sa, baicin
Allah, kuma shi bai kasance daga
masu taimakon kansu ba.
82. Kuma wacfanda suka yi bu-
rin matsayinsa a jiya suka wayi gari
suna cewa, "Wai ! Allah Yana shim-
ficfa arziki ga wanda Yake so daga
BayinSa, kuma Yana kuntatawa.
Ba domin Allah Ya yi mana falala
ba, da Ya shafe kasa da mu. Wai !
Lalle ne shi, kafirai ba su cin
nasara."
83. Wancan gidan Lahira Muna
sanya shi ga wacfanda suke ba su
nufin cfaukaka a cikin rayuwar du-
niya, kuma ba su son 6arna. Kuma
akiba ga masu takawa take.
84. Wanda ya zo da abu mai
kyau, to, yana da mafi alheri daga
gare shi, kuma wanda ya zo da
mugun abu, to, ba za a saka wa
wacfanda suka aikata miyagun
ayyuka ba, face da abin da suka
kasance suna aikatawa.
85. Lalle ne Wanda Ya faralta
Alkur'ani a kanka, hakika, Mai
mayar da kai ne^zuwa ga makoma.
Ka ce, "UbangijTna ne Mafi sani ga
wanda ya zo da shiriya, da kuma
wanda yake a cikin Bata bayyanan-
niya."
86. Kuma ba ka kasance kana
fatan a jefa Littafin nan zuwa gare
ka ba, face dai domin rahama daga
Oyj^i O^ 4 ^ \^y^b^A Vy^ vJ-X3i \ p^rAj
1%.».' ><" ^^x f ~>
'<*'
' *'
^bt^^-J^l
Allah, ta facfi gaskiya, sai ta ce Karuna ne ya yi tsada da ita, ta fadi hakanan. Sai Musa ya
yi addu'a a kansa, kasa ta hacfiye shi, shi da gidansa duka.
601
28 - Suratul Kasas
(!»j&-VA
Ubangijinka. Saboda haka kada ka
zama mai taimako (1) ga kafirai.
87. Kuma kada lalle su karkatar
da kai daga barin ayoyin Allah, a
bayan har an saukar da su zuwa
gare ka. Ka yi kira zuwa ga Ubangi-
jinka, kuma kada lalle ka kasance
daga masu shirka.
88. Kada ka kira wani abin bau-
tawa na dabam tare da Allah. Babu
abin bautawa face Shi. Kowane abu
mai halaka ne face YardarSa. Shi ne
da hukunci kuma zuwa gare Shi ake
mayar da ku. (2)
] C?^
4»
i+J:*
Tana karantar da cewa Kalmar Tmani kawai ba ta isa sai da
aikata abin da ta £unsa. Kuma Allah na jarraba Musulmi domin a
fitar da munafukai daga cikin nagari.
1. A. L.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
M.
2. Ashe, mutane sun yi zaton a
bar su su ce, "Mun yi Tmani," alhali
kuwa ba za a fitine su ba?
(1) Taimakon, shi ne ka yi burin musuluntarsu har ka wahala domin a saukake ma
hukuncin hijira wadda Allah Ya yi umurni da a yi ta a bayan musulunta. Sai ka iyar da
Manzanci, shiryarwa kuwa ga hannun Allah take. Wannan aya tana nunawa bayyana
karyar masu da'awar cewa wani mutum yana bai wa wani imani ko ya karbe shi daga gare
shi. Kowa a cikin tsoro yake, sai wanda Allah Ya sanya shi cikin aminci. Allah Ya sanya mu
cikin amincinSa domin rahamarSa.
(2) Wannan aya ta karshen surar, ta tara; ilmin da surar ta karantar a cikin abubuwa
biyar da ta zana.
602
29 - Suratul 'Ankabut
^A^Jij^ - n
3. Kuma lalle Mun fitini wadan-
da ke a gabaninsu, domin lalle Al-
lah Ya san wacfanda suka yi gas-
kiya, kuma lalle Ya san makaryata.
4. K6 wadanda ke aikata miya-
gun ayyuka sun yi zaton su tsere
Mana? Abin da suke hukuntawa ya
munana.
5. Wanda ya kasance yana fatan
gamuwa da Allah, to, lalle ajalin
Allah mai zuwa ne, kuma (Allah)
ShT ne Mai ji, Masani.
6. Kuma wanda ya yi jihadi, to,
yana yin jihadin^ne domin kansa.
Lalle Allah, haklka Wadatacce ne
daga barin talikai.
7. Kuma wadanda suka yi Tmani,
kuma suka aikata ayyukan kwarai,
lalle Muna kankare musu miyagun
ayyukansu, kuma lalle Muna saka
musu da mafi kyaun abin da suka
kasance suna aikatawa.
8. Kuma Mun yi wa mutum wa-
siyyar kyautatawa ga uwayensa,
kuma idan sun tsananta maka do-
min ka yi shirki da Ni game da abin
da ba ka da ilmi gare shi, to, kada ka
yi musu da'a. Zuwa gare Ni mako-
marku take, sa'an nan In ba ku
labari ga abin da kuka kasance
kuna aikatawa.
9. Kuma wadanda suka yi Tmani,
kuma suka aikata ayyukan kwarai,
lalle Muna shigar da su a cikin
mutanen kirki.
10. Kuma daga cikin mutane ak-
wai mai cewa, "Mun yi Tmani da
Allah," sa'an nan idan aka cuce shi
wajen aikin Allah, sai ya sanya
^y > *y * ^ y *y > s *y ' /i' y y »'*-
» >* »> x y y '« y y y ° }• y y ' k*s
603
29 - Suratul 'Ankabut
-H
fitinar mutane kamar azabar Allah,
kuma lalle idan^taimakon Ubangi-
jinka ya zo, hakika, yakan ce, "Lal-
le mu, mun kasance tare da ku."
Shin, Allah bai zama Mafi sani ba
ga abin da ke a cikin kirazan halit-
tunSa?
77. Kuma lalle^ Allah na sanin
wacfanda suka yi Tmani kuma lalle
Yana sanin munfukai.
12. Kuma wacfanda suka kafirta
suka ce wa wacfanda suka yi Tmani,
"Ku bi hanyarmu, kuma mu cfauki
laifuffukanku," alhali kuwa ba su
zamo masu cfauka daga kome ba
daga laifuffukansu. Lalle su,
makaryata ne.
13. Kuma lalle suna cfaukar
kayan nauyinsu da wacfansu nau-
yayan kaya tare da kayan nauyinsu,
kuma lalle za a tambaye su a Ranar
Kiyama game da abin da suka ka-
sance suna kirkirawa na karya.
14. Kuma lalle Mun aika Nuhu
zuwa ga mutanensa, sai ya zauna a
cikinsu shekara dubu face shekara
hamsin, sa'an nan cikowar (T)u-
fana) ta kama su, alhali kuwa su ne
masu zalunci.
15. Sa'an nan Muka tslrar da shi
da mutanen jirgin, kuma Muka sa-
nya jirgin ya zama wata aya ga
talikai.
16. Da Ibrahim a lokacin da ya
ce wa mutanensa, "Ku bauta wa
Allah, Jai bi Shi da takawa. Wan-
nan shine alheri a gare ku idan kun
kasance kuna sani.
j-ijji <s^ l^==» is^ y^J^i-^j j*/^
ki^^^^l^lJL^^JLiJj
p C>J^^jJ,]3^\^jJi
604
29 - Suratul 'Ankabut
^l&4 -H
17. "Abin da dai kuke bauta wa,
baicin Allah, gumaka ne, kuma kun
kirkira karya. Lalle wacfannan da
kuke bauta wa, baicin Allah, ba su
mallaka muku arziki. Saboda haka
ku nemi arziki a wurin Allah kawai,
kuma ku bauta Masa, kuma ku yi
godiya zuwa gare Shi. Zuwa gare
Shi ake mayar da ku.
18. "Kuma idan kun karyata, to,
lalle wacfansu aFummomi a gaba-
ninku sun karyata, kuma babu abin
da ke kan Manzo, face iyar da
manzanci, iyarwa bayyananna."
19. Shin, ba su (1 } ga yadda Allah
ke fara yin halitta ba, sa'an nan
kuma Ya mayar da ita? Lalle wan-
nan abu ne mai sauki ga Allah.
20. Ka ce, "Ku yi tafiya cikin
kasa, sa'an nan ku duba yadda
(Allah) Ya fara yin halitta, sa'an
nan kuma Allah Yana kaga wata
halittar mayarwa. Lalle Allah Mai
ikon yi ne a kan kome.
21. "Yana azabta wanda Ya so,
kuma Yana jin kan wanda Ya so.
Kuma zuwa gare Shi ake juya ku.
22. "Kuma ba ku zamo masu
buwaya ba a cikin kasa, kuma haka
a cikin sama, kuma ba ku da wani
majibinci wanda ba Allah ba, kuma
ba ku da wani mataimaki."
23. Kuma wacfanda suka kafirta
da ayoyin Allah da gamuwa da Shi,
wacfannan sun yanke kauna daga
rahamaTa, kuma wacfannan suna
da wata azaba mai racfacfi.
>xi>:
l$2 J^t(J*$ &SS9 aF' <^4
< ji A r < s' '* t '\ ' \ > 'V ^ fa
5p ^)^\^p^^^^j { j^j^\^ m
(1) Ga wata kira'a, ba ku ga... da lamirin abokan magana wacfanda Ibrahim ke yi wa magana. A
kan wannan kira'a, maganar Ibrahim ba ta yanke ba har Rarshen aya ta 23.
605
29 - Suratul 4 Ankabut
&£Hjgi _ n
24. Sa'an nan babu abin da ya
kasance jawabin mutanensa (Ibra-
him) face dai suka ce, "Ku kashe
shi ko, ku kona shi," sai Allah Ya
tsirar da shi daga wuta. Lalle a cikin
wannan akwai ayoyi ga mutanen da
ke yin imani.
25. Kuma Ibrahim ya ce,
"Babu abin da kuka yi sai dai kun
bar Allah kun riki gumaka saboda
soyayyar tsakaninku a cikin rayu-
war duniya, sa'an nan a Ranar
Kyama sashinku zai kafirce wa sas-
hi, kuma makomarku ita ce wuta,
kuma ba ku da wadansu matai-
maka."
26. Sai Ludu ya yi imani da shi.
Kuma Ibrahim ya ce, "Lajle ni mai
kaura ne zuwa ga Ubangijina. Lalle
Shi, Shi ne Mabuwayi, Mai
hikima."
27. Kuma Muka ba shi Is'haka
da Ya'akuba, kuma Muka sanya
Annabci da littafi a cikin zuriy-
arsa. Kuma Mun ba shi sakama-
konsa a duniya, kuma lalle shi, a
Lahira, tabbas, yana a cikin salihai.
28. Da Ludu, a lokacin da ya ce
wa mutanensa, "Lalle ku, hakika,
kuna je wa alfasha wadda wani
mahaluki daga cikin duniya bai riga
ku gare ta ba.
29. "Ashe, lalle ku, kuna je wa
maza, kuma ku yi fashin hanya
kuma ku je, a cikin majalisarku, da
abin da ba shi da kyau? To, jawabin
mutanensa bai kasance ba face dai
sun ce, 'Ka zo mana da azabar
Allah, idan ka kasance daga masu
gaskiya.'"
j_Jl4&\ 4lw3?l3 (>J*j>-j\
fe$$^*Jijxj£\&$&j
Ss>J^&^i^^4^1j
' *i'<»>^
, ^ t"
606
29 - Suratul 'Ankabut
&-tt
30. Ya ce, "Ya Ubangijlna! Ka
taimake ni a kan mutanen nan
mabarnata."
31. Kuma a lokacin da Manzan-
ninMu suka je wa Ibrahim da
bushara suka ce, "Lalle mu masu
halaka mutanen wannan alkarya
ne. Lalle mutanenta sun kasance
masu zalunci."
32. Ya ce, "Lalle akwai Lucfu a
cikinta!" Suka ce, "Mu ne mafiya
sani ga wadanda suke a cikinta, lalle
muna tsTrar da shi da mutanensa,
face fa matarsa ta kasance a cikin
masu wanzuwa."
33. Kuma a lokacin da Manzan-
ninMu suka je wa Ludu ya Bata rai
saboda su, kuma ya kuntata ga kirji
saboda su. Kuma suka ce, "Kada
ka ji tsdro, kuma kada ka yi bakin
ciki, lalle mu masu tslrar da kai ne
da iyalanka, face dai matarka ta
kasance daga masu wanzuwa.
34. "Lalle mu, masu saukar da
azaba ne daga sama a kan mutanen
wannan alkarya saboda abin da
suka kasance suna yi na fasikanci."
35. Kuma lalle Mun bar wata
aya bayyananna daga gare ta ga
mutane masu hankalta.
36. Kuma zuwa ga Madyana,
Mun aika dan'uwansu Shu'aibu, sai
ya ce, "Ya mutanena! Ku bauta wa
Allah kuma ku yi fatan (rahamar)
Ranar Lahira, kuma kada ku yi
6arna a cikin kasa, alhali kuwa
kuna masu lalatarwa."
37. Sai suka karyata shi, saboda
haka tsawa ta kama su, domin haka
sy&&^s^^y&~*
/juJLJI
?*4i^ ' m *Zf
frv
y^Rl£])&tt\fed%fc
>S s* sy
A 4. "4 j
<- ^- A ■>.<.
•11 € *s*
jy*±i J Lid L-^ p-*> UJ <LjA*a$j
^^ -r r> . -iff •
607
29 - Suratul 'Ankabut
i2~-tt
suka wayi gari suna guggurfane.
38. Da Adawa da Samudawa,
alhali kuwa lalle alamun azaba sun
bayyana a gare su daga gidajensu,
kuma Shaidan ya kawata musu
ayyukansu, saboda haka ya kange
su daga hanyar Allah, kuma sun
kasance masu basira!
39. Kuma Karuna da Fir'auna
da Hamana, kuma lalle Musa ya je
musu da hujjjqji, sai suka yi girman
kai a cikin kasa, kuma ba su kasan-
ce masu tserewa ba.
40. Saboda haka kowanensu
Mun kama shi da laifinsa: Watau
daga cikinsu akwai wanda Muka
aika iskar tsakuwa a kansa, kuma
daga cikinsu akwai wanda tsawa ta
kama, kuma daga cikinsu akwai
wanda Muka birkice kasa da shi,
kuma daga cikinsu akwai wanda
Muka nutsar. Ba ya yiwuwa ga
Allah Ya zalunce su, amma sun
kasance kansu suke zalunta.
41. Misalin wadanda suka riki
wadansu masoya wadanda ba Allah
ba, kamar misalin gizogizo ne wan-
da ya riki wani dan gida, alhali
kuwa lalle mafi raunin gidaje, shine
gidan gizogizo, da sun kasance suna
sane.
42. Lalle Allah Yana sane da
abin da suke kira, wanda ba SW ba,
na wani abu duka, kuma Shi ne
Mabuwayi, Mai hikima.
43. Kuma wadancan misalan
Muna bayyana su ga mutane, kuma
babu mai hankalta da su sai masu
ilmi.
SSft' ft 9 '* >"^ *.' {*''\&<
-^» -if- 'TV- >-<-t^ r
608
29 - Suratul 'Ankabut
&-tt
44. Allah Ya halitta sammai da
Jeasa da gaskiya. Lalle cikin wancan
akwai aya ga muminai.
45. Ka karanta abin da ake yin
wahayi zuwa gare ka daga Littafi,
kuma ka tsayar da salla. Lalle
salla tana hanawa daga alfasha da
abin kyama, kuma lalle ambaton
Allah ya fi girma, kuma Allah Yana
sane da abin da kuke aikatawa.
46. Kada ku yi jayayya da mazo-
wa Littafi sai fa da magana wadda
ta fi kyau, sai fa wacfanda suka yi
zalunci daga gare su, kuma ku ce,
"Mun yi imani da abin da aka
saukar a gare mu kuma aka saukar
a gare ku, kuma Abin bautawarmu
da Abin bautawarku Guda ne,
kuma mu masu sallamawa ne a gare
Shi."
47. Kuma kamar haka Muka
saukar da Littafi a gare ka, to,
wacfannan da Muka bai wa Littafi
suna imani da shi,_daga cikin
wacfannan akwai mai Tmani da shi,
kuma babu mai musun ayoyinMu,
face kafirai.
48. Kuma ba ka kasance kana
karatun wani littafi ba a gabaninsa,
kuma ba ka rubutunsa da daman-
ka, da haka ya auku, da masu 6arna
sun yi shakka.
49. A'a, shT ayoyi ne bayyanan-
nu a cikin kirazan wadanda aka bai
wa ilmi. Kuma babu mai musun
ayoyinMu face azzalumai.
50. Kuma suka ce, "Don me ba a
saukar masa da ayoyi ba daga
Ubangijinsa?" Ka ce, "Su ayoyi a
c «" ' Tf ' J- fi*>
609
29 - Suratul 'Ankabut
5S»4«II|^-«
wurin Allah kawai suke, kuma lalle
ni mai gargacfi kawai ne, mai bayya-
nawa."
51. Shin bai ishe su ba cewa lalle
Mu, Mun saukar da Littafin a kan-
ka, ana karanta shija kansu? Lalle a
cikin wancan, hakika, akwai raha-
ma da tunatarwa ga mutanen da ke
yin Tmani.
52. Ka ce, "Allah Ya isa Shaida a
tsakanlna da tsakanmku, Yana sane
da abin da ke a cikin sammai da
kasa, kuma warfanda suka yi Tmani
da karya kuma suka kaflrta da
Allah, warfannan su ne masu
hasara."
53. Kuma suna neman ka da
gaggauta azaba, to, ba domin ajali
kayyadadde ba, da azaba ta je
musu, kuma lalle da tana iske su
bisa ga abke, alhali kuwa su, ba su
sani ba.
54. Suna neman ka da gaggauta
azaba, kuma lalle Jahannama, tab-
bas, mai kewayewa ce ga kafirai.
55. Ranar da azaba ke rufe su
daga samansu da kuma kasan kafa-
funsu kuma Ya (1) ce, "Ku rfanrfani
abin da kuka kasance kuna aika-
tawa."
56. Ya bayiNa, warfanda suka yi
Tmani ! Lalle fa kasaTa mai yalwa (2)
ce, saboda haka ku bauta Mini.
* z
££&..
~'\A *ii>' ■
*f • ys.s
T? 'S % »'
^\!\A\&^o^3C~z
JVy o
»»fi
(1) Ga wata ruwayar "Mu" matsayin "Ya", watau Mala'iki wakilin azabarsu.
(2) Tun da kasa na da yalwa, sai mutum ya yi hijira zuwa wurin da yake sassauka a gare shi, ya
bauta wa Allah da sauki, idan garinsu ya buwaye shi.
610
29 - Suratul w Ankabut
■ n
57. Kowane rai mai cfancfanar
mutuwa ne, sa'an nan zuwa gare
Mu ake mayar da ku.
58. Kuma wacfanda suka yi ima-
ni kuma suka aikata ayyukan kwa-
rai, lalle za Mu zaunar da su daga
cikin Aljanna a gidajen bene, kora-
mu na gudana daga karkashinsu,
suna madawwama a cikinsu. To,
madalla da sakamakon masu aikin
kwarai.
59. Wadanda suka yi hakuri,
kuma suna dogara ga Ubangijinsu
kawai.
60. Kuma da yawa (1) dabba
wadda ba ta daukar abincinta, Al-
lah Yana^ciyar da ita tare da ku,
kuma Shi ne Mai ji, Mai ilmi.
61. Lalle idan ka tambaye su,
"Wane ne ya halitta sammai da
kasa kuma ya hore rana da wata?"
Lalle suna cewa Allah ne. To, yaya
ake karkatar da su (2) ?
62. Allah ne ke shimfida arziki
ga wanda Yake so daga cikin bayin-
Sa, kuma Yana kuntatawa ga (wan-
da Yake so). Lalle Allah, Masani ne
ga dukan kome.
63. Kuma lalle idan ka tambaye
su, "Wane ne ya saukar da ruwa
daga sama, har ya rayar da kasa
game da shi a bayan mutuwarta?"
Lalle suna cewa, "Allah ne." Ka ce,
^^^jrc^\^\i^jb
>&,"• *' V\>" < &
^P ^ C %iS* ltS 4$ 'Ol
(1) Saboda haka tunanin abinci kada ya hana ku yin hijira zuwa wurin yardar Allah, Mai ciyar
da dabbobin da ba su tattalin abincinsu.
(2) Yaya ake karkatar da su daga hijira domin tsoron yankewar abinci, alhali kuwa sun tafi wurin
yardar wanda Ya halitta sammai da kasa? Yin hijira yana a cikin jarrabawar Allah ga Musulmi.
611
29 - Suratul 'Ankabut
-rn
"Godiya ta tabbata ga Allah." A'a,
mafi yawansu ba su hankalta.
64. Kuma wannan rayuwa ta du-
niya ba ta zamo ba, face abar shaga-
la da wasa, kuma lalle Lahira, tab-
bas, ita ce rayuwa, da sun kasance
suna sani.
65. To, a lokacin da suka shiga
cikin jirgin ruwa, sun kirayi Allah
suna masu tsarkake addini a gare
Shi, to, a lokacin da Ya tsTrar da su
zuwa ga tudun kasa, sai ga su suna
shirki.
66. Domin su kafirce wa abin da
Muka ba su, kuma domin su ji dadi,
sa'an nan kuma za su sani.
67. Shin, ba su ga cewa, lalle
Mun sanya Hurumi amintacce ba,
alhali kuwa ana fisge mutane a
gefensu? Shin, da 6ataccen abu
suke imani kuma da ni'imar Allah
suka kafirta?
68. Kuma wane ne ya fi zalunci
bisa ga wanda ya kirkira karya ya
jingina ta ga Allah, ko kuma ya
karyata gaskiya a lokacin da ta je
masa? Ashe, a cikin Jahannama
babu mazauna ga kafirai?
69. Kuma wadannan da suka yi
kokari ga neman yardarMu, lalle
Muna shiryar da su ga hanyo-
yinMu, kuma lalle Allah, tabbas,
Yana tare da masu kyautatawa (ga
addTninsu).
(iM\^U^^^\\^
>y »>»> • -^rf < *
« .<.<'
o^^ii^Ui^lUi
<» x < \ *<»"'*' »*'~L\s'\' i >>
/&*< ».& '.I.,* '
<.'<'. ''?*
^^i^===tU
612
30 — Suratur Rum
fcsTO£-r-
Tana karantar da cewa duka abubuwan duniya suna da
dangantaka da junansu, dangantaka bayyananna ko 66yayya.
Kuma zumuntarsu na gudana gwargwadon dangantakarsu da juna
ga jiki da ma'ana.
."j*'^ * *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. A. L. M.
2. An rinjayi Rumawa. (1)
3. A cikin mafi kusantar kasar-
su, kuma su, a bayan rinjayarsu, za
su rinjaya.
4. A cikin 'yan shekaru. Al'ama-
ri na Allah ne a gabanin kome da
bayansa, kuma a ranar nan mumi-
nai za su yi farin ciki.
5. Da taimakon Allah, Yana tai^
makon wanda Yake so. Kuma Shi
ne Mabuwayi, Mai jin kai.
^1 ^J^JyJJLy^Jl
SJ^Qt^K
(1) Rumawa Kiristoci ne masu aiki da littafi, suna facfa da Farisawa masu bauta wa
wuta. Farisa suka rinjayi Rumawa, saboda haka FCuraishawa suka ji dadi saboda alfanu
cewa za su rinjayi Musulmi idan sun yi facfa. A bayan saukar Surar, sai Musulmi suka yi
farin ciki saboda alfanu cewa su kuma za su rinjayi FCuraishawa. Wannan ya sanya
Abubakar ya yi kuri'a da Ubaiyu bn Halafa kan rakuma goma a cikin shekaru uku. Sai
Annabi ya ce wa Abubakar ya kara rakuma da ajali zuwa shekaru tara. A bayan shekaru
bakwai sai Rumawa suka ci nasara a kan Farisawa, kuma wannan ya yi daidai da Badar,
watau ranar da Musulmi suka ci nasara a kan Kuraishawa. Abubakar ya ci rakumansa
daga magadan Ubaiyu. Amma sai ya yi sadaka da su da umurnin Annabi, domin Allah Ya
hana Musulmi su yi caca a lokacin.
613
30 — Suratur Rum
fcs£!ljgi-r-
6. Wa'adin Allah, Allah ba ya
saBawa ga wa'adinSa, kuma amma
mafi yawan mutane ba su sani ba.
7. Suna sanin bayyanannar
rayuwar duniya, alhali kuwa su
shagalallu ne daga rayuwar La-
hira. (1)
8. Shin, ba su yi tunani ba a cikin
zukantansu cewa Allah bai halitta
sammai da kasa ba da abin da ke
tsakaninsu, face da gaskiya (2) da
ajali ambatacce? Kuma lalle masu
yawa daga mutane kafirai ne ga
gamuwa da Ubangijinsu?
9. Shin, kuma ba su yi tafiya ba,
a cikin kasa domin su gani yadda
akibar wacfanda ke a gabaninsu ta
kasance? Sun kasance mafiya karfi
daga gare su kuma suka nomi kasa,
suka raya ta fiye da yadda suka raya
ta, kuma manzanninsu suka je
musu da hujjoji bayyanannu. Sabo
da haka Allah ba Ya yiwuwa Ya
zalunce su, amma kansu suka ka-
sance suna zalunta.
10. Sa'an nan akibar wacfannan
da suka aikata mugun aiki ta kasan-
ce mafi muni, watau sun karyata
game da ayoyin Allah, kuma suka
kasance suna izgili da su.
77. Allah ne ke fara yin halitta,
sa'an nan Ya sake ta, sa'an nan
zuwa gare Shi ake mayar da ku.
12. Kuma a ranar da Sa'a ke
tsayuwa, masu laifi za su kasa
magana.
^% <*. '-•*
\*2 OjJLfjP
; & > \ . f >
&S s> >,
5P O^r^^^U-^^^^ fjfifcP-J
( 1 ) Dangantakar rashin sanin ikon Allah da sanin sha'anin duniya da kuma jahiltar
al'amarin Lahira.
(2) Gaskiya ita ce tsari tabbatacce wanda ba ya canzawa.
614
30 — Suratur Rum
ta^l^-r-
13. Kuma ba su da masu ceto
daga abubuwan shirkinsu, kuma
sun kasance masu kafircewa daga
abubuwan shirkinsu.
14. Kuma a ranar da Sa'a ke
tsayuwa, a ranar nan mutane ke
rarraba.
75. To, amma wacfanda suka yi
Imani, kuma suka aikata ayyukan
kwarai, to, su ana faranta musu
rayuka a cikin wani lambu.
16. Kuma wadanda suka kafirta,
kuma suka karyata, game da ayo-
yinMu da kuma harfuwa da Ranar
Lahira, to, wadancan ana halartar
da su a cikin azaba.
17. Saboda haka tsarkakewa ta
tabbata ga Allah a lokacin da
kuke shiga maraice, da lokacin da
kuke shiga safiya. (1)
18. Kuma Shi ne da godiya, a
cikin sammai da kasa, kuma da
lokacin yamma da lokacin zawali.
19. Yana fitar da mai rai daga
matacce, kuma Yana fitar da matac-
ce daga mai rai, kuma Yana rayar
da kasa a bayan mutuwarta. Kuma
haka ake fitar da ku.
20. Kuma akwai daga ayoyin-
Sa, Ya halitta ku daga turbaya, sai
ga ku kun zama mutum, kuna wat-
suwa.
21. Kuma akwai daga ayoyinSa,
Ya halitta muku matan aure daga
!>i*A^ >4jd^ ot p*- 3 oN fb
*^>Jj£j>4*
^t< >'** \<'\i - ^ Jl.ir
Ml oj^c^2>cf^j>
>,>.
is-
(1) Akwai dangantaka a tsakanin tasbihi, watau ibada da rayuwa, da tsakanin fitar
hantsi da safiya, kamar yadda yake akwai dangantaka a tsakanin mutuwa da maraice, da
yamma da kafirci.
615
30 — Suratur Rum
tB$l!&-r.
kanku, domin ku natsu zuwa
gare ta, kuma Ya sanya soyayya da
rahama a tsakaninku. (1) Lalle a
cikin wancan akwai ayoyi ga muta-
ne masu yin tunani.
22. Kuma akwai daga ayoyinSa,
halittar sammai da kasa, da sa6a-
war harsunanku, da launukanku.
Lalle a cikin wannan akwai ayoyi ga
masu ilmi.
23. Kuma akwai daga cikin
ayoyinSa, barcinku, a cikin dare da
rana, da nemanku ga falalarSa.
Lalle a cikin wannan akwai ayoyi ga
mutane masu saurarawa.
24. Kuma akwai daga cikin
ayoyinSa, Ya nuna muku walkiya a
kan tsoro da cfammani, kuma Ya
dinga saukar da ruwa daga sama,
sa'an nan Ya rayar da kasa game da
shi a bayan mutuwarta. Lalle a
cikin wannan akwai ayoyi ga muta-
ne masu hankaltawa.
25. Kuma akwai daga ayoyin-
sa, tsayuwar sama da kasa bisa
umurninSa, sa'an nan idan Ya kira
ku, kira cfaya, daga kasa, sai ga ku
kuna fita.
26. Kuma wanda ke cikin sam-
mai da kasa Nasa ne, Shi kacfai.
Dukansu masu tawali'u ne a gare
Shi.
27. Kuma Shine Wanda Yafara
halitta, sa'an nan Ya sake ta, kuma
sakewarta ta fi sauki a gare Shi.
Kuma Yana da misali wanda ya fi
's \*'>s
£ A > , t rr" cfy <, » f ' t '
> x,^ x >x>> >x> ,*, ,^.> , 9 , fasy
(1) Akwai dangantaka a tsakanin halittar namiji da mace daga yum6u da kuma
natsuwar da suke samu daga junada soyayya da rahamar da ke a ciki.
616
30 — Suratur Rum
(i$l|gi-r.
cfaukaka ji cikin sammai da kasa,
kuma Shi ne Mabuwayi, Mai jin
kai.
28. Ya buga muku wani misali
daga kanku. K6 kuna da abokan
tarewa, daga cikin bayin da hanna-
yenku na dama suka mallaka, a
cikin arzikinku, watau ku zama
daidai a ciki, kuna tsoron su kamar
tsoronku ga kanku? Haka dai Mu-
ke bayyana ayoyi, daki-daki, ga
mutane masu hankaltawa.
29. A'aha ! Wadanda suka yi za-
lunci sun bi son zuciyoyinsu, ba tare
da wani ilmi ba. To, wane ne zai
shiryar da wanda Allah Ya batar,
kuma ba su da wacfansu matai-
maka?
30. Saboda haka, ka tsayar da
fuskarka ga addini, (1) kana mai
karkata zuwa ga gaskiya, halittar
Allah da Ya halitta mutane a kanta.
Babu musanyawa ga halittar Allah.
Wannan shl ne addini madaidaici,
kuma amma mafi yawan mutane ba
su sani ba.
31. Kuna masu mai da aPamari
gare Shi, kuma ku blShi da takawa,
kuma ku tsayar da salla, kuma
kada ku kasance daga mushi-
rikai. (2)
&i^2^5*>
( *rln*
*>'.*
$1 <L> $juo^ lii cJs$\
*Jb \aj Ato\ &—*>\ O 4 ^ J^ ( j^
^C&r^o*.
bp^yo-X^
' >1 < til > '\'* y M' A\' > rAi
(1) Yin addini dabl'a ce wadda Allah Ya halitta mutum a kanta. Idan mutum ya bi
abin da Allah Ya umurce shi da yikobari, to, ya yi addinin gaskiya, idan kuwa bai yi haka
ba, ya zama mushiriki game da wanda yake karbar umurni daga gare shi.
_ (2) Ya fassara mushirikai da aya ta 32. Wannan ya nuna ta yi nuni ga hana dukan
darikun Sufaye domin suna rarraba mutane kungiya-kungiya, kuma kowa na ganin abin
da yake yi ko kuma wanda yake bi ya fi na wani. Kuma wanda ke cikin wata kungiya ba zai
iya haduwa da wata ba a lokacin wurudinsu, a bayan abubuwan da suke kunsawa a cikin
ayyukansu na bidi'o'i da akidodi da suka saba wa Musulunci.
617
30 — Suratur Rum
^M\m-r-
32. Watau wacfanda suka rarra-
be addininsu, kuma suka kasance
kungiya-kungiya, kowace kungiya
tana mai farin ciki da abin da ke a
gare ta kawai.
33. Kuma idan cuta ta shafi mu-
tane, sai su kirayi Ubangijinsu, suna
masu mai da al'amari gare Shi,
sa'an nan idan Ya dandana musu
wata rahama daga gare Shi, sai ga
wani 6angare daga gare su suna
shirki da Ubangijinsu.
34. Domin su kafirta da abin da
Muka ba su. To, ku ji dacfi kacfan,
sa'an nan za ku sani.
35. Ko Mun saukar da wani dali-
li a gare su? Shi kuwa yana magana
da abin da suka kasance suna shir-
kin da shi?
36. Kuma idan Muka cfancfana
wa mutane wata rahama, sai su yi
farin ciki da ita, kuma idan cuta ta
same su, saboda* abin da hanna-
yensu suka gabatar, sai ga su suna
yanke kauna.
37. Shin, kuma ba su gani ba
cewa Allah na shimficfa arziki ga
wanda Yake so, kuma Yana kunta-
tawa? Lalle a cikin wancan^akwai
ayoyi ga mutane masu yin Tmani.
38. Saboda haka, ka bai wa
zumu hakkinsa, da miskinai, da dan
hanya. Wannan shi ne alheri ga
wacfanda ke nufin yardar Allah,
kuma wadancan su ne masu samun
babban rabo.
39. Kuma abin da kuka bayar na
riba domin ya karu a cikin dukiyar
mutane to, ba zai karu ba, a wurin
^y °> ' y »>^ ° *'' ^y ^*y
H0 &jLr~*j4ryv Lj
£ y . *s *■*' y ;/ **s y y *s y*)>** y //
dj>t^\p-*>
i^5ti^GU^3)j^vi t>Jui>^tl^
618
30 — Suratur Rum
fc^JIM-r-
Allah. Kuma abin da kuka bayar na
zakka, kuna nufin yardar Allah, to,
(masu yin haka) wadancan su ne
masu ninkawa (ga dukiyarsu).
40. Allah ne Wanda Ya halitta
ku, sa'an nan Ya arzuta ku, sa'an
nan Ya matar da ku, sa'an nan Ya
rayar da ku. Ashe, daga cikin abu-
buwan shirkinku akwai wanda ke
aikata wani abu daga wadannan
abubuwa? Tsarki ya tabbata ga
Allah, kuma Ya daukaka bisa ga
abin da suke yi na shirki.
41. TJarna ta bayyana a cikin
kasa da teku, saboda abin da han-
nayen mutane suka aikata. Domin
Allah Ya dandana musu sashin abin
da suka aikata, dammaninsu za su
komo.
42. Ka ce, "Ku tafi a cikin kasa,
sa'an nan ku dubi yadda akibar
wadanda suka kasance a gabaninku
ta kasance. Mafi yawansu sun ka-
sance masu yin shirki."
43. Saboda haka, ka tsayar da
fuskarka ga addini madaidaici a
gabanin wani yini ya zo, babu ma-
kawa gare Shi daga Allah, a ranar
nan mutane suna tsagewa (su rabu
biyu).
44. Wanda ya kafirta, to, kafir-
cinsa na kansa, kuma wanda ya
aikata aikin kwarai, to, saboda kan-
su suke yin shimficfa.
45. Domin Ya saka wa wadanda
suka yi imani, kuma suka aikata
ayyukan kwarai, daga falalarSa.
Lalle Allah ba Ya son kafirai.
y y *s ^ . XL ' * *S\'
(JUl1*J 1^-^cJij^l jjUjJ]^
"" 9S *
619
30 — Suratur Rum
^lj££-r-
46. Kuma akwai daga ayoyinSa,
ya aika iskoki masu bayar da bu-
shara kuma domin Ya cfancfana
muku daga rahamarSa, kuma do-
min jiragen ruwa su gudana da
umurninSa, kuma domin ku nema
daga falalarSa, fatanku za ku gode.
47. Kuma lalle Mun aiki wacfan-
su Manzanni a gabaninka, zuwa ga
mutanensu, sai suka je musu da
hujjoji, bayyanannu, sa'an nan
Muka azabtar da wadanda suka yi
laifi, kuma ya kasance tabbatacce,
taimakon muminai wajibi ne a Kan-
mu.
48. Allah ne Wanda ke aika isko-
ki, sai su motsar da girgije, sa'an
nan Ya shimficfa shi a cikin sama,
yadda Yake so, kuma Ya sanya shi
wani 6a66ake, sa'an nan ka ga ruwa
na fita daga tsakaninsa. Sa'an nan
idan Allah Ya sami wadanda Ya so
daga bayinSa, sai ga su suna busha-
ra da shi.
49. Kuma ko da sun kasance a
gabanin a saukar da shi a kansu,
kusa-kusa, suna bakin ciki har ba su
iya magana.
50. Sai ka dubi alamomin raha-
mar Allah yadda Yake rayar da
kasa a bayan mutuwarta. Lalle
wannan (Mai wannan aiki), tabbas,
Mai rayar da halitta ne, kuma Shi
Mai ikon yi ne a kan kome.
57. Kuma lalle idan Mun aika
wata iska, suka ganta fatsifatsi, lalle
za su yini a bayansa suna kafirta.
52. Saboda haka, kai, ba ka jiyar
da matattu kira, kuma ba ka jiyar
>>>
i&>ii
ij^aioiiy^iJ
$0^jSj^lS£
(Sj\3 UlS ^aU^j *U^eJa-S ^L^J^(j
fr^ ' > J" *' 9> \'\ \' *
*\*
EP^aJuJ
' »* ?' »>
&o
*u>
iLp2\J^\^ t .S^jd^\^J^^^
620
30 — Suratur Rum
£i£JIM-r-
da kurame kira idan sun juya baya
suna gudu.
53. Kuma ba ka zamo mai shi-
ryar da makafi ba daga Batarsu, ba
ka jiyarwa face wanda ke yin imani
da ayoyinMu, watau su ne masu
mika wuya, su sallama.
54. Allah ne Ya halitta ku daga
rauni, (1) sa'an nan Ya sanya wani
karfi a bayan wani rauni, sa'an nan
Ya sanya wani rauni da furfura a
bayan wani karfi, Allah na halitta
abin da Ya so, kuma Shi ne Mai
ilmi, Mai ikon yi.
55. Kuma a ranar da SaV 2) ke
tsayuwa, masu laifi na rantsu wa : ba
su zauna a cikin kabari ba face sa'a
guda. Kamar haka suka kasance
ana karkatar da su.
56. Kuma wacfanda aka bai wa
ilmi da Imani suka ce, "Lalle, haki-
ka, kun zauna a cikin Littafin Allah,
har zuwa ranar tayarwa, to, kuma
wannan ita ce ranar tayarwar,
kuma amma ku kun kasance (3) ba
ku sani ba."
57. To, a ranar da uzurin wacfan-
da suka yi zalunci ba ya amfaninsu,
kuma ba a neman yardarsu.
58. Kuma lalle, tabbas, Mun
buga kowane irin misali ga mutane
a cikin wannan Alkur'ani, kuma
*> *
(1) Raunin farko, shine maniyyi, na biyu j arm taka da karfm kuruciya, rauni na uku,
shT ne tsufa bayan karfin hankalin kamala ta dattako.
(2) Sa'a ta farko Ranar Kiyama, ta biyu dan lokaci, watau dan lokacin da suka sami
hutun azabar kabari a tsakanin busar farko da ta biyu. Akwai munasabar karyarsu ta
duniya da ta Lahira. Akwai munasabar dangantakar lafzin kalmomi.
(3) Rashin aiki da littafin Allah a duniya yakan sanya dimewa a ranar Lahira.
621
31 — Suratu Lu£man
SJ2yPi^-n
lalle idan ka je musu da kowace aya,
lalle, wadanda suka kafirta za su ce,
"Ku ba kome kuke ba face masu
6arna."
59. Kamar haka Allah Yake sha-
fe haske a kan zukatan wacfanda ba
su sani ba.
60. Saboda haka ka yi hakuri,
lalle wa'adin Allah gaskiya ne,
kuma kada wadanda ba su da yaki-
ni su sassabce maka hankali.
Tana karantar da yadda ake tarbiyya da renon yara, a cikin
harshe mai sauki.
Z>a sSwafl Allah, Mai rahama, Mai jin RaL
1. A. L. M.
2. Wadancan ayoyin Littafin ne
bayyananne.
3. Shiriya da rahama ne ga masu
tsarkake niyya.
4. Wadanda ke tsai da salla,
kuma suna bayar da zakka, kuma
su, suna yin imanin yakini ga La-
hira.
5. Wadannan suna a kan shiriya
ta daga Ubangijinsu, kuma wadan-
nan su ne masu babban rabo.
622
31 — Suratu Luicman
SiS^i^- - n
6. Kuma akwai daga cikin muta-
ne wanda ke sayen tatsuniyoyi (1)
domin ya Batar da mutane daga
hanyar Allah, ba da wani ilmi ba,
kuma ya ri£e ta abin izgili ! Wadan-
can suna da wata azaba mai
wulakantawa.
7. Kuma idan an karanta
ayoyinMu a gare shi, sai ya juya
baya, yana mai girman kai, kamar
dai bai saurare su ba, kamar dai
akwai wani danni a kan kunnu-
wansa! To, ka yi masa bushara da
azaba mai radadi.
8. Lalle, wadanda suka yi imani,
kuma suka aikata ayyukan kwarai,
suna da gidajen Aljannar ni'ima.
9. Suna dawwama a cikinsu, Al-
lah Ya yi alkawarin, Ya tabbatar da
shi. Kuma ShT ne Mabuwayi, Mai
hikima.
10. (Allah) Ya halitta sammai,
ba da ginshiki wanda kuke gani ba,
kuma Ya jefa duwatsu masu kafe-
wa a cikin Jcasa, domin kada ta
karkata da ku, kuma Ya watsa
daga kowanc irin dabba a cikinta,
kuma Mun saukar da ruwa daga
sama, sa'an nan Muka tsirar a ci-
kinta, daga kowane nau'i biyu
(nami ; i da mace) mai ban sha'awa.
11. Wannan shi ne halittar Al-
lah. To, ku nuna mini, "Mene ne
watfanan da ba Shi ba suka halitta?
A 'a, azzalumai suna a cikin Bata
bayyananna."
' At ^'S S\' • *\' '*i*Y \' '
■i i' E . >
Jp CfJ^ J^(^o^iilaJ\ ^$jj*Oi
(1) Tatsuniyoyi suna shagaltarwa daga ilmi mai sanya sanin Allah. Allah Ya hana a yi
tarbiyyar yara game da tatsuniya mai dauke hankalinsu daga ibada. Littattafan makaranta
na zamani da jandu duka tatsuniyoyi ne, sai abin da ya dace da Sunna.
623
31 — Suratu Luicman
12. Kuma lalle, haklka, Mun bai
wa Lukman hikima. (Muka ce
masa) Ka gode wa Allah, kuma
wanda ya gode, to, yana godewa ne
domin kansa kawai, kuma wanda
ya kafirta, to, lalle, Allah Mawada-
ci ne, Godadde.
13. Kuma a lokacin da Lukman
ya ce wa dansa, alhali kuwa yana yi
masa wa'azi, "Ya karamin dana!
Kada ka yi shirki game da Allah.
Lalle shirki wani zalunci ne mai
girma."
14. Kuma Mun yi wasiyya ga
mutum game da mahaifansa biyu;
uwarsa ta dauke shi a cikin rauni a
kan wani rauni, kuma yayensa a
cikin shekaru biyu (Muka ce masa),
"Ka gode Mini da kuma mahai-
fanka biyu. Makoma zuwa gare Ni
kawai take.
15. "Kuma idan mahaifanka
suka tsananta (1) maka ga ka yi
shirki game da Ni, ga abin da ba ka
da ilmi gare shi, to, kada ka yi musu
da'a. Kuma ka abuce su a cikin
duniya gwargwadon sharT'a, kuma
ka bi hanyar wanda ya mayar da
al'amari zuwa gare Ni, sa'an nan
zuwa gare Ni makomarku take,
sa'an nan In ba ku labari game da
abin da kuka kasance kuna aika-
tawa."
16. "Ya karamin dana ! Lalle ita,
idan gwargwadon kwayar komayya
ce ta kasance, to, ta kasance a cikin
wani falalen dutse, ko a cikin sam-
ZJ&xti JijM^J^
(1) A bayan haician Allah sai haician uwaye. Saboda haka ba za a yi cfa'a ga uwaye ba
ga abin da ya saba wa Allah.
624
31 — Suratu Lukman
££!#&£ -n
mai, ko a cikin kasa, Allah zai kawo
ta. Lalle Allah Mai tausasawa ne,
Masani.
17. "Ya karamin dana! Ka tsai
da salla, kuma ka yi umurni da
abin da aka sani, kuma ka yi hani
daga abin da ba a sani ba, kuma ka
yi hakuri a kan abin da ya same ka.
Lalle, wancan yana daga muhim-
man aFamura.
18. "Kada ka karkatar da
kundukukinka (1) ga mutane, kada
ka yi tafiya a cikin kasa kana mai
nuna fadin rai. Lalle, Allah ba Ya
son dukan mai takama, mai alfa-
hari.
19. "Kuma ka tsakaita a tafiyar-
ka, kuma ka runtse ga sautinka.
Lalle, mafi munin sautuka, hakika,
shl ne sautin jakuna. (2) "
20. Ashe, ba ku gani ba, cewa
Allah Ya hore muku abin da ke a
cikin sammai da abin da ke a cikin
kasa, kuma Ya zuba ni'imominSa a
kanku, bayyanannu da Boyayyu?
Kuma akwai daga mutane wanda
ke yin jidali ga al'amarin Allah, ba
da wani ilmi ba, kuma ba da wata
shiriya ba, kuma ba da wani littafi
mai haskakawa ba.
21. Kuma idan aka ce musu,
"Ku bi abin da Allah ya saukar,"
sai su ce, "A'a, muna bin abin da
muka sami ubanninmu a kansa."
Shin, ko da Shaidan na kiran su ne
zuwa ga azabar sa'ir,
» > »?/ <
I'tf" x ^t i^' 1 >" Y'f'X'
(nj _^^ty\J^^^^
(1) Karkata kundukuki ga mutane, alamar wulakanta su ne.
(2) A nan ne iyakar wasiyyar Lukman ga dansa. Sa'an nan kuma Allah Ya ci gaba da
bayanin yadda ake tarbiyyar mutane.
625
31 — Suratu Lukman
&&$$& - r\
22. Kuma wanda ya mlka fus-
karsa zuwa ga Allah, alhali kuma
yana mai kyautatawa, to, lalle ya yi
riko ga igiya amintacciya. Kuma
zuwa ga Allah akibar al'amura
take.
23. Kuma wanda ya kafirta, to,
kada kafircinsa ya bakanta maka
rai, zuwa gare Mu makomarsu take,
sa'an nan Mu ba su labari game da
abin da suka aikata. Lalle Allah,
Masani ne ga abin da ke a cikin
kiraza.
24. Muna jTshe su dacfi kacfan,
sa'an nan Mu tTlasta su ga shiga
zuwa azaba kakkaura.
25. Kuma lalle, idan ka tambaye
su, "Wane ne ya halitta sammai da
kasa?" Lalle, za su ce, "Allah ne."
Ka ce, ^'Godiya ta tabbata ga
Allah." A'a, mafi yawansu, ba su
sani ba.
26. Abin da yake a cikin sammai
da kasa duka na^ Allah kawai ne.
Lalle, Allah Shi ne Mawadaci,
Godadde.
27. Kuma da dai abin da ke a
cikin kasa duka, na itace, ya zama
alkalumma, kuma teku tana yi
masa tawada, a bayansa da wacfan-
su tekuna bakwai, kalmomin Allah
ba za su kare ba. (1) Lalle, Allah
Mabuwayi ne, Mai hikima.
'*\ >"> ' '* T6
5^ > A f> ^*f^>
(1) Wannan bayani ne ga yawan ilmin Allah, watau yana nuna wa mutane cewa su yi
aiki da ilmin da Ya ba su, mai amfani zuwa gare su, kada su wuce shi zuwa neman wani ilmi
daga wani abu, su bar Allah, su halaka a kan wani ilmi da bai umurce su da su yi aiki da shi
ba. Ilmin da Ya ba su a cikin Alkur'ani shi ne shan'a watau hanya mai kai su ga Aljanna.
Sauran hanyoyi bata ne.
626
31 — Suratu Luieman
&u±$%& - n
28. Halittarku ba ta zama ba,
kuma tayar da ku bai zama ba, face
kamar numfashi guda. Lalle, Allah
Mai jT ne, Mai gani.
29. Ashe, ba ku ga, lalle, Allah
Yana shigar da dare a cikin rana ba,
kuma Yana shigar da rana a cikin
dare, kuma Ya hore rana da wata,
kowane yana gudana zuwa ga ajali
ambatacce, kuma lalle Allah Ma-
sani ne ga abin da kuke aikatawa?
30. Wannan fa, domin Allah Shi
ne Gaskiya, kuma abin da suke kira
wanda ba Shi ba, shi ne karya,
kuma lalle, Allah Shi ne Macfau-
kaki, Mai girma.
31. Ashe, ba ka ga lalle jirgin
ruwa na gudana ba a ciki teku da
ni'imar Allah, domin Ya nuna
muku daga ayoyinSa? Lalle a cikin
wancan akwai ayoyi ga dukan mai
hakuri, mai godiya.
32. Kuma idan taguwar ruwa,
kamar duwatsu, ta rufe su, sai su
kira Allah, suna tsarkakewar addini
a gare Shi. To, a lokacin da Ya tsirar
da su zuwa ga tudu, sai daga cikinsu
akwai mai takaitawa, kuma babu
mai musun ayoyinMu face dukan
mayaudari mai yawan kafirci.
33. Ya ku mutane ! Ku bauta wa
Ubangijinku da takawa, kuma ku ji
tsoron wani yini, ranar da wani
mahaifi ba ya saka wa abin haifu-
warsa da kome kuma wani abin
haifuwa ba ya saka wa mahaifinsa
da kome. Lalle wa'adin Allah gas-
kiya ne. Saboda haka, kada wata
rayuwa ta kusa ta rude ku, kuma
» 'Zt *"'. "\{ <• •-\^.S?C *\{>\
's> M»
627
32 — Suratus Sajda
wmm>-r<
kada marudin (1) nan ya rude ku
game da Allah.
34. Lalle, Allah a wurinSa kawai
sanin Sa'a yake, kuma Yana saukar
da girgije, kuma Yana sanin abin da
yake a cikin mahaiffannai, kuma
wani rai bai san abin da yake aika-
tawa a gobe ba, kuma wani rai bai
san a wace kasa yake mutuwa ba.
Lalle Allah Masani ne, Mai kidid-
didigewa.
_ Tana karantar da wa'azi da Al£ur'ani gaskiya ne, mabiyinsa
shT ne mai riba, wanda ya saBa masa, shi ne mai hasara.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
L A. L. M.
2. Saukar da Littafin, babu
shakka a gare shi, daga Ubangijin
talikai yake.
3. Ko suna cewaJMuhammadu
ne) ya kirkira shi? A'a, shi ne gas-
kiya daga Ubangijinka, domin ka yi
gargadi ga mutane wadanda wani
mai gargadi bai je musu ba a gaba-
ninka, fatan za su shiryu.
0^'
(1) Shaicfan.
628
32 — Suratus Sajda
l^MM-n
4. Allah ne Wanda Ya halitta
sammai da kasa da abin da yake a
tsakaninsu a cikin kwanuka shida,
sa'an nan Ya daidaita a kan Al'ars-
hi. Ba ku da, baicin Shi, wani maji-
6inci, kuma babu wani maceci.
Shin, ba za ku yi tunani ba?
5. Yana shirya al'amari daga
sama zuwa ga kasa, sa'an nan ya
taka zuwa gare Shi a cikin yini,
wanda gwargwadonsa shekaru
dubu ne ga abin da kuke lissafawa.
6. Wannan ShT ne Masanin fake
da bayyane, Mabuwayi, Mai jin kai.
7. Wanda Ya kyautata kome,
wanda Ya halitta shi. Shi ne kuma
Ya fara halittar mutum daga laka.
8. Sa'an nan Ya sanya cfiyansa
daga wani asali na wani ruwa
wulakantacce.
9. Sa'an nan Ya daidaita shi,
kuma Ya hura a cikinsa, daga ru-
hinSa, kuma Ya sanya muku ji, da
ganunuwa da zukata. Godiyarku
kacfan ce kwarai.
10. Kuma suka ce, "Shin, idan
mun 6ace a cikin kasa, shin, lalle
mu, tabbas ne, muna zama a cikin
wata halitta sabuwa?" A'a, su game
da gamuwa da Ubangijinsu kafirai
ne.
11. Ka ce, "Mala'ikin mutuwa
wanda aka wakkala a gare ku, shi
ne ke karBar rayukanku. (1) Sa'an
nan zuwa ga Ubangijinku ake
mayar da ku."
^I^>>^UUl3i^^^
0X^^\Ij^\j^\^^>
>Ax> / s / s ^ % # ''/.'> '£-"' *-*
^ < > f* *' T-t * X
*A^ x, vi *>* 9'"** f y/"* "' *> .
(1) Watau ba ku ke mutuwa da kanku ba, sai an matar da ku, saboda haka tayarwar
ma ba ku za ku yi ta da kanku ba, balle ku yi musu.
629
32 — Suratus Sajda
JMJ&-tT
12. Kuma da ka gani a lokacin
da masu laifi suke masu sunkuyar
da kawunansu a wurin Ubangi-
jinsu, "Ya Ubangijinmu ! Mun gani,
kuma mun ji, to, Ka mayar da mu,
mu aikata^aiki na kwarai. Lalle mu
masu yaklni ne."
13. Kuma da Mun so da Mun
bai wa kowane rai shiriyarsa, to,
amma magana ta tabbata daga gare
Ni! Lalle ne Ina cika Jahannama
daga aljannu da mutane gaba daya.
14. To, ku cfancfana, saboda abin
da kuka manta na haduwa da ra-
narku wannan. Lalle Mu ma Mun
manta da ku, kuma ku dandani
azabar dawwama saboda abin da
kuka kasance kuna aikatawa.
75. Wacfanda ke imani da
ayoyinMu kawai, su ne wacfanda
idan aka karanta musu ayoyinMu,
sai su facfi suna masu sujada, kuma
su yi tasblhi game da gode wa
Ubangijinsu, alhali kuwa su ba su
yin girman kai.
16. Sasanninsu na nTsanta daga
wuraren kwanciya, suna kiran
Ubangijinsu bisa ga tsoro da dam-
mani, kuma suna ciryawa daga abin
da Muka arzuta su.
1 7. Saboda haka wani rai bai san
abin da aka Boye musu ba, na sa-
nyin idanu, domin sakamako ga
abin da suka kasance suna aika-
tawa.
18. Shin, wanda ya zama mumi-
ni yana kamar wanda ya zama fasi-
ki? Ba za su yi daidai ba.
(p \x£==>\ \\ti$^Xk &£i \\
630
32 — Suratus Sajda
JMi&-rf
19. Amma wacfanda suka yilma-
ni, kuma suka aikata ayyukan kwa-
rai, to, suna da gidajen Aljannar
makoma, a kan liyafa saboda abin
da suka kasance suna aikatawa.
20. Kuma wacfanda suka yi fasi-
kanci, to, makomarsu ita ce wuta,
ko da yaushe suka yi nufin su fita
daga gare ta, sai a mayar da su a
cikinta, kuma a ce musu,"Ku dan-
dana azabar wuta, wadda kuka ka-
sance kuna karyatawa game da
ita."
21. Kuma lalle Muna rfanrfana
musu daga azaba, mafi kaskanci,
kafin a kai ga azaba mafi girma,
domin fa tan za su komo.
22. Kuma wane ne ya fi zalunci
bisa ga wanda aka tunatar da
ayoyin Ubangijinsa, sa'an na ya
bijire daga barinsu? Lalle Mu,
Masu yin azabar ramuwa ne ga
masu laifi.
23. Kuma lalle haklka, Mun bai
wa Musa Littafi, (1) saboda haka
kada ka kasance a cikin shakka
daga haduwa da shi. Kuma Mun
sanya shi ya zama shiriya ga Bani
Isra'ila.
24. Kuma Mun sanya shugaban-
ni daga cikinsu, suna shiryarwa da
umurninMu, a lokacin da suka yi
hakuri, kuma sun kasance suna yin
yaklni da ayoyinMu.
3 s^jj;msJ^j^(J^\j\^\^j\jp
' * ^NM ^'h ^* *'< ■*?'
(1) Ba Alkur'ani ne farkon Littafin sama ba, kuma ba Muhammadu ne farkon
Manzannin Allah ba, Mun bai wa Musa Attaura, mutanensa sun yi aiki da ita, sun
cfaukaka kamar yadda ake neman Musulmi su yi aiki da Alkur'ani su cfaukaka.
631
32 — Suratus Sajda
%&$%&- n
25. Lalle Ubangijinka Shi ne zai
rarrabe a tsakaninsu, a Ranar Ki-
yama a cikin abin da suka kasance
suna saBa wa juna a cikinsa.
26. Shin, ba ya shiryar da su
cewa da yawa Muka halakar, a
gabaninsu, daga arummomi, suna
tafiya a cikin masaukansu? (1) Lalle
a cikinjvancan akwai ayoyi. Shin,
ba su jT ne?
27. Shin, kuma ba su gani ba
cewa lalle Mu, Muna kora ruwa
zuwa ga kasa kekasasshiya, sa'an
nan Mu fltar, game da shi, wata
shuka wadda dabbobinsu da su
kansu ke ci daga gare ta? Ashe fa,
ba su gani ba?
28. Kuma suna cewa, "Yaushe
wannan hukunci yake aukuwa,
idan kun kasance masu gaskiya?"
29.^ Ka ce, "Ranar hukuncin
nan, Tmanin wacfanda suka kafirta
ba zai amfane su ba (a cikinta),
kuma ba za a yi musu jinkiri ba."
30. Saboda haka, ka kau da kai
daga barinsu, kuma ka yi jira lalle,
su ma masu jira ne.
.. y 'Js"?'*' »^'*'^t »"•> <* x * .
»> >.
^r^\}jj^U^^y g^j^i J 5
/ >
-itH?
(1) Kuraishawa suna tafiya a cikin gidajen al'ummomin da suka halaka, suna ganin
abin da ya auku gare su.
632
33 — Suratul Ahzab
m$m>-rr
Tana karantar da yadda ake kashe miyagun al'adun Jahiliyya
da ba su dace da Musulunci ba, da musanyar wadanda suka dace da
shari'a.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ya kai Annabi ! Ka bi Allah da
takawa, kuma kada ka yi da'a ga
kafirai da munafukai. Lalle, Allah
Ya kasance Mai ilmi, Mai hikima.
2. Kuma ka bi abin da aka yi
wahayi da shi zuwa gare ka daga
Ubangijinka. Lalle, Allah Ya ka-
sance Mai labartawa ga abin da
kuke aikatawa.
3. Ka dogara ga Allah. ^Kuma
Allah Ya isa Ya zama WakTli.
4. Allah bai sanya zuciya biyu ba
ga wani namiji a cikinsa, kuma bai
sanya matanku wadanda kuke yin
zihari daga gare su, su zama uwa-
yenku ba, kuma bai sanya diyan
hankakarku su zama diyanku ba.
Wannan abu naku, maganarku ce
da bakunanku, alhali kuwa Allah
na fadar gaskiya, kuma Shi ne ke
shiryarwa ga hanyar kwarai.
5. Ku kira su ga ubanninsu, shi
ne mafi adalci a wurin Allah. To,
idan ba ku san ubanninsu ba, to,
'yan'uwanku ga addini da dimajo-
y s s , " E . -»'
x>'\>*
es^ \^Vy> * T'4 t »> >*r
633
33 — Suratul Ahzab
^W-yt
jinku. Kuma babu laifi a gare ku ga
abin da kuka yi kuskure da shi,
kuma amma (akwai laifi) ga abin da
zukatanku suka ganganta, kuma
Allah Ya kasance Mai gafara, Mai
jin kai.
6. Annabi ne mafi cancanta ( x } ga
muminai bisa ga su kansu, kuma
matansa uwayensu ne. Kuma
ma'abuta zumunta wacfansunsu
sun fi wadansu a cikin Littafin Al-
lah bisa ga muminai da Muhajirai,
face fa idan kun aikata wani alheri
zuwa ga majibintanku. Wancan ya
kasance a cikin Littafi, rubutacce.
7. Kuma a lokacin da Muka riki
alkawarin Annabawa daga gare su,
kuma daga gare ka, kuma daga
Nuhu da Ibrahim, da Musa, da
kuma Tsa dan Maryama, kuma
Muka riki wani alkawari mai kauri
daga gare su.
8. Domin Ya tambayi masu gas-
kiya a kan gaskiyarsu, kuma Ya yi
tattalin wata azaba mai radacfi ga
kafirai.
9. Ya ku wadanda suka yi imani !
Ku tuna ni'imar Allah a kanku a
lokacin da wadansu rundunoni
suka zo muku, sai Muka aika wata
iska a kansu da wadansu rundunoni
wadanda ba ku gani ba. Kuma
Allah Ya kasance Mai gani ga abin
da kuke aikatawa.
10. A lokacin da suka zo muku
daga samanku da kuma kasa daga
»'**'£ >'*
j^L^v*£^=Jf j^S^lL=
(1) Idan son mumini ya saba wa facfar Annabi, sai ya bar son ransa ya koma wa facfar
Annabi.
634
33 - Suratul Ahzab
W$&-rr
gare ku, kuma a lokacin da gannai
suka karkata, kuma zukata suka
kai ga makosai, kuma kuka yi zaton
zace-zace, game da Allah.
11. A can aka jarrabi muminai,
kuma aka yi girgiza, girgiza mai
tsanani.
12. Kuma a lokacin da munafu-
kai da wacfanda akwai cuta a cikin
zukatansu ke cewa, "Allah da Man-
zonSa, ba su yi mana wa'adin kome
ba, face rucfi."
13. Kuma a lokacin da watakun-
giya daga gare su, ta ce, "Ya muta-
nen Yasriba ! (1) Ba ku da wani mat-
sayi, saboda haka ku koma." Kuma
wata kungiya daga gare su na ne-
man izni ga Annabi suna cewa,
"Lalle gidajenmu kuranye suke,"
alhali kuwa ba kuranye suke ba, ba
su da nufin kome face gudu.
14. Kuma da an shige ta (Madi-
na) a kansu, daga sasanninta, sa'an
nan aka tambaye su fitina (kafirci),
lalle, da sun je mata, kuma da ba su
zauna a cikinta (Madina) ba face
kacfan.
75. Kuma lalle, hakika, sun ka-
sance suna yi wa Allah alkawari, a
gabanin wannan: ba za su juya
domin gudu ba, kuma alkawarin
Allah ya kasance abin tambaya.
16. Ka ce, "Gudun nan, ba zai
amfane ku ba daga mutuwa ko kisa.
Kuma har in kun gudu, ba za a jTshe
ku dacfi ba face kacfan."
<^ '.Tu-t >'A\' \'\'A 9 * *\'*\. y *\'
y^Vj3c^3 ]}X^\ybJjij
(1) Sun koma ga sunan MadTna na zamanin Jahiliyya suna izgili da cewa ba su yarda
da sabon sunan ba na MadTna, face Yasriba, svinanta da suka sani na asali.
635
33 — Suratul Ahzab
m^\m-rr
17. Ka ce, ' 'Wane ne wanda yake
tsare ku daga Allah, idan Ya yi
nufin wata cuta game da ku?"
Kuma ba za su samar wa kansu
wani maji&inci ba, banda Allah,
kuma ba za su samar wa kansu wani
mataimaki ba.
18. Lalle, Allah Ya san masu
hana mutane fita daga cikinku, da
masu cewa ga 'yan'uwansu, "Ku zo
nan a wurinmu." Kuma ba za su
shiga yaki ba face kacfan.
19. Suna masu rowa gare ku,
sa'an nan idan tsoro ya zo, sai ka
gan su suna kallo zuwa gare ka,
idanunsu suna kewaya, kamar wan-
da ake rufe hankalinsa saboda mu-
tuwa. Sa'an nan idan tsoron ya tafi,
sai su yi muku miyagun maganganu
da harussa masu kaifi, suna masu
rowa a kan dukiya. Wacfannan, ba
su yi imani ba, saboda haka Allah
Ya 6ata ayyukansu. Kuma wannan
ya kasance mai sauki ga Allah.
20. Suna zaton kungiyoyin kafi-
rai ba su tafi ba. Kuma idan kungi-
yoyin kafirai sun zo, suna gurin da
dai sun zama a karkara a cikin
kauyawa, suna tambayar laba-
ranku. Kuma ko da sun kasance a
cikinku, ba za su yi yaki ba, face
kacfan.
21. Lalle, abin koyi mai kyau ya
kasance gare ku daga Manzon Al-
lah, ga wanda ya kasance yana
fatan rahamar Allah da Ranar La-
hira, kuma ya ambaci Allah da
yawa.
22. Kuma a lokacin da muminai
suka ga kungiyoyin kafirai, sai suka
^ ,j^
>u*vrr -t-.rt>-
Cyo, ^yS^-^>- \yZu\ 4ji\ oyj ij jpvJ cJoJJu
<4sa> i^ &*','&■"' $7f '■"■!{' sill >
\fr-y.
^ZjC\%\j^\pi\spp\mj
636
33 — Suratul Ahzab
•#eM&-rr
ce, "Wannan ne abin da Allah da
ManzonSa suka yi mana wa'adi,
Allah da ManzonSa sunyi gaskiya."
Kuma wannan bai kara musu kome
ba face Imani da sallamawa.
23. Daga muminai akwai wa-
cfansu mazaje da suka gaskata abin
da suka yi wa Allah alkwari a kan-
sa, sa'an nan a cikinsu, akwai wan-
da ya biya bukatarsa, (1) kuma daga
cikinsu akwai wanda ke jira. Kuma
ba su musanya ba, musanyawa.
24. Domin Allah Ya saka wa
masu gaskiya da gakiyarsu, kuma
Ya azabtar da munafukai idan Ya
so, ko Ya kar6i tuba a kansu. Lalle,
Allah Ya kasance Mai gafara, Mai
jin kai.
25. Kuma Allah Ya mayar (2) da
wadanda suka kafirta da fushinsu,
ba su sami wani alheri ba. Allah Ya
isar wa muminai daga barin yaki.
Kuma Allah Ya kasance Mai karfi,
Mabuwayi.
26. Kuma Ya saukar (3) da wa-
dannan da suka taimake su daga
mazowa Littafi, daga biranensu,
kuma Ya jefa tsoro a cikin zuka-
tansu: wata kungiya kuna kashewa,
kuma kuna kama wata kungiyar.
27. Kuma Ya gadar da ku gona-
kinsu da gidajensu da dukiyoyinsu,
*Jb }\j\jtj>Aj*>l)J A^\(JjJ^j >Ay*JJ 4$\
^JU**jj
v$j
( 1 ) Biyan bukatarsa watau ya mutu, cikinsu akwai wanda yake jirar mutuwa.
(2) Allah Ya kore kungiyoyin kafirai da iskarSa mai tsananin sanyi, watau iskar Saba.
(3) Sa'an nan kuma Musulmi suka tsare Yahudu, Bani Kuraiza, a cikin birninsu, har
suka sallama kansu ga hukuncin Sa'ad bn Mu'azu wanda ya hukunta a kashe wanda ya
balaga daga cikinsu, kuma a bautar da mata da yara. Aka yi musu hakanan, aka zartar da
hukuncinsa a kansu.
637
33 — Suratul Ahzab
W&-rr
da wata Rasa wadda ba ku taba
takarta ba. Kuma Allah ya kasance
Mai ikon yi ne a kan kome.
28. Ya kai Annabi! Ka ce wa
matanka, "Idan kun kasance kuna
nufin rayuwar duniya da kawarta,
to, ku zo in yi muku kyautar ban
kwana, kuma in sake ku, saki mai
kyau.
29. "Kuma idan kun kasance
kuna nufin Allah da ManzonSa da
gidan Lahira, to, lalle, Allah Ya yi
tattalin wani sakamako mai girma
ga masu kyautatawa daga gare ku."
30. Ya matan Annabi ! Wadda ta
zo da alfasha bayyananna daga
cikinku, za a ninka mata azaba
ninki biyu. Kuma wancan ya ka-
sance mai sauki ga Allah.
31. Kuma wadda ta yi tawali'u
daga cikinku ga Allah da Man-
zonSa, kuma ta aikata aiki na kwa-
rai, za Mu ba ta sakamakonta ninki
biyu, kuma Mun yi mata tattalin
arziki ma karimci.
32. Ya matan Annabi! Ba ku
zama kamar kowa ba daga mata,
idan kun yi takawa, saboda haka,
kada ku sassautar da magana, har
wanda ke da cuta a cikin zuciyarsa
ya yi cfammani, kuma ku facfi maga-
na ta alheri.
33. Kuma ku tabbata a cikin
gidajenku (1) , kuma kada ku yi fitar
gaye-gaye irin fitar gaye-gaye ta
jahiliyyar farko. Kuma ku tsai da
salla, kuma ku bayar da zakka,
jJi^^^^gU^p
<£$* S ' t s.yy <V -. >4^$^ *'4
^ !^^t£
■ » ss y ,x
E^
'\1 f'..'
(1) Umurni ga matan Annabi umurni ne
ya halatta mace ta fita daga gidanta face da
ga matan sauran Musulmi. Saboda haka ba
lalura.
638
33 - Suratul Ahzab
7\^Ai\£<A
W&mSt-rr
ku yi da'a ga Allah da ManzonSa.
Allah na nufin Ya tafiyar da £azam-
ta kawai daga gare ku, ya mutanen
Babban Gida! Kuma Ya tsarkake
ku, tsarkakewa.
34. Kuma ku tuna abin da ake
karantawa a cikin dakunanku daga
ayoyin Allah da hukunci. Lalle Al-
lah Ya kasance Mai tausasawa,
Mai labartawa.
35. Lalle, Musulmi maza da Mu-
sulmi mata da muminai maza da
muminai mata, da masu tawalTu
maza da masu tawali'u mata, da
masu gaskiya maza da masu gas-
kiya mata, da masu hakuri maza da
masu hakuri mata, da masu tsoron
Allah maza da masu tsoron Allah
mata, da masu sadaka maza da
masu sadaka mata, da masu azumi
maza da masu azumi mata, da masu
tsare farjojinsu maza da masu tsare
farjojinsu mata, da masu ambaton
Allah da yawa maza da masu amba-
tonSa mata, Allah Ya yi musu tat-
talin wata gafara da wani sakamako
mai girma.
36. Kuma ba ya halatta ga mu-
mini kuma haka ga mumina, a loka-
cin da Allah da ManzonSa Ya hu-
kunta wani umurni, wani zabi daga
aFamarinsu ya kasance a gare su.
Kuma wanda ya saba wa Allah da
ManzonSa, to, ya bace, bacewa
bayyananna. (1)
T>4>£(> > i*^^i E >f >"0*f^*t
LP
' + yy^*- m ^y «, s't^ ' ' ' \\'
(1) Wannan ay a hani ne ga kowane Musulmi ko Musulma ga sa6a wa umurnin Allah
da ManzonSa, su bi son rayukansu ga kdme. Kuma ba a lokacin auren Zainab da Zaidu ne
cfai ta sauka ba kamar yadda wadansu masu tafslri ke rubutawa domin an yi wannan aure a
gabanin hijira da nlsa, ita ayar kuwa ta sauka a MadTna ne a bayan yakin Ahzab, kamar
yadda tsarin maganarta ya nuna.
639
33 - Suratul Ahzab
mmm-rr
37. Kuma a 16kacin (1) da kake
cewa ga wanda Allah Ya yi ni'ima a
gare shi kai kuma ka yi ni'ima a gare
shi, "Ka rike matarka, kuma ka bi
Allah da takawa." Kuma kana
Boyewa a cikin ranka abin da Allah
zai bayyana (2) shi, kana tsoron mu-
tane, alhali kuwa Allah ne Mafi
cancantar ka ji tsoronSa. To, a
lokacin da Zaidu ya kare bukatarsa
daga gare ta, Mun aurar da kai ita,
domin kada wani kunci ya kasance
a kan muminai a cikin (auren ma-
tan) (Cyan hankakarsu, idan sun
kare bukata daga gare su. Kuma
umurnin Allah ya kasance abin
aikatawa.
38. Wani kunci bai kasance a
kan Annabi ba ga abin da Allah Ya
faralta a kansa, a kan ka'idar Allah
a cikin (Annabawa) wadanda suka
shige daga gabaninsa. Kuma umur-
nin Allah ya kasance abin kad-
darawa tabbatacce.
39. Wadanda ke iyar da Man-
zancin Allah, kuma suna tsoron Sa,
kuma ba su tsoron kowa face Allah.
Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai
hisabi.
(1) Idan Allah ya umurci mutane da yin wani abu ko da barinsa, to, Annabi shi ne mai
fara bin umurnin ko kange kansa daga abin da aka hana. Wannan kissa misali ce ga ayar
da ke a gaba da ita, yadda Annabi ya bi umurni wajen auren matar Zaidu bn Harisa wanda
Annabi ya yi tabanninsa a gabanin a hana aiwatar da tabanni. Auren ya auku Annabi na
da shekara 58 ita kuwa da shekara 43. Sunanta Zainab binta Jahash cfiyar goggon Annabi.
Allah Ya nuna cewa dai tabanni ya mutu sosai.
(2) Abin da Annabi ke Boyewa shi ne umurnin Allah da Ya gaya masa cewa, zai auri
Zainab matar Zaidu a bayan Zaidun ya sake ta. Saboda haka Annabi ke lallashin Zaidu
domin kada sakin ya auku har aurenta ya zama wajibi a kansa, a bayan abin da aka sani
na cewa, Zaidu ya zama dansa da tabanni a gabanin haka.
640
33 — Suratul Ahzab
®&&\m-rr
40. Muhammadu bai kasance
uban kowa ba daga mazanku,
kuma amma shT ya kasance Man-
zon Allah kuma cikon Annabawa.
Kuma Allah Ya kasance Masani ga
kome.
41. Ya ku wacfanda suka yi 7ma-
ni! Ku ambaci Allah, ambata mai
yawa.
42. Kuma ku tsarkake shi, a sa-
fiya da maraice.
43. (Allah) ShT ne Wanda ke
tsarkake ku, da mala'ikunSa (suna
yi muku addu'a), domin Ya fiiar da
ku daga duffai zuwa ga haske.
Kuma (Allah) Ya kasance Mai jin
kai ga muminai.
44. Gaisuwarsu a ranar da suke
haduwa da Shi "Salam", kuma Ya
yi musu tattalin wani sakamako na
karimci.
45. Ya kai Annabi! Lalle Mu,
Mun aike ka kana mai shaida,
kuma mai bayar da bushara kuma
mai gargadi.
46. Kuma mai kira zuwa ga Al-
lah da izninSa, kuma fitila mai
haskakawa.
47. Kuma ka yi bushara ga mu-
minai cewa, suna da falala mai
girma daga Allah.
48. Kuma kada ka yi da'a ga
kafirai da munafukai, kuma ka kya-
le cutarsu (gare ka), kuma ka doga-
ra ga Allah. Allah Ya isa zama
Waklli.
49. Ya ku wacfanda suka yiTma-
ni! Idan kun auri muminai mata,
^^> </ 'y's/' a )&+■*• *'*'' *%.*.'%*■ '
^>
S ' < '•' Xt""?, > It" '%+ '
(|p I^£l/— J** j^^l j^Ufrljj
m\
s <^ y
-f »< if
641
33 — Suratul Ahzab
m&m-rr
sa'an nan kuka sake su a gabanin ku
shafe su, to, ba ku da wata idda da
za ku lissafa a kansu, kuma ku yi
musu kyautar jin dadi, (1) kuma ku
sake su saki mai kyau.
50. Ya kai Annabi! Lalle Mu,
Mun halatta maka matanka wa-
danda ka bai wa sadakokinsu, da
abin da hannun damanka ya mal-
laka daga abin da Allah Ya ba ka na
ganima, da 'ya'yan baffanka, da
'ya'yan goggonninka da 'ya'yan ka-
wunka da 'ya'yan innoninka, wa-
cfanda suka yi hijira tare da kai, da
wata mace mumina idan ta bayar da
kanta ga Annabi, idan shi Annabi
yana nufin ya aure ta, (halin wan-
nan hukunci) kebe yake gare ka,
banda ga muminai. Lalle Mun san
abin da Muka faralta a kansu (su
muminai) game da matansu da abin
da hannayensu suka mallaka. Do-
min kada wani kunci ya kasance a
kanka, kuma Allah Ya kasance Mai
gafara, Mai jin kai.
51. Kana iya jinkirtar da (2) wad-
da ka ga dama daga gare su, kuma
kana taro wadda kake so zuwa gare
ka. Kuma wadda ka nema daga
wadanda ka nisantar, to, babu laifi
a gare ka. Wannan ya fi kusantar da
sanyaya idanunsu, kuma ba za su yi
bakin ciki ba, kuma su yarda da
abin da ka ba su, su duka. Kuma
Allah Yana sane da abin da yake a
cikin zukatanku. Kuma Allah Ya
kasance Masani, Mai hakuri.
* > » »*< '*
" < f +> ^ -ft
\Z^&&&£&
(1) Kyautar jin dacfi ita ce kyautar ban kwana ga matar da aka saki.
(2) Rabon kwana ga matan Annabi, ba sharl'a ba ce a kan hususiyyarsa, saboda
yawan nauyin da yake dauke da shi na iyar da Manzancin Allah.
642
33 — Suratul Ahzab
W£M&-rr
52. Wacfansu mata ba su halatta
a gare ka a bayan haka, kuma ba za
ka musanya su da matan aure ba,
kuma ko kyaunsu ya ba ka sha'awa,
face dai abin da hannun damanka
ya mallaka. Kuma Allah Ya kasan-
ce Mai tsaro ga dukan kome.
53. Ya ku wacfanda suka yi Tma-
ni! Kada ku shiga gidajen Annabi,
face fa idan an yi izni a gare ku zuwa
ga wani abinci, ba da kun tsaya
jiran nunarsa ba, kuma amma idan
an kira ku, to, ku shiga, sa'an nan
idan kun ci, to, ku watse, kuma ba
da kun tsaya kuna masu hira da
wani labari ba. Lalle wannan yana
cutar da Annabi, to, yana jin kun-
yarku, alhali kuwa Allah ba Ya jin
kunya daga gaskiya. Kuma idan za
ku tambaye su wacfansu kaya, to,
ku tambaye su daga bayan shama-
ki. Wannan ya fi muku tsarki ga
zukatanku da zukatansu. Kuma ba
ya halatta a gare ku, ku cuci Man-
zon Allah, kuma ba ya halatta ku
auri matansa a bayansa har abada.
Lalle wannan a gare ku ya kasance
babban abu a wurin Allah.
54. Idan kun bayyana wani abu,
ko kuma kuka 66ye shi, to, lalle
Allah Ya kasance Masani ga kome.
55. Babu laifi a kansu game da
ubanninsu, kuma babu game da
cfiyansu, kuma babu game da 'ya-
n'uwansu maza, kuma babu game
da cfiyan 'yan'uwansu maza, kuma
babu game da cfiyan 'yan'uwansu
mata, kuma babu game da matan
muminai, kuma babu game da abin
da hannayensu suka mallaka, kuma
s'ss 1~>'.'
»•>> »^<f>^,'
.1-*^ -
*> y y Ky* y ■< G y y *y 9 «. < ^
kbc3^0*
643
33 — Suratul Ahzab
ij^-rr
sun bi Allah da takawa. Lalle Allah
Ya kasance Mahalarci a kan kome.
56. Lalle, Allah da mala'ikunsa
suna salati (1) ga Annabi. Ya ku
wadanda suka yilmani ! Ku yi salati
a gare shi, kuma ku yi sallama
domin amintarwa a gare shi.
57. Lalle wadanda ke cutar Al-
lah da ManzonSa, Allah Ya la'ane
su, a cikin duniya da Lahira, kuma
Ya yi musu tattalin azaba mai
wulakantarwa.
58. Kuma wadanda suke cutar
muminai maza da muminai mata,
ba da wani abu da suka aikata ba,
to, lalle sun dauki kiren karya da
zunubi bayyananne.
59. Ya kai Annabi! Ka (2) ce wa
matan aurenka da 'yS'y an ^ a da
matan muminai su kusantar da
kasa daga manyan tufafin da ke a
kansu. Wancan ya fi sauki ga a gane
su domin kada a cuce su. Kuma
Allah Ya kasance Mai gafara, Mai
jin kai.
60. Lalle, idan munafukai da wa-
cfanda yake akwai wata cuta a cikin
zukatansu, da masu tsegumi, a cikin
Madura, ba su hanu ba (daga hala-
yensu), (3) lalle, za Mu shushuta ka a
©il^fA^^
*'*%^ . >*f>>'V»>l' > '"' -
' E* " " > ~
(5 i^b>i^<^^^i>>
(1) Salatin Allah ga Annabi, shine cfaukaka darajarsa a koyaushe. Salatin mala'iku,
shi ne istigfari da addu'a a gare shi. Salatin mutane, shi ne ibada da istigfari da addu'a a
gare shi da tawassuli da shi domin neman Allah Ya karBi ibadarsu. Salati sau cfaya wajibi
ne a kan kowane Musulmi a tsawon ransa, sa'an nan kuma sunna ce a cikin kowace sal la.
Kuma mustahabbi ne a cikin kowane mazauni da wurin ambatonsa.
(2) Ana fara gyara daga sama, sa'an nan gyaran ya sauko £asa, kamar Barnar da ta
faru daga sama, sai ta kai kasa.
(3) Munafukai da shaidanu da masu tsegumi babu abin da ke hana su mugun halinsu
sai tsanani da tsoro.
644
33 — Suratul Ahzab
Ij^-rr
gare su, sa'an nan ba za su yi mak-
wabtaka da kai ba, a cikinta, face
kacfan.
61. Suna la'anannu, inda duka
aka same su a kama su, kuma a
karkashe su karkashewa.
62. A kan hanyar Allah (ta gya-
ran jama'a) a cikin wacfanda suka
shude gabaninka, kuma ba za ka
sami musanyawa ba ga hanyar
Allah.
63. Suna tambayar ka (1) ga Sa'a.
Ka ce, "Saninta yana wurin Allah
kawai." Kuma me ya sanar da kai
cewa ana tsammanin Sa'a ta kasan-
ce kusa?
64. Lalle, Allah Ya la'ani kafirai,
kuma Ya yi musu tattalin wata
wuta mai kuna.
65. Suna madawwama a cikinta
har abada, ba su samun majiBinci,
kuma ba su samun mataimaki.
66. Ranar da ake juya fuskokin-
su a cikin wuta, suna cewa, "Kai-
tonmu, saboda rashin biyarmu ga
Allah da rashin biyarmu ga Manzo !"
67. Kuma suka ce, "Ya Ubangi-
jinmu! Lalle mu, mun (2) bi
shugabanninmu da manyanmu! Sai
suka 6atar da mu daga hanya!
68. "Ya Ubangijinmu! Ka ba su
ninki biyu na azaba, kuma ka la'ane
su, la'ana mai girma."
$ ^^fe<^^^^(^
TC
•^
(1) Shiryarwa ce ga Musulmi cewa idan za su yi tambaya su tambayi addininsu da
abubuwa masu amfani a gare su, kada su tambayi a bin da ya fi hankalinsu kamar Sa'a da
abubuwan gaibi da Allah Ya kebanta da saninsu.
(2) Wannan ya nuna biya da jahilci ga addini ba uzuri ba ne. Ana azabtar da mai biya,
kamar yadda ake azabtar da shugaban bata.
645
33 - Suratul Ahzab
\\\£<*
m^m-rr
69. Ya ku wacfanda suka yi ima-
ni ! Kada ku kasance kamar wadan-
da suka cuci (1) Musa, sa'an nan
Allah Ya barrantar da shi daga abin
da suka ce. Kuma ya kasance mai
daraja a wurin Allah.
70. Ya ku wadanda suka yi ima-
ni ! Ku bi Allah da takawa, kuma ku
facfi magana madaidaiciya.
71. Ya kyautata muku ayyukan-
ku, kuma Ya gafarta zunubanku.
Kuma wanda ya yi da'a ga Allah da
ManzonSa, to, lalle, ya rabbanta,
babban rabo mai girma.
72. Lalle Mu, Mun gitta amana
ga sammai da kasa da duwatsu, sai
suka ki daukarta kuma suka ji tsoro
daga gare ta, Jaima mutum ya dau-
ke ta, lalle shi (mutum) ya kasance
mai yawan zalunci, mai yawan
jahilci.
73. Domin Allah Ya azabta mu-
nafukai maza da munafukai mata,
da mushirikai maza da mushirikai
mata, kuma Allah Ya kar6i tuba ga
muminai maza da muminai mata.
Kuma Allah Ya kasance Mai gafa-
ra, Mai jin kai.
tfti <-
<>^*li^l* ^^I^^^I^^^^C^bS
's*hS
fpby^
(1) Kada ku cuci Muhammadu da kazaflko muguwar magana kamar yadda Yahudu
suka yi kazafi ga Musa da neman wata karuwa ta ce ya neme ta da zina ko kuma da cewa
shi mai gwaiwa ne, sai Allah Ya tsare Musa daga kazafin, kuma Ya sanya wani dutse, ya
gudu da tufafinsa daga wurin wanka har suka gan shi mai cikakkiyar halitta ne, babu
nakasa game da shi. Allah Ya barrantar da shi daga dukan aibi. Haka Yake barrantar da
Muhammadu ga mai son ya sa masa aibi.
646
34 - Suratus Saba
'iSS^-ri
Tana karantar da cewa wanda ya bauta wa Allah, sai Allah Ya
saukake masa ibadar nan kuma Ya hore masa abincinsa, kuma
wanda ya saba wa Allah, idan yana da wadata ne, to, Allah zai
karbe wadatarsa.
Z># sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
L Godiya ta tabbata ga Allah,
Wanda Yake abin da yake a cikin
sammai da abin dajake a cikin kasa
Nasa ne, kuma Shi ne Mai hikima,
Mai labartawa.
2. Ya san abin da yake shiga a
cikin kasa da abin da yake fita daga
gare ta, da abin da yake sauka daga
sama da abinda yake hawa a cikin-
ta, kuma Shi ne Mai jin kai, Mai
gafara.
3. Kuma wadanda suka kafirta
suka ce, "Sa'a ba za to zo mana ba."
Ka ce,_"Kayya! Na rantse da
Ubangijina, lalle, za ta zo muku."
Masanin gaibi, gwargwadon zarra
ba ta msanta daga gare Shi a cikin
sammai, kuma ba ta msanta a cikin
kasa, kuma babu mafi karanci daga
wancan kuma babu mafi girma face
yana a cikin Littafi bayyananne.
4. Domin Ya saka wa wadanda
suka yi Tmani kuma suka aikata
o^^l<3l^oy3i<^
> >
UJL
jyui\
S sT .? \ * /"• >>'>'
cl^JUi
^U^\^>J
647
34 — Suratus Saba'
OT&-W
ayyukan kwarai. Wacfancan suna
da wata gafara da wani arziki mai
karimci.
5. Kuma wacfanda suka yi ma-
kirci ga ayoyinMu, suna masu gaji-
yarwa, wacfannan suna da wata
azaba daga azaba mai radacfi.
6. Kuma wadanda aka bai wa
ilmi suna ganin abin nan da aka
saukar zuwa gare ka daga Ubangi-
jinka, shi ne gaskiya, kuma yana
shiryarwa zuwa ga hanyar Mabu-
wayi, Godadde.
7. Kuma wadanda suka kafirta
suka ce, "Shin, za mu nuna muku
wani namiji wanda yake gaya muku
wai idan an tsattsage ku, kowace
inn tsattsagewa, lalle ku, tabbas,
kuna a cikin wata halitta sabuwa. ?
8. "Ya kaga karya ga Allah ne
ko kuwa akwai wata hauka a gare
shi?" A'a, wadanda ba su yilmani
da Lahira ba, suna a cikin azaba da
Bata mai nlsa.
9. Ashe fa, ba su yi dubi ba zuwa
ga abin da ke a gaba gare su da abin
da ke a bayansu daga sama da kasa?
Idan Mun so, sai Mu shafe kasa da
su, ko kuma Mu kayar da wani
BaBBake daga sama a kansu. Lalle,
a cikin wancan akwai aya ga dukan
bawa mai mai da al'amarinsa ga
Allah.
10. Kuma lalle, haklka, Mun bai
wa Dawuda wata falala daga gare
Mu. Ya duwatsu, ku konkoma sau-
tin tasblhi tare da shi, kuma da
tsuntsaye. Kuma Muka tausasa
masa bakin karfe.
V > £^ 4*
jjjy t [ ^\jjCS2\ J jP^SfX
<yr$^>J f^^Cf^ fyjjj&\
T'<
> „x ^V'^
Ajk
648
34 — Suratus Saba'
«ifcar*rvi
l^^-ri
11. Ka aikata sulkuna, kuma ka
kaddara lissafi ga tsarawa, kuma ka
aikata aikin kwarai. Lalle Nl, Mai
gani ne ga abin da kuke aikatawa.
12. Kuma ga Sulaiman, Mun
hore masa iska, tafiyarta ta safiya
daidai da wata, kuma ta maraice
daidai da wata. Kuma Muka gu-
danar masa da marmaron gaci,
kuma daga aljannu (Muka hore
masa) wacfanda ke aiki a gaba gare
shi, da iznin Ubangijinsa. Wanda ya
karkata daga cikinsu, daga umur-
ninMu, sa^Mu cfancfana masa daga
azabar sa'ir.
13. Suna aikata masa abin da
yake so, na masallatai da mutum-
mutumai da akussa kamar kudud-
dufai, da tukwane kafaffu. Ku aika-
ta godiya, ya cfiyan Dawuda, kuma
kacfan ne mai godiya daga baylNa.
14. Sa'an nan a lokacin da Muka
hukunta mutuwa a kansa, babu
abin da ya ja hankalinsu a kan
mutuwarsa, face dabbar kasa (gara)
wadda take cin sandarsa. To, a
lokacin da ya facfi, sai aljannu suka
bayyana (ga mutane) cewa da sun
kasance sun san gaibi, da ba su
zauna ba a cikin azaba mai wula-
kantarwa.
15. Lalle, hakika, akwai aya ga
Saba'awa (1) a cikin mazauninsu:
gonakin lambu biyu, dama da hagu.
"Ku ci daga arzikin Ubangijinku,
kuma ku yi godiya gare Shi. Gari
y y y /" /
» ' S'X 1<s
(1) Kissar Dawuda da ta Sulaiman suna nuna yadda Allah ke saukake wa bayinSa
hanyar ibada da ta samun abinci da sauki idan sun mayar da al'amuransu gare Shi. Kissar
Saba'awa tana nuna yadda Allah ke karfte wadata daga wanda ya kafirce Masa.
649
34 — Suratus Saba'
%%$?&- ri
mai dakfin zama, da Ubangiji Mai
gafara."
16. Sai suka bijire, saboda haka
Muka saki malalin Arimi (dam) a
kansu, kuma Muka musanya musu
gonakinsu biyu da wacfansu gonaki
biyu masu 'ya'yan itace kadan:
talakiya da goriba da wani abu na
magarya kadan.
17. Wancan, da shi Muka yi
musu sakamako saboda kafircinsu.
Kuma lalle, ba Mu yi wa kowa (1)
irin wannan sakamako, face kafirai.
18. Kuma Muka sanya, a tsaka-
ninsu da tsakanin (2) garuruwan da
Muka sanya albarka a cikinsu, wa-
cfansu garuruwa masu ganin juna
kuma Muka kaddara tafiya a cikin-
su, "Ku yi tafiya a cikinsu, daru-
ruwa da ranaiku, kuna amintattu."
19. Sai suka ce, "Ya Ubangi-
jinmu! Ka nTsantar da tsakanin
tafiyoyinmu", kuma suka zalunci
kansu, saboda haka Muka sanya su
labaran hlra, kuma Muka kekkece
su (3) kowace irin kekkecewa. Lalle,
a cikin wancan akwai ayoyi ga
dukan mai yawan hakuri, mai ya-
wan godiya.
20. Kuma lalle, haklka, Iblis ya
gaskata zatonsa a kansu, sai suka bi
shi face wani 6angare na muminai.
» > < i "t'«
ho
■^ i^ *. ' ■
">T{,
A^~*Jb\ \ySj0j \j\slJ\ OJj J^\^j\y\ii
|(>Cj4^l (
(1) Allah na saka wa kafirai gwargwadon aikinsu, kuma Yana yin falala ga mumini da
kyautar da ta fi aikinsa.
(2) Tafiya a tsakanin Yemen, kasar Saba'awa da Syria, watau Sham, kasa mai
albarka, kasar Annabawa kuma kasa mai yawan ruwa da itace.
(3) Muka sanya Saba'awa suka watse a cikin wacfansu kasashe saboda ruwa ya
halaka kasarsu, sa'an na kuma ta bushe babu wadata, har ana cewa 'Sun yi rarrabar
Saba'awa' watau sun watse.
650
34 — Suratus Saba'
im-n
21. Kuma ba ya da wani dalili a
kansu, face dai jiomin Mu san
wanda yake yin Tmani da Lahira
daga wanda yake a cikin shakka
daga gare ta. Kuma Ubangijinka, a
kan kome, Mai tsaro ne.
22. Ka ce, "Ku kirayi wacfanda
kuka riya (cewa abubuwan bau-
tawa ne) baicin Allah, ba su mal-
lakar ma'aunin zarra a cikin sam-
mai, kuma ba su mallakarsa a cikin
icasa, kuma ba su da wani rabon
tarewa a cikinsu (sammai da £asa),
kuma ba Shi da wani mataimaki
daga gare su.
23. "Kuma wani ceto ba ya am-
fani a wurinSa face fa ga wanda Ya
yi izni a gare shi. Har a lokacin da
aka kuranye (1) tsoro daga zuka-
tansu, sai su ce, 'Mene ne Ubangi-
jinku Ya ce?' Suka ce, 'Gaskiya,
kuma Shi ne Macfaukaki, Mai
girma."
24. Ka ce, "Wane ne yake arzuta
ku daga sama da icasa?" Ka ce,
"Hah, kuma lalle mu, ko ku, wani
yana a kan shiriya, ko yana a cikin
6ata bayyananniya."
25. Ka ce, "Ba za a tambaye ku
ba ga abin da muka aikata daga
laifi, kuma ba za a tambaye mu
daga abin kuke aikatawa ba."
^x,x <> < » y
's >;/.
•Iff > m " t
m A^>>,^ ^ ►>
(1) Babu wanda ya san lokacin bayar da izni ga yin ceto ko wanda za a bai wa iznin ya
yi, ko a yi masa, saboda haka mutane a Lahira na a cikin tsoro har a lokacin da aka
kuranye tsoron ta hanyar bayar da izni ga ceto babba ga Annabi Muhammadu, sai
muminai su yi farin ciki su dinga tambayar juna da cewa, "Mene ne Ubangijinku Ya ce?"
Wadansu su ce, "Ya fadi gaskiya, ShT ne Macfaukaki, Mai girma."
651
34 — Suratus Saba
1^&-ri
26, Ka ce, "Ubangijinmu zai
tara tsakaninmu, sa'an nan Ya yi
hukunci a tsakaninmu da gaskiya.
Kuma Shine Mahukunci, Masani."
27, Ka ce, "Ku nuna mini wa-
cfanda kuka riskar da Shi, su zama
abokan tarayya. A'a, Shi ne Allah,
Mabuwayi, Mai hikima."
28, Kuma ba Mu aika ka ba face
zuwa ga mutane gaba daya, kana
mai bayar da bushara kuma mai
gargacfi, kuma amma mafi yawan
mutane ba su sani ba.
29, Suna cewa, "Yaushe ne wan-
nan wa'adi zai auku idan kun ka-
sance masu gaskiya?"
30, Ka ce, "Kuna da mi'adin
wani yini wanda ba ku jinkirta daga
gare shi ko da sa'a cfaya, kuma ba
ku gabata."
31, Kuma wadanda suka kafirta
suka ce, "Ba za mu yi Tmani da
wannai^Alkur'ani ba, kuma ba za
mu yi imani da abin da yake a
gabaninsa ba (na wadansu littat-
tafan sama)." Kuma da ka gani a
lokacin da azzalumai suke abin
tsayarwa wurin Ubangijinka, sa-
shensu na mayar wa sashe maganar
maraunana (mabiya) suke cewa
makangara (shugabanni) "Ba do-
minku ba, lalle, da mun kasance
muminai."
32, Makangara suka ce wa
maraunana, "Ashe, mu ne muka
kange ku daga shiriya a bayan ya zo
muku? A'a, kun dai kasance masu
laifi."
03 ^^VLjL4j»_y^
^. *
*> >
4 >.
]y
oyi
652
34 — Suratus Saba'
W%&-ri
33. Kuma maraunana suka ce
wa makangara, "A'a, (ku tuna)
makircin dare da na rana a lokacin
da kuke umurnin mu da mu kafirta
da Allah, kuma mu sanya Masa
abokan tarayya." Kuma suka assir-
tar da nadama a lokacin da suka ga
azaba. Kuma Muka sanya kukum-
ma a cikin wuyoyin wacfanda suka
kafirta. Lalle, ba za a yi musu saka-
mako ba face da abin da suka ka-
sance suna aikatawa.
34. Kuma ba mu aika wani mai
gargacfi ba a cikin wata alkarya face
mani'imtanta (shugabanni) sun ce,
"Lalle mu, masu kafirta ne da abin
da aka aiko ku da shi."
35. Kuma suka ce, "Mu ne ma-
fiya yawa ga dukiya da cfiya, kuma
mu ba mu zama wacfanda ake yi wa
azaba ba."
36. Ka ce, "Lalle, Ubangijlna
Yana shimficfa arziki ga wanda Ya
so, kuma Yana kukuntawa, kuma
amma mafi yawan mutane ba su
sani ba."
37. Kuma dukiyarku ba ta zamo
ba, haka cfiyanku ba su zamo abin
da yake kusantar da ku ba a wu-
rinMu, kusantarwar mukami, face
wanda ya yi imani kuma ya aikata
aikin kwarai. To, wacfannan suna
da sakamakon ninkawa saboda
abin da suka aikata. Kuma su amin-
tattu ne a cikin benaye.
38. Kuma wacfanda suke makir-
ci a cikin ayoyinMu, suna neman
gajiyarwa, wacfannan abin halar-
tawa ne a cikin azaba.
A''*>-
te&WjJ^&liti;
653
34 — Suratus Saba'
lSS#&-rt
39. Ka ce, "Lalle, UbangijTna
yana shimfida arziki ga wanda Ya
so daga bayinSa, kuma Yana kun-
tatawa a gare shi, kuma abin^da
kuka ciyar daga wani abu,jto, Shine
zai musanya shi, kuma Shi ne MafT-
ficin masu arzuttawa."
40. Kuma ranar da Allah Ya ke
tara su gaba daya, sa'an nan Ya ce
wa mala'iku, "Shin, wadannan, ku
ne suka kasance suna bauta wa?"
41. Suka ce, "Tsarki ya tabbata a
gare Ka. Kai ne Maji6incinmu, ba
su ba. A'a, sun kasance suna bauta
wa aljannu. Mafi yawansu, da su
suka yi Tmani."
42. Saboda haka, a yau sashenku
ba ya mallakar wani amfani ga wani
sashen, kuma ba ya mallakar wata
cuta, kuma Muna cewa ga wadanda
suka yi zalunci, "Ku dandani aza-
bar wuta wadda kuka kasance,
game da ita, kuna karyatawa."
43. Kuma idan an karanta ayo-
yinMu bayyanannu a kansu, sai su
ce, "Wannan bai zama ba, face
namiji ne yana son ya kange ku
daga abin da ubanninku suka ka-
sance suna bauta wa." Kuma su ce,
"Wannan bai zama ba face kiren
karya da aka kaga." Kuma wadan-
da suka kafirta suka ce, ga gaskiya a
lokacin da ta je musu, "Wannan ba
kome ba face sihiri ne bayya-
nanne."
44. Kuma ba Mu ba su wadansu
littattafai ba wadanda suke karatun
su, kuma ba Mu aika wani mai
gargacfi ba zuwa gare su a gaba-
ninka !
,*Jq&z}4* t^Cj^j*^**^ x^j^jJ^j
\}\^Pl0jti
M by-ty* rt-fr **lfi==> < o->t) ' OJ -Lou
'v'\i W\'\.' ?u\*s.'
&o*.
«H3
o >';» 4*s S s*L /s »>J &"> -** ~*' s s
LJLj^i ' *j i\) jJ V ^ '- jr*.* j* A } r \j
654
34 — Suratus Saba'
1^&-n
45. Kuma wacfanda suke a gaba-
ninsu, sun Raryata, alhali kuwa ba
su kai ushurin ushurin abin da
Muka ba^su ba, sai suka Icaryata
ManzannlNa! To, yaya musuNa
(ga malcaryata) ya kasance?
46. Ka ce, "Ina yi muku wa'azi
ne kawai da kalma guda ! Watau ku
tsayu domin Allah, bibbiyu da dai-
dai, sa'an nan ku yi tunani, babu
wata hauka ga ma'abucinku. Shi
bai zama ba face mai gargadi ne a
gare ku, a gaba ga wata azaba mai
tsanani.
47. Ka ce, "Abin da na ro£e ku
na wani sakamako, to, amfaninsa
naku ne. Ijarata ba ta zama ba face
daga Allah, kuma Shi Mahalarci ne
a kan dukan kome."
48. Ka ce, "Lalle Ubangijina
Yana jefa gaskiya. (Shi) Masanin
abubuwan fake ne."
49. Ka ce, "Gaskiya ta zo, kuma
Icarya ba ta iya fara (kome) kuma ba
ta iya mayarwa."
50. Ka ce, "Idan na Bace, to, ina
6acewa ne kawai a kan kaina.
Kuma idan na shiryu, to, saboda
abin da Ubangijina Yake yowar
wahayi ne zuwa a gare ni. Lalle Shi,
Mai ji ne, Makusanci."
57. Kuma da ka gani, a lokacin
da suka firgita, to, babu ku6uta,
kuma aka kama su daga wuri
makusanci.
52. Kuma suka ce, "Mun yi ima-
ni da Shi." To, inaza su samu kama-
wa daga wuri mai nlsa?
J$$* < ,< x * '"•' ¥\» .'A\ '* ».
»X?*\' '"'fT ■% .z' -'+ 9 *
rf^ ><Tt>1 x " \\ * -Z' ~"Zi'Z
655
35 — Suratu Facfir
Z&A
ii-ro
53. Kuma lalle sun kafirta da Shi
a gabanin haka, kuma suna jTfa da
jahilci daga wuri mai nisa.
54. Kuma an shamakance a
tsakaninsu da tsakanin abin da suke
marmari, kamar yadda aka aikata
da irin kungiyoyinsu a gabaninsu.
Lalle su, sun kasance a cikin shakka
mai sanya kokanto.
Tana karantar da cewa bauta wa Allah, shi ne mabucfin dukan
alheri kuma bautar nan da sanin yadda ake yin ta daga gare Shi
yake.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Godiya ta tabbata ga Allah,
Mai fara halittar sammai da kasa,
Mai sanya mala'iku manzanni
masu fukafukai, bibbiyu, da uku-
uku da hurhudu. Yana karawar
abin da Ya ke so a cikin halittar. Lalle
Allah Mai ikon yi ne a kan kome.
2. Abin da Allah Ya butfa wa
mutane daga rahama, to, babu mai
rikewa a gare shi, kuma abin da Ya
rike, to, babu maijsaki a gare shi,
waninSa, kuma Shi ne Mabuwayi,
Mai hikima.
^£lk£^
J J^/J 1 §&&c$£4*
0^%?
656
35 — Suratu Facfir
^-fo
3. Ya ku mutane! Ku tuna
ni'imar Allah a kanku. Shin, akwai
wani mai halitta wanin Allah, da zai
arzutta ku daga sama da kasa?
Babu wani abin bautawa, face Shi.
To, yaya ake karkatar da ku?
4. Kuma idan sun karyata ka, to,
lalle, an karyata wacfansu Man-
zanni a gabaninka, kuma zuwa ga
Allah ake mayar da aFamura.
5. Ya ku mutane! Lalle, wa'adin
Allah gaskiya ne, saboda haka kada
rayuwar duniya ta rutfar da ku,
kuma kada marudi ya rude ku game
da Allah.
6. Lalle Shaidan makiyi ne a gare
ku, sai ku like shi makiyi. Yana
kiran kungiyarsa kawai ne, domin
su kasance 'yan sa'Tr.
7. Wadanda suka kafirta suna da
azaba mai tsanani, kuma wadanda
suka yi Imani, kuma suka aikata
ayyukan kwarai, suna da wata gafa-
ra da sakamako mai girma.
8. Shin, to, wanda aka kawata
masa aikinsa, har ya gan shi mai
kyau (yana daidai da waninsa)?
Saboda haka, lalle, Allah Yana 6a-
tar da wanda Yake so, kuma Yana
shiryar da wanda Yake so, saboda
haka kada ranka ya halaka a kansu
domin bakin ciki. Lalle Allah Ma-
sani ne ga abin da suke
sana'antawa.
9. Kuma Allah ne Ya aika da
iskoki har su motsar da girgije,
sa'an nan Mu kora shi zuwa ga gari
matacce, sa'an nan Mu rayar da
'he.
657
35 — Suratu Facfir
-ro
kasa game da shi a bayan mutu-
warta. Kamar wancan ne Tashin
Kiyama yake.
10. Wanda ya kasance yana ne-
man wata izza, to, Allah ne da izza
gaba daya. Zuwa gare Shi magana
mai dadi ke hawa, kuma aiki na
kwarai Yana cfaukar ta. Kuma wa-
cfanda ke yin makircin munanan
ayyuka, suna da wata azaba mai
tsanani, kuma makircin wadannan
yana yin tasgaro.
77. Kuma Allah ne Ya halitta ku
daga tur6aya, sa'an nan daga cfigoh
maniyyi, sa'an nan Ya sanya ku
surkin maza da mata. Kuma wata
mace ba ta yin ciki, kuma ba ta
haihuwa, face da saninSa, kuma ba
za a rayar da wanda ake rayarwa
ba, kuma ba za a rage tsawon ransa
ba face yana a cikin Littafi. Lalle,
wancan mai sauki ne ga Allah.
12. Kuma koguna biyu ba su
daidaita: Wannan mai ruwan dacfi,
mai zaki, mai saukin hadiya, kuma
wannan mai ruwan gishiri, mai zart-
si, kuma daga kowane, kuna cin
wani nama sabo, kuma kuna fitar
da kawa wadda kuke tufantarta,
kuma kana ganin jirage a cikinsa
suna masu gudana, domin ku nemo
daga falalarSa, kuma dammaninku
za ku dinga godewa.
13. Yana shigar da dare a cikin
rana, kuma Yana shigar da rana a
cikin dare. Kuma Ya hore rana da
wata kowannensu yana gudana
zuwa ga ajali ambatacce. Wannan
Shine Allah, Ubangijinku, gare Shi
mulki yake, kuma wadanda kuke
»Ai
^* " —
E T k1i>"-m' 'A* A ~<\"Vf 9 '\
*tv » *'* »
' "+^\" ' •' % "S
658
35 — Suratu Facfir
%m~ro
kira, waninSa, ba^su mallakar ko
fatar gurtsun dablno.
14. Idan kun kira su, ba za su ji
kiranku ba, kuma ko sun jiya, ba za
su kar6a muku ba, kuma a Ranar
Kiyama za su kafirce wa shirkinku,
kuma babu mai ba ka labari, kamar
wanda ya sani.
15. Ya ku mutane! Ku ne masu
bukata zuwa ga Allah, kuma Allah,
Shi ne Mawadaci, Godadde.
16. Idan Ya so, zai tafi da ku,
kuma Ya zo da wata halitta sabuwa.
17. Kuma wancan bai zama ma-
buwayi ba ga Allah.
18. Kuma wani rai mai daukar
nauyi, bai daukar nauyin wani rai.
Kuma idan ran da aka nauyaya wa
kaya ya yi kira (ga wani mataimaki)
zuwa ga kayansa, ba za a dauki
kome ba daga gare shi, kuma ko da
(wanda ake kiran) ya kasance
makusancin zumunta ne. Kana gar-
gadi kawai ne ga wadanda ke tsoron
Ubangijinsu a fake, kuma suka
tsayar da salla. Kuma wanda ya
tsarkake, to, yana tsarkaka ne do-
min kansa. Kuma zuwa ga Allah
kawai makoma take.
19. Kuma makaho ba ya daidai-
ta da mai gani.
20. Kuma duffai ba su daidaita,
kuma haske ba ya daidaita.
21. Kuma inuwa ba ta daidaita,
kuma iskar zafi ba ta daidaita.
22. Kuma rayayyu ba su daidai-
ta, kuma matattu ba su daidaita.
Lalle Allah Yana jiyar da wa'azi ga
^y s~ > ' ' " \ ' y>
^$y ^•—^ ** s ""
^*>*s s » •■ **
^5^ > ^t» Ml """'i^
659
35 - Suratu Facfir
ii-ro
wanda Ya so, kuma ba ka jiyar da
wacfanda suke a cikin kaburbura.
23. Ba ka zama ba face mai gar-
gadi kawai.
24. Lalle Mu, Mun aike ka da
gaskiya, kana mai bayar da bushara
kuma mai gargadi. Kuma babu
wata arumma face wani mai garga-
di ya shude a cikinta.
25. Kuma idan suna karyata ka,
to, haiuka, wacfanda suke a gaba-
ninsu sun karyata. Manzanninsu
sun je musu da hujjoji, kuma da
takardu, kuma da Littafi mai haske.
26. Sa'an nan Na kama wadanda
suka kafirta. To, yaya musuNa
yake?
27. Ba ka gani ba, lalle Allah Ya
saukar da ruwa daga sama? Sai
Muka fitar, game da shi, 'ya'yan
itace masu sa6anin launuka, kuma
daga duwatsu akwai zane-zane, far-
faru da jajaye, masu saBanin launin,
da masu launin bakin karfe, baka-
ke.
28. Kuma daga mutane da dab-
bobi da bisashen gida, masu saBa-
nin launinsu kamar wancan. Mala-
mai kawai ke tsoron Allah daga
cikin bayinSa. Lalle, Allah, Mabu-
wayi ne, Mai gafara.
29. Lalle, wadanda ke karatun
Littafin Allah (1) kuma suka tsayar
da salla, kuma suka ciyar daga
abin da Muka arzuta su da shi, a
>>rf . ^ *> ^ '\X"
(1) Littattafan sama a gabanin Annabi Muhammadu, tsira da aminci su tabbata a
gare shi.
660
35 — Suratu Facfir
£_ro
asirce da bayyane, suna fatan (sa-
mun) wani fatauci ne wanda ba ya
yin tasgaro.
30. Domin (Allah) zai cika musu
sakamakonsu, kuma Ya kara musu
daga falalarSa. Lalle Shi Mai gafara
ne, Mai godiya.
31. Kuma abin da Muka yi wa-
hayi zuwa gare ka, daga Littafi, (1)
shi ne gaskiya, mai gaskatawa ga
abin da yake a gaba gare shi. Lalle
ne Allah ga bayinSa, haklka, Mai
labartawa ne, Mai gani.
32. Sa'an nan Mun gadar da Lit-
tafin, ga wacfanda Muka zaba daga
bayinMu, sa'an nan daga cikinsu,
akwai mai zalunci ga kansa, kuma
daga cikinsu akwai mai tsakaitawa,
kuma daga cikinsu akwai mai tse-
rewa da ayyukan alheri da iznin
Allah. Waccan ita ce falalar (Allah)
mai girma.
33. Gidajen Aljannar zama, suna
shigar su. Ana kawace su a cikinsu,
da kawa ta mundaye daga zlnariya
da lu'ulu'u, kuma tufafinsu, a cikin-
su alharlni ne.
34. Kuma suka ce, "Godiya ta
tabbata ga Allah Wanda Ya tafiyar
da bakin ciki daga^gare mu. Lalle
Ubangijinmu, hakTka Mai gafara
ne, Mai godiya.
35. "Wanda Ya saukar da mu a
gidan zama, daga falalarSa, wata
wahala ba ta shafar mu a cikinsa,
kuma wata kasawa ba ta shafar mu
a cikinsa."
*>* '* it* >» - "'1*tif- ***<
>»>x
^^l^^U^^jJ^yAJ^
6^1l^C^^3^^Jui^lo
(1) Alleur'ani.
661
35 — Suratu Facfir
&-ro
36. Kuma wacfanda suka kafirta
suna da wutar Jahannama, ba a yin
hukunci a kansu balle su mutu,
kuma ba a saukaka musu daga
azabarta. Kamar haka Muke saka
wa kowane mai yawan kafirci.
37. Kuma su, suna hargowar ne-
man agaji a cikinta. (Suna cewa)
"Ya Ubangijinmu! Ka fitar da mu,
mu aikata aiki mai kyau, wanin
wanda muka kasance muna aika-
ta wa." Ashe, kuma, ba Mu rayar da
ku ba, abin da mai tunani zai iya yin
tunani a ciki, kuma mai gargacfi ya
je muku? To, ku cfancfana, saboda
haka babu wani mataimaki ga azza-
lumai.
38. Lalle Allah ne Masaninjai-
bin sammai da kasa. Lalle Shi ne
Masani ga abin da yake ainihin
zukata.
39. Shi ne Wanda Ya sanya ku
masu maye wa juna, a cikin kasa.
To, wanda ya kafirta, to, kafircinsa
yana a kansa. Kuma kafircin kafirai
ba ya kara musu kome face bakin
jini, kuma kafircin kafirai ba ya
kara musu kome face hasara.
40. Ka ce, "Shin, kun ga abubu-
wan shirkinku, wacfanda kuke kira,
wasun Allah? K\i nuna mini, mene
ne suka halitta daga kasa? Ko suna
da tarayya ne a cikin sammai? Ko
kuma Mun ba su wani littafi ne
saboda haka sunaa kan wata hujja
ce daga gare shi? A'a, azzalumai ba
su yin wani wa'adi, sashensu zuwa
ga sashe, face rudi."
\' '* "IT'"*'
> ,y *s •>.
0^i(j3^ fo^Jp^ ^]>^L lid <^jt
E
662
35 — Suratu Facfir
-ro
41. Lalle Allah Yana rike sam-
mai da kasa domin kada su gushe.
Kuma hakika, idan sun gushe, babu
wani baicinSa da zai rike su. Lalle
Shi, Ya kasance Mai hakuri, Mai
gafara.
42. Kuma suka ( l } yi rantsuwa da
Allah, mafi nauyin rantsuwarsu,
"Lalle, idan wani mai gargadi ya zo
musu, tabbas, za su kasance mafi
shiryuwa, daga dayan al'ummomi."
To, a lokacin da mai gargadi ya je
musu, bai kara su da kome ba face
gudu.
43. Domin nuna girman kai a
cikin kasa da makircin cuta. Kuma
makirci na cuta ba ya fadawa face a
kan mutanensa. To, shin, suna jiran
(wani abu ne) face dai hanyar (kafi-
ran) farko. To, ba za ka sami musa-
nya ba ga hanyar Allah. Kuma ba
za ka sami juyarwa ba ga hanyar
Allah.
44. Ashe, kuma ba su yi tafiya
ba, a cikin kasa, domin su duba
yadda akibar wadannan da suke a
gabaninsu ta kasance? Alhali kuwa
sun kasance mafifita karfi daga gare
su? Kuma Allah bai kasance wani
abu na iya rinjayarSa ba, a cikin
sammai, kuma haka a cikin kasa.
Lalle^Shi ne Ya kasance Masani,
Mai Tkon yi.
45. Kuma da Allah Yana kama
mutane saboda abin da suka aikata,
da bai bar wata dabba ba a kanta
fp]^^^>!;ii
Ik— -
>uL> L pd]i^il^i>ij
(1) Larabawa sun kasance suna guri su sami mai ja musu gora kamar Yahudu ko
Nasara, sa'an nan Muhammadu ya je musu, sai suka kafirce.
663
36 - Suratu Y.S.
£52 4 j#£ - r\
(Rasa). Amma Yana jinkirta musu
zuwa ga ajalin da aka ambata.
Sa'an nan idan ajalinsu ya zo, to,
lalle Allah ya kasance Mai gani ga
bayinSa.
Tana karantar da imani game da Ubangiji Mai aikowa, da
Manzon, da abin aikowa, da halin wacfanda aka aiko sakon zuwa
gare su, domin haka Annabi ya yi mata suna 'Zuciyar Alkur'ani'.
s . * <* *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Y. S.
2. Ina rantsuwa da Alkur'ani (1)
Mai hikima.
3. Lalle kai, hakika kana cikin
Manzanni.
4. A kan hanya madaidaiciya.
5. (Allah Ya saukar da Al-
kur'ani) Saukarwar Mabuwayi,
Mai jin kai.
6. Domin ka yi gargacfi ga wa-
cfansu mutane da ba a yi gargacfi ga
ubanninsu ba, saboda haka su
masu rafkana ne.
(1) Al£ur'ani ma'anarsa abin karatu.
664
36 - Suratu Y.S.
fe'i££ - r\
7. Lalle, haklka, kalma (1) ta wa-
jaba a kan mafi yawansu, domin su,
ba za su yi imani ba.
8. Lalle Mu, Mun sanya kukum-
ma a cikin wuyoyinsu, sa'an nan su
(kukumman sun kai) har zuwa ga
habobinsu, saboda haka, su banka-
rarru ne.
9. Kuma Muka sanya wata tos-
hiya a gaba gare su, da wata toshiya
a bayansu, saboda haka Muka rufe
su, sai suka zama ba su gani.
10. Kuma daidai yake a gare su,
shin, ka yi musu gargadi ko ba ka yi
musu gargadi ba, su ba za su yi
imani ba.
11. Kana yin gargacfi kawai ga
wanda ya bi Alkur'ani ne, kuma ya ji
tsoron mai rahama a fake. To, ka yi
masa bushara da gafara da wani
sakamako na karimci.
12. Lalle Mu, Mu ne ke rayar da
matattu kuma Mu rubuta abin da
suka gabatar, da gurabunsu, kuma
kowane abu Mun kididdige shi, a
cikin babban Littafi Mabayyani.
13. Kuma ka buga musu misali :
Wacfansu ma'abuta alkarya, a loka-
cin da Manzanni (2) suka je mata.
14. A lokacin da Muka aika
(Manzannin) biyu zuwa gare su, sai
suka karyata su, sa'an nan Muka
' > •>•/>**'
1 $\iy>-Jjk
ofc^^y^s? i&^^$^\
\^^Lr^y^<+&^^
AyMJ
^ ' > *>•/»
^ < \ ' 9> Y\
> >
'9* a
t£ysi
(1) Kalma a nan ita ce facfar Allah da take cewa zai yi azaba ga kafirin da bai yi imani
ba.
(2) Su Manzannin Tsa ne zuwa Antakiya, babban garin kasar Rumu. Su ne Yohana
da Pulis. Na uku, shT ne Sham'un. Mutumin da ya je yana gaggawa, shi ne Hablb
Masassaki wanda ya fara gamuwa da Manzannin farko, ya yi Imani da su, sa'an ya je yana
wa'azi ga mutanensa.
665
36 - Suratu Y.S.
£*ii$£-n
karfafa (su) da na uku, sai suka ce,
"Lalle mu, Manzanni ne zuwa gare
ku."
15. Suka ce, "Ku ba ku zamo ba
face mutane ne kamarmu, kuma
Mai rahama bai saukar da kome ba,
ba ku zamo ba face karya kuke yi."
16. Suka ce, "Ubangijinmu Ya
sani, lalle mu, hakika Manzanni ne
zuwa gare ku.
/ 7. "Kuma babu abin da ke kan-
mu, face iyar da manzanci bayya-
nanne."
18. Suka ce, "Lalle mu, muna
shu'umci da ku ! Hakika, idan ba ku
hanu ba, JiakTka, za mu jefe ku,
kuma hakika wata azaba mai racfa-
cfi daga gare mu za ta shafe ku."
19. Suka ce, "Shu'umcinku,
yana tare da ku. Ashe, domin an
tunatar da ku? A'a, ku dai mutane
ne masu ketare haddi."
20. Kuma wani mutum daga
mafi nTsan birnin ya je, yana tafiya
da gaggawa, ya ce, "Ya mutanena!
Ku bi Manzannin nan.
21. "Ku bi wacfanda ba su
tambayar ku wata ijara, kuma su
shiryayyu ne.
22. "Kuma me ne a gare ni, ba
zan bauta wa Wanda Ya kaga halit-
tata ba, kuma zuwa gare Shi ake
mayar da ku?
23. "Shin, zan riki waninSa abu-
buwan bauta wa? Idan Mai rahama
Ya nufe ni da wata cuta, to, cetonsu
ba ya amfanma da kome, kuma ba
za su iya tsamar da ni ba.
^Gi^Uoiiyis
®^^V^\$$&tj
666
36 - Suratu Y.S.
fe'i&£ - ri
24. "Lalle ni, a lokacin nan, tab-
bas, ina a cikin Bata bayyananna.
25. "Lalle ni, na yi Tmani da
Ubangijinku, saboda haka ku sau-
rare ni."
26. Aka ce (1) (masa), "Ka shiga
Aljanna." Ya ce, '"Da dai a ce
mutanena suna iya sani.
27. "Game da gafarar da
UbangijTna ya yi mini, kuma Ya
sanya ni a cikin wacfanda aka
girmama."
28. Kuma ba Mu saukar da wa-
cfansu runduna ba daga sama (2) a
kan (halaka) mutanensa, daga
bayansa, kuma ba za Mu kasance.
Masu saukarwa ba.
29. Ba ta kasance ba face tsawa
guda, sa'an nan sai ga su soma-
mmu.
30. Ya nadama a kan bayiNa!
Wani Manzo ba ya zuwa gare su
face sun kasance suna masu yi masa
izgili.
31. Ba su gani ba, da yawa Muka
halakar da (mutanen) karnoni a
gabaninsu kuma cewa su ba za su
komo ba?
32. Kuma lalle babu kowa face
wacfanda ake halartarwa ne a wu-
rinMu.
33. Kuma aya ce a gare su : Kasa
matacciya, Mu rayar da ita, Mu
>«f^r >A<\?VS~?\*'':<\
(1) An ce masa haka a bayan mutane sun kashe shi saboda Tmaninsa. Wannan shi ne
sakamakon mai wa'azi idan ya yi shahada a kan aikinsa na wa'azi.
(2) Watau halakar da su abu ne mai sauki a gare Mu, ba Mu yi bukatar saukar da
wasu sojojin mala'iku daga sama ba.
667
36 - Suratu Y.S.
fe'i&£ - n
fltar da kwaya daga gare ta, sai ga
shi daga gare ta suke ci.
34. Kuma Muka sanya, a cikinta
(kasa), wadansu gonaki na dablno
da inabobi, kuma Muka 6u66ugar
da ruwa daga maremari a cikinta.
35. Domin su ci 'ya'yan itacensa,
alhali kuwa hannayensu ba su aika-
ta shi ba. Shin, to, ba za su godewa
ba?
36. Tsarki ya tabbata ga Wanda
Ya halitta nau'uka, namiji da mace,
dukansu, daga abin da kasa ke
tsirarwa, kuma daga kansu, kuma
daga abin da ba su sani ba.
37. Kuma aya ce a gare su : Dare,
Muna fede rana daga gare shi, sai ga
su suna masu shiga duhu.
38. Kuma rana tana gudana
zuwa ga wani matabbaci nata.
Wannan kaddarawar Mabuwayi
ne, Masani.
39. Kuma da wata, Mun kadda-
ra masa manziloli, har ya koma
kamar tsumajiyar murlin dablno,
wadda ta tsufa.
40. Rana ba ya kamata a gare ta,
ta riski wata. Kuma dare ba ya
kamata a gare shi ya zama mai tsere
wa yini, kuma dukansu a cikin sara-
ri guda suke yin iyo.
41. Kuma aya ce a gare su : Lalle
Mu, Mun dauki zuriyarsu a cikin
jirgin, wanda aka yi wa lodin.
42. Kuma Muka halitta musu,
daga irinsa, abin da suke hawa.
43. Kuma idan Mun so, za Mu
nutsar da su, har babu kururuwar
ftp 0£*3\>5 \& l^3Jv*l^»j
>»trr
f^ > *.'u xltXt • *>'-"* ,^r" rt»>^ ^V
668
36 - Suratu Y.S.
neman agaji a gare su, kuma ba su
zama ana tsTrar da su ba.
44. Sai fa bisa ga wata rahama
daga gare Mu, da jiyarwa dacfi zuwa
ga wani dan lokaci.
45. Kuma idan aka ce musu,
"Ku kare abin da ke a gaba gare ku
da abin da yake a bayanku, domin
tsammaninku a ji tausayinku."
46. Kuma wata aya daga ayoyin
Ubangijinsu ba ta zuwa a gare su,
sai sun kasance suna masu bijirewa
daga gare ta.
47. Kuma idan aka ce musu,
"Ku ciyar daga abin da Allah Ya
arzuta ku," sai wadanda sukajcafir-
ta su ce ga wadanda suka yi imani,
"Ashe, za mu ciyar da wanda idan
Allah Ya so Yana ciyar da shi? Ba
ku zama ba face a cikin Bata bayya-
nanniya."
48. Kuma suna cewa, "A yaushe
wannan wa'adi yake (aukuwa),
idan kun kasance masu gaskiya?"
49. Ba su jiran (kome) face wata
tsawa guda, za ta kama su, alhali
kuwa suna yin husuma.
50. Ba za su iya yin wasiyya (1)
ba, kuma ba za su iya komawa zuwa
ga iyalansu ba.
57. Kuma aka yi busa a cikin
kaho, to, sai ga su, daga kaburbura
zuwa ga Ubangijinsu, suna ta gudu.
52. Suka ce, "Ya bonenmu!
Wane ne ya tayar da mu daga
ISP C^o]y^^^J^v^i
\ y * * - /i / ■
JbU<
*VK' * >.
Art . ' A'
(1) Masu izgili ga addini idan ajali ya je musu bisa ga abke, ba za a ba su damar
wasiyya ba ga iyalansu.
669
36 - Suratu Y.S.
fe'j££ - T"\
barcinmu?" "Wannan shi ne abin
da Mai rahama ya yi wa'adi da shi,
kuma Manzanni sun yi gaskiya."
53. Ba ta kasance ba face wata
tsawa ce guda, sai ga su duka, suna
abin halartarwa a gare Mu.
54. To, a yau, ba za a zalunci
wani rai da kome ba. Kuma ba za a
saka muku ba face da abin da kuka
kasance kuna aikatawa.
55. Lalle, 'yan Aljanna, a yau,
suna cikin shagali, suna masu
nishacfi.
56. Su da matan aurensu, suna
cikin inuwowi, a kan karagai, suna
masu gincira.
57. Suna da 'ya'yan itacen mar-
mari a cikinta, kuma suna samun
abin da suke kiran a kawo.
58. "Aminci," da magana, (1)
daga Ubangiji Mai jin kai.
59. "Ku rarrabe dabam, a yau,
ya ku masu laifi!
60. "Ashe, ban yi mukuumurni
na alkawari ba, ya cfiyan Adamu?
Cewa kada ku bauta wa Shaidan,
lalle shT, makiyi ne a gare ku bayya-
nanne?
61. "Kuma ku bauta Mini. Wan-
nan ita ce hanya madaidaciya."
62. "Kuma lalle, haklka, (Shai-
dan) ya 6atar da jama'a masu yawa
daga gare ku. Ashe, to, ba ku kasan-
ce kuna yin hankali ba?
s">\\ s^ 1 ""' >' 9 <>\\
*> \'\<c' "Z s
t - z ~'<":»<s
Wp*
\j&^t&Zk£0l S 4d$+
» -1*\
X^\xk c^JL^yj
EloJioi
i/2^1
( 1 ) Ana ce musu aminci ya tabbata a gare ku, da magana daga wajen Ubangijinsu
Mai rahama, watau ana fada musu haka da magana ba da wata ishara ba.
670
36 - Suratu Y.S.
£j?ii$£-r\
63. "Wannan ita ce Jahannama
wadda kuka kasance ana yi muku
wa'adi da ita.
64. "Ku shige ta a yau, saboda
abin da kuka kasance kuna yi na
kafirci."
65. A yau, Muna sanya hatimin
rufi a kan bakunansu, kuma hanna-
yensu su yi Mana magana, kuma
kafafunsu su yi shaidu da abin da
suka kasance suna aikatawa.
66. Da Mun so, da Mun shafe
gani daga idanunsu, sai su yi tsere
ga hanya, to, yaya za su yi gani? (1)
67. Kuma da Mun so, da Mun
juyar da halittarsu a kan halinsu,
saboda haka ba za su iya shucfewa
ba, kuma ba za su komo ba.
68. Kuma wanda Muka raya shi,
Muna simkuyar da shi ga halittarsa.
Ashe, ba su hankalta?
69. Ba Mu sanar da shi (Annabi)
waka ba, kuma waka ba ta kamata
da shi (Annabi) ba. Shi (Alkur'ani)
bai zama ba face tunatarwa ce, da
abin karatu bayyananne.
70. Domin ya yi gargadi ga wan-
da ya kasance mai rai, kuma maga-
na ta wajaba a kan kafirai.
71. Shin, ba su gani ba (cewa)
lalle Mun halitta musu dabbobi
daga abin da HannayenMu suka
aikata, sai suna mallakar su?
}<#-*£> j.
\f***t£*
l\o ^vi£j ^TtL;a»iiaLa
&*j£\\jk£+^
lli^t^^tcLi^lli^ llilXbf li^>y
©0
(1) Da Mun so shafe ganinsu na ido kamar yadda Muka shafe basirarsu ta hankali, da
Mun shafe shi, sai su zama makafin idanu kamar yadda suke makafin zuci. saboda haka ko
sun so gani, ba za su yi ba.
671
36 - Suratu Y.S.
eai^-n
72. Kuma Muka hore su, sabo-
da su, saboda haka daga gare su
abin hawansu yake, kuma daga
gare su suke ci.
73. Kuma suna da wadansu am-
fanoni a cikinsu, da abubuwan sha.
Ashe fa, ba za su godewa ba?
74. Kuma suka riki wadansu
abubuwan bautawa wanin Allah,
dammaninsu za su taimake su.
75. Ba za su iya taimakonsu ba,
alhali kuwa su runduna ce wadda
ake halartarwa (a cikin wuta).
76. Saboda haka, kada maga-
narsu ta 6ata maka rai. Lalle Mu,
Muna sanin abin da suke asirtawa
da abin da suke bayyanawa.
77. Ashe, kuma mutum bai ga
(cewa) lalle Mu, Mun halitta shi
daga maniyyi ba, sai ga shi mai
yawan husuma, mai bayyanawar
husumar.
78. Kuma ya buga Mana wani
misali, kuma ya manta da halit-
tarsa, ya ce, "Wane ne ke rayar da
kasusuwa alhali kuwa suna rudud-
dugaggu?"
79. Ka ce, "Wanda ya kaga
halittarsu a farkon lokaci, ShT ke
rayar da su, kuma Shi, game da
kowace halitta, Mai ilmi ne.
80. "Wanda ya sanya muku
wuta daga itace kore, sai ga ku kuna
kunnawa daga gare shi.
81. "Shin, kuma Wanda Ya ha-
Htta sammai da kasa bai zama Mai
ikon yi ba ga Ya halitta kwatan-
kwacinsu? Na'am, zai iya! Kuma
fvp O^tl^J^^l^^l^ jj
./t^<uf^i^j^a^j
<. '*>>>
" *\ 9 - /\ *"*
Z^}^p^\ % j^^^^^^
>\*>\"
l^-i^cA^(^^'
< Z~?' <
-Jbli
672
37 - Stiratus Saffat
mmm-rs
ShT Mai yawan halittawa ne, Mai
ilmi.
82. UmurninSa, idan Ya yi nufin
wani abu, sai Ya ce masa kawai,
"Ka kasance," sai yana kasancewa
(kamar yadda Yake nufi).
83. Saboda haka, tsarki ya tab-
bata ga Wanda mallakar kowane
abu take ga HannayenSa, kuma
zuwa gare Shi ake mayar da ku.
>^J* Jll'
Tana karantar da yadda Allah Ya shirya abubuwan da ke
tunkucfe masu Barna a cikin halittarSa.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ina rantsuwa da masu yin
sahu-sahu (a cikin salla ko yaki).
2. Sa'an nan masu yin tsawa (1)
domin gargacd.
3. Sa'an nan da masu karatun
abin tunatarwa.
4. Lalle Abin bautawarku haki-
ka T)aya ne.
(1) Masu tsawa, su ne Malamai masu samun ilmin wa'azi daga Annabawa wadanda
ke karatun abin tunawa daga Allah Ubangijin sammai da £asa, Mai bayar da haske ga
rana, Mai haskaka taurari masu kawatar da sama kuma su tsare ta daga shaidanu. An
siffanta rana da Annabawa, Malamai da taurari, ilmi da haske da sababin £awa da
shiryarwa da korar masu 6arna.
673
37 - Suratus Saflat
mmm-rv
5. Ubangijin sammai da kasa da
abin da ke tsakaninsu, kuma
Ubangijin wuraren fitar rana.
6. Lalle Mu, Mun kawatar da
sama ta kusa da wata kawa, watau
taurari.
7. Kuma suna tsari daga dukan
Shaidan mai tsaurin kai.
8. Ba za su iya saurare zuwa ga
jama'a mafi daukaka (Mala'iku)
ba, kuma ana jlfar su daga kowane
gefe.
9. Domin tunkudewa, kuma
suna da wata azaba tabbatacciya.
10. Face wanda ya fizgi wata
kalma, sai yula mai haske ta bT shi.
//. Ka tambaye su, "Shin, su ne
mafi wuya ga halittawa, ko kuwa
wacfanda Muka halitta?" Lalle
Mu, Mun halitta su daga laka mai
dauri.
12. A'a, ka yi mamaki, alhali
kuwa suna ta yin izgili.
13. Kuma idan aka tunatar da
su, ba su tunawa.
14. Idan suka ga wata aya, sai su
dinga yin izgili.
15. Kuma su ce, "Wannnan ba
kome ba, face sihiri ne bayyananne.
16. "Shin, idan mun mutu, kuma
muka kasance turBaya da kasu-
suwa, ashe, lalle mu, tabbas, wa-
danda ake tayarwa ne?
17. "Ashe, ko da ubanninmu na
farko?"
18. Ka ce, "Na'am, alhali kuwa
kuna kaskantattu."
©^^yil^Ci;i§iIiiieJ
^5jjVii3)ti;ji
> v»^^ »>
674
37 - Suratus Saffat
m$m>-rs
19. Tsawa guda kawai ce, sai ga
su, suna dubi.
20. Kuma su ce, "Ya bonenmu!
Wannan ita ce ranar sakamako."
21. Wannan ita ce ranar rarra-
bewa wadda kuka kasance kuna
£aryatawa.
22. Ku tara wacfanda suka yi
zalunci, da abokan hacfinsu, da abin
da suka kasance suna bautawa.
23. Wanin Allah, saboda haka
ku ^hiryar da su zuwa ga hanyar
Jahim.
24. Kuma ku tsayar da su, lalle
su, wacfanda ake yi wa tambaya ne.
25. Me ya same ku, ba ku tai-
makon juna?
26. A'a, su a yau, masu sal-
lamawa ne.
27. Kuma sashensu ya fuskanta
ga sashe, suna tambayar juna.
28. Suka ce, "Lalle ku, kun ka-
sance kuna je mana daga wajen
dama (inda muka amince)."
29. Suka ce, "A'a, ba ku kasance
muminai ba.
30. "Kuma wani dalTli bai kasan-
ce ba gare mu a kanku. A'a, kun
kasance mutane ne masu £etare
iyaka.
31. "Saboda haka maganar
Ubangijinmu ta wajaba a kanmu.
Lalle mu, masu cfancfanawa ne.
32. "Saboda haka muka Batar
da ku. Lalle mu, mun kasance Batat-
tu."
> f >^ • • ^^ '»,*'
> >•
^utnTT^V?
Q oyu lil £j£^<^l^<3>t3
675
37 - Suratus Saffat
mmm-r*
33. To, lalle su, a ranar nan,
masu tarayya ne a cikin azabar.
34. Lalle Mu, kamar haka Muke
aikatawa game da masu laifi.
35. Lalle sii, sun kasance idan an
ce musu, "Babu abin bautawa, face
Allah," sai su dora girman kai.
36. Kuma suna cewa, "Shin, mu
lalle masu barin gumakanmu ne,
saboda maganar wani mawaici
mahaukaci?
37. A 'a, ya zo da gaskiya kuma
ya gaskata Manzanni.
38. Lalle ku, ha£i£a, masu dan-
dana azaba mai radadi ne.
39. Kuma ba za a saka muku ba
face da abin da kuka kasance kuna
aikatawa.
40. Face bayin Allah wadanda
aka tsarkake.
41. Wadannan suna da abinci
sananne.
42. 'Ya'yan itacen marmari,
kuma suna wadanda ake girma-
mawa.
43. A cikin gidajen Aljannar
ni'ima.
44. A kan karagu, suna masu
fuskantar juna.
45. Ana kewayawa a kansu da
hinjalan giya, ta daga wadansu
maremari.
46. Fara mai dadi ga mashayan.
47. A cikinta babu jiri, kuma ba
su zama masu maye daga gare ta ba,
676
37 - Suratus Saffat
mmm-rv
48. Kuma a wurinsu, akwai ma-
tan aure masu takaita kallonsu,
masu manyan idanu.
49. Kamar dai su kwai ne 6oyay-
ye.
50. Sai sashensu ya fuskanta a
kan sashe, suna tambayar juna.
51. Wani mai magana daga ci-
kinsu ya ce, "Lalle ni wani aboki ya
kasance a gare ni (a duniya)."
52. Yana cewa, "Shin, kai, lalle,
kana daga masu gaskatawa ne?
53. "Ashe, idan muka mutu,
kuma muka kasance turbaya da
kasusuwa, ashe, lalle, mu tabbas
wacfanda ake saka wa ne?"
54. (Mai maganar) ya ce, "Shin,
ko ku, masu tsinkaya ne (mu gan
shi)?"
55. Sai ya tsinkaya, sai ya gan shi
a cikin tsakar Jahim.
56. Ya ce (masa), "Wallahi, lalle,
ka yi kusa, haklka, ka halaka ni.
57. "Kuma ba domin ni'imar
Ubangijma ba, lalle, da na kasance
daga wacfanda ake halartarwa (tare
da kai a cikin wuta).
58. "Shin fa, ba mu zama masu
mutuwa ba,
59. "Sai mutuwarmu ta farko,
kuma ba mu zama wacfanda ake
azabtarwa ba?"
60. Lalle, wannan shine babban
rabo mai girma.
61. Saboda irin wannan, sai
masu aiki su yi ta aikatawa.
||p fjjA&J^ Jib J\s
. *' >*<
I cA^^-> (
4,v-
© <^I^c^Jd#i Li>v i
*' > 9S *"'/L , ^
677
37 - Suratus Saffat
s\l\*l\\i<*
*gi_rv
62. Shin, wancan shi ne mafi
zama alheri ga liyafa ko itaciyar
zakkum?
63. Lalle, Mu, Mun sanya ta
fitina ga azzalumai.
64. Lalle ita wata itaciya ce wad-
da take fita daga asalin Jahlm.
65. Gundarta, kamar dai shi ka-
nun Shaicfan ne.
66. To, lalle su, haklka, masu ci
ne daga gare ta. Sa'an nan masu
cika cikuna ne daga gare ta.
67. Sa'an nan lalle suna da wani
garwaye a kanta, daga ruwan zafi.
68. Sa'an nan lalle makomarsu,
hakTka, zuwa ga Jahlm take.
69. Lalle su, sun iske ubanninsu
6atattu.
70. Saboda haka su, a kan gura-
bunsu, suke gaggawa.
71. Kuma tabbas, haklka, mafi
yawan mutanen farko sun 6ace a
gabaninsu.
72. Kuma tabbas, haklka, Mun
aika masu gargacfi a cikinsu.
73. Sai ka duba yadda akibar
wacfanda aka yi wa gargacfi ta ka-
sance.
74. Face bayin Allah wacfanda
aka tsarkake.
75. Kuma lalle, hakika, Nuhu ya
kira Mu. To, madalla da masu kar-
6awa, Mu.
76. Kuma Mun tslrar da shi da
mutanensa daga bakin ciki babba.
*>i>.
$ ^^^l?j3J Qfe Ji£ C)Vf
> y *y C **
f3f^ I Sr^N * ^Sj'^1^ ^~?£j
678
37 - Suratus Saffat
\i<*
£-rv
77. Muka sanya zurriyarsa suna
masu wanzuwa.
78. Kuma Muka bar masa
(yabo) a cikin jama'ar karshe.
79. Aminci ya tabbata ga Nuhu,
a cikin halittu.
80. Lalle Mu, kamar haka Muke
saka wa masu kyautatawa.
81. Lalle shi, yana daga bayin-
Mu muminai.
82. Sa'an nan Muka nutsar da
wacfansunsu.
83. Kuma lalle daga kungiyarsa,
haklka, Ibrahim yake.
84. A lokacin da ya je wa
Ubangijinsa da zuciya kubutacciya.
85. A lokacin da ya ce wa ubansa
da mutanensa, "Mene ne kuke
bautawa?
86. "Shin, kiren karya, (watau)
gumaka, wanin Allah, kuke bau-
tawa?
87. "To, mene ne zatonku game
da Ubangijin halittu?"
88. Sai ya yi dubi, duba ta sosai,
a cikin taurari.
89. Sa'an nan ya ce, "NT mai
rashin lafiya ne."
90. Sai suka juya ga barinsa,
suna masu juyawa da baya.
91. Sai ya karkata zuwa ga
gumakansu, sa'an nan ya ce, "Ashe
ba za ku ci ba?
92. "Me ya same ku, ba ku
magana?"
^ ' - \'\t» *'~~i \'\'"
*r** • '' '/£''
fej j*~*L** cJli) » <£j £U- J \
Ep ^A^*<j|JU3
679
37 - Stiratus Saffat
mm&-r*
93. Sai ya zuba duka a kansu da
hannun dama.
94. Sai suka fuskanto zuwa gare
shi, suna gaggawa.
95. Ya ce, "Kuna bauta wa abin
da kuke sassakawa,
96. "Alhali,Allah ne Ya halitta ku
game da abin da kuke aikatawa?"
97. Suka ce, "Ku gina wani gini
saboda shi, sa'an nan ku jefa shi a
cikin Jahlm.
9& Saboda haka suka yi nufin
makTda game da shi. Sai Muka
sanya su, su ne mafi kaskanci.
99. Kuma (Ibrahim) ya ce, "Lal-
le, nTmai tafiya ne zuwa ga Ubangi-
jma, zai shiryar da ni.
100. "Ya UbangijTna! Ka ba ni
(abokin zama) daga salihan
mutane."
101. Sai Muka yi masa bushara
da wani yaro (1) mai hakuri.
102. To, a lokacin da ya isa aiki
tare da shi, ya ce, "Ya karamin
dana ! Lalle ne ina gani, a ciki barci,
lalle ina yanka ka. To, ka duba, me
ka gani?" (Yaron) ya ce, "Ya Ba-
bana! Ka aikata abin da aka umur-
ce ka, za ka same ni, in Allah Ya so,
daga masu hakuri."
103. To, a lokacin da suka yi
sallama, (Ibrahim) ya kayar da shi
ga gefen goshinsa.
i© ^^ ^ W^rnr^ f]j
>' * ' T. \~%
m^>^\ y>yS\j> is^&uje
Q^j^B ,4jjj CjL^i llS
(1) Yaron da aka yi bushara da shi a nan, shine Isma'Tla, saboda abin da yake tafe a
gaba wanda ya shafi Is'haica da sunansa a bayyane ya nuna a nan ba shi ba ne. Watau
Isma'ila kawai ne.
680
37 - Stiratus Saffat
immxA
_rv
104. Kuma Muka kira shi cewa
"Ya Ibrahim!
105. "Haklka ka gaskata mafar-
kin." Lalle kamar haka Muke saka
wa masu kyautatawa.
106. Lalle, wannan ita ce jarra-
bawa bayyananna.
707. Kuma Muka yi fansar ya-
ron da wani abin yanka, mai girma.
108. Kuma Muka bar (yabo) a
kansa a cikin mutanen Rarshe.
^109. Aminci ya tabbata ga Ibra-
him.
110. Kamar haka Muke saka wa
masu kyautatawa.
111. Lalle shi, yana daga bayin-
Mu muminai.
112. Kuma Muka yi masa bus-
hara (1) da Is'haka ya zama Annabi
daga salihan mutane.
113. Kuma Muka yi albarka a
gare shi, kuma ga Is'haka. Kuma
daga cikin zurriyarsu akwai mai
kyautatawa da kuma mai zalunci
domin kansa, mai bayyanawa (ga
zaluncin).
114. Kuma lalle, Mun yi ni'ima
ga Musa da Haruna.
115. Kuma Muka tsTrar da su da
mutanensu daga bakin ciki mai
girma.
4»S j^^y^o ]A ^i J ^ > j
^^^J^\i^^
G3 Cfi^^\<£j£^&
u^^4..,«flJ^ljg^^j ...<^
(1) Wannan sabuwar bushara da Is'haka tana nuna cewa ba shi ne wanda kissar
yanka ta shafa ba. Saboda haka Isma'Tla dai ne, tabbas, mai kissar yanka. Saboda haka
AllahJYa sanya shi wata al'umma dabam, domin a saka masa, sa'an nan aka saka wa
Ibrahim da Is'haka domin ya zama wata al'umma ta dabam.
681
37 - Suratus Saffat
\z<*
£-rv
116. Kuma Muka taimake su,
saboda haka suka kasance masu
rinjaya.
117. Kuma Muka ba su Littafi
mai iyakar bayani.
118. Kuma Muka shiryar da su
ga hanya mikakkiya.
119. Kuma Muka bar (yabo) a
gare su a cikin mutanen karshe.
120. Aminci ya tabbata ga Musa
da Haruna.
121. Lalle kamar haka, Muke
saka wa masu kyautatawa.
122. Lalle, suna daga bayinMu
muminai.
123. Kuma lalle Ilyas, hakTka,
yana daga Manzanni.
124. A lokacin da yake ce wa
mutanensa, "Ashe, ba za ku yi taka-
wa ba?
125. "Shin, kuna bauta wa Ba'al
ne, kuma kuna barin Mafi kyau-
tatawar masu halitta?
126. "Allah Ubangijinku, kuma
Ubangijin ubanninku na farko?"
127. Sai suka karyata shi. Sabo-
da haka su, lalle, wadanda za a
halartawa ne (a wuta).
128. Sai bayin Allah wadanda
aka tsarkake.
129. Kuma Muka bar (yabo) a
gare shi, a cikin mutanen karshe.
130. Aminci ya tabbata ga
Ilyas.
131. Lalle Mu, kamar haka,
Muke saka wa masu kyautatawa.
9 S' S
dl&^%&&\2£[
{^^y])»J9 ~Ja>r^ Lu^\& oy
682
37 - Suratus S&ffat
mmm-r*
132. Lalle shi, yana daga bayin-
Mu muminai.
133. Kuma lalle Ludu, haklka,
yana daga Manzanni.
134. A lokacin da Muka tslrar da
shi, da mutanensa gaba daya.
135. Sai wata tsohuwa tana a
cikin masu wanzuwa (a cikin azaba).
136. Sa'an nan Muka darkake
wadansu mutanen.
137. Kuma lalle ku, haklka,
kuna shudewa a kansu, kuna masu
asubanci.
138. Kuma da dare. Shin fa, ba
za ku hankalta ba?
139. Kuma lalle Yunusa, hakika,
yana daga Manzanni.
140. A lokacin da ya gudu zuwa
ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lodi.
141. Sa'an nan yayikuri'a, sai ya
kasance a cikin wadanda aka rin-
jaya.
142. Sai klfi ya yi loma da shi,
alhali kuwa yana wanda ake zargi.
143. To, ba domin lalle shi ya
kasance daga masu tasbihi ba,
144. Lalle da ya zauna a cikin
cikinsa har ya zuwa ranar da za a
tayar da su.
_ 145. Sai Muka jefa shi ga wani
fili, alhali kuwa yana mai raunin
rashin lafiya.
146. Kuma Muka tsirar da wata
itaciya ta kankana a kusa da shi.
147. Kuma Muka aika shi zuwa
ga wadansu mutane dubu dari, ko
lit ^^£4&$Uj
t\i\
r -f^y^^Tf^
683
37 - Suratus Saffat
WKWifA
£-rv
suna karuwa (a kan haka).
148. Sai suka yi Tmani, saboda
haka Muka jiyar da su dacfi, har
wani lokaci.
149. Saboda haka, ka tambaye
su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya
mata, kuma su da cfiya maza?"
150. K6 kuma Mun halitta ma-
la'iku mata ne, alhali kuwa su, suna
halarce?
151. To! Lalle su, daga kiren
karyarsu suna cewa,
152. "Allah Yahaihu," alhali
kuwa lalle su, hakTka makaryata ne.
153. Shin, Ya zaBi 'ya'ya mata
ne a kan diya maza?
154. Me ya same ku? Yaya kuke
hukuntawa (wannan hukunci)?
755. Shin, ba ku tunani?
^ 156. Ko kuma kuna da wani da-
lili bayyananne ne?
157. To, ku zo da littafinku idan
kun kasance masu gaskiya.
158. Kuma suka sanya nasaba a
tsakaninSa da tsakanin aljannu.
Alhali kuwa Lalle aljannu sun sani,
"Lalle su, hakTka, wacfanda ake
halartarwa ne (a cikin wuta.)"
159. Tsarki ya tabbata ga Allah
daga abin da suke siffantawa.
160. Sai bayin Allah wacfanda
aka tsarkake.
161. To, lalle, ku da abin da kuke
bautawa,
162. Ba ku zama masu buwaya
ba a gare Shi.
p ujfo^lp ^:»:<3Jy^b3
<&&\&jL^d$j*4piL&
>'\* -^i - ^
^b^i '^=^2\ Ls£' f l
A >
^jJr l C^-Up Jjij LlJi 4jJL\ cfaj > <CJo ]y»^j
^U^l^^ljL^f^
@ ajjiokj;^
fcp qullli) *^£>j^i\ li
684
37 - Suratus Saffat
mm&-rs
163. Sai wanda yake mai shiga
babbar wuta JahTm.
164. "Kuma babu kowa daga
cikinmu, (1) face yana da matsayi
sananne.
165. "Kuma lalle mu, haklka,
mu ne masu yin sahu-sahu (domin
ibada).
166. "Kuma lalle mu,hakika,mu
ne masu yin tasbihi."
167. Kuma ko da sun kasance
suna cewa,
168. "Da lalle muna da wani
littafi irin na mutanen farko.
169. "Lalle da mun kasance
bayin Allah wacfanda aka tsar-
kake."
770. Sai suka kafirta da shi. Sa-
boda haka za su sani.
171. Kuma lalle, haklka kalmar-
Mu ta gabata ga bayinMu, Manza-
nni.
172. Lalle su, hakTka, su ne wa-
cfanda ake taimako.
173. Kuma lalle rundunarMu,
hakika, su ne marinjaya.
174. Saboda haka juya daga ba-
rinsu, har a wani lokaci.
1 75. Ka nuna musu (gaskiya), da
haka za su dinga nunawa. (2)
fp^^yi^Z^
E9 ixJ^S 1 4ifSl^K)
(1) Mala'iku da sauran halitta duka kowa ya san matsayinsa na bauta ga Allah wanda
ba Ya da da ko cfiya, kuma ba Ya da dangantaka da kowa.
(2) Wannan karin bayani ne ga abin da surar ke karantarwa na cewa Annabawa su ne
kamar rana mai haske na asali. Malamai kamar taurari suke masu samun haske daga rana
su watsa ga duniya kuma su kore 6arna. Aya ta 1 79 da ke tafe karfafawa ce ga ma'anar
wannan.
685
37 - Suratus Saffat
^l^!ji^-rv
176. Shin fa, da azabarMu suke
neman gaggawa?
177. To, idan ta sauka ga farfa-
jiyarsu, to, safiyar wacfanda ake yi
wa gargacfi ta munana.
1 78. Kuma ka juya daga barinsu
har a wani lokaci.
1 79. Ka nuna (musu gaskiya), da
haka za su dinga nunawa.
180. Tsarki ya tabbata ga
Ubangijinka, Ubangijin rinjaye,
daga barin abin da suke siffantawa.
181. Kuma aminci ya tabbata ga
Manzanni.
182. Kuma godiya ta tabbata ga
Allah Ubangijin halittu.
f*p Sj^^iCfjl^
>\t>
%^£\&^j
Kp ^aJiU) \ <1d4& SIX^j
Tana karantar da hanyar mulkin Musulunci da yadda ake
gudanar da shari'a da adalci, da gargacfi ga bin wata hanya.
» s* ^ L * y *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. S, Ina rantsuwa da Alkur'ani
mai hukunce-hukunce.
2. A 'a, wadanda suka kafirta
suna cikin girman kai (ga rikon
al'adunsu) da saBani (tsakanin
junansu).
686
38 - Siiratu S
tfei^-^A
3. Da yawa Muka halakar da
wani karni, a gabaninsu, suka yi
kira (neman ceto), babu lokacin
kubucewa.
4. Kuma suka yi mamaki domin
Mai gargacfi, daga cikinsu, ya je
musu. Kumakafirai sukace, "Wan-
nan mai sihiri ne, makaryaci.
5. "Shin, ya sanya gumaka duka
su zama abinbautawa guda? Lalle
wannan, hakika, abu ne mai ban
mamaki!"
6. Shugabanni daga cikinsu,
suka tafi (suka ce), "Ku yi tafi-
yarku, ku yi hakuri a kan abu-
buwan bautawarku. Lalle wannan,
haklka, wani abu ne ake nufi!
7. "Ba mu taba ji ba, game da
wannan, a cikin addinin karshe.
Wannan bai zama ba face kiren
karya.
8. "Shin, an saukar da Alkur'ani
ne a kansa, a tsakaninmu (mu kuma
ba mu gani ba)?" A'a, su dai suna
cikin shakka daga hukunciNa. A'a,
ba su i da dandanar azaba ba.
9. Ko kuma a wurinsu ne ake
ajiye taskokin rahamar Ubangi-
jinka, Mabuwayi, Mai yawan
kyauta?
10. K6 kuma su ne da mallakar
sammai da kasa da abin da ke a
tsakaninsu? To, sai su hau a cikin
sammai (domin su hana saukar Al-
kur'ani ga Muhammadu).
11. Rundunoni ne abin da ke
can, rusassu, na kungiyoyinsu.
♦• .'y/
Jte£&3&4^$l^W
<£*$, ft >y {\ ' U Y. "
n-lt a.
687
38 - Suratu S
12. Mutanen Nuhu sun karyata,
a gabaninsu, da Adawa da Fir'auna
mai turakun (da suka kafe mul-
kinsa).
13. Da Samudawa da mutanen
Ludu da ma'abuta Kunci, (1) wa-
dancan ne kungiyoyin.
14. Babu kowa a cikinsu face ya
karyata Manzanni, saboda haka
azabaTa ta wajaba.
15. Kuma wadannan, (2) ba su
jiran kome face tsawa guda, wadda
ba ta da hani.
16. Kuma suka ce, "Ya Ubangi-
jinmu! Ka gaggauta mana da
rabonmu, a gabanin ranar
bincike." (3)
17. Ka yi hakuri bisa ga abin da
suke fada (na izgili), kuma ka am-
baci bawanMu Dawuda, ma'abucin
karfin ibada. Lalle, shi, mai mayar
da al'amari ga Allah ne.
18. Lalle Mu, Mun hore duwat-
su tare da shi, suna yin tasbThi
maraice da fitowar rana.
19. Da tsuntsaye wadanda ake
tattarawa, kowannensu mai koma-
wa ne a gare shi.
20. Kuma Muka karfafa mul-
kinsa, kuma Muka ba shi hikima (4)
da rarrabewar magana.
."ff / » ./> ^
< .S ? ■* '■*
(1) Mutanen Kunci, su ne mutanen Annabi Shu'aibu. A cikin Sham suke.
(2) Watau mutanen Annabi Muhammadu: FCuraishawa da waninsu har ya zuwa
Tashin Kiyama.
(3) Wannan ita ce maganar dukan kafirai na kowane zamani, masu neman rabon
duniya kawai, ba su yarda da Tashin Kiyama ba, balle samun sakamako a cikinsa.
(4) Hikima, ita ce Annabci, rarrabe magana, shT ne sanin hanyar yin shari'a, da
rarrabe mai kara daga wanda aka yi kara, da neman shaidu daga mai kara da neman
rantsuwa ga mai musu.
688
38 - Suratu S
21. Kuma shin, labarin masu hu-
suma ya zo maka, a lokacin da suka
haura garun masallaci?
22. A lokacin da suka shiga ga
Dawuda, sai ya firrgita daga gare
su. Suka ce, "Kada ka ji tsoro, masu
husuma biyu ne; sashenmu ya za-
lunci sashe. Saboda haka, ka yi
hukunci a tsakaninmu da gaskiya.
Kada ka Retare haddi, kuma ka
shiryar da mu zuwa ga tsakar
hanya."
23. "Lalle, wannan tfan'uwana
ne, yana da tunkiya casa'in da tara,
kuma ina da tunkiya guda, sai ya ce,
'Ka lamunce mini ita.' Kuma ya
buwaye ni ga magana."
J24. (Dawuda) ya ce, "Lalle, ha-
£i£a ya zalunce (1) ka game da tam-
bayar tunkiyarka zuwa ga tuma-
kinsa. Kuma lalle ne masu yawa
daga abokan tarayya, ha£i£a, sas-
hensu na zambatar sashe, face wa-
tfanda suka yi imani, kuma suka
aikata ayyukan £warai." Kuma
Dawuda ya tabbata cewa Mun fiti-
ne shi ne, saboda haka, ya nemi
Ubangijinsa gafara, kuma ya facfi
yana mai sujada, kuma ya mayar da
aFamari ga Allah.
25. Saboda haka Muka gafarta
masa wancan, kuma lalle yana da
r/ r^V <"'.
*<^>»..^»- K -\X<
(1) Dawuda ya yi hukunci da zalunci ga wanda ya yi £ara, saboda abin da ya rufe shi
na £in zaluntar mai rauni wanda Allah Ya hana. Nauyin wani laifi ya rufe shi daga tunawa
da wani laifi, watau yin hukunci tun binciken shari'a bai cika ba, saboda iya maganar wani
abokin £ara. Wannan shT ne fitinar da ta same shi kawai kuma a kanta ya yi nadama, kuma
a kanta ne Allah Ya yi masa gargadin kada ya bi son rai mai sanya hushi ko yarda ga abin
da bai cancanci haka ba. Yarda da wata £issar matar Uriya wadda Yahudawa ke sanyawa,
a nan, kafirci ne ga Musulmi, domin ta kore ismar Annabawa, kuma ba ta dace da lafazin
Allcur'ani ba.
689
38 - Suratu S
mm-r*
wata kusantar daraja a wurinMu,
da kyaun makoma.
26. Ya Dawuda! Lalle Mu, Mun
sanya ka Halifa a cikin kasa. To, ka
yi hukunci tsakanin mutane da gas-
kiya, kuma kada ka biye wa son
zuciyar, har ya 6atar da kai daga
hanyar Allah. Lalle wacfanda ke
6acewa daga hanyar Allah, suna da
wata azaba mai tsanani domin abin
da suka manta, a ranar hisabi.
27. Kuma ba Mu halitta sama da
kasa da abin da ke a tsakaninsu ba a
kan karya. Wannan shl ne zaton
wacfanda suka kafirta. To, bone ya
tabbata ga wacfanda suka kafirta
daga wuta.
28. Ko za Mu sanya wacfanda
suka yi imani, kuma suka aikata
ayyukan kwarai kamar wacfanda
suke masu 6arna ne a cikin kasa?
Ko kuma za Mu sanya masu bin
Allah da takawa kamar fajirai
makarkata?
29. (Wannan) Littafi ne, Mun
saukar da shi zuwa gare ka, yana
mai albarka, domin su lura da ayo-
yinsa, kuma don masu hankali su
rika yin tunani.
30. Kuma Muka bai wa Dawuda
Sulaiman. Madalla da bawanMu,
shi. Lalle shi (Sulaiman) mai mayar
da al'amari ne ga Allah.
31. A lokacin da aka gitta masa
dawaki masu asali, (1) a lokacin
maraice.
*«~y<\'*\ .<
A* r
^ll^ivlil^^^t^^^^
(1) Shine doki mai tsayuwa a kan kafafu uku. Wannan yana nuna asalinsa mai kyau
ne.
690
38 - Stiratu S
&£i££-rA
32. Sai ya ce, "Lalle nl, na fifita
son dukiya daga tunawar Ubangi-
jina, har (rana) ta faku da shamaki !
33. "Ku mayar da su a gare ni."
Sai ya shiga yankansu (1) da takobi
ga kwabrukansu da wuyoyinsu.
34. Kuma lalle, hakika, Mun fiti-
ni (2) Sulaiman kuma Muka jefa
wani jikin mutum a kan karagarsa.
Sa'an nan ya mayar da aPamari
zuwa gare Mu.
35. Ya ce, "Ya Ubangijlna! Ka
gafarta mini, kuma Ka ba ni mulki
wanda ba ya kamata da kowa daga
bayana. (3) Lalle Kai, Kai ne Mai
yawan kyauta.
36. Saboda haka Muka hore
masa iska (4) tana gudu da umurnin-
sa, tana tashi da sauki, inda ya nufa.
37. Da shaicfanu, dukan mai
gini, da mai nutsa (a cikin koguna.)
38. Wacfansu, cfacfcfaure a cikin
maruruwa.
i^jte*
- *¥ '\ ' \' 9 '°&' ' ' *"f > & " 9 'i'
(1) Sulaimana ya yanka dawakin, domin kallonsu ya hana shi salla, wadda take
farlu ainin ce a gare shi, amma tattalin kayan yaki farlu kifaya ce. Ana gabatar da farlu
ainin a kan farlu kifaya. Wannan kuma ya nuna cewa ana cin doki idan wani dalili bai hana
ba. Dubi Sura ta 16, aya ta8.
(2) Wata rana Sulaiman ya yi tunanin ya sadu da matansa cfari uku, domin su yi
cikunna, su haifi cfiya masu taimakonsa jihadi fi sabilillahi, amma ya manta, bai ce in Allah
Ya so ba. Sai ya sadu da su, ba su yi cikin ba, sai guda cfaya daga cikinsu, kuma ta haife_shi
babu rai. Ma'anar kissar, ita ce ko aikin Allah, sai mutum ya mayar da yinsa ga mashi'ar
Allah, sa'an nan zai ci nasara a kansa.
(3) Ya yi wannan addu'a domin kada wani ya yi alfahari da sarauta a bayansa, ya
halaka kuma ya halakar da wani. Sarauta ita ce asalin girman kai da alfahari. Ba ka ganin
wanda ya shiga wa Sarki, domin ya gaishe shi, idan ya fito daga gare shi, sai ya cfora yin
takama domin abin da zuciyarsa ta cfebo daga girman kan Sarkin da alfaharinsa?
(4) An hore masa iska matsayin dawakin da ya yanke domin Allah. An hore masa
aljannu domin niyyarsa ta samun cfiya masu jihadi domin Allah.
691
38 - Sftratu S
ffi£&&-™
39. Wannan kyautarMu ce. Sai
ka yi kyauta ga wanda kake so, ko
kuma ka rike, babu wani bincike.
40. Kuma lalle, haklka yana da
kusantar daraja a wurinMu, da
kyaun makoma.
41. Kuma ka ambaci bawanMu
Ayyuba, (1) a lokacin da ya^kirayi
Ubangijinsa, ya ce, "Lalle ni, Shai-
cfan ya shafe ni da wahala da kuma
wata azaba."
42. Ka shura da Rafarka. Wan-
nan abin wanka ne mai sanyi da
abin sha.
43. Kuma Muka ba shi iyalansa
da kwatankwacinsu tare da su, sa-
boda rahama daga gare Mu, da
tunatarwa ga masu hankali.
44. Kuma ka riki wata kulla da
hannunka, ka yi duka da ita, kuma
kada ka karya rantsuwarka. Lalle
Mu, Mun same sin mai hakuri.
Madalla da bawa, shl Lalle shlmai
mayar da al'amari ga Allah ne.
45._Kuma ka ambaci bayinMu:
Ibrahim da Is'haka da Ya'akuba,
ma'abuta karfin (cfaukar umur-
ninMu) da basTra.
46. Lalle Mu, Mun ke6ance su
game da wata tsattsarkar aba:
Hukunce-hukuncen gidan duniya
(mai tunatar da su Lahira).
47. Kuma lalle su a wurinMu,
tabbas,suna daga za6a66u, mafifita.
m| ^\^^o > ^l^^^^\^\]^\x^
0u£ o^j<jQ kJc&,<Ao£
' * ' '\ 9< C?4x
(«j JjJI c^fe=»>f^U5 aI^U \j[
f 9 \*Xt'*' \' 9 ^
p^^^^uyLk^^kjc^^JJ
(1) Wannan Rissa tana nuna haRuri ga riRon iyali, mulkin Rasa da mulkin gida duka
daidai suke, sai yadda Allah Ya yi umurni a yi su. Haka mallakar rai, idan mutum bai bi
umurnin Allah ba a cikinsu, sai su buwaye shi tsarewa, kamar yadda mulkin Rasa ke
buwaya a riRe shi tare da kafirci da zalunci.
692
38 - Suratu S
&9Z&-TA
48. Kuma ka ambaci Isma'ila da
Ilyas da Zulkifli, kuma dukansu
suna daga za6a66u.
49. Wannan tunatarwa ce, kuma
lalle masu bin Allah da takawa,
suna da kyakkyawar makoma.
50. Gidajen Aljannar zama, al-
hali kuwa tana abar bucfe wa kofofi
saboda su.
57. Suna gingincire a cikinsu,
suna kira a cikinsu, ga 'ya'yan ita-
cen marmari masu yawa, da abin
sha.
52. Kuma a wurinsu akwai ma-
tan aure masu gajarta ganinsu ga
mazansu, tsarar juna.
53. Wannan shi ne abin da ake yi
muku wa'adi ga ranar hisabi.
54. Lalle wannan, hakika, arzut-
tarwarMu ce, ba ta karewa.
55. Wannan shi ne, kuma lalle
makangara, hakika, suna da mafi
sharrin makoma.
56. Jahannama, suna shigarta.
To, shimfkfar ta munana, ita.
57. Wannan shine ! To, su cfancfa-
ne shi: ruwan zafi ne da ru6a66en
jini.
58. Da wani daga siffarsa nau'i-
nau'i.
59. Wannan wani yanki ne mai
kutsawa tare da ku, babu maraba a
gare su, lalle su, masu shiga wuta ne.
60. Suka ce, "A'a, ku ne babu
maraba a gare ku, ku ne kuka gaba-
tar da shi a gare mu." To, matab-
batar ta munana (ita wutar).
<&$$$> ." ' ' ' '
1 ^lrt3$J^
•A<>S*\'\'\<i
^9 7^'z^-^Ul^'<tJ
693
38 - Suratu S
&9Z&-V*
61. Suka ce, "Ya Ubangijinmu !
Wanda ya gabatar da wannan a
gare mu, to, Ka kara masa azaba,
ninki, a cikin wuta."
62. Kuma suka ce, "Me ya same
mu, ba mu ganin wadansu mazaje,
mun kasance muna kidaya su daga
ashararai?
63. "Shin, mun rike su abin izgili
ne ko idanunmu sun karkata daga
gare su ne?"
64. Lalle wannan, hakika, gas-
kiya ne, husumar mutanen wuta.
65. Ka ce, "Nlmai gargacfi kawai
ne, kuma babu wani abin bautawa
sai Allah, Makadaici, Mai tilastawa.
66. "Ubangijin sammai da kasa
da abin da ke a tsakaninsu, Mabu-
wayi, Mai gafara."
67. Ka ce, "Shi (Alkur'ani) bab-
ban labari ne mai girma.
68. "Ku, masu bijirewa ne daga
gare shi!
69. "Wani ilmi bai kasance a
gare ni ba game da jama'a (ma-
la'iku) mafi daukaka a lokacin da
suke yin husuma.
70. "Ba a yi mini wahayin kome
ba face cewa ni mai gargacfi kawai
ne, mai bayyanawa."
71. A lokacin da Ubangijinka Ya
ce wa mala'iku, "Lalle NT Mai
halitta mutum ne daga laka.
72. "Sa'an nan idan Na daidaita
shi, kuma Na hura (wani abu) daga
RuhiNa a cikinsa, to, ku fadi kuna
masu sujada a gare shi."
U^biJ^Oj3lJLlAU^JL3^l^;|yl3
&*^. I '%S" 9 ' , l s *■* S ft-' ** s ** **- "*s s • •* ^
7, 'fi"»:
© ^J*falj^^l ^/LM ^j<3 li \
694
38 - Suratu S
(I0i^-^
73. Sai mala'ikun suka yi sujada
dukansu, gaba cfaya.
74. Face Iblis, ya yi girman kai,
kuma ya kasance daga kafirai.
75. (Allah) Ya ce, "Ya Ibilis!
Me ya hana ka, ka yi sujada ga abin
da Na halitta da HannayeNa biyu?
Shin, ka yi girman kai ne, ko kuwa
ka kasance daga madaukaka ne?"
76. Ya ce, "Ni, mafifici ne daga
gare shi: Ka halitta ni daga wuta,
kuma Ka halitta shi daga laka."
77. Ya ce, "To, ka flta daga gare
ta, domin lalle kai la'ananne ne.
78. "Kuma lalle a kanka akwai
la'anaTa har zuwa ranar saka-
mako."
79. Ya ce, "Ya Ubangijina! To,
Ka yi mini jinkiri zuwa ga ranar da
ake tayar da su."
80. Ya ce, "To, lalle kana daga
wadanda aka yi wa jinkiri,
81. "Zuwa ga yinin lokaci sana-
nne.
82. Ya ce, "To, ina rantsuwa da
buwayarKa, lalle ina 6atar da su
gaba day a.
83. "Face bayinKa tsarkakakku
daga gare su."
84. (Allah) Ya ce, "To, (wannan
magana ita ce) gaskiya. Kuma gas-
kiya Nake facfa.
85. "Lalle za Ni cika Jahannama
daga gare ka, kuma daga wanda ya
bl ka daga gare su, gaba daya."
*>\ t &
)^cA'a^\^^~&ji
|A0j ju^-l AU dUo j-»-^
695
39 — Suratuz Zumar
mm-™
86. Ka ce, "Ba ni tambayar ku
wata ijara, a kansa, kuma ba ni
daga masu kakalen facfarsa.
87. "Shi (Alkur'an) bai zama ba
face ambato ne ga dukan halitta.
88. "Kuma lalle za ku san bab-
ban labarinsa (1) a bayan dan
lokaci."
(SS h^^^jj^l^^^^^
»r "ti ^>
*i\y>ci
Tana karantar da cewa^sanin akwai Allah, da sanin Shi ne Ya
halitta kome, ba ya isa ga imani, sai an tsarkake ibada gare Shi.
Watau tauhidin Rububiyya, ba ya isa sai da na Uluhiyya.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Saukar da Littafin daga Allah
ne, Mabuwayi, Mai hikima.
2. Lalle Mu, Mun saukar da Lit-
tafi zuwa gare ka, da gaskiya. Sabo-
da haka, ka bauta wa Allah, kana
mai tsarkake addini a gare Shi.
3. To, addini tsarkakakke na Al-
lah ne, kuma wadanda suka riki
^u
ili \ J~£- 1$ &rJ \i el
^^i^^iii^iiuvi
( 1 ) Watau za ku san aikin da Alkur'ani zai yi wa wacfanda suka yi aiki da shi a bayan
cfan lokaci, sa'ilin da za su cfaukaka a idan duniya, su zama wadatattu a bayan talauci,
kuma sarakuna a bayan moranci. Wannan kuwa ya auku inda suka mallake duniya a cikin
rabin karni.
696
39 — Suratuz Zumar
mz&-n
wacfansu maji6inta, ba Shi (1) ba,
(suna cewa) "Ba mu bauta musu ba
face domin su kusantar da mu zuwa
ga Allah, kusantar daraja." Lalle
Allah na yin hukunci a tsakaninsu
ga abin da suka zama suna sabawa a
cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da
wanda yake mai karya, mai kafirci.
4. Da Allah Ya yi nufin Ya riki
da, to, lalle sai Ya za6a daga abin da
Yake halittawa, abin da Yake^so.
Tsarki ya tabbata a gare Shi. Shine
Allah, Makacfaici, Mai tilastawa.
5. Ya halitta sammai da kasa da
gaskiya. Yana shigar da dare a kan
rana, kuma Yana shigar da rana a
kan dare, kuma Ya hore rana da
wata, kowannensu yana gudana
zuwa ga ajali ambatacce. To, Shine
Mabuwayi, Mai gafara.
6. Ya halitta ku daga rai guda,
sa'an nan Ya sanya ma'auranta
daga gare shi. Kuma ya saukar
muku daga dabbobin gida nau'i
takwas, Yana halitta ku a cikin
cikunnan uwayenku, halitta a
bayan wata halitta, a cikin duffai
uku. Wannan shi ne Allah Ubangi-
jinku. Mulki a gare Shi yake. Babu
abin bautawa face Shi. To, yaya ake
karkatar da ku?
7. Idan kun kafirta, to, lalle Al-
lah Wadatacce ne daga barinku,
kuma ba Shi yarda da kafirci ga
bayinSa, kuma idan kun gode, zai
yarda da ita (godiyar) a gare ku,
J'
(1) Bauta wa gumaka da hidimar shehunai da suka mutu wacfanda suka shirya wani
sabon abu da babu ga Sunnar Annabi duka cfaya suke, domin kowanensu kiran wanin
Allah saboda neman agaji ne.
697
39 — Suratuz Zumar
m®>-™
kuma wani rai mai cfaukar nauyi, ba
ya cfaukar nauyin wani. Sa'an nan
kuma makomarku zuwa ga Uban-
gijinku take, domin Ya ba ku labari
game da abin da kuka kasance kuna
aikatawa. Lalle Shi, Masani ne ga
abin da yake a ainihin zukata.
8. Kuma idan wata cuta ta shafi
mutum, sai ya kira Ubangijinsa,
yana mai mai da aFamari zuwa gare
Shi, sa'an nan idan Ya juyar da
cutar da ni'ima ta daga gare Shi, sai
ya manta da abin da ya kasance
yana kira zuwa gare shi a gabanin
haka, kuma ya sanya wa Allah wa-
cfansu abokan tarewa domin ya
6atar (da su) daga hanyarSa. Ka ce
(masa), "Ka ji dacfi da kafircinka, a
cfan lokaci, lalle kai daga 'yan wuta
ne."
9. Shin, wanda yake mai tawali'u
sa'o'in dare, yana mai sujada kuma
yana mai tsayi ga salla, yana tso-
ron Lahira, kuma yana fatan raha-
mar Ubangijinsa, (yana daidai da
waninsa?) Ka ce, "Ashe, wacfanda
suka sani, suna daidaita da wadan-
da ba su sani ba?" Masu hankali
kawai ke yin tunani.
10. Ka ce, (Allah Ya^ce), "Ya
baylNa wacfanda suka yilmani ! Ku
bi Ubangijinku da takawa. Wacfan-
da suka kyautata a cikin wannan
duniya suna da sakamako mai
kyau, kuma kasar Allah mai facfi (1)
i ■" i . T T
>>*',^*>
jd \^Xf, £j\* ^i£*i *o^ ^ ♦
<>•**„ ~. >'y<< \<{\
"^ "'a
(1 ) Babu dalili da zai sanya mutum ya zauna a inda ba ya iya bauta wa Ubangijinsa da
kyau. Watau hijira zuwa wurin yardar Allah, wajibi ne, sai idan duniya ta zama haka a
ko'ina babu wurin tafiya, ko kuma tafiya can da wuya kwarai tana kallafa nauyin da zai
zama wani laifin da ke daidai da rashin hijirar, to, sai mutum ya zauna, ya tsare kansa
gwargwadon hali.
698
39 — Suratuz Zumar
mm-*
ce. Masu haloiri kawai ake cika wa
ijararsu, ba da wani lissafi ba.
11. Ka ce, "Lalle nT, an umurce
ni da in bauta wa Allah, ina tsarka-
ke addini a gare Shi.
12. "Kuma an umurce ni da in
kasance farkon masu mlRa wuya
(ga umurnin Allah)."
13. Ka ce, "Lalle ni, ina tsoro,
idan na saBa wa UbangijTna, ga
azabar yini mai girma."
14. Ka ce, "Allah nake bauta wa,
ina mai tsarkake addinina a gare
Shi.
75. "To, ku bauta wa abin da
kuke so, waninSa." Ka ce, "Lalle
masu hasara, su ne wadanda suka yi
hasarar rayukansu da iyalansu, a
Ranar Kiyama. To, waccan fa, ita
ce hasara bayyananna."
16. Suna da wadansu inuwowi
na wuta daga samansu, kuma daga
Rasansu akwai wadansu inuwowi.
Wancan shine Allah ke^tsoratar da
bayinSa da shi. Ya bayiNa ! To, ku
bT Ni da taRawa.
17. Kuma wadanda suka nlsanci
shaidannu ga bauta musu, kuma
suka mai da al'amari ga Allah,
suna da bushara. To, ka bayar da
bushara ga bayiNa.
18. Wadanda ke sauraren (1) ma-
gana, sa'an nan su bi mafi kyaunta.
ftp CJ^^o^ C)y^o%C>^j
4\\' "*'\t 9 ~ 9< "A
©2&^<^"j#
( 1 ) Bay in Allah na kwarai su ne wadanda suke sauraren maganar Allah, sa'an nan su
yi aiki da abin da yake mai bayyanannar ma'ana daga gare ta, kuma su bar abin da ba su
gane ma'anarsa ba bayan sun yi imani da shi cewa daga Allah yake, kuma su tsarkake
Allah daga abin da bai sifantuwa da shi na surorin halittarSa.
699
39 — Suratuz Zumar
m®k-n
Wacfancan su ne Allah Ya shiryar
da su, kuma wacfancan su ne masu
hankali.
19. Shin fa, wanda kalmar azaba
ta wajaba a kansa? Shin fa, kana iya
tsamar da wanda ke a cikin wuta?
20. Amma wacfanda suka bi
Ubangijinsu da takawa, suna da
benaye, daga samansu akwai wa-
cfansu benaye ginannu, koramu na
gudana daga karkashinsu. Alkawa-
rin Allah. Allah ba Ya saBa wa
alkawarinSa.
21. Shin, ba ka gani ba cewa lalle
Allah Ya saukar da ruwa daga
sama, sa'an nan Ya gudanar da shi
yana maremari a cikin kasa, sa'an
nan Ya fitar da shuka game da shi,
launukan shukar masu saBanin
juna, sa'annan shukar ta kekashe
har ka gan ta fatsifatsi, sa'an nan
Allah Ya sanya ta dandakakkiya?
Lalle ne ga wancan akwai tuna-
tarwa ga masu hankali (ga iyawar
gudanar da ruwa a cikin gidajen
Aljanna).
22. Shin fa, wanda Allah Ya
bucfa kirjinsa domin Musulunci,
sa'an nan shi yana a kan haske daga
Ubangijinsa, (zai zama kamar wa-
ninsa)? To, bone ya tabbata ga
makekasa zukatansu daga ambaton
Allah. Wadancan suna a cikin wata
6ata bayyananna.
23. Allah Ya sassaukar da mafi
kyaun labari, Littafi mai kama da
juna, wanda ake konkoma kara-
tunsa, fatun wacfanda ke tsoron
Ubangijinsu, suna takura saboda
■ **
Qp ^13 ij<y^&
700
39 — Suratuz Zumar
W$&-n
shi, sa'an nan fatunsu da zukatansu
su yi laushi zuwa ga ambaton Allah.
Waccan ita ce shiryarwar Allah,
Yana shiryar da wanda Ya so game
da ita. Kuma wanda Allah Ya 6a-
tar, to, ba shi da wani mai shir-
yarwa.
24. Shin fa, wanda ke kare mu-
guwar azaba da fuskarsa (yana
zama kamar waninsa) a Ranar Ki-
yama? Kuma a ce wa azzalumai,
"Ku cfancfani abin da kuka kasance
kuna aikatawa."
25. Wadanda ke a gabaninsu,
sun karyata, sai azaba ta je musu
daga inda ba su sani ba.
26. Sai Allah Ya dandana musu
azabar wulakanci a cikin rayuwar
duniya, kuma lalle azabar Lahira
ita ce mafi girma, da sun kasance
suna da sani.
27. Kuma lalle ne, haklka, Mun
buga wa mutane a cikin wannan
Alkur'ani, daga kowane misali,
dammaninsu su yi tunani.
28. Abin karantawa ne na La-
rabci, ba mai wata karkata ba, dam-
maninsu, su yi takawa.
29. Allah Ya buga misali; wani
mutum (bawa) a cikinsa akwai
masu tarayya, masu mugun halin
jayayya, da wani mutum (bawa)
dukansa ga wani mutum. Shin, za
su daidaita ga misali? Godiya ta
tabbata ga Allah (a kan bayani).
A'a, mafi yawan mutane ba su sani
ba.
30. Lalle kai mai mutuwa ne,
kuma su ma lalle masu mutuwa ne.
Gw
rj <jy^rt-fVJ<— ^<.
701
39 — Suratuz Zumar
imm-ry
31. Sa'an nan lalle ku, a Ranar
Kiyama, a wurin Ubangijinku, za
ku yi ta yin husuma.
32. To, wane ne mafi zalunci
daga wanda ya yi karya ga Allah,
kuma ya karyata gaskiya a loka-
cin da ta je masa? Shin, babu ma-
zauni a cikin Jahannama ga kafirai ?
33. Kuma wanda ya zo da gas-
kiya, kuma ya gaskata a game da
ita, warfancan su ne masu takawa.
34. Suna da abin da suke so wa-
jen Ubangijinsu. Wancan shT ne
sakamakon masu kyautatawa.
35. Domin Allah Ya kankare
musu mafi munin abin da suka
aikata, kuma Ya saka musu ijararsu
da mafi kyaun abin da suka kasance
suna aikatawa.
36. Ashe, Allah bai zama Mai isa
ga BawanSa ba? Kuma suna tsora-
tar da kai ga wacfanda suke wanin-
Sa, kuma wanda Allah Ya batar, to,
ba shi da mai shiryarwa.
37. Kuma wanda Allah Ya shi-
ryar, to, ba shi da mai batarwa.
Ashe, Allah bai zama Mabuwayi
ba, Mai azabar ramuwa?
38. Kuma lalle idan ka tambaye
su, "Wane ne ya halitta sammai da
kasa?" Hakika, za su ce, "Allah
ne." Ka ce, "Ashe, to, kun gani abin
da kuke kira, wadanda suke wanin
Allah ne, idan Allah Ya nufe ni da
wata cuta, shin, su abubuwan nan
masu kuranye cutarSa ne? K6
kuma Ya nufe ni da wata rahama,
shin, su abubuwan nan masu kame
rahamarSa ne?" Ka ce, "Mai isata
M
MjU
JKI
\>i S
702
39 — Suratuz Zumar
j^9l^-n
Allah ne, gare Shi masu tawakkali
ke dogara."
39. Ka ce, "Ya mutanena ! Ku yi
aiki a kan halinku, lalle ni, ina aiki a
kan halma. Sa'an nan za ku sani.
40. "Wanda azaba ta je masa, za
ta wulakanta shi, kuma wata azaba
mai dawwama za ta sauka a kansa."
41. Lalle Mu, Mun saukar da
littafi a gare ka domin mutane da
gaskiya. Sa'an nan wanda ya nemi
shiriya, to, domin kansa, kuma
wanda ya bace, to, yana bacewa ne
a kanta. Kuma ba ka zama wakfli a
kansu ba.
42. Allah ne ke kar6ar rayuka a
lokacin mutuwarsu, da wadannan
da ba su mutu ba, a cikin barcinsu.
Sa'an nan Ya rike wanda Ya hukun-
ta mutuwa a kansa, kuma Ya saki
gudar, har zuwa ga ajali ambatacce.
Lalle a cikin wancan, hakika, akwai
ayoyi ga mutane wadanda ke yin
tunani.
43. Ko kuma sun riki masu ceto
ne, wadansun Allah? Ka ce, "Shin,
kuma ko da sun kasance ba su da
mallakar kome, kuma ba su han-
kalta?"
44. Ka ce, "Ceto gaba daya ga
Allah yake. Mulkin sammai da kasa
Nasa ne. Sa'an nan zuwa gare Shi
ake mayar da ku."
45. Kuma idan aka ambaci Al-
lah, Shi kadai, zukatan wadanda ba
su yi imani ba da Lahira, su yi
kyama, kuma idan an ambaci wa-
danda suke kiran, wasunSa, sai ga
su suna yin busharar farin ciki.
*>>
<^ ^ >' *- "\\ <J L h * •iff-'
703
39 — Suratuz Zumar
J^IB^-n
46. Ka ce, "Ya Allah, Mai kaga
halittar sammai da kasa, Masanin
gaibi da bayyane! Kai ne ke yin
hukunci a tsakanin bayinKa a cikin
abin da suka kasance suna saba wa
juna a cikinsa."
47. Kuma da wacfanda suka yi
zalunci suna da abin da ke cikin
kasa gaba cfaya, da misalinsa a tare
da shi, lalle da sun yi fansa da shi
daga mummunar azaba, a Ranar
Kiyama. Kuma abin da ba su ka-
sance suna zato ba, daga Allah, ya
bayyana a gare su.
48. Munanan ayyuka da suka
aikata, suka bayyana a gare su,
kuma abin da suka kasance suna yi,
na izgili, ya wajaba a kansu.
49. To, idan wata cuta ta shafi
mutum, sai ya kiraye Mu, sa'an nan
idan Muka canza masa ita, ya sami
ni'ima daga gare Mu, sai ya ce, "An
ba ni ita ne a kan wani ilmi nawa
kawai." A'a ita wannan (magana)
fitina ce, kuma amma mafi yawansu
ba su sani ba.
50. Lalle wacfanda ke a gabanin-
su, sun fade ta, saboda haka abin da
suka kasance suna aikatawa bai
wadatar da su da kome ba.
57. Sai (sakamakon) munanan
abin da suka aikata ya same su.
Kuma wacfanda suka yi zalunci
daga wacfannan, (sakamakon) mu-
nanan abin da suka aikata zai same
su, kuma ba su zama mabuwaya ba.
52. Ashe, kuma ba su sani ba
cewa Allah na shimficfa arziki ga
wanda Yake so, kuma Yana kukun-
,r^>f # f >
r*>^^
" \ > ^ ^ \' >
\a olil— » /LA » Jb
1^»1A
K^U
\^
<L*'<s**
704
39 — Suratuz Zumar
m&-ri
tawa? Lalle a cikin wancan akwai
ayoyi ga mutane wacfanda ke yin
imani.
53. Ka ce, (Allah Ya ce), "Ya
baylNa wacfanda suka yi Barna a
kan rayukansu! Kada ku yanke
kauna daga rahamar Allah. Lalle
Allah na gafarta^ zunubai gaba
tfaya. Lalle Shi, ShT ne Mai gafara,
Mai jin kai.
54. "Kuma ku mayar da al'ama-
ri zuwa ga Ubangijinku, kuma ku
sallama Masa, a gabanin azaba ta
zo muku, sa'an nan kuwa ba za a
taimake ku ba.
55. "Kuma ku bi mafi kyaun
abin da aka saukar zuwa gare ku
daga Ubangijinku, a gabanin azaba
ta zo muku, bisa auke, kuma ku ba
ku sani ba.
56. "Kada wani rai ya ce, 'Ya
nadamata a kan abin da na yi sakaci
a cikin sashen Allah, kuma lalle na
kasance, haklka, daga masu izgili !'"
57. "Ko kuma (kada) ya ce, 'Da
Allah Ya shiryar da ni, da na kasan-
ce daga masu takawa.'"
58. "Ko kuma (kada) ya ce, a
lokacin da yake ganin azaba, 'Da
lalle a ce ina da wata komawa (zuwa
duniya) domin in kasance daga
masu kyautatawa.'
59. "Na'am! Lalle ne ayoyiNa
sun je maka, sai ka karyata a game
da su, kuma ka yi girman kai, kuma
ka kasance daga kafirai."
60. Kuma a Ranar Kiyama kana
ganin warfanda suka yi karya ga
m li^^t^o^jlj^iT
;L^===J< J £b Jut 4i(^31jl J^iljl
(Sc^oltf--
o2
\^cZ JCxi <J^* ^^ *W ^dk
705
39 — Suratuz Zumar
mm-™
Allah fuskokinsu suna masu yin
baki. Ashe, babu mazauni a cikin
Jahannama ga masu girman kai?
61. Kuma Allah na tsirar da wa-
cfanda suka yi takawa a game da
wurin samun babban rabonsu, cuta
ba za ta shafe su ba, kuma ba su
zama suna bakin ciki ba.
62. Allah ne Mai halitta dukan
kome, kuma Shi ne WakTli a kan
kome.
63. Shi ke da mabudan sammai
da kasa. Kuma wacfanda suka ka-
firta da ayoyin Allah, wacfannan su
ne masu hasara.
64. Ka ce, "Shin, wanin Allah
kuke umurni na da in bauta wa ? Ya
ku jahilai!"
65. Kuma an yi wahayi zuwa
gare ka da kuma zuwa ga wacfanda
suke a gabaninka, "Lalle idan ka yi
shirki, hakika, aikinka zai Bad,
kuma lalle za ka kasance daga masu
hasara."
66. A'aha! Ka bauta wa Allah
kacfai, kuma ka kasance daga masu
godiya.
67. Kuma^ba su kaddara Allah
a kan haklkanin (1) Tkon yinSa
ba: Kasa duka damkarSa ce, a Ra-
nar Kiyama, kuma sammai abubu-
wan nadewa ne ga damanSa. Tsarki
ya tabbata a gare Shi, kuma Ya
daukaka daga barin abin da suke
shirki da shi.
>>%">
>>*"<\~ -<\<" f'-'ip AU*1 *'>'
^^^*< 9> *&' t-'t.K
\>''<Cs' >\u & -iff" "<$> w<'?\
(1) Ya yi bayanin yadda za a iya kaddara Allah a kan halolcanin Ikon yinSa da cewa,
"Kasa duka damicarSa ce..." har zuwa Icarshen surar. Watau ya dunitule surar abiibuwan
da za su auku a Ranar Kiyama domin su bai wa mai hankali yadda suranta ikon yi na
Allah Mai girma zai yiwu.
706
39 — Suratuz Zumar
jgglll^-n
68. Kuma aka busa a cikin kaho,
sai wacfanda ke a cikin sammai da
kasa suka suma, sai wanda Allah Ya
so (rashin sumarsa), sa'an nan aka
hura a cikinsa, wata hurawa, sai ga
su tsaitsaye, suna kallo.
69. Kuma kasa ta yi haske da
hasken Ubangijinta, kuma aka aza
littafl, kuma aka zo da Annabawa
da masu shaida, kuma aka yi hu-
kunci a tsakaninsu, da gaskiya, al-
hali kuwa, su, ba za a zalunce su ba.
70. Kuma aka cika wa kowane
raiabin da ya aikata. Kuma (Allah)
Si! ne Mafi sani game da abin da
suke aikatawa.
71. Kuma aka kdra wadanda
suka kafirta zuwa Jahannama,
jama'a-jama'a, har a lokacin da
suka je mata, sai ka bude kofofinta,
kuma matsaranta suka ce musu,
"Ashe, wadansu Manzanni, daga
cikinku ba su je muku ba, suna
karanta ayoyin Ubangijinku a kan-
ku, kuma suna yi muku gargadin
gamuwa da yininku wannan?"
Suka ce, "Na'am," kuma amma kal-
mar azaba ita ce ta wajaba a kan
kafirai !
72. Aka ce, "Ku shiga kofofin
Jahannama, kuna madawwama a
cikinta. Sa'an nan mazaunin
makangara ya munana."
73. Kuma aka kora wadanda
suka bi Ubangijinsu da takawa
zuwa Aljanna, jama'a-jama'a, har a
lokacin da suka je mata, alhali kuwa
an bude kofofinta, kuma matsa-
ranta suka ce musu, "Aminci ya
Ar>f i/Vf *>' i'\\ >'"
&<y^
\*'<* „*^ \t y \\. 9 >^ y \ m
JLjl J \s>j Cg-^ » 0>c^ij ljbji£- \'^^>-
707
39 — Suratuz Zumar
jgg!li&-™
tabbata a gare ku, kun ji dacfi,
saboda haka ku shige ta, kuna
madawwama (a cikinta)."
74. Kuma suka ce, "Godiya ta
tabbata ga Allah Wanda Ya yi
mana gaskiya ga wa'adinSa, kuma
Ya gadar da mu kasa, muna zama a
cikin Aljanna a inda muke so." To,
madalla da ijarar ma'aikata.
75. Kuma kana ganin mala'iku
suna masu tsayawa da hakkokin da
aka cfora musu daga kewayen Al'ar-
shi, suna tasbihi game da gode wa
Ubangijinsu. Kuma aka yi hukunci
a tsakaninsu da gaskiya. Kuma
aka ce, "Godiya ta tabbata ga Al-
lah, Ubangijin halittu."
o5j^ ^Jp-05 ^C^^ iSs-jllll \ c^jJ
Tana karantar da wajabcin bayyana gaskiya da haramcin yin
jidali domin 6ata gaskiya.
* J* <s , *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. H. M.
2. Saukar da Littafi daga Allah
ne, Mabuwayi, Masani.
3. Mai gafarta zunubi kuma
Mai karBar tuba Mai tsananin aza-
ba, Mai wadatarwa, babu abin bau-
tawa face Shi, zuwa gare Shi mako-
ma take.
9h
708
40 - Suratu Ghafir
-i-
4. Babu mai jayayya a cikin
ayoyin Allah, face wadanda suka
kafirta. Saboda haka kada juya-
warsu a cikin garuruwa ta rude ka.
5. Mutanen Nuhu sun karyata a
gabaninsu, da kungiyoyin da suke a
bayansu, kuma kowace aFumma ta
yi nufi game da Manzonsu, domin
su kama shi. Kuma suka yi jayayya
da karya domin su gusar da gaskiya
da ita. Sai Na kama su. To, yaya
azabaTa take?
6. Kuma kamar haka, kalmar
Ubangijinka ta wajaba a kan wa-
danda suka kafirta, domin su
'yan wuta ne.
7. Wadanda ke daukar AFarshi
da wadanda ke kewayenta, suna
tasbThi game da gode wa Ubangi-
jinsu, kuma suna yin imani da Shi,
kuma suna yinjstigfari domin wa-
danda suka yi imani, (suna cewa),
"Ya Ubangijinmu! Ka yalwaci du-
kan kome da rahama da ilmi, to, Ka
yi gafara ga wadanda suka tuba
kuma suka bi hanyarKa, kuma Ka
tsare musu azabar JahTm.
8. " Ya Ubangijinmu ! Kuma Ka
shigar da su a gidajen Aljannar
zama, wannan da Ka yi musu
wa'adi, su da wanda ya kyautatu
daga ubanninsu da matan aurensu
da zurriyarsu. Lalle Kai, Kai ne
Mabuwayi, Mai hikima.
9. "Kuma Ka tsare su daga mu-
nanan ayyuka, kuma wanda Ka
tsare shi daga munanan ayyuka a
ranar nan, to, lalle, Ka yi masa
rahama, kuma wancan shi ne bab-
ban rabo mai girma."
%>
Ai> 9 <\^>
709
40 - Suratu Ghafir
££'jg£ _ i-
10. Lalle wacfanda suka kafirta,
ana kiran su^'Haklka, kin Allah (a
gare ku) shl ne mafi girma daga
kinku ga kanku a lokacin da ake
kiran ku zuwa ga Imani, sai kuna ta
kafircewa."
77. Suka ce, "Ya Ubangijinmu!
Ka ma tar da mu sau biyu, kuma Ka
rayar da mu sau biyu, saboda haka
mun yarda da laifuffukanmu. To,
shin, akwai wata hanya zuwa ga
fita?"
72. Wancan sababinsa, lalle (shi
ne) idan an kirayi Allah Shi kacfai,
sai ku kafirta, kuma idan aka yi
shirki game da Shi, sai ku yi imani.
To, hukuncin fa, na Allah Madau-
kaki, Mai girma ne.
13. Shi ne Wanda ke nuna muku
ayoyinSa, kuma Ya saukar da arziki
daga sama saboda ku, kuma babu
mai yin tunani face mai mayar da
al'amari ga Allah.
14. Saboda haka ku kirayi Allah,
kuna masu tsarkake addini a gare
Shi, kuma ko da kafirai sun ki.
75. Mai daukaka darajoji (do-
min muminai), Mai Al'arshi, Yana
jefa ruhi (1) daga al'amarinSa a kan
wanda Ya so daga bayinSa, domin
ya yi gargadi kan ranar gamuwa.
16. Ranar da suke bayyanannu,
babu wani abu daga gare su wanda
yake iya Boyuwa ga Allah. "Mulki
c
^(1) Ruhi a nan, ga fahimtata, Allah ne Mafi sani, shl ne karfin rai da basTrar fahimtar
addini da aiki wajen rayar da shi, wanda Allah Yake sakawa ga malamin da Yake nufin
jaddada addini da shi a kan kowane karni kamar yadda Hadisi ya zo da shi, ya kore jidalin
masu jidali.
710
40 - Suratu Ghafir
$&%& - I-
ga wa yake a yau?]' Yana ga Allah,
Makacfaici, Mai tilastawa.
77. Yau ana saka wa kowane rai
a game da abin da ya aikata, babu
zalunci a yau. Lalle Allah Mai gag-
gawar hisabi ne.
18. Kuma ka yi musu gargacfi kan
ranar (Sa'a) makusanciya, a lokacin
da zukata suke masu cika da bakin
ciki, ga makosansu. Babu wani ma-
soyi ga azzalumai, kuma babu wani
mai ceto da za a yi wa da'a (ga
cetonsu).
19. (Allah) Ya san yaudarar ida-
nu da abin da kiraza ke boyewa.
20. Kuma Allah ShT ke yin hu-
kunci da gaskiya, wacfannan da
kuke kira, waninSa, ba su yinjiu-
kunci da kome. Lalle Allah, ShT ne
Mai ji, Mai gani.
21. Ashe, ba su yi tafiya ba, a
cikin kasa, domin su duba ga yadda
akibar wacfanda suka kasance a
gabaninsu ta zama? Sun kasance su
ne mafi tsananin karfi daga gare su,
da kufaifan aiki a cikin kasa, sai
Allah Ya kama su da laifuffukansu.
Kuma ba su da wani mai tsarewa
daga Allah.
22. Wancan sababinsa, domin
su, Manzanninsu sun kasance suna
zuwa gare su da hujjoji bay-
yanannu, sai suka kafirta, sai Allah
Ya kama su. Lalle ShT Mai karfi ne,
Mai tsananin azaba.
23. Kuma lalle ne, hakTka, Mun
aika Musa a game da ayoyinMu da
wani dalili bayyananne.
is?* ^if i
9 S S ■
*' s * * * <"
p ^iixi^^d^^
Jr
< r 'CX-\ i£jl <L>j^'^b^l \*J>ljbjx>\j
■/y» 5uJLiai! U
l£U
.&
>A l'<sro
^t^SllS o^V(^ \3iS\^i5i j^u
711
40 - Suratu Ghafir
iSvJgi. - i-
24. Zuwa ga Fir'auna da Hama-
na da Karuna, sai suka ce, "Mai
sihiri ne, makaryaci."
25. Sa'an nan a lokacin da ya je
musu da gaskiya daga wurinMu,
suka ce,J'Ku kashe cfiyan wacfanda
suka yi imani tare da shi, kuma ku
rayar da matansu." Kuma mugun
shirin kafirai, bai zama ba face a
cikin 6ata.
26. Kuma Fir'auna ya ce, "Ku
bar ni in kashe Musa, kuma shT, ya
kirayi Ubangijinsa. Lalle ne ni, ina
tsoron ya musanya addininku, ko
kuwa ya bayyana barna a cikin
kasa."
27. Kuma Musa ya ce,^'Lalle ni,
na nemi tsari da Ubangijina kuma
Ubangijinku, dagajJukan makan-
gari, wanda ba ya imani da ranar
Hisabi."
28. Kuma wani namiji mumini
daga dangin Fir'auna, yana 66ye
Tmaninsa, ya ce, "Ashe, za ku kashe
mutum domin ya ce Ubangijina
Allah ne, alhali kuwa hakika ya zo
muku da hujjqji bayyanannu daga
Ubangijinku? Idan ya kasance
makaryaci ne, to, karyarsa na kan-
sa, kuma idan ya kasance mai gas-
kiya ne, sashen abin da yake yi
muku wa'adi zai same ku. Lalle ne
Allah ba Ya shiryar da wanda yake
mai 6arna, mai yawan karya.
29. " Ya ku mutanena ! Kuna da
mulki a yau, kuma ku ne marinjaya
a cikin kasa, to, wane ne zai taimake
mu daga azabar Allah idan ta zo
mana?" Fir'auna ya ce, "Ba ni nuna
muku kome face abin da na gani,
.0 * SS
$ ^dtflUz&Xjg^K
^ '\^<Y\ Aii • ' C A 1*1
P3 <^\ZM * *-»/>* v*
^ »\1^. *>^> *' + "S\
712
40 - Suratu Ghafir
lA-'i^ - &•
kuma ba ni shiryar da ku, sai ga
hanyar shiryuwa."
30. Kumawannandayayilmani
ya ce, "Ya mutanena! Lalle ne ni,
ina yi muku tsoron kwatankwacin
ranar kungiyoyi.
31. "Kwatankwacin al'adar mu-
tanen Nuhu da Adawa da Samu-
dawa da wacfanda ke a bayansu.
Kuma Allah ba Ya nufin zalunci ga
bayinSa.
32. "Kuma ya mutanena! Lalle
ni, ina yi muku tsoron ranar kiran
juna.
33. "A ranar da za ku juya, kuna
masu bayar da baya (gudane) ba ku
da wani mai tsaro daga Allah.
Kuma wanda Allah Ya 6atar, to, ba
shi da wani mai shiryarwa."
34. "Kuma lalle ne, haklka, Yu-
sufu ya zo muku daga gabani, da
hujjqji bayyanannu, ba ku gushe ba
kuna a cikin shakka daga abin da ya
zo muku da shi, har a lokacin da ya
halaka kuka ce, 'Allah ba zai aiko
wani Manzo ba a bayansa.' Kamar
haka Allah ke 6atar da wanda yake
mai 6arna, mai shakka.
35. "Wacfanda ke jayayya acikin
ayoyin Allah, ba da wani dalTli da
ya zo musu ba. Jidalin ya girma ga
zamansa abin ki a wurin Allah da
wurin wacfanda suka yi Tmani. Ka-
mar haka Allah ke bicewar haske a
kan zuciyar dukan makangari, mai
tTlastawa."
36. Kuma Fir'auna ye ce, "Ya
Hamanaj Ka gina mini bene,
cfammanlna za ni isa ga kofofi.
|5J ^Ub^AJ \J 4X>jjJ^& i j*J
' s . * r s<
A >' o"t }$< ^ '*' t f> i* /if''
». *> '> *' >>
*4
< f> »y -if ^.^ • y A s> ^ fa
vJsj^^-J^
'^li^^^J^^
713
40 - Suratu Ghafir
i: £gj££ - 1-
37. "Kofofin sammai, domin in
yi ninkaya zuwa ga abin bautawar
Musa. Kuma lalle ni, hakika, ina
zaton sa makaryaci." Kuma haka
dai aka kawace wa Fir'auna muna-
nan aikinsa, kuma aka danne shi
daga barin tafarki. Kuma mugun
nufin Fir'auna bai zama ba face
yana a cikin hasara.
38. Kuma wannan da ya yiTmani
ya ce, "Ya mutanena! Ku bT ni, in
shiryar da ku tafarkin shiryuwa.
39. "Kuma ya mutanena ! Wan-
nan rayuwa ta duniya dan jin dadi
ne kawai, kuma lalle Lahira ita ce
gidan tabbata.
40. "Wanda ya aikata mummu-
nan aiki, to, ba za a saka masa ba
face da misalinsa, kuma wanda ya
aikata aiki na kwarai daga namiji
ko mace, alhali kuwa shi mumini
ne, to, wacfannan suna shiga Al-
janna, ana ciyar da su a cikinta, ba
da lissafi ba.
41. "Kuma ya mutanena! Me ya
same ni, ina kiran ku zuwa ga tslra,
kuma kuna kira na zuwa ga wuta?
42. "Kuna kira na zuwa ga in
kafirta da Allah, kuma in yi shirki,
game da Shi, da abin da babu wani
ilmi game da shi gare ni, kuma ni ina
kiran ku zuwa ga Mabuwayi, Mai
gafara.
43. "Hakkan ne, abin da kawai
kuke kira na zuwa gare shi, ba ya da
wani kira a cikin duniya, kuma ba
shi da shi a Lahira, kuma lalle
makomarmu zuwa ga Allah take,
kuma lalle mabarnata su ne 'yan
wuta.
" ^ s
714
40 - Suratu Ghafir
i: ^i& - 1.
44. "To, za ku ambaci abin da
nake gaya muku, kuma ina fawwala
aramarina zuwa ga Allah. Lalle
Allah Mai gani ne ga bayinSa."
45. Sai Allah Ya tsare shi daga
munanan abubuwa da suka yi na
makirci, kuma mummunar azaba ta
wajaba ga mutanen Fir'auna.
46. Wuta, ana gitta su a kanta,
safe da maraice, kuma a ranar da
Sa'a take tsayuwa, ana cewa, "Ku
shigar da mutanen Fir'auna a mafi
tsananin azaba."
47. Kuma a lokacin da suke hu-
suma a cikin wuta, sai raunana
(mabiya) su ce wa wacfanda suka
kangara (shugabanni), "Lalle mu,
mun kasance mabiya gare ku, to,
shin, ku masu wadatar da mu ne
daga barin wani rabo daga wuta?"
48. Wacfanda suka kangara suka
ce, "Lalle mu duka muna a cikinta.
Lalle ne, Allah Ya yi hukunci a
tsakanin bayinSa."
49. Kuma wacfanda suke a cikin
wuta suka ce wa matsaran Jahan-
nama, "Ku roki Ubangijinku Ya
saukaka mana, a yini cfaya, daga
azaba."
50. Suka ce, "Ashe, Man-
zanninku ba su je muku da hujjoji
bayyanannu ba?" Suka ce,
"Na'am, sun je!" Suka ce, "To, ku
roka." Kuma rokon kafirai bai
zamo ba face a cikin bata.
57. Lalle Mu, hakika, Muna tai-
makon ManzanninMu da wacfanda
suka yi Tmani, a cikin rayuwar du-
niya da ranar da shaidu ke tsayawa.
M<w>UJi *j^oy^ Jl^pU^
> ><
-' .<£ *> ^ <v
03 j^CiJt\~+ ) ^^\^^Lj>y>^j^\
©j^ci^oA
715
40 - Suratu Ghafir
< K 1vjg£ - 1-
52. Ranar da uzurin azzalumai
ba ya amfaninsu, kuma suna da
la'ana, kuma suna da munin gida.
53. Kuma lalle haklka, Mun bai
wa Musa shiriya, kuma Mun gadar
da BanT Isra'ila Littafi.
54. Shiryarwa da tunawa ga ma-
abuta hankali.
55. Saboda haka, ka yi hakuri,
lalle wa'adin Allah gaskiya ne.
Kuma ka nemi gafara ga zunu-
binka, kuma ka yi tasbThi game da
gode wa Ubangijinka, maraice da
kuma wayewar safiya.
56. Lalle wadanda ke jayayya a
cikin ayoyin Allah, ba game da wani
dalili wanda ya je musu ba, babu
kome a cikin kirazansu, face girman
kai, ba su zama masu isa ga gurinsu
ba, saboda haka kajiemi tsari daga
Allah. Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Mai
gani.
57. Lalle halittar sammai da
kasa, ita ce mafi girma daga halittar
mutane, kuma amma mafi yawan
mutane ba su sani ba.
58. Kuma makaho da mai gani
baju daidaita, kuma wadanda suka
yi imani suka aikata ayyukan kwa-
rai, da mai munanawa ba su dai-
daita. Kadan kwarai, kuke yin
tunani.
59. Lalle Sa'a haklka mai zuwa
ce, babu shakka a gare ta, kuma
amma mafi yawan mutane ba su yin
imani.
60. Kuma Ubangijinku ya ce,
"Ku kira Ni in karba muku. Lalle
if&* \<>\i>^> *>Y*' A\\>*'\'
^SXji JU^-jJtl^ulj < j^A^\j^Cj CjJiJ^i^
l^j^^^j^<^ %xi&i>\
c
716
40 - Suratu Ghafir
i : £gjg£ - i-
wacfannan da ke kangara daga ba-
rin bauta Mini, za su shiga Jahan-
nama suna kaskantattu."
61. Allah ne Wanda Ya sanya
muku dare domin ku natsu a cikin-
sa, da rana mai ganarwa. Lalle
Allah, haklka, Ma'abucin falala ne
a kan mutane, kuma amma mafi
yawan mutane ba su godewa.
62. Wancan ShT ne Allah Uban-
gijinku, Mahaliccin dukan kome,
babu abin bautawa face Shi. To,
yaya ake karkatar da ku?
63. Kamar haka ake karkatar da
wacfanda suka kasance suna
jayayya game da ayoyin Allah.
64. Allah ne Ya sanya muku kasa
tabbatacciya, da sama glnanniya,
kuma Ya suranta ku, sa'an nan Ya
kyautata surorinku, kuma Ya ar-
zutta ku daga abubuwa masu dacfi.
Wancan Shi ne Allah Ubangijinku.
To, albarkar Allah Ubangijin halit-
tu ta bayyana.
65. Shi ne Mai rai, babu abin
bautawa face Shi. Saboda haka ku
kira Shi, kuna masu tsarkake addini
a gare Shi. Godiya ta tabbata ga
Allah Ubangijin halittu.
66. Ka ce, "Lalle nl, an hana ni
in bauta wa wadanda kuke kira,
wadansun Allah a lokacin da hujjoji
bayyanannu suka zo mini daga
Ubangijlna, kuma^an umurce ni in
sallama ga Ubangijin halittu. "
67. Shi ne Wanda Ya halitta ku
daga turbaya, sa'an nan daga
maniyyi, sa'an nan daga saren jini,
sa'an nan Ya fitar da ku kuna jarlri,
{J^\l^C^OJJp^S^^LJt^o\
ts/s>>
<U3
<4$^ ^ its'" <
ff > *>
$3 J£i! I j^=0 J^i-^lii»
"fa's*
717
40 - Suratu Ghafir
l^jgd _ f
sa'an nan domin ku isa ga cikar
karfinku, sa'an nan domin ku ka-
sance tsofaffi, kuma daga cikinku,
akwai wanda ake kar6ar ransa a
gabanin haka, kuma domin ku isa
ga ajali ambatacce, kuma dam-
maninku ko za ku hankalta.
68. Shi ne Wanda ke rayarwa
kuma Yana kashewa. To, idan Ya
hukunta wani al'amari, to, Yana
cewa kawai gare shi, ka kasance, sai
yana kasancewa (kamar yadda ake
bukatar sa.)
69. Ashe, ba ka gani ba ga wa-
danda ke jayayya a cikin ayoyin
Allah, yadda ake karkatar da su?
70. Wadanda suka karyata,
game da Littafin, kuma da abin da
Muka aika Manzanninmu da shi.
To, za su sani.
71. A lokacin da kukumma suke
a cikin wuyoyinsu, da sarkoki ana
jan su.
72. A cikin ruwan zafi, sa'an nan
a cikin wuta ana babbaka su.
73. Sa'an nan a ce musu, "Ina
abin da kuka kasance kuna shirki
da shi,
74. "Wanin Allah?" Suka ce,
"Sun Bace mana. A'a, ba mu kasan-
ce muna kiran kome ba a gabani."
Kamar wancan ne Allah Yake Batar
da kafirai.
75. Wancan domin abin da kuka
kasance ne kuna farin ciki da shi, a
cikin kasa, ba da hakki ba, kuma da
abin da kuka kasance kuna yi na
nishacfi.
o]<*&&d
>yt
s A ^ *> ".%
^.^s^'s&k/SA aij
^^\JJ^\^\^^\bj^ot
•"*?
^*^ *->^< A
718
40 - Suratu Ghafir
'££\&-l*
76. Ku shiga kofofin Jahan-
nama, kuna madawwama a cikinta.
To, mazaunin masu girman kai ya
munana.
77. Saboda haka ka yi hakuri.
Lalle wa'adin Allah gaskiya ne. To,
ko dai lalle Mu nuna maka sashen
abin da Muka yi musu wa'adi da
shi, ko kuwa lalle Mu kar6i ranka,
to, zuwa gare Mu ake mayar da su.
78. Kuma lalle haklka, Mun aika
wasu Manzanni daga gabaninka,
daga cikinsu akwai wanda Muka
kissanta maka labarinsa, kuma
daga cikinsu akwai wanda ba Mu
kissanta labarinsa ba a gare ka. Ba
ya yiwuwa ga wani Manzo ya je da
wata ayar mu'ujiza face da iznin
Allah. Sa'an nan idan umurnin Al-
lah ya je, sai a yi hukunci da gas-
kiya, masu Batawa sun yi hasara a
can.
79. Allah ne Wanda Ya sanya
muku dabbobi domin ku hau daga
gare su, kuma daga gare su kuke ci.
80. Kuma kuna da abubuwan
amfani a cikinsu, kuma domin ku
isar da wata bukata, a cikin kira-
zanku a kansu, kuma a kansu da a
kan jirage ake cfaukar ku.
81. Kuma Ya nuna muku
ayoyinSa. To, wane ayoyin Allah
kuke musu?
82. Ashe fa, ba su yi tafiya a cikin
kasa ba, domin su duba yadda aki-
bar wacfanda ke a gabaninsu ta
kasance? Sun kasance mafi yawa
daga gare su. Kuma sun fi tsananin
karfi, da (yawan) gurabun sana'o'i
ixyok
719
40 - Suratu Ghafir
K^ijg, - i-
a cikin kasa. To, abin da suka ka-
sance suna aikatawa bai wadatar da
su ba.
83. A lokacin da Manzanninsu
suka je musu da hujjoji bay-
yanannu, suka yi farin ciki da abin
da ke wurinsu, na ilmi, (1) kuma
abin da suka kasance suna yi na
izgili da shi ya wajaba a kansu.
84. Sa'an nan a lokacin da suka
j*a azabarMu, suka ce, "Mun yi
imani da Allah, Shi kadai, kuma
mun kafirta da abin da muka ka-
sance muna shirki da shi."
85. To, Tmaninsu bai kasance
yana amfaninsu ba a lokacin da
suka ga azabarMu. Hanyar Allah
wadda ta gabata a cikin bayinSa.
Kuma kafirai sun yi hasara a can.
StRATU FU§SILAT
,^F ^*B
Tana karantar da mutane cewa halayensu duka cuta ne,
Alicur'ani ne maganin wannan cutar.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kal
1. H. M.
(1) Ilmin duniya na sana'o'i ya zo ne daga Annabawa kamar na ibadodi. Nuhu ya
fara sassakar jirgin ruwa da wahayi daga Allah, Zulkarnaini ya fara hada 6akin karfe da
gaci domin hana tsatsa, Yusufu ya fara barin hatsi a cikin soshiya domin hana kwari.
Dawuda ya fara sana'ar sulke. Adam ya fara rubutu, IdirTsu ya fara yin alkalami. Tsa ya
fara warkar da majinyata, Alkur'ani ya nuna ana iya tashi sama da jirgin sama. Shu'aibu
shi ya nuna kasuwanci, da sauransu.
720
41 — Suratu Fussilat
&£-i>
2. Saukarwa (da Alkur'ani) daga
Mai rahama ne, Mai jin kai.
3. Littafi ne an bayyana ayo-
yinsa daki-daki, yana abin karan-
tawa na Larabci, domin mutanen
da ke sani.
4. Yana mai bayar da bushara
kuma mai gargacfi. Sai mafi yawan-
su suka bijire. Saboda haka su, ba
su saurarawa.
5. Kuma suka ce, "Zukatanmu
na a cikin kwasfa daga abin da kake
kiran mu zuwa gare shi, kuma a
cikin kunnuwanmu akwai wani
nauyi, kuma daga tsakaninmu da
tsakaninka akwai wani shamaki.
Saboda haka ka yi aiki, lalle mu,
masu aiki ne."
6. Ka ce, "Ni mutum kawai ne
kamarku, ana yin wahayi zuwa gare
ni cewa abin bautawarku, abin bau-
tawa guda ne. Sai ku daidaitu zuwa
gare Shi, kuma ku nemi gafararSa."
Kuma bone ya tabbata ga masu yin
shirki.
7. Wadanda ba su bayar da zak-
ka, kuma su a game da Lahira su
kafirai ne.
8. Lalle wadanda suka yi imani,
kuma suka aikata ayyukan kwarai,
suna da wani sakamako wanda bai
yankewa.
9. Ka ce, "Ashe lalle ku, hakika,
kuna kafurta a game da Wanda Ya
halitta kasa a cikin kwanuka biyu,
kuma kuna sanya^Masa kishiyoyi?
Wancan fa, Shi ne Ubangijin
halittu.
S * y»*
,x *»<
.' . <X >'
Z\\ '*'*+,
y\>^jo^3\bj&o>-$
vT
I
721
41 — Suratu Fussilat
&m&-»
10. Kuma Ya sanya, a cikinta,
duwatsu kafaffu daga samanta,
kuma Ya sanya albarka a cikinta,
kuma Ya kaddara abubuwan cinta
a cikinta, a cikin kwanuka hucfu
masu daidaita, domin matambaya.
11. Sa'an nan Ya daidaita zuwa
ga sama alhali kuwa ita (a lokacin)
hayaki ce, sai Ya ce mata, ita da
kasa,^"Ku zo, bisa ga yarda ko a
kan tTlas. " Suka ce, "Mun zo, muna
masu da'a."
12. Sai Ya hukunta su sammai
bakwai a cikin kwanuka biyu.
Kuma Ya yi wahayi, a cikin kowace
sama da al'amarinta, kuma Muka
kawata sama ta kusa da fitilu kuma
don tsari. Wancan kaddarawar
Mabuwayi ne, Masani.
13. To, idan sun bijire sai ka ce,
"Na yi muku gargadi ga wata tsawa
kamar irin tsawar Adawa da Samu-
dawa."
14. A lokacin da Manzanninsu
suka je musu daga gaba gare su
kuma daga bayansu, "Kada ku
bauta wa kowa face Allah." Suka
ce, "Da Ubangijinmu Ya so, lalle da
Ya saukar da mala'iku, saboda
haka lalle mu, masu kafirta ne a
game da abin da aka aiko ku da shi."
15. To, amma Adawa, sai suka yi
girman kai a cikin kasa, ba da wani
hakki ba, suka ce, "Wane ne mafi
tsananin karfi daga gare mu?"
Ashe, kuma ba su gani ba cewa
Allah, Wanda Ya halitta su, Shi ne
Mafi karfi daga gare su, kuma sun
kasance a game da ayoyinMu suna
yin musu?
»* 9 \' \'\ 'w" '* \' * '
;y&ate£gi£>&(
&
i-y?*>LjjJl£l«i r,ilLo3»L A r^' *l*-**
c
9(J~+4UL±i£>y*J)Jz\ JJ13 i^>^«o«
722
41 — Suratu Fussilat
£ii^g~--i>
16. Sai Muka aika, a kansu, da
iska mai tsananin sauti da sanyi, a
cikin kwanuka na shu'umci, domin
Mu cfancfana musu azabar wula-
kanci, a cikin rayuwar duniya,
kuma lalle azabar Lahira ita ce mafi
wulakantarwa, kuma su ba za a
taimake su ba.
17. Kuma amma Samudawa, sai
Muka shiryar da su, sai suka fi son
makanta a kan shiriya, domin haka
tsawar azabar wulakanci, ta kama
su, saboda abin da suka kasance su-
na aikatawa (domin neman wata
fa'ida) .
18. Kuma Muka tsTrar da wa-
tfanda suka yi Tmani kuma suka
kasance suna yin ta£awa.
19. Kuma ranar da ake tara
ma£iyan Allah zuwa wuta, to, su
ana kakkange su.
20. Har idan sun je mata, sai
jinsu da ganinsu da fatunsu, su yi
shaida a kansu a game da abin da
suka kasance suna aikatawa.
21. Kuma suka ce wa fatunsu,
"Don me kuka yi shaida a
kanmu?" Suka ce, "Allah, Wanda
ke^sanya kowane abu ya yi furuci,
ShT ne Ya sanya mu mu yi furuci,
kuma ShT ne Ya halitta ku, can da
farko, kuma zuwa gare Shi ake
mayar da ku.
22. "Ba ku kasance kuna sani ba
a 6oye, cewa jinku zai yi shaida a
kanku kuma ganinku zai yi, kuma
fatunku za su yi. Kuma amma kun
yi zaton cewa Allah bai san abu-
buwa masu yawa daga abin da kuke
aikatawa ba.
S^O
fib < m ^A \:\\ It *rf'r5 > < ?>'":
s*** ^xi^ - •^t^iCy bjjCZj^jtzJ^ uj
$&&&$'>&%$&&
%>
723
41 — Suratu Fussilat
m^l^-iN
23. "Kuma wancan zaton naku
wanda kuka yi zaton shi, game da
Ubangijinku, ya halakar da ku, sai
kuka wayi gari a cikin masu
hasara."
24. Saboda haka idan sun yi ha-
kuri, to, wutar, ita ce mazauni a
gare su, kuma idan sun nemi yarda,
to, ba su zama daga warfanda ake
yardarwa ba.
25. Kuma Muka sallatfar da ma-
biya (1) a gare su, sai suka kawata
musu abin da ke a gabansu da abin
da ke a bayansu. Kuma kalmar
azaba ta wajaba a kansu, a cikin
wasu arummomi da suka shurfe a
gabaninsu daga aljannu da mutane.
Lalle su, sun kasance masu hasara.
26. Kuma warfanda suka kafirta
suka ce, "Kada ku saurara ga wan-
nan Alkur'ani, kuma ku yi ta yin
kuwwa a cikin (lokacin karatun) sa,
rfammaninku za ku rinjaya."
27. Saboda haka lalle za Mu rfan-
rfana wa warfanda suka kafirta wata
azaba mai tsanani, kuma lalle za
Mu saka musu da mafi munin abin
da suka kasance suna aikatawa.
28. Wancan shT ne sakamakon
makiyan Allah, watau wuta. Suna a
gidan dawwama a cikinta, domin
sakamako ga abin da suka kasance
suna yin musu game da ayoyinMu.
29. Kuma warfanda suka kafirta
suka ce, "Ya Ubangijinmu ! Ka
nuna mana warfannan biyun da
suka 6atar da mu daga aljannu da
(1) Mabiya, su ne aljannun ko shaicfannun da ke tare da mutum.
724
41 — Suratu Fussilat
£&£&£- ^
mutane, mu sanya su a Rarkashin
Rafafunmu, domin su kasance daga
Raskantattu."
30. Lalle wacfannan da suka ce,
"Ubangijinmu, ShTne Allah," sa'an
nan suka daidaitu, mala'iku na
sassauka a kansu (a lokacin saukar
ajalinsu suna ce musu), "Kada ku ji
tsoro, kuma kada ku yi bakin ciki,
kuma ku yi bushara da Aljanna,
wadda kun kasance ana yi muku
wa'adi da ita.
31. "Mu ne majibintanku a cikin
rayuwar duniya da kuma a cikin
Lahira, kuma a cikinta kuna da
abin da rayukanku ke sha'awa,
kuma kuna da abin da kuke kira (a
kawo muku) a cikinta.
32. "A kan liyafa daga Mai gafa-
ra, Mai jin Rai."
33. Kuma wane ne mafi kyau ga
magana daga wanda ya yi kira zuwa
ga Allah, kuma ya aikata aiki na
kwarai, kuma ya ce, "Lalle nl, ina
daga masu sallamawar al'amari
zuwa ga Allah?"
34. Kuma kyautatawa ba ta dai-
daita, kuma haka munanawa. Ka
tunkude cuta da abin da yake mafi
kyau, sai ga shi wanda akwai
kiyayya a tsakaninka da tsaka-
ninsa, kamar dai shi majibinci ne,
masoyi.
35. Kuma ba za a cusa wa kowa
wannan hali ba face warfanda suka
yi haRuri, kuma ba za a cusa shi ba
face ga mai rabo mai girma.
36. Kuma idan wata fizga ta fiz-
ge ka daga Shaidan, to ka nemi tsari
ftp cru-L^^^^^JlSj
725
41 — Suratu Fussilat
£!£&£- in
ga Allah. Lalle Shi, Shi ne Mai ji,
Masani.
37. Kuma akwai daga ayoyinSa,
dare da yini, da rana da wata. Kada
ku yi sujada ga rana, kuma kada ku
yi ga wata. Kuma ku yi sujada ga
Allah Wanda Ya halitta su, idan
kun kasance Shi ne kuke bauta wa.
38. To, idan sun yi girman kai,
to, wacfandajce a wurin Ubangijin-
ka, suna tasblhi a gare Shi, a dare da
rana, alhali kuwa su, ba su kosawa.
39. Kuma akwai daga ayoyinSa
cewa lalle kai kana ganin kasa
kekasasshiya, to, idan Mun saukar
da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma
ta kumbura^ Lalle Wannan da Ya
raya ta, haklka, Mai rayar da ma-
tattu ne. Lalle Shi, Mai Ikon yi ne a
kan kowane abu.
40. Lalle wacfannan da ke karka-
cewa a cikin ayoyinMu, ba su faku-
wa a gare Mu. Ashe fa, wanda ake
jefawa a cikin wuta ne maflfici ko
kuwa wanda zai je amintacce a
Ranar Kiyama? Ku aikata abin da
kuke so ! Lalle Shi Mai gani ne ga
abin da kuke aikatawa.
41. Wacfannan da suka kafirta
game da Alkur'ani a lokacin da ya je
musu... kuma lalle shi, haklka, litta-
fi ne mabuwayi.
42. *Barna ba za ta je masa ba
daga gaba gare shi, kuma ba za ta zo
ba daga bay a gare shi. Saukar wa ce
daga Mai hikima, Godadde.
43. Ba za a facfa maka ba face
abin da aka riga aka facfa ga Man-
zannin da suke a gabaninka. Lalle
J^jX&^£$+c
CrtJ
>> ~<.*C\>"A\'
»> >
3 dlsS^r^- ^'^\^)j^^\3
y £> -" ^-^ t^ ft -* y 9 ' s "% / ' £ s} ,,
726
41 — Suratu Fussilat
&&££&-*
Ubangijinka, hakika, Ma'abucin
gafara ne, kuma Ma'abucin azaba
mai racfacfi ne.
44. Kuma da Mun sanya shi abin
karatu na ajamanci, lalle da sun ce,
"Don me ba a bayyana ayoyinsa
ba? Ashe, zai yiwu a sami littafi
ba'ajame da Manzo Balarabe?" Ka
ce, "Shi, shiriya ne da warkewa ga
wacfanda suka jd Tmani. Kuma wa-
cfanda ba su yi imani ba akwai wani
nauyi a cikin kunnuwansu, kuma
shi wata makanta ne a kansu. Wa-
cfannan ana kiran su daga wuri mai
nisa.
45. Kuma lalle Mun bai wa Mu-
sa Littafi, sai aka yi sabani a cikin-
sa. Kuma ba domin wata kalma da
ta gabata ba daga Ubangijinka,
lalle da an yi hukunci a tsakaninsu.
Kuma lalle su, haiaka, suna a cikin
shakka daga gare shi, mai sanya
kokanto.
46. Wanda ya aikata aiki na kwa-
rai, to, saboda kansa ne, kuma
wanda ya munana, to, yana a kan-
sa. Kuma Ubangijinka, ba Mai
zalunci ga bayinSa ne ba.
47. Zuwa gare Shi ake mayar da
sanin Sa'a. Kuma wacfansu 'ya'yan
itace ba su fita daga kwasfofinsu,
kuma wata mace ba ta yin ciki,
kuma ba ta haihuwa, face da sanin-
Sa, kuma a ranar da Yake kiran su
(Ya ce), "Ina abokan tarayyaTa?"
Sai su ce, "Mun sanar da Kai, babu
mai bayar da shaida da haka nan
daga gare mu."
> >»„
^(^^^j^ctjLi
aJa-aj.I
>iJ
V w ^ '
727
41 — Suratu Fussilat
m&m-*
48. Kuma abin da suka kasance,
suna kira a gabanin haka ya 6ace
musu, kuma suka yi zaton cewa ba
su da wata mafaka.
49. Mutum ba ya kosawa daga
addu'ar neman alheri, kuma idan
sharri ya shafe shi, sai ya zama mai
yanke kauna, mai nuna kasawa.
50. Kuma lalle idan Mun cfancfa-
na masa wata rahama daga gare
Mu, daga bayan wata cuta ta shafe
shi, lalle zai ce, "Wannan (ni'ima)
tawa ce, kuma ba ni zaton Sa'a mai
tsayuwa ce, kuma lalle idan aka
ma^ar da ni zuwa ga Ubangijlna,
hakika, ina da makoma mafi kyau,
a wurinSa." To, lalle za Mu ba da
labari ga wacfanda suka kafirta
game da abin da suka aikata, kuma
lalle Muna cfancfana musu daga
azaba, mai kauri.
51. Kuma idan Muka yi ni'ima
ga mutum, sai ya bijire, kuma ya
nisantar da gefensa, kuma idan
sharri ya same shi, sai ya zama
ma'abucin addu'a mai facfL
52. Ka ce, "Ashe, kun gani ! Idan
(Alkur'ani) ya kasance daga Allah
ne, sa'an nan kun kafirta a game da
shi, wane ne mafi 6ata daga wanda
yake yana a cikin sa6ani manisanci
(daga gaskiya)?"
53. Za Mu nuna musu ayoyin-
Mu a cikin sasanni da kuma a cikin
rayukansu, har ya bayyana a jare
su cewa lalle (Alkur'ani), shi ne
gaskiya. Ashe, kuma Ubangijinka
bai isa ba, ga cewa lalle Shi Halar-
tacce a kan kowane abu ne?
'sA*?*Hi
IP jfif <^*y^y^
-\&
,S*s
' 9*
Zf^^XJte <&*\^}^)*J^j^
^k
><J&JjZX$ Cy^^f^^iCs
<&~
^J^^ji^^^i
Zj*3f>£&
728
42 — Suratush Shura
m$m-x
54. To, lalle su, suna a cikin
shakka daga gamuwa da Ubangi-
jinsu. To, lalle Shi Mai kewayewa
ga dukan kome ne.
Tana karantar da muhimmancin hacfuwar jama'ar Musulmi da
hanawar rarrabar kalmarsu, a kowane hali.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L H. M.
2. 1 S. K.
J. Kamar wancan (1) (asirin) Al-
lah, Mabuwayi, Mai hikima, ke yin
wahayi zuwa gare ka da zuwa ga
wadanda ke gabaninka.
4. (Allah) Shi ne da abin da ke
cikin sammai da abin da ke cikin
kasa, kuma Shi ne Madaukaki, Mai
girma.
5. Sammai na kusan su tsage
daga bisansu, kuma mala'iku na
yin tasblhi game da gode wa Uban-
gijinsu kuma suna istigfari domin
wanda ke cikin kasa. To, lalle Allah
ShT ne Mai gafara, Mai jin kai.
jbj jefi \ <q*j o y^r J \ <JXa,A
(pj^^!>^^'
(1) Asirin hacfa jama'a ba za su rarrabu ba. Watau su riici Allah Shi kacfai ne Ubangiji
Mai yin umurni ko hani, kuma su riki cewa Muhammadu, tsTra da aminci su tabbata a gare
shi, shi ne cikamakin Annabawa, bayansa ba a bai wa kowa kome face fahimta ga abin da
ya zo da shi.
729
42 — Suratush Shura
^£JJj^-ir
6. Kuma wacfanda suka riki wa-
cfansu maji6inta wacfanda ba ShT
ba, Allah ne Mai tsaro a kansu,
kuma kai, ba wakili ne a kansu ba.
7. Kuma kamar haka ne
Muka yi wahayin abin karantawa
(Alkur'ani) na Larabci zuwa gare
ka, domin ka yi gargacfi ga Uwar
Alkaryu (Makka) da wanda ke a
kewayenta, kuma ka yi gargacfi
game da ranar taruwa, babu shakka
gare ta, wata kungiya tana a cikin
Aljanna kuma wata kungiya tana a
cikin sa'Ir.
8. Kuma da Allah Ya so, da Ya
hacfa su al'umma guda, kuma
amma Yana shigar da wanda Ya so
a cikin rahamarSa, alhali kuwa az-
zalumai ba su da wani maji6inci,
kuma ba su da wani mataimaki.
9. K6 kuma sun riki waninSa
maji6inta? To, Allah ShT ne Maji-
6inci, kuma ShT ne ke^ rayar da
matattu, alhali kuwa ShT Mai Tkon
yi ne a kan dukan kome.
10. Kuma abin da kuka sa6a wa
juna a cikinsa, ko mene ne, to,
hukuncinsa (a mayar da shi) zuwa
ga Allah. Wancan ShT ne Allah
UbangijTna, a gare Shi na dogara,
kuma zuwa gare Shi nake mayar da
al'amanna.
11. (ShT ne) Mai kaga halittar
sammai da kasa, Ya sanya muku
ma'aura daga jinsinku, kuma (Ya
sanya) daga dabbobi maza da mata,
Yana shuka ku a cikinsu, wani abu
bai zama kamar tamkarSa ba,
kuma ShT ne Mai ji, Mai gani.
Ji/ A./j^jJ^r fjO-^J U*J > 'O a J
ijy&ij
' >"*' ■£
4^ ^J^ljcJ^=^y^^(Jj^^^^
|nj y^^i » fc*^ \j*J <■ ^ls*° ^£ir^
730
42 — Suratush Shura
t£&~)iM - ir
12. Shi ne da mabucfan sammai
da kasa, Yana shimficfa arziki ga
wanda Ya so, kuma Yana kukun-
tawa. Lalle ne, ShT Masani ne ga
dukan kome.
13. Ya shar'anta muku, game da
addini, abin da Ya yi wasiyya da shi
ga Nuhu da abin da Muka yi wa-
hayi da shi zuwa gare ka, da abin da
Muka yi wasryya da shi ga Ibrahim
da Musa da Isa, cewa ku tsayar da
addini sosai, kuma kada ku rarrabu
a cikinsa. (1) Abin da kuke kira zuwa
gare shi, (2) ya yi nauyi a kan masu
shirki. Allah na za6en wanda Yake
so zuwa gare Shi, kuma Yana shi-
ryar da wanda ke tawakkali gare
Shi, ga hanyarSa.
14. Kuma ba su rarraba ba face
bayan da ilmi ya je musu, domin
zalunci a tsakaninsu, kuma ba do-
min wata kalma (3) ta gabata ba
\&7 && %<S*i~r*i, >^IJ-^J ^^o^i
&y*J f^y^^j^r^J ^J ^r I ^-^1? '
$ -4^.<y* ^S-^tj $&&4&l
j*^ ILL Jl*S\/va * \ZXa Juo cy^i \)yy£ ^j
(1) Ku bi umurnin Allah kamar yadda Ya aza muku hukunce-hukuncensa, kada ku
karkace da bin umurnin wadansu na dabam, wadanda ba Allah ba, ko kuma kada ku bi
son zuciyarku. Bin umurnin wani zai sanya ku sa6a wa junanku, ku rarrabu, ku rasa karfi a
kan ma£iyanku. Wanda ya bi umurnin wadansu, wadanda ba Allah ba, to, ya yi shirki da
Allah ke nan, kuma haduwar masu bin umurnin wadansu wadanda ba Allah ba, to, tana da
wuya. Wannan aya ta hana bin dariicokin icungiyoyin sufaye duka, domin bin su, bin
umurnin wadansu ne wadanda ba Allah ba, kuma yana rarraba Musulmi, su zama
iamgiya-icungiya, da sa6ani mai nlsa. Ba za a ce ba, "A'aha! Wannan aya ta sauka ga
Yahudu da Nasara kawai", domin ayoyi biyu 14 da 1 5, masu bin wannan, sun gama har da
Musulmi, domin umurni ga Annabi, umurni ne saboda al'ummarsa. Kuma saBanin masu
darlkoici, sa6ani ne a kan asali, watau alclda, ba sa6ani ne a kan rassuna na Furu'a ba.
Saboda haka babu Iciyayya a tsakanin mabiya mazhabobi, domin safcaninsu, na fahimta ne
kawai. Sa6ani ga reshe, rahama ce, amma sa6ani ga asali azaba ce.
(2) Watau haduwar jama'a ga bin addini guda, ba da sa6awa ba ga asalinsa. Wanda
ya ce : An saukar wa wani mutum, baicin Muhammadu, da wani abu daga Allah, to, shi ya
sa6a wa asali. SaBawa ga asali kafirci ne.
(3) Kalmar da ta gabata, ita ce "Allah ba zai halaka mutane ba saboda zunubi sai
ajalinsu ya zo." Zalunci da ke hana su haduwa a bayan sanin gaskiya, shi ne hassadar juna,
sa kwadayi da son shugabanci a cikin mu'amala.
731
42 — Suratush Shura
&S£Mj2&-tr
daga Ubangijinka, zuwa ga wani
ajali ambatacce, da an yi hukunci a
tsakaninsu. Kuma lalle ne, wacfan-
da akagadar wa Littafi daga bayan-
su, hakika, suna cikin shakka a gare
shi, mai sanya kokanto.
15. Saboda haka, sai ka yi
kira, kuma kai, ka daidaitu kamar
yadda aka umurce ka, kuma kada
ka bi son zuciyoyinsu, kuma ka ce,
"Na yi Tmani da abin da Allah Ya
saukar na littafi, kuma an umurce ni
da in yi adalci a tsakaninku. Allah
ne Ubangijinmu, kuma Shi ne
Ubangijinku, ayyukanmu na gare
mu, kuma ayyukanku na gare ku,
kuma babu wata hujja a tsaka-
ninmu da tsakaninku. Allah zai
tara mu, kuma zuwa gare Shi ma-
koma take."
16. Kuma wacfannan da ke
jayayya a cikin al'amarin Allah
daga bayan an karBa masa, huj-
jarsu Batacciya ce a wurin Ubangi-
jinsu, kuma akwai fushi a kansu,
kuma suna da wata azaba mai tsan-
ani.
17. Allah ne Wanda Ya saukar
da Littafi da gaskiya, da sikeli.
Kuma me ya sanar da kai (cewa
ana) tsammanin Sa'ar kusa take?
18. Wacfanda ba su yi Tmani da
ita ba, (su) ke neman gag-
gautowarta. alhali kuwa wacfanda
suka yi Tmani, masu tsoro ne daga
gare ta, kuma sun sani, cewa ita
gaskiya ce. To, lalle ne wacfanda ke
shakka a cikin Sa'a, hakika, suna a
cikin Bata mai nTsa.
\j fob dJU Uid
*^E * '\\ T» ^ \' ' *' A ^ 9 ' >*f *fcs*"f*'
C^Zm\ ^-&&$&^jjpr&U$j
»i> fi'
EJJoJ^vLIj^
r*rt: *>
p4Jj
732
42 — Suratush Shura
<£&£!,$& - ir
19. Allah Mai tausasawa ne ga
bayinsa. Yana arzuta wanda Yake
so, alhali kuma Shi ne Mai karfi,
Mabuwayi.
20. Wanda ya kasance yana nu-
fin noman Lahira, za Mu Rara masa
a cikin nomansa, kuma wanda ya
kasance yana nufin noman duniya,
za Mu sam masa daga gare ta, alhali
kuwa ba shi da wani rabo a cikin
Lahira.
21. K6 suna da wadansu abokan
tarayya (da Allah) wadanda suka
shar'anta musu, game da addini,
abin da Allah bai yi izni ba da shi?
Kuma ba domin kalmar hukunci
ba, da lalle, an yi hukunci a tsaka-
ninsu. Kuma lalle azzalumai suna
da azaba mai radadi.
22. Kana ganin azzalumai suna
masu tsSro daga abin da suka sa-
na'anta, alhali kuwa shi abin tso-
ron, mai aukuwajie gare su, kuma
wadanda suka yi imani kuma suka
aikata ayyukan kwarai suna a cikin
fadamun Aljanna, suna da abin da
suke so a wurin Ubangijinsu. Wac-
can fa ita ce falala mai girma.
23. Wancan shi ne Allah ke
bayar da bushara da shi ga bayinSa
wadanda suka yi Imani kuma suka
aikata ayyukan kwarai. Ka ce, "Ba
ni tambayar ku wata ijara a kansa,
face dai sSyayya ta cikin zumunta/'
Kuma wanda ya aikata wani abu
mai kyau, za Mu kara masa kyau a
cikinsa, lalle Allah Mai gafara ne,
Mai godiya.
I^<j^M^)
\ ^ "\ >
r> .. .^ ^> '
733
42 — Suratush Shura
>~>,I|S£ - tr
24. K6 za su ce, "Ya kirkira ka-
rya ga Allah ne"? To, idan Allah
Ya so, zai yunke a kan zuciyarka,
kuma Allah Yana shafe karya
kuma Yana tabbatar da gaskiya da
kalmominSa. Lalle ne, Shi Masani
ne ga abin da ke cikin zukata.
25. Kuma Shi ne ke kar6ar tuba
daga bayinSa, kuma Yana yafe
kananan laifuffuka, alhali kuwa
Yana sanin abin da kuke aikatawa.
26. Kuma Yana kar6a wa wa-
cfannan da suka yilmani kuma suka
aikata ayyukan kwarai, kuma Yana
kara musu (sakamako) daga fala-
larSa. Kuma kafirai suna da wata
azaba mai tsanani.
27. Kuma da Allah Ya shimficfa
arziki ga bayinSa, da sun yi zaluncin
rarraba jama'a a cikin kasa, kuma
amma Yana sassaukarwa gwargwa-
do ga abin da Yake so. Lalle ne Shi,
game da bayinSa, Mai labartawa
ne, Mai gani.
28. Kuma Shi ne ke sassaukar
da girgije (ruwa) a bayan sun yan-
ke kauna, kuma Yana^watsa raha-
marSa, alhali kuwa Shi ne Maji6in-
ci, Mai godiya.
29. Kuma akwai daga ayoyinSa,
halittar sammai da kasa, da abin da
Ya watsa a cikinsu na dabba alhali
kuwa Shi Mai Tko ne ga tara su, a
lokacin da Yake so.
30. Kuma abin da ya same ku na
wata masTfa, to, game da abin da
hannayenku suka sana'anta ne,
kuma (Allah) Yana yafewar (wa-
cfansu laifuffuka) masu yawa.
3p JJ JL^J\C>\ Jo^^^k^oilKo
>> ^
734
42 — Suratush Shura
<Mi&-w
31. Kuma ba ku zama masu bu-
waya ba a cikin Jcasa, kuma ba ku
da wani majibinci, wanin Allah,
kuma ba ku da wani mataimaki.
32. Kuma akwai daga ayoyinsa,
jirage masu gudana a cikin teku
kamar duwatsu.
55. Idan Ya so sai Ya kwantar da
iskar, sai jiragen su yini suna masu
kawaici a kan bayan tekun, lalle ne
ga wancan, halnka, akwai ayoyi ga
dukan mai haioiri, mai godiya.
34. K6 Ya halaka su (su jiragen)
saboda abin da masu su suka sa-
na'anta, alhali kuwa Yana yafe
(laifuffuka) masu yawa.
35. Kuma domin wacfanda ke
jayayya a cikin ayoyinMu su sani
(cewa) ba su da wata mafaka.
36. Saboda haka abin da aka ba
ku, ko mene ne, to, jin dadin rayu-
war duniya ne, kuma abin da ke a
wurin Allah, shl ne mafifici, kuma
shl ne mafi wanzuwa ga wacfanda
suka yi imani kuma suna dogara a
kan Ubangijinsu kawai.
37. Kuma wacfanda (1) ke nisan-
tar manyan zunubbai da ayyukan
alfasha, kuma idan sun yi fushi, su,
suna gafartawa.
38. Da warfanda suka karBa kira
ga Ubangijinsu, kuma suka tsayar
da salla, kuma al'amarinsu shawa-
y s
* '>.
HUoe^&p* ^ ^w *t|^ j^of J»u«y
(1) Bayanin siffofin muminai, wacfanda suke tsare su, yana lamunce zama hade, da
gamuwar Musulmi, su ne siffofi shida, nTsantar manyan zunubbai da zina, da gafarta fushi,
da tsayar da salla, da shawara ga al'amuran tsakaninsu, da ciyar da dukiya da ta wajabci
mutum ya ciyar da ita ga cikin alheri ga inda Allah Ya ce a ciyar da ita.
735
42 — Suratush Shura
m\£<iA.
-if
ra ne a tsakaninsu, kuma daga abin
da Muka arzuta su suna ciyarwa.
39. Da wadanda (1) idan zalunci
ya same su, suna neman taimako
(su rama).
40. Kuma sakamakon cuta, shl
ne wata cuta kamarta, sai dai wan-
da ya yafe kuma ya kyautata, to^
ladarsa na ga Allah. Lalle ne, Shi
(Allah) ba Ya son azzalumai.
41. Kuma lalle ne wanda ya nemi
taimakon ramawa a bayan an za-
lunce shi, to, wacfannan babu wata
hanyar zargi a kansu.
42. Inda hanyar zargi kawai
take, shi ne a kan wacfanda ke za-
luntar mutane, kuma suna ketare
haddin shari'a cikin kasa, ba tare da
hakki ba. Wacfannan suna da azaba
mai radadi.
43. Kuma lalle ne, wanda ya yi
hakuri kuma ya gafarta (wa wanda
ya zalunce shi), to shi wancan aiki,
haklka, yana daga manyan al'amu-
ra (da Allah ke so).
44. Kuma wanda (2) Allah Ya 6a-
tar, to, ba shi da wani majiBinci,
bayanSa, kuma za ka ga azzalumai,
a lokacin da suka ga azaba, suna
cewa, "Shin, akwai hanya zuwa ga
komawa?"
45. Kuma kana ganin su ana
gitta su a kanta, suna kaskantattu
'.l' * . S <".
fey jy^s^ : o4 ^^>i
'*£<&
y x ' <' y > "* » >
(1) Wajen rama zalunci ko yinsa, mutane sun kasu kashi hudu. Masu ramawa
gwargwadon zalunci, ba su da laifi ; da masu ramawa da abin da ya fi laifin da aka yi musu,
to, suna da laifi kamar masu fara zalunci, da masu gafartawa, wacfannan su ne Allah ke so.
(2) Bayanin mai zalunci da sakamakonsa a Ranar Lahira.
736
42 — Suratush Shura
>A\i<*
-ir
saboda wulakanci, suna hange daga
gefen ganijioyayye. Kuma wadan-
da suka yi Tmani sai su ce, "Lalle ne,
masu hasara, su ne wadanda suka yi
hasarar rayukansu da iyalansu a
Ranar Kiyama." To, lalle ne, azza-
lumai suna a cikin wata azaba
zaunanniya.
46. Kuma wadansu maji6inta ba
su kasance ba a gare su, wadanda ke
iya taimakonsu, baicin Allah.
Kuma wanda Allah Ya Batar, to, ba
shi da wani godabe na tsira.
47. Ku karBa wa Ubangijinku
tun gabanin wani yini ya zo, babu
makawa gare shi daga Allah, ba ku
da wata mafaka a ranar nan, kuma
ba ku iya yin wani musu.
48. To, idan sun bijire, to, ba Mu
aike ka kana mai tsaro a kansu ba,
babu abin da ke a kanka face iyar da
Manzanci. Kuma lalle ne, Mu idan
Mun dandana wa mutum wata ra-
hama daga gare Mu, sai ya yi farin
ciki da ita, kuma idan wata masTfa
ta same su saboda abin da hanna-
yensu suka gabatar, to, lalle ne
mutum mai tsananin kafirci ne.
49. Mulkin sammai da kasa na
Allah kawai ne. Yana halitta abin
da Yake so. Yana bayar da 'ya'ya
mata ga wanda Yake so, kuma Yana
bayar da diya maza ga wanda Yake
so.
50. Ko kuma Ya hada su maza
da mata, kuma Yana sanya wanda
Ya so bakarare. (1) Lalle Shi, Mai
ilmi ne, Mai Ikon yi.
S^^ , ^^5iC^\i C>^ c^-^€L>5 f^^rf^i l^-^2^— ^
i\S'\' *%"*■ •!
•*s*"\S. .<,',
'>> <*A
(1) Bakarare, shi ne wanda ba ya haihuwa.
737
42 — Suratush Shura
&&M£&-if
51. Kuma ba ya kasancewa ga
wani mutum Allah Ya yi masa ma-
gana (1) face da wahayi, ko daga
bayan wani shamaki, ko Ya aika
wani Manzo, sa'an nan ya yi wa-
hayi, da jzninSa ga abin da Yake so.
Lalle Shi, Madaukaki ne Mai hiki-
ma.
52. Kuma kamar wancan, Mun
aika wani ruhi (rai mai hada ja-
ma'a) zuwa gare ka, daga gare Mu.
Ba ka kasance ka san abin da yake
littafi ba, ko abin da yake Tmani,
kuma amma Mun sanya shi (ruhin,
watau Alkur'ani) wani haske ne,
Muna shiryar da wanda Muke so
daga cikin bayinMu game da shi.
Kuma lalle kai, ha£i£a, kana shir-
yarwa zuwa ga hanya madaidai-
ciya.
53. Hanyar Allah Wanda ke da
mulkin abin da ke cikin sammai da
abin da ke cikin kasa. To, zuwa ga
Allah kawai aFamura ke komawa.
E ^
(1 ) Annabawa a lokacin da Allah Ya yi musu magana ba su gan Shi ba, sai dai su ji
maganarSa kamar yadda Musa ya ji, ko kuma da wasidar mala'ika kamar sauran
Annabawa, ko kuwa da ilhami watau ya san hukunci ba da magana ko wani wasidar
mala'ika ba. Ilhamin Annabawa da mafarkinsu gaskiya ne. Ilhami da mafarkin sauran
mutane ba ya zama hujja sai idan ya dace da shari'a, sai a yi aiki da shi a kan shari'a ba a
kan mafarkin ko ilhamin ba.
738
43 — Suratuz Zukhruf
&$%& -vr
Tana karantar da halayen mutane na son rikon al'adunsu da
jayayya da Rarya domin haka a kan gaskiya.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. H. M.
2. Ina rantsuwa da Littafi
Mabayyani.
3. Lalle Mu, Mun sanya shi abin
karatu na Larabci, tsammaninku,
kuna hankalta.
4. Kuma lalle shi, a^ cikin uwar
littafi, a wurinMu, haklka, macfau-
kaki ne, bayyananne.
5. Shin, za Mu kau da kai daga
saukar da hukunci daga gare ku ne
domin kun kasance mutane masu
6arna?
6. Alhali kuwa sau nawa
Muka (1) aika wani Annabi a cikin
mutanen farko!
7. Kuma wani Annabi bai je
musu ba face sun kasance, game da
shi, suna masu yin izgili.
8. Sai Muka halakar da watfan-
da suke su ne maflya karfin damka
"i ' V^ff
l^£|iiS^
L>ii^J^=» Ji W^£- c-^/v^i \
' y > I
<, <z ^
fe^jLLb* fr^A JLil LI
(1) Tun da ba Mu bar mutanen farko masu barna ba, sai da Muka aika musu
Manzanni, kuma kowace kungiya daga cikin wadanda aka aika wa wani Manzo sai da ta yi
izgili game da Manzonsu, har abin ya kai ga halakar shugabanninsu. To, haka mutanenka,
ba za Mu bar su ba, saboda barnansu, sai Mun aike ka zuwa gare su, su yi izgili game da
kai, har a halaka shugabanninsu, sa'an nan sauransu, su bi abin da aka umurce su da shi.
739
43 — Suratuz Zukhruf
mm?-*
daga gare su. Kuma abin misalin
mutanen farkon ya shucfe.
9. Kuma lalle ne, idan ka tam-
baye su, "Wane ne ya halitta sam-
mai da Rasa?" Lalle za su ce, "Ma-
buwayi Mai ilmi ne Ya halitta su."
10. Wanda Ya sanya muku £asa
shimficfa kuma Ya sanya muku ha-
nyoyi a cikinta, tsammaninku, za
ku nemi shiryuwa.
11. Kuma wanda Ya saukar da
ruwa daga sama, a kan wani gwarg-
wado, sai Muka rayar da gari ma-
tacce game da shi. Kamar haka
nan ake fitar da ku (daga kabari).
12. Kuma Wanda Ya halitta
ma'aura dukansu, kuma Ya sanya
muku, daga jirgi da dabbobin
ni'ima, abin da kuke hawa.
13. Domin ku daidaitu a kan
bayansa, sa'an nan ku tuna ni'imar
Ubangijinku a lokacin da kuka dai-
daita a kansa, kuma ku ce, "Tsar-
ki ya tabbata ga Wanda Ya hore
mana wannan, alhali kuwa ba mu ka-
sance masu iya rinjaya gare shi ba.
14. "Kuma lalle mu, halaica,
masu (1) juyawa muke zuwa ga
Ubangijinmu."
15. Kuma suka sanya (2) Masa
juz'i daga bayinSa. Lalle ne mutum,
>s 9 s A
!ojjX4>
ps-kx^p
iy&_)JjJX> ^llti^ls* S$*S3$iy
'*>*.
IM
Q9 oji/^'^J Lfa»Ujl jcaU
' *\-S'\\*' \\Y-\
©6>i^lyJ\6^
s^A^V^i **lP?*£^ u fio*>A !>^i?
(1) Ku yi dalili da horewar abin hawa gare ku zuwa ga tabbatar tashinku, domin
hisabin Kiyama, domin ku bi umurninSa a duniya, kuma ku bar al'adunku.
(2) Suka ce mala'iku 'ya'ya mata ne na Allah, suna bauta musu ne domin su kusantar
da su zuwa ga Allah, watau domin su cece su daga azaba. Sun yi wannan karya ne domin su
tabbatar da al'adarsu ta surkulle. Saboda haka suka yi wa Allah Icarya, suka nakasa Shi da
haka, kuma suka nalcasa mala'iku masu daraja a wurin Allah, kuma suka kafirce wa
ni'imar da Allah Ya yi musu wajen aiko musu Manzo mai shiryar da su. Sa'an suka kafa
hujja da karya domin su danne gaskiya.
740
43 — Suratuz Zukhruf
mm&-*
haklka, mai yawan kafirci ne, mai
bayyanawar kafircin.
16. K6 za Ya cfauki 'ya'ya mata
daga abin da Yake halittawa ne,
kuma Ya za6e ku da cliya maza?
/ 7. Alhali kuwa idan an bayar da
bushara ga dayansu da abin da ya
buga misali da shi ga Mai rahama,
sai fuskarsa ta yini tana wadda aka
bakanta launinta, kuma yana cike
da bakin ciki.
18. Ashe, kuma (Allah zai zaBi)
wanda ake reno a cikin kawa, alhali
kuwa ga shi a husuma ba mai iya
bayyanawar magana ba?
19. Kuma suka mayar da ma-
la'iku fya'ya) mata, alhali kuwa su,
wacfanda suke bayin (Allah) Mai
rahama ne! Shin, sun halarci halit-
tarsu ne? Za a rubuta shaidarsu,
kuma a tambaye su.
20. Kuma suka ce, "Da Mai ra-
hama ya so, da ba mu bauta musu
ba." Ba su da wani ilmi game da
wancan! Babu abin da suke yi face
yanki-facfi.
21. K6 Mun ba su wani littafi ne
a gabaninsa (Alkur'ani) saboda
haka da shi suke like?
22. A'a, sun ce dai, "Lalle mu,
mun sami ubanninmu a kan wani
addini (na aFada) kuma lalle mu, a
kan gurabunsu muke masu neman
shiryuwa."
23. Kuma kamar haka, ba Mu
aika wani mai gargadl ba a gabanin-
ka, a cikin wata alkarya, face ma-
ni'imtanta sun ce, "Lalle mu, mun
i£\ Z K.'Z't'tf"'* * > 9 " 1i.
^$$± ^ Sis**'
741
43 — Suratuz Zukhruf
W$&-ir
sami ubanninmu a kan wani addini,
kuma lalle mu, masu koyi ne a kan
gurabunsu."
24. (Sai mai gargacfin) ya ce,
"Shin, ban zo muku da abin da ya fi
zama shiriya daga abin da kuka
sami ubanninku a kansa ba?" Suka
ce, "Lalle mu dai masu kafirta ne
game da abin da aka aiko ku da
shi."
25. Saboda haka Muka yi musu
azabar ramuwa. To, ka dubi yadda
akibar masu karyatawa take.
26. Kuma (ka ambaci) lokacin
da Ibrahim ya ce wa ubansa da
mutanensa, "Lalle ni mai barranta
ne daga abin da kuke bautawa.
27. "Face Wannan (1) da Ya kaga
halittata, to, lalle ShT ne zai shiryar
da ni."
28. Kuma (Ibrahim) ya sanya
(ita wannan magana) kalma mai
wanzuwa a cikin zuriyarsa, tsam-
maninsu su komo daga Bata.
29. A'a, Na jiyar da wadannan
mutane, dacfi, su da ubanninsu har
gaskiya da Manzo mai bayyanawar
gaskiyar, ya zo musu.
30. Kuma a lokacin da gaskiyar
ta je musu, sai suka ce, "Wannan
sihiri ne, kuma mu, masu kafirta da
shi ne."
31. Kuma suka ce, "Don me ba a
saukar da wannan Alkur'ani a kan
/ >^--2
ObjrJb-
A\' \ .\\ U--C
^ o^^^^ji i^qO ii>t;\;
cp c^jx^^y^^i
ss +* "*
£j^,£bjfa<JJi\ ^l
£&&^&'s&$$>
(1) Ba ni bauta wa gumaka, amma ina bauta wa Allah Wanda Ya £aga halittata.
742
43 — Suratuz Zukhruf
(WP^-tr
wani mutum mai girma daga alkar-
yun (1) nan biyu ba?"
32. Shin, su ne ke raba rahamar
Ubangijinka? Mu ne, Muka raba
musu abincinsu a cikin rayuwar
duniya, kuma Muka cfaukaka
wacfansunsu a kan wacfansu da
darajoji, domin wadansunsu su riki
wacfansu leburori, kuma rahamar
Ubangijinka (ta Annabci (2) ), ita ce
mafTficiya daga abin da suke ta-
rawa.
33. Kuma ba domin mutane su
kasance al'umma cfaya ba, lalle ne,
da Mun sanya wa masu kafirce wa
Mai Rahama, a gidajensu, rufi na
azurfa, kuma da matakalai, ya
zama a kanta suke takawa.
34. Kuma a gidajensu (Mu sa-
nya) kyamare da gadaje, a kansu
suke kishingicfa.
35. Da zlnariya. Kuma dukan
wancan abu bai zama ba, sai jin
dacfin rayuwar duniya ne kawai,
alhali kuwa Lahira, a wurin
Ubangijinka, ta masu takawa ce.
36. Kuma wanda ya makanta
daga barin hukuncin Mai rahama,
to, za Mu lulluBe shi da Shaicfan,
watau shi ne abokinsa.
/»^Jl» La ■ . *&{j>- <i^L> O^l? Oj *. ni a> j£ \
ZJlxa
i'»4if 'Ai*
uja»^^Q^ij£«^u>^
(1) Suna nufin Makka da Ta'ifa, kuma suna nufl a saukar da Alkur'ani ga Walidu
dan Mugira na Makka ko ga Urwatu dan Mas'udi As Sakafl a Ta'ifa. Watau suna sukar
Muhammadu, domin ba shi da dukiya. A gare su mai dukiya shi ne babban mutum, wanda
ya cancanta Allah Ya aiko shi ga mutane.
(2) Tun da ba Mu bar rabon abincin rayuwarsu ta duniya a hannunsu ba, to, ta yaya
ne za Mu bar babban abu kamar Annabci da shiryar da mutane ga hannayensu? Watau ba
zai yiwu Mu yi ba sai yadda Muke so kawai, ko su bi, ko su kafirta, duka daidai ne a gare
Mu.
743
43 — Suratuz Zukhruf
®$li&-tr
37. Kuma lalle su, haklka, suna
kange su daga hanya, kuma suna
zaton cewa su masu shiryuwa ne.
38. Har a lokacin da (abokin
Shaidan) ya zo Mana (ya mutu) sai
ya ce, (wa Shaidan) "Da dai a tsaka-
nina da tsakaninka akwai nTsan
gabas da yamma, saboda haka, tir
da kai ga zama abokin mutum!"
39. Kuma (wannan magana) ba
za ta amfane ku ba, a yau, domin
kun yi zalunci, lalle ku masu tarewa
ne a cikin azaba.
40. Shin to, kai kana jiyar da
kurma ne, ko kana shiryar da ma-
kaho da wanda ke a cikin bata
bayyananna?
41. To, ko dai Mu tafi (1) da kai,
to, lalle Mu, masu yin azabar ramu-
wa ne a kansu.
42. Ko kuma Mu nuna maka
abin da Muka yi musu wa'adi, to,
lalle Mu, Masu Tkon tasarrufi a
kansu ne.
43. Saboda haka, ka yi riko ga
abin da aka yi wahayi da shi zuwa
gare ka. Lalle ne kai, kana a kan
hanya madaidaiciya.
44. Kuma shi (abin wahayin)
ambato (na daukaka) ne a gare ka
da kuma ga mutanenka, kuma za a
tambaye ku.
45. Kuma ka tambayi wadanda
Muka aika a gabaninka daga
ManzanninMu, "Shin, Mun sanya
f^k ^ >S t >» i-if ^1 '^ *"i-i^
^^^^i^jb^iJi^:^
*-*
^^-c^
^Joi ^rt 5 02 Li^O^ J^J
(1) Mu tafi da kai, watau Mu kar6i ranka, ka mutu, to, da Mun yi musu azaba ke nan,
domin sun rasa mai shiryar da su.
744
43 — Suratuz Zukhruf
£$$$&-*
wacfansu gumaka, wasun (Allah),
Mai rahama, ana bauta musu?"
46. Kuma lalle ne, haklka, Mun
aika Musa, game da ayoyinMu,
zuwa ga Fir'auna da masha-
wartansa, sai ya ce, "Lalle nl, Man-
zo ne daga Ubangijin halittu."
47. To, a lokacin da ya je musu
da ayoyinMu, sai ga su suna yi
musu dariya.
48. Kuma ba Mu nuna musu
wata aya ba, face ita ce mafi girma
daga 'yar'uwarta. Kuma Muka
kama su da azaba, tsammaninsu ko
suna komowa.
49. Kuma suka ce, "Ya kai mai
sihiri! Ka roka mana Ubangijinka
da albarkacin abin da Ya y\ alkawa-
ri a wurinka, lalle mu, hakika, masu
shiryuwa ne."
50. To, a lokacin da duk Muka
kuranye musu azaba, sai ga su suna
warware alkawarinsu.
51. Kuma Fir'auna ya yi kira a
cikin mutanensa, ya ce, "Ya muta-
nena ! Ashe, mulkin Masar ba a gare
ni yake ba, kuma wacfannan kogu-
na suna gudana daga karkashina?
Ashe, ba ku gani ba?
52. "Ko kuma ba nl ne mafifici
ba daga wannan wanda yake shl
wulakantacce ne, kuma ba ya iya
bayyanawar magana sai da kyar?
53. "To z don me, ba a jefa mun-
daye na zlnariya a kansa ba, ko
kuma mala'iku su taho tare da shi
hade?"
Jp bfZfZ^&f ^S^^t^
**, ~A ,
3 ^^yix^Ijbl j^UuJI A^LLtS Uii
***.
745
43 — Suratuz Zukhruf
mm -tr
54. Sai ya sassabce hankalin
mutanensa, saboda haka suka bT
shi. Lalle su, sun kasance wacfansu
irin mutane ne fasikai.
55. Saboda haka a lokacin da
suka husatar da Mu, Muka yi musu
azabar ramuwa, sai Muka nutsar da
su gaba daya.
56. Sai Muka sanya su magabata
kuma abin misali ga mutanen
karshe.
57. Kuma a lokacin da aka buga
misali da T>an Maryama, sai ga
mutanenka daga gare shi (shi misa-
lin) suna dariya da izgili.
58. Kuma suka ce, "Shin, guma-
kanmu ne mafifita ko shi (T)an
Maryama)?" Ba su buga wannan
misali ba a gare ka face domin yin
jidali. (1) A'a, su mutane ne masu
husuma.
59. Shi (T)an Maryama) bai
zama ba face wani bawa ne, Mun yi
ni'ima a gare shi, kuma Muka sanya
shi abin koyi ga Bam Isra'Tla.
60. Kuma da Muna so, lalle ne,
da Mun sanya mala'iku, daga ci-
kinku, a cikin kasa, suna maye-
wa
(2)
61. Kuma lalle shi, haklka, wani
ilmi ne na Sa'a, saboda haka, kada
Uy \y b (V^^_^Q?l3 ,4^j3 ci>c^ui\3
&^%te$fc$$s£
^jjj>y>\ jyfe* >^*oi'sdr^Q^
^s M" m ~<Tt .
03
j>ji^jyi apuJJ JLJjaiij
(1) Watau da aka ce gumaka da masu bauta musu duka abincin wutar Jahannama ne,
kamar yadda yake a cikin Sura ta 21 aya ta 98 da 99, sai suka ce sun yarda gumakansu su
zama tare da dan Maryama.
(2) Da Mun so da Mun sanya cfiyansu su zama mala'iku, su fi Tsa cfan Maryama zama
abin mamaki ga halitta, sa'an nan su maye muku a cikin kasa maimakon cfiya masu siffofi
irin na jikunkunanku. Zai fi zama abin mamaki mutum ya haifi mala'ika bisa mace ta haifi
da ba da wani namiji ya kusance ta ba.
746
43 — Suratuz Zukhruf
mm -tr
ku yi shakka a gare ta, kuma ku bl
Ni. Wannan ita ce hanya madaidai-
ciya.
62. Kuma kada Shaicfan ya taus-
he ku (daga hanyar). Lalle shT ma-
iciyi ne a gare ku, mai bayyanawar
iciyayya.
63. Kuma a lokacin da Tsa ya je
da hujjoji bayyanannu, ya ce, "Lalle
ne na zo muku da hikima, kuma
domin in bayyana muku sashen
abin da kuke sa6a wa juna a cikinsa,
saboda haka ku bi Allah da taicawa,
kuma ku yi mini cfa'a.
64. "Lalle ne, Allah ShT ne
Ubangijina kuma Shi ne Ubangi-
jinku, saboda haka ku bauta Masa.
Wannan ita ce hanya madaidaiciya.
65. Sai £ungiyoyi (1) suka sa6a a
tsakaninsu. To, bone ya tabbata ga
wacfanda suka yi zalunci daga aza-
bar yini mai racfacfi!
66. Shin, suna jiran wani abu ne ?
Sai dai Sa'a ta je musu bisa ga
abke, alhali kuwa ba su sani ba.
67. Masoya a yinin nan, sashen-
su zuwa ga sashe malciya ne, face
masu ta£awa (su kam masu son
juna ne).
68. Ya bayiNa! Babu tsoro a
kanku a yau, kuma ba za ku yi
baicin ciki ba.
»*----l!U
Qhj Zg~*Z J*y<f\X*
^ -\d J 6 C^J Vcs-4£ aU-LJj
* *>°"[< &" *"* ^'\» ' \
UU
<3$^ -£~^ -£^.. > w^_^
(1) Nasara suka kasu a cikin kungiyoyi a bayan Tsa. Ya'akubiyya, masu cewa Tsa dan
Allah ne, da Malakaniyya, masu cewa Isa dayan uku ne. Wadansu kuma suka ce bawan
Allah ne, watau su ne Musulminsu, kuma wadansu daga Musulmin suka kafirta a bayan
zakuwar Muhammadu, tsTra da amincin Allah su tabbata a gare shi, saboda sun ki yarda
da Annabcinsa. Yahudu suka ce, "Tsa ba Annabi ba ne dan zina ne." Allah Ya la'ani kafirai
dukansu.
747
43 — Suratuz Zukhruf
WX%&-vr
69. Wacfanda suka yi Tmani da
ayoyinMu, kuma suka kasance
masu sallamawar aFamari (ga
Allah).
70. Ku shiga Aljanna, ku da ma-
tan aurenku, ana girmama ku.
71. Anajcewayawa a kansu da
akussa na zlnariya da kofuna, alhali
kuwa a cikinsu akwai abin da rayu-
ka ke marmari, kuma idanu su ji
dacfi, kuma ku, a cikinta (Aljannar),
madawwama ne.
72. Kuma waccan ita ce Aljan-
nar, wannan da aka gadar da ku ita
saboda abin da kuka kasance kuna
aikatawa.
73. Kuna samu, a cikinta,
'ya'yan itacen marmari masu yawa,
daga cikinsu kuke ci.
74. Lalle masu laifi madawwama
ne a cikin azabar Jahannama.
75. Ba a saukakar da ita (azabar)
daga gare su, alhali kuwa su, a
cikinta, masu kasa magana ne.
76. Kuma ba Mu zalunce su ba,
amma su ne suka kasance azza-
lumai.
77. Kuma suka yi kira, "Ya Ma-
liku! Ubangijinka Ya kashe mu
mana (1) " (Maliku) ya ce, "Lalle ku
mazauna ne."
78. Lalle ne, haklka, Mun je
muku da gaskiya, kuma amma mafl
yawanku masu ki ga gaskiyar ne.
|p druLI^ \y\^=>j tillLiy^CojJjl
*' 9 * >s* '*fc**\'
9 \ Y> CAT 9 * \ - * ' \\ f \ *> *f
E| 0>o ^l^ Iji "' < x " '
p Oy^^jUjyK^
loybPc^tJu
#tfi*^rrTf *
>*>
( 1 ) Watau suna neman su mutu su huta da cfaukar azaba.
748
43 — Suratuz Zukhruf
&£!!££ -tr
79. Ko kuma sun tukka wani
al'amari ne? To, lalle Mu, Masu
tukkawa ne.
80. Ko suna zaton lalle Mu, ba
Mu jin asirinsu da ganawarsu?
Na'am! Kuma manzanninMu na
tare da su suna rubutawa.
81. Ka ce, "Idan har akwai da ga
Mai rahama, to, ni ne farkon masu
bauta (wa dan)."
82. Tsarkin Ubangijin sammai
da kasa, Ubangijin AFarshi, ya tab-
bata daga abin da suke sifantawa.
83. Saboda haka ka kyale su, su
kutsa kuma su yi wasa har su hadu
da yininsu, wanda ake yi musu
wa'adi da shi.
84. Kuma Shi ne Wanda ke abin
bautawa a sama, kuma abin bauta-
wa a Icasa, kuma Shi ne Mai hikima,
Masani.
85. Kuma albarkar Wanda ke da
mulkin sammai da icasa abin da ke a
tsakaninsu ta bayyana, kuma a wu-
rinSa ne ilmin Sa'a yake, kuma
zuwa gare Shi ake mayar da ku.
86. Kuma wadanda suke kira
baicinSa, ba su mallaki ceto ba, face
wanda ya yi shaida da gaskiya,
kuma su, suna sane (1) (da haka).
87. Kuma lalle idan ka tambaye
su, "Wane ne ya halitta su?" Lalle
(SJ byj^ lib \ja\ [y*j>){\
yS>'*' x" Aft' - ' X -tf *i\> >\ /• ^i^X'f-'
(1) Su wadanda suka yi shaida da gaskiya sun san babu mai mallakar ceto ga wani
face Allah. Saboda haka Allah na yi musu izni su ceci wanda Yake son su cece shi, ba
wanda su suke so ba. Ma'anar iznin da ceto ga bayin Allah salihai ita ce domin Allah Ya
bayyana darajar mai ceton ne kawai, ba don yana da wani hakki ba, ga Allah. Allah Ya
tsarkaka daga wata halittarSa ta sami wani hakki a kanSa. Kowa bawanSa ne.
749
44 — Suratud Dukhan
&m$&-it
ne za su ce Allah ne. To, yaya ake
juyar da su?
88. Kuma da (ilmin) maganarsa
(Annabi) "Ya UbangijTna! Lalle
wacfannan mutane ne wacfanda ba
za su yi imani ba."
89. To, sai ka kau da kai daga
gare su, kuma ka ce, "Salama".
Sa'an nan kuma za su sani.
> *>
Tana karantar da cewa Allah Yana tadbiri ga al'amuranSa
kafin Ya bayyana su ga bayinSa. Kuma ni'imarSa tana gushewa
saboda sa6a wa umurninSa.
j*^ >* ^ *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. H. M.
2. Ina rantsuwa da Littafi
Mabayyani.
3. Lalle ne Mu, Muka saukar da
shi a cikin wani dare mai albarka.
Lalle Mu, Mun kasance Masu yin
gargacfi.
4. A cikinsa (shi daren) ake rar-
rabe kowane umurni bayyananne.
5. Umurni na daga wurinMu.
Lalle Mu ne Muka kasance Masu
aikawa.
750
44 — Suratud Dukhan
®mm-*
6. Saboda rahama daga Ubangi-
jinka. Lalle ShT, Shi ne Mai ji, Ma-
sani.
7. (Shine) Ubangijin sammai da
kasa da abin da ke a tsakaninsu,
idan kun kasance masu yakini (za
ku gane haka).
8. Babu abin bautawa face Shi.
Yana rayarwa kuma Yana kashewa.
(Shi ne) Ubangijinku, kuma
Ubangijin ubanninku na farko.
9. A'a su suna wasa a cikin
shakka.
10. Saboda haka, ka dakata, ra-
nar da sama za ta zo da hayaki
bayyananne.
11. Yana rufe mutane. Wannan
wata azaba ce mai radacfi.
12. Ya Ubangijinmu! Ka kura-
nye mana azaba. Lalle mu, masu
imani ne.
13. Ina tunawa^take a gare su,
alhali kuwa, haklka, Manzo mai
bayyanawa ya je musu (da gargadin
saukar azabar, ba su karba ba)?
14. Sa'an nan suka juya baya
daga gare shi, kuma suka ce, "Wan-
da ake gayawa (1) ne, mahaukaci."
75. Lalle Mu, Masu kuranyewar
azaba ne, a dan lokaci kacfan, lalle
ku, masu komawa ne (ga laifin).
16. Ranar da Muke damka,
damka mafi girma, lalle ne Mu
masu azabar ramuwa ne.
> \'\U < »T"> >?. ".
l*4^i! v*J dfJ^ [) o£*-l! I
S-L>
> *>s
o£- JbiL-lil (^Lj *£ i^JbJ&
^<Sj^^^ v QT^i^\
(1) Suna nufin wacfansu mutane ne ke gaya wa Annabi Alkur'ani, ko kuma daga
alama, watau wai Annabi tababbe ne, mahaukaci. Tababbbe da mahaukaci duka
ma'anarsu guda ce, watau marashin hankali, wanda aka yi wa alama da rashin hankali.
751
44 — Suratud Dukhan
m&\%&-tL
17. Kuma lalle ne, haiolca, a
gabaninsu, Mun fitini mutanen Jm-
r'auna, kuma wani Manzo karimi
ya je musu.
18. (Manzon ya ce), "Ku kawo
mini (Tmaninku) ya bayin Allah!
Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa
gare ku.
19. "Kuma kada ku nemi cfauka-
ka a kan AllalL Lalle ni, mai zo
muku ne da dalTli bayyananne.
20. "Kuma lalle ni, na nemi tsari
da Ubangijlna, kuma Ubangijinku,
domin kada ku jefe ni.
21. "Kuma idan ba ku yi Tmani
saboda nT ba, to, ku msance ni."
22. Sai ya kirayi Ubangijinsa
cewa wacfannan mutane ne masu
laifi.
23. (Allah Ya ce), "To, ka yi
tafiyar dare da bayiNa, ^da dare.
Lalle ku, wadanda ake bi ne (do-
min a kama ku.)
24. "Kuma ka bar teku rarrabe.
Lalle su, runduna ce abar nutsar-
wa."
25. Da yawa suka bar gonaki da
maremari.
26. Da shuke-shuke da matsayi
mai kyau.
27. Da wata ni'ima da suka ka-
sance a cikinta suna masu raha.
28. Kamar haka! Kuma Muka
gadar da ita ga warfansu mutane na
dabam.
© ^4^>^4i^^fe^ll?^^
f$j£^]£$c£
*>".£».* »>~\f m "
752
44 — Suratud Dukhan
Mflj&-it
29. Sa'an nan sama da kasa ba su
yi kiika (1) a kansu ba, kuma ba su
kasance wadanda ake yi wa jinkiri
ba.
30. Kuma lalle ne, hakika, Mun
tslrar da BanT Isra'Tla daga azaba
mai wulakantawa.
31. Daga Fir'auna. Lalle shi, ya
kasance madaukaki daga cikin
masu Barna.
32. Kuma lalle ne, haklka, Mun
zabe su saboda wani ilmi (na Tau-
rata) a kan mutane.
33. Kuma Muka ba su, daga
ayoyin mu'ujizoji, abin da yake a
cikinsa, akwai ni'ima bayya-
nanna (2) .
34. Lalle wadannan mutane (3) ,
hakika, suna cewa,
35. "Babu wani abu sai
mutuwarmu ta farko, kuma ba mu
zama wadanda ake tayarwa ba.
36. "Sai ku zo da ubanninmu,
idan kun kasance masu gaskiya."
37. Shin, su ne mafifita ko kuwa
mutanen Tubba'u, kuma da wadan-
da ke a gabaninsu? Mvm halaka su,
Lalle su, sun kasance masu laifi.
>»*L Zt' .TV^f
n
«?> .<"?+
^o^'v^^Ji^i^^-^
'*{ <' 7 <' *>
|p OJ^JI ^jX^^^J^^J
0^si^^^«^:;
Kp ^J^jk^oy^ukj^li
•>f-?.*o?j
(!) Watau sama da Rasa ba su girgizu ba saboda halaka su da aka yi kamar ba a yi,
kome ba.
(2) An bai wa Bani Isra'ila ni'imar ilmi na Taurata, an daukaka su, saboda aiki da
ilmin, a kan sauran mutanen zamaninsu, kuma aka ba su ayoyin mu'ujiza kamar tsage teku
da mannu da salwa da sauransu, amma kuma dukkan wadannan ni'imomin sai da suka
gushe a lokacin da suka sa6a wa umurnin Allah, sai kuma kaskanci ya maye musu daga
baya. Wannan kuma wa'azi ne ga Musulmi wadanda Allah Ya daukaka su da Alkur'ani a
kan sauran mutane, idan sun kauce masa za su walakantu.
(3) Ana nufin mutanen zamanin Annabi Muhammadu, tsira da aminci su tabbata a
gare shi, wadanda ake kiran su zuwa ga Musulunci.
753
44 — Suratud Dukhan
m*&*&-*
38. Kuma ba Mu halitta sammai
da kasa da abin da ke a tsakaninsu
ba, alhali kuwa Muna masu wasa.
39. Ba Mu halitta su ba face da
manufa ta gaskiya, kuma amma
mafi yawansu, ba su sani ba.
40. Lalle ranar rarrabewa, ita ce
lokacin wa'adinsu gaba daya.
41. Ranar da wani zumu ba ya
amfanin wani zumu da kome, kuma
ba su zama ana taimakon su ba.
42. Face wanda Allah Ya yi^wa
rahama. Lalle Shi (Allah), Shi ne
Mabuwayi, Mai jin kai.
43. Lalle itaciyar Zakkum (da-
nyen wuta),
44. Ita ce abincin mai laifi.
45. Kamar narkakken kwalta,
yana tafasa a cikin cikunna.
46. Kamar tafasar ruwan zafi.
47. (A ce wa mala'ikun wuta),
"Ku kama shi, sa'an nan ku fizge
shi zuwa ga tsakiyar JahTm.
48. "Sa'an nan ku zuba, a kansa,
daga azabar ruwan zafi."
49. (A ce masa), "Ka dandana!
Lalle kai ne, kai ne mabuwayi mai
girma!
50. "Lalle wannan shi ne abin da
kuka kasance kuna shakka game da
shi."
51. Lalle masu takawa suna ci-
kin matsayi amintacce.
52. A cikin gidajen Aljanna da
maremari.
^ oJJuJy
^^ ^** "~\ ~ ** ' ~ ^ k* '" *" *
Jin**
({) ^ff lit
754
44 — Suratud Dukhan
mmm-ii
53. Suna tufanta daga tufafin
alhanni ra£i£i, da mai kauri, suna
masu zaman fuskantar juna.
54. Kamar haka, kuma Mun au-
rar da su da mata masu kyaun
idanu, masu girmansu.
55. Suna kira, a cikinsu (gidajen)
ga dukan 'ya'yan itacen marmari,
suna amintattu (daga dukan abin
tsdro).
56. Ba su dandanar mutuwa, a
cikinsu, face mutuwar farko, kuma
(Allah) Ya tsare musu azabar JahTm.
57. Saboda falala daga
Ubangijinka. Wancan shi ne bab-
ban rabo, mai girma.
58. Domin haka kawai Muka
saukakar da shi (Alkur'ani) da
harshenka, tsammaninsu, su rika
tunawa.
59. Sai ka yi jira. Lalle su, masu
jira ne. (1)
S . ' > •'
\ * ^4x13 J^j L^i 0j& J*j
^p^l^p'l^^yj^
^tf-i<r -a<
• •**< -2 V
* \> \\ - -A\ "L
M^J^O^^^iJcjjiSLii
(1) Masu jira ne ga abin da zai same su idan ba su yi imani ba, watau nfimar da aka
ba su za ta gushe ke nan domin ba su aiwatar da ita ba a kan umurnin Allah.
755
45 — Suratul Jathiya
mm&-»
Tana karantar da wajabcin bin shari'ar Allah. Wanda ya bi waninta,
ya 6ace, ko da ya ga kansa a kan wani ilmin da jarrabawa ko wani
mutum ya ba shi.
«* J* <* i <o ^ **
m&&,
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L H. M.
2. Saukar Littafi daga Allah
Mabuwayi Mai hikima yake.
3. Lalle ne a cikin sammai da
kasa akwai ayoyi (1) ga masu imani.
4. Kuma a cikin halittarku da
abin da ke watsuwa na dabba akwai
ayoyi ga mutane masu yaklni.
5. Kumadasa6awardaredayini
da abin da Allah Ya saukar daga
sama na arziki, sa'an nan Ya rayar
da kasa game da shi a bayan mutu-
warta, da juyawar iskoki, akwai
ayoyi ga mutane masu yin hankali.
6. Warfancan ayoyin Allah ne,
Muna karanta su gare ka da gas-
kiya. To, da wane labarij>ayan
Allah da ayoyinSa suke yin Imani?
7. Bone ya tabbata ga dukan mai
yawan Riren karya, mai laifi.
^^\yj2\^\^L^^\^^
$ pfe^9^^t^5 v^^i
***, „ss,s ->iff ^*V-*-
(1) Aya, ita ce alama mai jan hankalin mutum zuwa ga shiriya. Jam'inta, shi ne ayoyi.
756
45 — Suratul Jathiya
%m*&-*
8. Yana jin ayoyin Allah ana
karanta su a kansa, sa'an nan ya
doge yana makangari, kamar bai jT
su ba. To, ka yi masa bushara da
azaba mai racfacfi.
9. Kuma har idan ya san wani
abu daga ayoyinMu, sai ya rika su
da izgili. Wacfancan suna da wata
azaba mai wulakantawa (a duniya).
10. Gaba gare su (a Lahira) ak-
wai Jahannama, kuma abin da suka
sana'anta ba ya wadatar da su daga
kome, kuma abubuwan da suka
rika majiBinta, baicin Allah, ba su
wadatar da su daga kome. Kuma
suna da wata azaba mai girma.
11. Wannan (Alkur'ani) shi ne
shiryuwa. Kuma wadanda suka ka-
firta game da ayoyin Ubangijinsu,
suna da wata azaba ta wulakanci
mai radadi.
12. Allah ne Wanda Ya hore
muku teku domin jirgi ya gudana a
cikinta da umurninSa, kuma domin
ku nema daga falalarSa, kuma
tsammaninku za ku gode.
13. Kuma Ya hore muku abin da
ke a cikin sammai da abin da ke a
cikin kasa, gaba daya daga gare Shi
yake. Lalle ne, a cikin wancan,
haklka, akwai ayoyi ga mutane wa-
danda ke yin tunani.
14. Ka ce wa wadanda suka yi
Tmani, su yi gafara ga wadanda ba
su fatan rahama ga kwanukan Al-
lah, (1) domin (Allah) Ya saka wa
^tO**f - " '\' IK'S' ?\\'*'*K< '
(X) Kwanukan Allah, su ne masifu wadanda ke samun kafirai wadanda ba su bin
sharT'ar Allah. Watau Allah Ya umurci Annabi ya gaya wa Musulmi, cewa wanda ba ya
757
45 — Suratul Jathiya
m&%&-*
mutane da abin da suka kasance
suna aikatawa.
15. Wanda ya aikata aikin kwa-
rai, to, domin kansa, kuma wanda
ya munana aiki, to, a kansa. Sa'an
nan zuwa ga Ubangijinku ake
mayar da ku.
16. Kuma lalle ne, hakika, Mun
bai (1) wa BanT Isra'Tla littafi da
hukunci da Annabci, kuma Mun
arzuta su daga^abubuwa masu dacfi,
kuma Mun fifita su a kan mutanen
duniya (a zamaninsu).
17. Kuma Muka ba su hujjoji na
umurni. Ba su sa6a ba face bayan
ilmi ya je musu, saboda zalunci a
tsakaninsu. Lalle ne, Ubangijinka
zai yi hukunci a tsakaninsu, a Ra-
nar Kiyama a cikin abin da suka
kasance suna sa6a wa (juna).
18. Sa'an nan Muka sanya ka a
kan wata sharl'a ta al'amarin. Sai
ka bi ta, kuma kada ka bi son
zuciyoyin wacfannan da ba su sani
ba.
19. Lalle ne su, ba za su wadatar
da kai da kome ba daga Allah.
Kuma lalle ne azzalumai, sashensu
maji6intan sashe ne. Kuma Allah
ne Maji6incin masu takawa.
'->y*it.
\~'S> " *<J» S' i=S. 9* *'S *
lyi!c>J U3 ^*)1 1 (j* C^lX|o +^Z\*.j
' *T\ f.' A \\ >* A'
, ' * *<" -t ,?/
tsoron masifu saboda ya lei aiwatar da sharT'ar Allah a kansa, to, kada Musulmi su damu
da shi, watau kafiran amana na iya bin dokokinsu na al'ada, babu ruwan Musulmi,
matukar dai ba su shuka wata fitina ba a gare su. A bayan haka Allah zai saka wa kowa
game da aikinsa.
(I) Ba Musulmi kawai aka aiko waManzo ba, ba su kawai aka ba su shan'a ba kuma
aka umurce su da binta ba, BanT Isra'ila^ma, an ba su haka, kuma sun cfaukaka a kan
mutane a lokacin da suka yi aiki da shari'ar, kuma suka kaskanta a lokacin da suka bar
aiki da ita. Musulmi ma haka suke idan sun bar sharT'ar da Allah Ya aza su a kanta, za su
kaskanta yadda Yahudawa suka kaskanta.
758
45 - Siiratul Jathiya
&W£&-i'
20. Wannan (Alkur'ani)
hukunce-hukuncen natsuwa ne ga
mutane, da shiryuwa, da rahama,
ga mutane wadanda ke da yakini.
21. Ko wadanda suka yagi miya-
gun ayyuka suna zaton Mu sanya su
kamar wadanda suka yi imani,
kuma suka aikata ayyukan kwarai,
su zama daidai ga rayuwarsu da
mutuwarsu? Abin da suke hukun-
tawa ya munana!
22. Alhali kuwa Allah ne Ya ha-
litta sammai da kasa saboda gas-
kiya, kuma domin a saka wa kowa-
ne rai da abin da ya sana'anta,
kuma su, ba za a zalunce su ba.
23. Shin, ka ga wanda ya riki son
zuciyarsa shT ne abin bautawarsa,
kuma Allah Ya 6atar da shi a kan
wani ilmi, (1) kuma Ya sa hatini a
kan jinsa, da zuciyarsa, kuma Ya sa
wata yana a kan ganinsa? To,
wane ne zai shiryar da shi bayan
Allah? Shin to, ba za ku yi tunani ba?
24. Kuma suka ce, "Babu kome
face rayuwarmu ta duniya; muna
mutuwa kuma muna rayuwa (da
haihuwa) kuma babu abin da ke
2s *" S>' \'w >~"\''s'
. '» > s^ * " \"
tig* 0^41^11 !A^j lA^ \+U$£
1^CJi2J£j!^
(1) Ilmin Allah ba ya da iyaka, Yana buda shi ga wanda Ya ga dama, a inda ko a
lokacin da Ya ga dama, amma dai duk ilmin da bai saukar da shi ga Annabi Muhammadu
ba, tsTra da amincin Allah su tabbata a gare shi, to, ba a aiki da shi ga hukunci ko shart'a,
wanda ya bi shi kuwa, to, ya 6ace ga aikinsa, ba ya cikin shiryayyu masu zaman lafiya a
duniya kuma su shiga Aljanna a Lahira, domin sharacfin haka shine bin sunna. Wanda ya
bar sunna kuwa, ya yi kuskuren hanya, babu mai shiryar da shi kuma sai Allah idan Ya so
shi da rahama, watau Ya sanya shi ya tuba. Wannan ya nuna cewa ibada da mu'amala
duka cfaya suke ga Musulunci, barin aiki da shari'a a cikin kowannensu duka, kafirci ne ga
wanda ya halatta yin haka nan. Mafi yawan kafircin da ya sami Musulmi, ya zo musu ne
ta hanyar barin mu'amaloli da sharPar Allah, suka cfauki yin salla da mai kama da ita, shi
kadai ne Musulunci, suka kafirta da haka.
759
45 — Suratul Jathiya
m&*&-*
halaka mu sai zamani." Alhali
kuwa (ko da suke facfar maganar)
ba su da wani ilmi game da wannan,
ba su bin kome face zato.
25. Kuma idan ana karanta
ayoyinMu bayyanannu a kansu,
babu abin da ya kasance hujjarsu
face suka ce, "Ku zo mana da uban-
ninmu, idan kun kasance masu
gaskiya."
26. Ka ce, "Allah ne ke rayar (1)
da ku, kuma Shine ke matar da ku,
sa'an nan Ya tara ku zuwa ga Ranar
Kiyama, babu shakka a gare ta,
kuma amma mafl yawan mutane ba
su sani ba.
27. "Kuma mulkin sammai da
Kasa na Allah ne ShT kadai. Kuma
ranar da Sa'a ke tsayuwa, a ranar
nan masu 6atawa (ga hujjojin Allah
domin su ki bin shari'arSa) za su
yi hasara."
28. Kuma za ka ga kowace
al'umma tana gurfane, kowace
al'umma ana kiran ta zuwa ga litta-
finta. (A ce musu) "A yau ana saka
muku da abin da kuka kasance
kuna aikatawa."
29. "Wannan littafinMu ne,
yana yin magana a kanku da gas-
kiya. Lalle Mu, Mun kasance Muna
sauya rubutun tamkar abin da kuka
kasance kuna aikatawa."
30. To, amma wadanda suka yi
Tmani kuma suka aikata ayyukan
^ 5>^v^oi5ei! J^il ^i^Sji^J \ ^\
*'-- ' 'fa "'\t'\<' * ,f> \*>C\'
jl^i^ i^s^^^^iii^s ia^^^^i^v^
( 1 ) Watau ba ku ne ke rayuwa da kanku ba, sai an rayar da ku, haka ne ga mutuwa,
ba ku ne ke mutuwa da kanku ba, sai an matar da ku, kuma Allah Shi T)aya ke iya rayarwa
ko matarwa. To, yaya ne za ku ki bin sharl'ar da Ya umurce ku da binta?
760
45 — Suratul Jathiya
m&%&-»
kwarai, to, Ubangijinsu zai sanya su
a cikin rahamarSa. Wannan shT ne
babban rabo bayyananne.
31. Kuma amma wadanda suka
kafirta (Allah zai ce musu), "Shin,
ayoylNa ba su kasance ana karanta
su a kanku ba sai kuka kangare,
kuma kuka kasance mutane masu
laifi?
32. "Kuma idan aka ce, lalle
wa'adin Allah gaskiya ne, kuma
Sa'a, babu shakka a cikinta, sai
kuka ce, 4 Ba mu san abin da ake
cewa Sa'a ba, ba mu zato (game da
ita) face zato mai rauni, kuma ba
mu zama masu yaklni ba. 5 "
33. Kuma munanan abin da
suka aikata ya bayyana a gare su,
kuma abin da suka kasance suna yi
na izgili ya wajaba a kansu.
34. Kuma aka ce, "A yau za Mu
manta da ku, kamar yadda kuka
manta da gamuwa da yininku wan-
nan. Kuma makomarku wuta ce,
kuma ba ku da wadansu masu
taimako.
35. "Wancan domin lalle ku,
kun riki ayoyin Allah da izgili,
kuma rayuwar duniya ta rude ku.
To, a yau ba za su fita daga gare ta
ba, kuma ba za su zama wadanda
ake neman yardarsu ba."
36. Saboda haka, godiya ta tab-
bata ga Allah Ubangijin sammai,
kuma Ubangijin kasa, Ubangijin
halittu.
37. Kuma gare Shi girma yake, a
cikin sammai da kasa, kuma ShT ne
Mabuwayi, Mai Hikima.
>r > ,
<>x ,>•"*£*
firr
\<'*t^ "T-*~* '•&$'<' .'."Ai'i -'
'<\'\* '>"\i '*<
Jfjd I <^JJ £S£J^ \ L>j JLU-U&d
ra hJ&\^Lx)
761
46 - Suratul Ahicaf
$*£$&& -v\
Tana karantar da cewa duka mai yin naslha ga kansa, ko ga
wani, to, mai gargacfi ne, Annabi ne ko waninsa, mutum ne ko
aljani.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L H. M.
2. Saukar da littafi daga Allah,
Mabuwayi, Mai hikima yake.
3. Ba Mu halitta sammai da kasa
ba, da abin da ke tsakaninsu, face
da gaskiya da wani ajali ambatac-
ce, kuma wadanda suka kafirta,
masu bijirewa ne daga abin da aka
yi musu gargacfi (da shi).
4. Ka ce, "Shin, kun gani, abin
da kuke kira, wanda yake baicin
Allah ? Ku nuna mini, mene ne suka
halitta daga kasa? Ko kuwa suna da
tarayya a cikin sammai? Ku zo mini
da wani littafi na gabanin wannan
(Alkur'ani) ko wata alama daga
wani ilmi, idan kun kasance masu
gaskiya."
5. Kuma wane ne mafi 6ata daga
wanda ke kiran wanin Allah wanda
da ba zai kar6a masa ba, bar Ranar
Kiyama, alhali su (wadanda ake
kiran) shagaltattu ne daga kiransu?
762
46 - Suratul Ahicaf
tJS^t^-n
6. Kuma idan aka tara mutane,
sai su kasance makiya a gare su,
alhali sun kasance masu ki ga iba-
darsu.
7. Kuma idan ana karatun
ayoyinMu bayyanannu a kansu, sai
wadanda suka kafirta ga gaskiya a
lokacin da ta je musu, su ce, "Wan-
nan sihiri ne bayyananne."
8. K6kuwasunacewa,"Yakirki-
ra shi (Alkur'ani) ne"? Ka ce, "Idan
na kirkira shi ne, to, ba ku mallaka
mini kome daga Allah. Shi ne Mafi
sani ga abin da kuke kutsawa a
cikinsa na magana. (Allah) Jtfa isa
Ya zama Shaida a tsakanlna da
tsakaninku. Kuma Shi ne Mai ga-
fara, Mai jin kai."
9. Ka ce, "Ban kasance farau ba
daga Manzanni, kuma ban san abin
da za a yi game da ni ko game da ku
(na gaibi) ba, ba ni bin kome face
abin da ake yin wahayi zuwa gare
ni, kuma ban zama ba, face mai
gargadi mai bayyanawa."
10. Ka ce, "Shin, kun gani, idan
(Alkur'ani) ya kasance daga wurin
Allah yake, kuma kuka kafirta da
shi, Jkuma^ wani mai shaida daga
BanI Isra'Ila ya bayar da shaida a
kan kwatankwacinsa, sa'an nan ya
yi imani, kuma kuka kangare? Lalle
Allah ba Ya shiryar da mutane azza-
lumai."
11. Kuma wadanda suka kafirta
suka ce wa wadanda suka yi Imani,
"Da (Alkur'ani) ya kasance, wani
alheri ne, da ba su riga mu zuwa
gare shi ba." Kuma tun da ba su
GJ >&} by** ^jy^Jts^. '-^st - * 1
763
46 - Suratul Ahkaf
lli^-n
shiryu game da shT ba, to, za su ce,
"Wannan kiren karya ne dacfacfcfe."
12. Alhali kuwa a gabaninsa ak-
wai littafln Musa, wanda ya kasan-
ce abin koyi, kuma rahama. Kuma
wannan (Alkur'ani) littafi ne mai
gaskatawa (ga littafln Musa), a
harshe na Larabci domin ya gar-
gacfi wacfanda suka yi zalunci,
kuma ya zama bushara ga masu
kyautatawa.
13. Lalle ne, wadanda (1 ) suka ce,
"Ubangijinmu Allah ne," sa'an nan
suka daidaitu, to, babu wani tsoro a
kansu, kuma ba za su yi bakin ciki
ba.
14. Wacfannan 'yan Aljanna
ne, suna madawwama a cikinta,
a kan sakamako ga abin da suka
kasance suna aikatawa.
75. Kuma Mun yi wasiyya ga
mutum (2) game da mahaifansa biyu
da kyautatawa, uwarsa ta yi cikinsa
wahala, kuma ta haife shi wahala. Ci-
kinsa da yayensa wata talatin. Har a
lokacin da ya kai ga mafi karfmsa,
kuma ya kai^shekara arba'in, ya ce,
"Ya UbangijTna ! Ka kange ni domin
in gode wa ni'imarka, wadda Ka
ni'imta a kaina, da kuma a kan
mahaifana biyu, kuma domin in
aikata aikin kwarai, wanda Kake
yarda da shi, kuma Ka kyautata
mini a cikin zuriyata. Lalle ni, na
4$
( 1 ) Ya fara da wanda ya yi wa kansa nasiha, kuma ya yi aiki da ita, to, shi mai gargadi
ne. Haka kuma mai yin nasTha ga mutane, shi ma mai gargadi ne.
(2) Mutum a cikin iyalinsa, ko ya zama mai gargadi ga kansa da nashiha ga
mahaifansa da zuriyarsa kamar yadda ya bayyana a cikin ayoyi 13, 14 da 15, ko kuma ya
zama mai butulci ga kansa, ya tozartar da iyayensa da zuriyarsa, kamar yadda ya bayyana
a cikin ayoyi 17 da 18.
764
46 - Suratul Ahicaf
-n
tuba zuwa gare Ka, kuma lalle ni,
ina daga masu sallamawa (ga
umurninKa)."
16. Wacfancan ne wadanda
Muke kar6a, daga gare su, mafi
kyaun abin da suka aikata, kuma
Muke gafarta mafi munanan ayyu-
kansu, (suna) a cikin 'yan Al-
janna, a kan wa'adin gaskiya wanda
suka kasance ana yi musu alkawari
(da shi).
17. Kuma wanda ya ce wa
mahaifansa biyu, "Tir gare ku!
Shin, kuna tsoratar da ni cewa za a
fitar da ni daga (kabari) ne, alhali
kuwa karnoni na mutane da yawa
sun shude a gabanlna (ba su komo
ba)?" Kuma su (mahaifan) suna
neman Allah taimako^ (suna ce
masa) "Kaitonka ! Ka yilmani, lalle
wa'adin Allah gaskiya ne." Sai shi
kuma ya ce. "Wannan ba kome ba
ne face tatsuniyoyin mutanen
farko."
18. Wadancan ne wadanda kal-
mar azaba ta wajaba a kansu, a
cikin arummomi wadanda suka
shude, (ba da dadSwa ba), a gaba-
ninsu, daga aljannu da mutane. Lal-
le su, sun kasance masu hasara.
19. Kuma ga kowane nau'i,
yana da darajoji daga abinda suka
aikata. Kuma domin (Allah) Ya
cika musu (sakamakon) ayyukan-
su, alhali kuwa su, ba za a zalunce
su ba.
20. Kuma ranar da ake gitta wa-
danda suka kafirta a kan wuta (a ce
musu), "Kun tafiyar da abubu-
wanku na jin dacfi a cikin rayu-
is*
If < 1*
^t^ s< f^l^ »>*.<^ .+A\'" \i' - \~-
*tf\1
©OjiLV
^'X**"^ \'\\\'\>'.f' ?\\>">'»"
765
46 - Suratul AMaf
$&*\%&-v\
warku ta duniya, kuma kun nemi jin
dadi da su, to, a yau ana saka muku
da azabar wulakanci, domin abin
da kuka kasance kuna yi na girman
kai a cikin kasa, ba da wani hakki
ba, kuma domin abin da kuka ka-
sance kuna yi na fasikansi."
21. Kuma ka ambaci rfa-
n'uwan (1) Adawa a lokacin da ya yi
gargadi ga mutanensa, a Tuddan
Rairayi, alhali kuwa wadansu masu
gargadi sun shude a gaba gare shi da
baya gare shi (da cewa) "Kada ku
bauta wa kowa face Allah. Lalle nl,
ina tsorata muku azabar yini mai
girma."
22. Suka ce, "Shin, ka zo mana
ne domin ka karkatar da mu daga
gumakanmu? To, ka zo mana da
abin da kake yi mana wa'adin, idan
ka kasance daga masu gaskiya."
23. Ya ce, "Ilmin a wurin Allah
kawai yake, kuma ina iyar muku
abin da aka aiko ni da shi, kuma
amma ina ganin, ku, wasu mutane
ne, kuna jahiltar gaskiya."
24. To, a lokacin da suka ga
azabar, kamar hadari mai fuskan-
tar rafukansu, suka ce, "Wannan
hadari ne mai yi mana ruwa." A'a,
shi na abin da kuke neman gag-
gawar saukarsa: iska ce, a cikinta
akwai wata azaba mai radadi.
(1) Ya ambaci Hudu da mutanensa Adawa da misalin wadansu masu gargadi daga
Annabawan da suka shude da kuma mutanensu, da yadda aka halaka su daga inda suke
zaton rahama ta je musu. Haka ne hukuncin dukan wanda aka yi wa gargadi da bin
umurnin Allah, idan ya ki bi, sa'an nan ya bi son zuciyarsa, Allah zai kawo masa azaba
daga inda yake zaton alheri ga kansa.
766
46 - Suratui Ah£af
Ul^-n
25. Tana darkake kowane abu
da umurnin Ubangijinta. Sai suka
wayi gari, ba a ganin kome face
gidajensu. Kamar wannan ne Muke
saka wa mutane masu laifi.
26. JCuma lalle ne, hakika, Mun
ba su iko ga abin da ba Mu ba ku
Iko gare shi ba,Jaima Muka sanya
musu wani irin jTda gani da zukata.
Sai dai jinsu bai amfane su ba, kuma
zukatansu ba su amfane su ba ga
kome, domin sun kasance suna
musu game da ayoyin Allah, kuma
abin da suka kasance suna aikatawa
na izgili game da shi ya wajaba (1) a
gare su.
27. Kuma lalle ne, hakika, Mun
halakar da abin da yake kewayenku
na alkaryu, kuma Muka jujjuya
ayoyi, tsammaninsu za su komo.
28. To, don mene ne wadanda
suka ri£a, baicin Allah, abubuwan
yi wa baiko, gumaka, ba su taimake
su ba? A'a, sun 6ace musu. Kuma
wannan shi ne kiren karyarsu da
abin da suka kasance suna kirkir-
awa.
29. Kuma a lokacin da Muka
juya wadansu jama'a na aljannu (2)
zuwa gare ka suna sauraren Alku-
r'ani. To, a lokacin da suka halarce
shi, suka ce, "Ku yi shiru." Sa'an
nan da aka kare, suka juya zuwa ga
jama'arsu suna masu gargadi.
&^j&jA \&%^s*^* \&Jjb\jjAj
\j^>&\ \y li 6Js&*- LUI3 o I ^^-^^
(1) Ya wajaba a gare su, watau sakamakonsa ya tabbata a kansu da azaba.
(2) Wannan ya nuna cewa a cikin aljannu akwai Musulmi da masu gargadi, kuma
idan mutum ya yi gargadi domin Allah, Allah zai taimake shi da masu saurara masa, ko da
daga wadansu jinsin da ba nasa ba. Kuma zama a cikin wani addinin Allah da ya shige, ba
ya isa ga wanda bai shiga Musulunci ba, a bayan bayyanar Musuluncin.
767
46 - Suratul Ah£af
li^-n
30. Suka ce, "Ya mutanenmu!
Lalle mu, mun ji wani littafi an
saukar da shi a bayan Musa, mai
gaskatawa ga abin da ke a gaba da
shi, yana shiryarwa ga gaskiya da
kuma zuwa ga hanya madaidaiciya.
31. "Ya mutanenmu! Ku kar6a
wa mai kiran Allah, kuma ku yi
Tmani da Shi, Ya gafarta muku daga
zunubanku, kuma ya tserar da ku
daga azaba mai radadi.
32. "Kuma wanda bai karba wa
mai kiran Allah, ba, to, bai zama
mai buwaya a cikin kasa ba, kuma
ba ya da wadansu majiBinta, baicin
Shi. Wadannnan suna a cikin bata
bayyananna."
33. Shin, kuma ba su gani ba
cewa, "Lalle Allah, Wanda Ya ha-
Utta sammai da kasa, kuma bai kasa
ga halittarsu ba, Mai Ikon yi ne a
kan rayar da matattu?" Na'am,
lalle Shi, Mai Ikon yi ne a kan kome.
34. Kuma ranar da ake gittar
da wadanda suka kafirta a kan
wuta, (a ce musu) "Ashe, wannan
ba gaskiya ba ne?" Su ce, "Na'am,
gaskiya ne, mun rantse da Ubangi-
jinmu!" Sai Ya ce, "To, ku cfancfani
azabar, saboda abin da kuka kasan-
ce kuna yi na kafirci."
35. Saboda haka, ka yi hakuri
kamar yadda masu karfin niyya
daga Manzanni suka yi hakuri.
Kuma kada ka yi musu gaggawa.
Kamar dai su, a ranar da suke ganin
(sakamako) abin da ake yi musu
wa'adi, ba su zauna ba, fiice sa'a
guda daga yini. Iyarwa (dai da
o^J^i £M^ Oi^L- VJJ£Jy)
768
47 — Suratu Muhammad
\<X±i<*
\$&m-*
Manzanci). Shin, akwai wanda za a
halakar? (Babu), face mutane
fasikai.
JL S ♦.#> *' T{
(jpSj^^^l
Tana karantar da kwacfaitarwa ga yin jihadi domin tsaron
addini da takobi, kuma tana gargadi ga barin jihadi.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin fcai.
1. Wadanda suka kafirta, kuma
suka kange mutane daga tafarkin
Allah, (Allah) Ya 6atar da ayyu-
kansu.
2. Kuma wadanda suka yi imani,
kuma suka aikata ayyukan kwarai,
kuma suka yi imani da abin da aka
sassaukar ga Muhammadu, alhali
kuwa shl ne gaskiya daga Ubangi-
jinsu, (Allah) Ya karkare musu
miyagun ayyukansu, kuma Ya
kyautata halayensu.
3. Wannan kuwa saboda, lalle,
wadanda suka kafirta sun bi karya,
kuma lalle wadanda suka yi imani,
sun bi gaskiya daga Ubangijinsu.
Kamar wannan ne Allah Yake
bayyana wa mutane misalansu.
4. Saboda haka, idan kun hadu
da wadanda suka kafirta, sai ku yi
ta dukan wuyoyinsu har a lokacin
•>»"»fr'i Z' iC'if ' *'<\ KZ'' A\** -Iff
769
47 — Suratu Muhammad
%&%&-*
da kuka yawaita musu kisa, to, ku
tsananta cfaurinsu, sa'an nan imma
karimci a bayan haka ko biyan
fansa, har yaki ya saukar da kayan-
sa masu nauyi. Wancan, da Allah
na so, da Ya ci nasara a kansu, (ba
tare da yakin ba) kuma amma (Ya
wajabta jihadi) domin Ya jarraba
sashenku da sashe. Kuma wacfanda
aka kashe a cikin tafarkin Allah, (I)
to, ba zai batar da ayyukansu ba.
5. Zai shiryar da su, kuma Ya
kyautata halayensu.
6. KumaYashigardasuAljanna
(wadda) Ya siffanta ta a gare su.
7. Ya ku wacfanda suka yi imani !
Idan kun taimaki Allah, zai taimake
ku, kuma Ya tabbatar da dugadu-
ganku. (2) .
8. Kuma wacfanda suka kafirta,
to, rubushi ya tabbata a gare su,
kuma (Allah) Ya Batar da ayyukansu.
9. Wannan, saboda lalle su, sun
ki abin da Allah Ya saukar, domin
haka Ya Bata ayyukansu.
10. Shin, ba su yi tafiya ba, a
cikin kasa, domin su gani yadda
akibar wacfanda ke a gabaninsu ta
kasance? Allah Ya darkake a kansu.
Kuma akwai misalan wannan aki-
bar ga kafirai (na kowane zamani).
p^plj^eoli
(1) Tafarkin Allah, (fi sabilillahi) a wannan sura tana nufin jihadi na takobi domin
daukaka kalmar Allah da tsare ta. Ana fassara tafarkin Allah a wadansu wurare da jihadi
na takobi ko na magana domin shiryar da mutane ko domin tsaron gaskiya, ko kuma
karantarwa, da kuma tsare rai daga shawarta da hushinta. A cikin Hadisi ana ruwaitowa
cewa tsaron rai daga shawarta da hushinta shT ne jihadi wanda ya fi girma.
(2) Tabbatar da dugadugan kafafun, yana nufin sanya musu zarumci a cikin
zukatansu, domin kafafunsu, su kafu a wurin yaki, domin kada su gudu.
770
47 — Suratu Muhammad
&^J&-iV
11. Wancan! Sabdda lalle Allah
ne Maji6incin wacfanda suka yi
Tmani, kuma lalle, kafirai babu wani
majiBinci a gare su.
12. LaUe ne, Allah na shigar da
wacfanda suka yi Tmani kuma suka
aikata ayyukan kwarai a gidajen
Aljanna, kogunan ruwa na gudana
daga karkashinsu, kuma wadanda
suka kafirta, suna jin dan dadi (a
duniya) kuma suna ci, kamar yadda
dabbobi ke ci, kuma wuta ita ce
mazauni a gare su.
13. Kuma da yawa akwai alka-
rya, ita ce mafi tsanani ga karfi daga
alkaryarka wadda ta fitar da kai,
Mun halaka ta, sa'an nan kuwa
babu wani mai taimako a gare su.
14. Shin, wanda ya kasance a
kan wata hujja daga Ubangijinsa,
zai zama kamar wanda aka kawace
masa mugun aikinsa, kuma suka
bibbiyi son zuciyoyinsu?
75. Misalin Aljanna, wadda aka
yi wa'adinta ga masu takawa, a
cikinta akwai wadansu koguna na
ruwa, ba mai sakewa ba, da wadan-
su koguna na madara wadda tfan-
danonta ba ya canjawa, da wadansu
koguna na giya mai dadi ga mas-
haya, da wadansu koguna na zuma
tatacce, kuma suna samu, a cikinta,
daga kowane irin 'ya'yan itace, da
wata gafara daga Ubangijinsu.
(Shin, masu wannan ni'ima na dai-
daita) kamar wanda yake madaw-
wami ne a cikin wuta, kuma an
shayar da su wani ruwa mai zafi har
ya kakkatse hanjinsu?
'•* ^st**'*
(g^^^li^U-
771
47 — Suratu Muhammad
O^^-IY
16. Kuma daga cikinsu akwai
wanda ke saurare (1) zuwa gare ka,
har idan sun fita daga wurinka, su
ce wa wacfanda aka bai wa ilmi,
"Mene ne (Muhammadu) ya facfa
cfazu?" Wacfannan ne wacfanda Al-
lah Ya shafe haske daga zukatansu,
kuma suka bi son zuciyoyinsu.
17. Kuma wacfannan da suka
nemi shiryuwa (Allah) Ya kara
musu shiryuwarsu, kuma Ya ba su
(sakamakon) takawarsu. (2)
18. To, shin, suna jiran (wani
abu)? Face Sa'a ta je musu bisa
abke, domin lalle sharucfcfanta sun
zo. To, yaya tunawarsu (3) take,
idan har ta je musu?
19. Saboda haka ka sani, cewa
babu abin bautawa face Allah,
kuma ka nemi gafara ga zunubin-
ka, (4) kuma saboda muminai maza
da muminai mata, kuma Allah Ya
san majuyarku da mazauninku.
20. Kuma wacfanda suka yi Tma-
ni suna cewa, "Don mene ne ba a
saukar da wata sura ba?" To, idan
aka saukar da wata sura bay-
yananna, kuma aka ambaci yaki a
cikinta, za ka ga wacfanda yake
'&>- JU3 -CJo ^boWui^ V )&Jb*j$&
cJ^ »tak ijyj* <jJ/ jy Jy> »* -ClJ^oJ**}
(1) Wannan shi ya nuna cewa wani cfan rahoto ba zai iya fahimtar gaskiya ba,
matukar ana aikin Allah da gaskiya. Allah na sanya tsoro a cikin zukatan kafirai.
(2) Takawa, ita ce bin umurnin Allah da nlsantar haninSa. Saboda haka abin da
Allah ke bai wa mai takawa, shi ne sakamakon aikinsa wanda ya yi daidai da Sunnar
Annabi, tslra da amincin Allah su tabbata a gare shi.
(3) Tunawarsu da wa'aztuwarsu ga Sa'a ba zai yi musu amfani ba, a bayan ta je
musu. Wa'azi ba ya amfani, sai idan wanda aka yi wa shi, ya yi aiki da shi a gabanin
mutuwa ta je masa.
(4) An umurci Annabi ya nemi gafara domin mutane su yi koyi da shi, domin Allah
Ya riga ya tsare shi daga zunubi a gabani da bayan Manzanci.
772
47 — Suratu Muhammad
flg»j»-iv
akwai wata cuta a cikin zukatansu
suna kallo zuwa gare ka, irin kallon
wanda aka rufe da magagi saboda
mutuwa. To, abin da yake mafifici a
gare su:
21. Yin da'a da magana mai
kyau. Sa'an nan idan aTamarin ya
£ullu, (1) to, da sun yi wa Allah
gaskiya, lalle da ya kasance mafifi-
ci a gare su.
22. To, shin, kuna fatan idan
kun juya (daga umurnin) za ku yi
6arna a cikin £asa, kuma ku yan-
yanke (2) zumuntarku?
23. Wadannan su ne wadanda
Allah Ya la'ane su, sa'an nan Ya
kurumtar da su, kuma Ya makantar
da ganinsu.
24. Shin to, ba za su kula da
Al£ur'ani ba, ko kuwa a kan zuka-
tansu akwai makullansu?
25. Lalle ne, wadanda suka
koma baya a kan dugadugansu a
bayan shiryuwa ta bayyana a gare
su, Shaidan ne ya £awata (3) musu
(haka), kuma ya yi musu shibta.
26. Wancan, domin lalle su, sun
ce wa wadanda suka £i abin da
Allah Ya saukar, "Za mu yi muku
da'a ga sashen aTamarin," alhali
kuwa Allah Yana sane da gana-
warsu ta aslri.
(1) Kulluwar aramari, shi ne umurni da yin yaici, yi wa Allah gaskiya, shi ne zartar da
umurninSa, ba tare da tsoro ba. Tsoro, munafunci ne.
(2) Domin barin jihadi yana kai ga watsuwar 6arna da fasadi a cikin £asa. Watsuwar
fasadi, yana kai ga yanke zumunta tsakanin dangi, saboda zaluntar juna.
(3) Barin jihadi, ridda ne da komawa zuwa ga kafirci da £awatawar Shaidan cewa
rashin zuwa ya£i na sanya kwanciyar hankali da rashin mutuwa, kuma yana sanya musu
waswasi da haka.
773
47 — Suratu Muhammad
lg&%&-M
27. To, yaya halinsu yake a loka-
cin da mala'iku ke kar6ar rayukan-
su, suna dukan fuskokinsu da
cfuwaiwansu?
28. Wannan, domin lalle su, sun
bi abin da ya fusatar da Allah,
kuma sun ki yardarSa, saboda
haka Ya 6ata ayyukansu.
29. Ko kuwa wacfanda ke da wa-
ta cuta a cikin zukatansu, suna za-
ton cewa Allah ba zai fitar da mu-
gun kulle-kullensu (ga Musulunci)
ba?
30. Kuma da Muna so, da lalle
Mun nuna maka su. To, lalle kana
sanin su game da alamarsu. Kuma
lalle kana sanin su ga tuntu6en
harshe, alhali kuwa Allah Yana
sanin ayyukanku.
31. Kuma lalle ne, Muna jarraba
ku, har Mu san masu jihadi daga
cikinku, da masu hakuri, kuma
Muna jarraba labaranku.
32. Lalle ne wacfanda suka kafir-
ta, kuma suka kange daga tafarkin
Allah, kuma suka sa6a wa Manzon
Sa a bayan shiriyar ta bayyana a
gare su, ba za su cuci Allah da kome
ba, kuma za Ya 6ata ayyukansu.
33. Ya ku wadanda suka yi ima-
ni ! Ku yi da'a ga Allah, kuma ku yi
da'a ga ManzonSa, kuma kada (1)
ku 6ata ayyukanku.
v<^*^>, »> ■
(1) Kada ku bata ayyukanku da kin cfa'a ga Allah da ManzonSa ga fita zuwa yaki da
waninsa. Ridda na bata ayyuka, kuma riya da mamakin kai na bata ladar ayyuka, kuma
kware da cutarwa suna bata ladar sadaka. Sauran manyan zunubbai, ba su bata ayyuka sai
ga ra'ayin Mu'utazilawa masu cewa manyan zunubbai na bata ladar ayyuka kamar ridda.
An bata maganarsu da ayar da ke cewa, "Allah na gafarta abin da ya kasa haka ga wanda
Ya so". Suratun Nisa aya ta 48.
774
47 — Stiratu Muhammad
S^iS^-iv
34. Lalle ne, wacfanda suka ka-
firta, sa'an nan kuma suka kange
(mutane) daga tafarkin Allah, sa'an
nan suka mutu, alhali kuwa suna
kafirai, to, Allah ba zai yi gafara ba
a gare su.
35. Saboda haka kada ku yi rau-
ni, kuma (kada) ku yi kira zuwa ga
sulhi alhali kuwa ku ne mafi dauka-
ka, kuma Allah na tare da ku, kuma
ba zai nakasa muku ayyukanku ba.
36. Rayuwar duniya, wasa da
abin shagala kawai (1) ce, kuma idan
kun yi imani, kuma kun yi takawa,
Allah zai kawo muku ijarorinku,
kuma ba zai tambaye ku dukiyarku
ba.
37. Da Allah zai tambaye ku su
(dukiyoyin) har Ya wajabta muku
bayarwa, za ku yi rowa kuma Ya
fitar da miyagun kulle-kullenku.
38. Ga ku, ya ku wadannan!
Ana kiran ku domin ku ciyar ga
tafarkin Allah, sa'an nan daga ci-
kinku akwai mai yin rowa. Kuma
wanda ke yin rowa, to, yana yin
rowar ne ga kansa. Kuma Allah^ne
Wadatacce alhali kuwa ku faklrai
ne. Kuma idan kuka juya (daga yi
Masa cfa'a), zai musanya wacfansu
mutane, wadansunku, sa'an nan ba
za su kasance kwatankwacinku ba.
?>-i^ -if
ftp psJiopl^obp^^L?
*f • ^ • i 4 . >\ ^ "">- tvs 9> \~?
(1) Wasa, shi ne dukan aiki wanda aka yi ba da nufin wata fa'ida ta addini ba, watau
ana yin sa ne domin a sami abin aikatawa a 6ata lokaci. Dukan ayyukan da mutum ya yi da
nufin rayuwar duniya kawai, to, ya zama wasa ko da cin abinci ne da karatu. Kuma duk
abin da mutum ya yi da niyyar bin umurnin Allah, wajibi, to, ya zama aikin Lahira ko da
cin abinci ne da jima'insa da matarsa, kamar yadda yake a cikin Hadisin Annabi, tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi.
775
48 - Suratul Fat'h
&s4-£A
Tana karantar da yadda Allah Ya shirya tsayuwar daular
Musulunci ta hanyar siyasa domin ta tsare hakkokin Allah da na
Musulmi.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Lalle Mu, Mun yi maka rin-
jaye (a kan makiyanka), rinjaye
bayyananne.
2. Domin Allah Ya shafe abin da
ya gabata na laifinka (1) da abin da
ya jinkirta, kuma Ya cika ni'imarSa
a kanka, kuma Ya shiryar da kai ga
hanya madaidaiciya.
3. Kuma Allah Ya taimake ka,
taimako mabuwayi.
4. ShT ne Wanda Ya saukar da
natsuwa a cikin zukatan muminai
domin su kara wani imani tare da
imaninsu, alhali kuwa rundunonin
OJl^^^l^ilSl
^iSl^j^J^iOJf-^^^^r^J
(1) Laifin Annabi wanda Allah Ya gafarta, shi ne a lokacin da ya fara kiran mutane
zuwa ga bauta wa Allah, Shi Kacfai, masu bauta wa wacfansu abubuwa sun ga laifinsa a
wannan, sun yi iciyayya da shi saboda haka, har suka yi yaki da shi, domin tsare ibadarsu,
da al'adunsu, har a lokacin da Allah Ya ba shi rinjaye bayyananne a kansu, suka gane
amfanin abin da yake kiran su zuwa gare shi na alheri, suka yafe laifin da suke zato, kuma
suka so shi son da ba ya karewa har Tashin ICiyama. Wannan ni'imar Allah ce babba ga
AnnabinSa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Hanya madaidaiciya, ita ce
shari'ar da Allah Ya ba shi, wadda ke jan jama'arsa a kan alheri^ har ya zuwa Tashin
ICiyama, kuma su tashi a cikin aleri mafi girma, matukar dai sun bT ta, sun yi aiki da ita
gwargwadon yadda ya nuna musu ita.
776
48 - Stiratul Fat'h
-1A
sammai da Rasa, na Allah kawai ne,
kuma Allah Ya kasance Masani,
Mai hikima.
5. Domin Ya shigar da muminai
maza da muminai mata gidajen Al-
janna, kogunan ruwa na gudana
daga karkashin gidajen, suna ma-
da wwama a cikinsu, kuma Ya kan-
kare musu munanan ayyukansu.
Wannan abu ya kasance a wurin
Allah babban rabo, mai girma.
6. Kuma Ya yi azaba ga munafi-
kai maza da munafikai mata da
mushirikai maza da mushirikai
mata, masu zaton mugun zato game
da Allah, mugunyar masifa mai
kewayewa ta tabbata a kansu,
kuma Allah Ya yi hushi da su, kuma
Ya la'ane su, kuma Ya yi musu
tattalin Jahannama, kuma ta muna-
na ta zama makoma (gare su).
7. Rundunonin sammai da kasa
na Allah kawai ne, kuma Allah Ya
kasance Mabuwayi, Mai hikima.
8. Lalle Mu, Mun aike ka, kana
mai shaida, kuma mai bayar da
bushara kuma mai gargacfi.
9. Domin ku yi Tmani da Allah
da ManzonSa, kuma ku karfafa shi,
kuma ku girmama shi, kuma ku
tsarkake Shi (Allah) safiya da
maraice.
10. Lalle wacfanda ke yi maka
mubaya'a (1) , Allah kawai ne suke yi
$^££&&l£%
%:'" :*:rr. *»■
■%<&$$£-■'*
<"*- r'ki
fry ]j^j^LA o <\**jj j^ ^ j^j
^ . **v '"\ ^ * l<*l -I I > 1^' ^ .»•-•
(1) Asalin mubaya'a daga bai'u ne, watau ciniki, wanda ya yi mubaya'a ga Limamin
Musulmi kamar ya yi ciniki ne ya sayar da ransa, domin ya karbi Aljanna daga Allah a
Ranar Kiyama. Mubaya'a ta farko, ita ce wadda aka yi wa Annabi a Hudaibiyya wani cfan
gari ne kusa da Makka a hanyar Jadda, tafiyar kwana daya. An ce tana a cikin Hurumi,
wadansu sun ce ba ta cikinsa.
777
48 - Suratul Fat'h
£&#lj&-tA
wa mubaya'a, Hannun Allah na
bisa hannayensu, saboda haka wan-
da ya warware, to, yana warwarewa
ne a kan kansa kawai, kuma wanda
ya cika ga alkawarin da ya yi wa
Allah a kansa, to, (Allah) zai kawo
masa ijara mai girma.
11. Wacfanda aka bari daga
kauyawa (1) za su ce maka,
"Dukiyoyinmu da iyalanmu sun
shagaltar da mu, sai ka nema mana
gafara." Suna fada, da harsunansu,
abin da ba shi ne a cikin zukatansu
ba. Ka ce, "To, wane ne ke mallakar
wani abu daga Allah saboda ku,
idan Ya yi nufin wata cuta a gare ku
ko kuma (idan) Ya yi nufin wani
amfani a gare ku? A'a, Allah Ya
kasance Mai labartawa ne ga abin
da kuke aikatawa."
12. A'a kun yi zaton Annabi da
muminai, ba za su komo zuwa ga
iyalansu ba, har abada. Kuma an
kawata wannan (tunani) a cikin
zukatanku, kuma kun yi zato, zaton
mugunta, kuma kun kasance muta-
ne halakakku.
13. Kuma wanda baiyiTmani da
Allah da kuma Manzonsa ba, to,
lalle Mu, Mun yi tattalin wuta mai
tsananin kuna, domin kafirai.
9 )&\*jj^^ygS\Qj*J-&j
(1) Annabi, tslra da aminci su tabbata a gare shi, ya yi nufin tafiya Makka domin ya
yi Umra saboda mafarkin da ya yi cewa ya ga ya shiga Makka shi da Sahabbansa, suna
masu yin aski da suisuye na ibada, sai ya ce wa kauyawan da ke gefen Madina su fita tare
da shi domin kada Kuraishawa su facfa shi da yaki, su tsare shi daga Dakin. Kuma ya yi
harama ya kora hadaya domin mutane su san ba yaki yake nufi ba. Sai wacfansu masu
yawa daga kauyawa suka yi nauyin fita, suka yi zamansu kuma suka ce, "Zai tafi zuwa ga
mutanen da suka yake shi a tsakar gidansa a Madina, suka kashe Sahabbansa. Ba za mu b!
shi ba domin mu halaka kanmu."
778
48 - Suratul Fat'h
§g#ljg£. - 1A
14. Mulkin sammai da kasa na
Allah kawai ne, Yana gafartawa ga
wanda Yake so, kuma Yana azabta
wanda Yake so, alhali kuwa Allah
Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin
kai.
75. Wacfanda aka bari za su ce
idan kun tafi zuwa ga wacfansu
ganimomi (1) domin ku karBo su,
"Ku bar mu, mu b! ku." Suna son
su musanya maganar Allah ne. Ka
ce, "Ba za ku bl mu ba. Kamar
wannan ne Allah Ya ce, a gabanin
haka." Sa'an nan za su ce, "A'a,
kuna dai hassadar mu ne." A'a, sun
kasance ba su fahimtar (abubuwa)
sai kacfan.
16. Ka ce wa wacfanda aka bari
daga kauyawa, "Za a kira ku zuwa
ga wacfansu mutane (2) masu tsana-
nin yaki (domin) ku yake su ko
kuwa su musulunta. To, idan kun yi
cfa'a, Allah zai kawo muku wata
ijara mai kyau, kuma idan kuka
juya baya kamar yadda kuka juya a
gabanin wancan, zai azabta ku,
azaba mai racfacfi."
17. Babu laifi a kan makaho,
kuma babu laifi a kan gurgu, kuma
babu laifi a kan majiyyaci. Kuma
wanda ya yi cfa'a ga Allah da Man-
zonSa, (Allah) zai shigar da shi a
gidajen Aljanna, koguna na gudana
" ' ' \ > . r^ ^ . *t,
<.f-V>
fry '** ff '\'S\'»" "\.u'S 'A
(1) A bayan sulhun Hudaibiyya Allah Ya yi wa Annabi alkawarin zai bucfe masa
Haibara ya sami gamma mai yawa, amma kuma kada ya bari kauyawan da aka nema su
fita zuwa Makka, suka ki su flta tare da shi.
(2) Abubakar zai kira su domin su yaki mutanen Musailama, ko kuma su yaki Rumu
da Farisa a bayan rayuwar Annabi, tsTra da amincin Allah su tabbata a gare shi.
779
48 - Stiratul Fat'h
g5$IJ&-lA
daga karkashinsu. Kuma wanda ya
juya baya, (Allah) zai azabta shi,
azaba mai racfacfi.
18. Lalle ne, haklka, Allah Ya
yarda da muminai a lokacin da suke
yi maka mubaya'a (1) a karkashin
itaciyar nan domin Ya san abin da
ke cikin zukatansu, sai Ya saukar
da natsuwa a kansu, kuma Ya saka
musu da wani cin nasara maku-
sanci.
19. Da wacfansu ganimomi masu
yawa da za su kar6o su. Kuma
Allah Ya kasance Mabuwayi, Mai
hikima.
20. Kuma Allah Ya yi muku
wa'adin wacfansu ganimomi masu
yawa, wacfanda za ku kar6o su,
©Ot;u*
*?>^
(1) A bayan da Annabi ya sauka a Hudaibiyya, ya kirayi Khuraish bn Umaiya el
Khuza'i ya aike shi Makka ya aza shi a kan rakuminsa domin ya gaya wa shugabanninsu
cewa ya taho Umra ne, bai zo da yaki ba. Sai suka soke rakumin Annabi, kuma suka yi
nufln kashe Khuraish amma Ahabish suka hana su, ya zo ya gaya wa Annabi. Sa'an nan
Annabi ya kira Umar bn Khattab domin ya aika shi zuwa Makka, sai ya ce, "Ya Manzon
Allah ina tsoron raina ga Kuraishawa, babu bani Adiyyin bn Ka'ab a Makka balle su kare
ni daga gare su, amma ina nuna maka wani mutum wanda ya ft ni dangi a cikinta, shi ne
Usman bn Affan." Sai Annabi ya kira Usman ya aike shi zuwa ga Abi Sufyan da
shugabannin Kuraish, ya ba su labarin cewa bai zo yaki ba. ya taho ne domin ziyara kawai
ga wannan T)aki domin ya girmama alfarmarsa. Ya rubuta masa takarda ya tafi da ita.
Kuma ya umurce shi da ya yi bushara ga Musulmi masu rauni, cewa cin nasara ya yi kusa,
kuma Allah zai daukaka addininSa. Usman ya fita ya tafi Makka ^a iske cewa Kuraishawa
sun hacfu a kan hana Annabi shiga Makka. Abban bn Sai'Td bn Asi ya hadu da Usman a
lokacin shigarsa Makka, sai ya dauke shi a kan rakumarsa, ya ba shi makwabtaka domin
kada a kashe shi, har ya kai takardar Annabi. Suka nace cewa Annabi ba zai shiga ba, suka
ce wa Usman, "Idan yana son cfawafi sai ya yi," Sai ya ce ba zai yi ba sai Manzon Allah ya
yi. Musulmi suka ce, "Usman ya ji dadi ya yi dawafi," sai Annabi ya ce, "Ban yi zaton
Usman zai yi ba." Sa'an nan labari ya zo wa Annabi, cewa an kashe Usman, saboda haka
Annabi ya ce, "Idan sun kashe shi, sai mun yake su." Wannan ya sa aka yi masa mubaya'a
a karkashin itaciyar talh mai kama da farar kaya. A bayan haka Annabi ya aza hannunsa
na hagu a kan hannunsa na dama, ya ce, "Ga hannun Usmanu." Masu mubaya'a dubu da
dari uku ko dari hudu ne, da cewa za su yi yaki da Kuraishawa, ba za su gudu ba, sai dai su
mutu. Daga nan shugabancin ya tabbata. Umar bn Khattab ya sanya an sare itaciyar nan
domin mutane sun fara salla a karkashinta. Ba a yi' yaki ba, sai aka yi sulhu. Annabi ya
koma a shekara mai zuwa ya yi Umra.
780
48 - Suratul Fat'h
^$JJj^ - tA
kuma Ya gaggauta (1) muku wan-
nan. Kuma Ya kange (2) hannayen
mutane daga gare ku, kuma domin
ta kasance wata aya ce ga muminai,
kuma Ya shiryar da ku ga hanya
madaidaiciya.
21. Da wadansu (ganimomin (3) )
da ba ku da iko a kansu, lalle Allah
Ya kewaye su da saninSa, kuma
Allah Ya kasance Mai ikon yi ne a
kan dukan kome.
22. Kuma da wadanda suka ka-
firta sun ya£e ku, da sun juyar da
duwaiwai (domin gudu) sa'an nan
ba za su sami majibinci ba, kuma ba
za su sami mataimaki ba.
23. Hanyar Allah wadda ta shu-
de daga gabanin wannan, kuma ba
za ka sami musanya ba ga hanyar
Allah (ta taimakon muminai a kan
mai zaluntarsu).
24. Kuma Shi ne Ya kange han-
nayensu (4) daga gare ku, kuma da
hannayenku daga gare su, a cikin
Makka, bayan Ya rinjayar da ku a
kansu. Kuma Allah Ya kasance Mai
gani ga abinda kuke aikatawa.
&-&t& , S£ so 3 > fficJ&
(1) Cin nasara makusanci, shi ne cin Haibara, a bayan komawar Annabi Madina a
karshen Zul Hajji. Sa'an nan ya fita wajen karshen Muharram shekara ta bakwai. Aka
samo ganima mai yawa. Wadansu ganimomi na wacfansu kasashen da za a ci a nan gaba
har karshen duniya. Ganimar Haibara ita ce aka gaggauta.
(2) A lokacin da Annabi ya fita daga Madina zuwa Hudaibiyya Allah Ya kange
hannuwan Yahudawa daga iyalan Musulmi na cikin Madina, in da ba domin haka ba, sai
su je su facfa su da kashi da kamu. Sai Allah Ya jefa tsoro a cikin zukatansu.
(3) Ganima da aka yi musu gaggawa da ita, ita ce Haibara. Gamma wadda ba su da
Tko da ita, ita ce sauran kasashen duniya inda Musulmi suka ci, suka mallake shi, na kasar
Rumawa da Farisawa da Masar da sauransu.
(4) Wadansu Kuraishawa ne, su tamanin, suka kewaye Musulmi a Hudaibiyya, da
niyyar yaudara, sai aka kame su, su duka, aka kai su ga Annabi, shi kuma ya yafe musu, a
bayan ya nuna musu rinjaya. Wannan shi ne ya sabbaba yin sulhu.
781
48 - Suratul Fat'h
-1A
25. Su ne wacfanda suka kafirta,
kuma suka kange ku daga Masal-
lacin Harami, da hadaya tana tsare
(sun hana ta) ta isa ga wurinta.
Kuma ba domin wadansu maza
muminai da wacfansu mata mumi-
nai ba, ba ku sansu ba, ku taka su
har wani aibi ya same ku daga gare
su, ba da sani ba, (da Allah Ya yi
muku iznin yaki), domin Allah Ya
shigar da wanda Yake so a cikin
rahamarSa. Da (muminai) sun
tsabbace da Mun azabtar da wa-
cfanda suka kafirta daga gare su da
azaba mai radacfi.
26. A lokacin da wacfanda suka
kafirta suka sanya hananar kabi-
lanci a cikin zukatansu, hananar
kabilanci irin (1) na Jahiliyya, sai
Allah Ya saukar da natsuwarSa a
kan ManzonSa, kuma da a kan
muminai, kuma Ya lazimta musu
kalmar takawa, (2) alhali kuwa sun
kasance mafi dacewa da ita, kuma
ma'abutanta. Kuma Allah Ya ka-
sance Masani game da dukan kome.
27. Lalle ne, hakika, Allah Ya
gaskata wa ManzonSa mafarkinsa
da gaskiya : lalle za ku shiga Masal-
-£>> »'< ^ ^ \f x' turf > ' %*i ^< ' ' ' *""\
^(1) A lokacin da Kuraishi suka ga ba su iya yaki da Annabi, suka doge da
kabTlancinsu, ta hanyar sulhu. Suka aika Sahlu bn Amru da Huwaitib bn Abdul Uzza da
Makraz bn Hafs bn Ahnaf domin neman sulhu bisa kada Annabi ya shiga Makka a
wannan shekara, amma shekara mai komowa ya je ya shiga Makka kwana uku, su kuma
su flta har ya kare Umra ya fita. Annabi ya karbi sulhun. Aka ce Aliyu bn Abi Talib ya
rubuta. Wajen rubutun kuma aka so a yi tashin hankali, domin ya rubuta 'Manzon Allah
ya yi sulhu da Kuraishawa', sai kuma suka ce ba su yarda a rubuta kalmar Manzon Allah
ba. Sai Annabi ya sanya hannunsa mai daraja ya soke kalmar da ake sabani a kanta. Allah
Ya saukar da natsuwa ga kowa.
(2) Kalmar takawa ita ce kalmar shahada domin daukar alkawari da ita yana lazimta
wa mai ita bin umurnin Allah, da dadi ko ba dadi, ta haka sai natsuwa ta samu. Ana ce
mata kalmar takawa domin da ita ake kare rai daga bin Shaidan. Ma'anar takawa, ita ce
kariya.
782
48 - Suratul Fat'h
&3ljg£-£A
lacin Harami, in Allah Ya so, kuna
masu natsuwa, masu aske kawu-
nanku da masu suisuye, ba ku jin
tsoro, domin (Allah) Ya san abin da
ba ku sani ba, sa'an nan Ya sanya
wani cin nasara makusanci a bayan
wannan.
28. Shi ne Wanda Ya aiki Man-
zonSa da shiriya da addinin gaskiya
domin Ya rinjayar da shi a kan
addinai dukansu. Kuma Allah Ya
isa Ya zama Mai shaida.
29. Muhammadu Manzon Allah
ne. Kuma wadannan da ke tare da
shi masu tsanani ne a kan kafirai,
masu rahama ne a tsakaninsu, kana
ganin su suna masu ruku'i masu
sujada, suna neman falala (1) daga
Ubangijinsu, da yardarSa. Ala-
marsu tana a cikin fuskokinsu, daga
kufan sujuda. (2) Wannan shi ne
siffarsu, a cikin Attaura. Kuma
siffarsu a cikin InjTla, ita ce kamar
tsiron shuka wanda ya fitar da res-
hensa, sa'an nan ya karfafa shi, ya
yi kauri, sa'an nan ya daidaita a kan
kafafunsa, yana bayar da sha'awa
ga masu shukar, domin (Allah) Ya
fusatar da kafirai game da su.
Kuma Allah Ya yi wa'adi ga wadan-
da suka yi imani, kuma suka aikata
ayyukan kwarai, daga cikinsu, da
gafara da ijara mai girma.
.Y^<* \ *-z»t'*
>\ss'l '.*.'. .*\'.' -,.r C **\k'C\"
(1) Neman falala da sana'ar hannunsu, ko fatauci, ba su zama nauyi a kan mutane ba,
kowanensu ya dogara ga Allah, sa'an nan yana rayuwa a kan halaliyarsa.
(2) Kufan sujuda, shi ne hasken fuskokinsu da annurinsu. Fuska ita ce madubin
zuciya. Ana gane zuciyar kwarai daga fuskarta. Ba ya halatta ga mutum ya rika darkaka
goshinsa ga Rasa domin ya yi kwadon salla. Wannan alamar riya ce.
Facfakarwa.Nan ne Rarshen dogayen surori da ake ce wa Mutfawwalatu. An Rare su da
surori biyu, Kital domin yaki, da Fat'h domin tsarin gudanar da siyasa saboda tsaron
Addlni. Bayan haka kuma sai gajerun surori, watau Mufassalatu.
783
49 — Suratul Hujurat
&mm-*
Tana karantar da halayen kwarai da ladubba na addini da na
zaman jama'a a tsakaninsu.
&!&£*.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kal
1. Ya ku wacfanda suka yi imani !
Kada ku gabata (da kdme) gaba ga
Allah da ManzonSa. (1) Kuma ku yi
da'a ga Allah da takawa. Lalle Al-
lah Mai ji ne, Masani.
2. Ya ku wadanda suka yi Tmani !
Kada ku daukaka saututtukanku (2)
bisa sautin Annabi, kuma kada ku
bayyana sauti gare shi a magana,
kamar bayyanawar sashenku ga
sashe, domin kada ayyukanku su
6aci, alhali kuwa ku ba ku sani ba.
3. Lalle wadanda ke runtsewar
saututtukansu a wurin Manzon Al-
lah, wadannan ne wadanda Allah
Ya jarrabi zukatansu ga takawa.
Suna da wata irin gafara da ijara
mai girma.
(1) Wannan ya nuna mana cewa ba ya halatta ga Musulmi ya yi wani aiki ko ya facfi
wata magana sai ya san hukuncin Allah a cikinsu. Kuma kada ya kara wayonsa a kan abin
da Allah Ya ce, kuma kada ya rage idan yana da ikon cikawa. Dukan wannan yakan ja
Musulmi ga 6acin ayyukansa, watau ya yi ridda daga Musulunci.
(2) Ladubban zama da shugaba. Annabi shi ne kan shugabanni, sai dai da'a gare shi
wajibi ne ga kome, sauran shugabanni ga abin da bai sa6a wa shari'a ba.
784
49 — Suratul Hujurat
omm-*
4. Lalle wacfanda ke kiranka
daga bayan cfakuna, mafi yawansu
ba su aiki da hankali.
5. Kuma da lalle su, sun yi haku-
ri har ka fita zuwa gare su, hakika,
da ya kasance mafi alheri gare su,
kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin
kai.
6. Ya ku wacfanda suka yi Tmani !
Idan fasiki (1) ya zo muku da wani
babban labari, to, ku nemi bayani,
domin kada ku cuci wacfansu muta-
ne a cikin jahilci, saboda haka ku
wayi gari a kan abin da kuka aikata
kuna masu nadama.
7. Kuma ku sani (cewa) lalle ne,
a cikinku akwai Manzon Allah. Da
yana bin ku ga (halaye) masu yawa
na aFamarin, da kun auku a cikin
zunubi, kuma amma Allah Ya soyar
da Tmani a gare ku, kuma Ya kawa-
ta shi a cikin zukatanku, kuma Ya
kyamantar da kafirci da fasicci da
sabo zuwa gare ku. Wacfannan (da
suka lazimci sifofin nan) su ne
shiryayyu.
8. Bisa ga falala daga Allah da
ni'ima. Kuma Allah Masani ne,
Mai hikima.
9. Kuma idan jama'a biyu ta
muminai suka yi yaki, to, ku yi
sulhu, a tsakaninsu. Sai idan cfayan-
su ta yi zalunci a kan gudar, to, sai
(1) Idan wani ya kai labarin 6arna, kada a yi aiki da shi sai bayan an bincika an san
gaskiyar al'amarin, kafin a yi aiki da shi. Fasiki ga asalin kalma shi ne duka wanda ya
karkace daga hanyar kwarai wadda aka sani. A nan, fasiki, shi ne mai kai labarin da yake
akwai tashin hankali a cikinsa, ko kuma abin tsoro domin ya sanya riidu a tsakanin jama'a
tun ba a san hakikanin al'amarin ba.
785
49 - Suratul Hujurat
&mm-*
ku yaki wadda ke yin zalunci har ta
kdma, zuwa ga umurnin Allah. To,
idan ta koma, sai ku yi sulhu a
tsakaninsu da adalci, kuma ku dai-
daita. (1) Lalle Allah na son masu
daidaitawa.
10. Muminai 'yan'uwan juna ka-
wai ne, saboda haka ku yi sulhu a
tsakanin 'yan'uwanku biyu, kuma
ku bi Allah da takawa, tsam-
maninku, a yi muku rahama.
11. " Ya ku wacfanda suka yi ima-
ni ! Kada wadansu mutane su yi
izgili game da wadansu mutane,
mai yiwuwa ne (abin yi wa izgilin) su
kasance mafifita daga gare su (masu
izgilin), kuma wadansu mata kada
su yi izgili game da wadansu mata
mai yiwuwa ne su kasance mafifita
daga gare su. Kuma kada ku aiban-
ta kanku, kuma kada ku jefijuna da
miyagun sunaye na lakabobi. Tir da
suna na fasicci a bayan Tmani.
Kuma wanda bai tuba ba, to, wa-
cfannan su ne azzalumai.
12. Ya ku wadanda suka yi Tma-
ni! Ku nisanci abu mai yawa na
zato. Lalle sashen zato laifi ne.
Kuma kada ku yi rahoto, kuma
kada sashenku ya yi gibar sashe.
Shin, cfayanku na son ya ci naman
"H ^^»r»-r *^ v 1 f >-
'opMf^&LX$£j
t^A A^pjJ J^=*b OU ^=>J^\ six*)
(I) Wannan tsari na sulhu a tsakanin al'umma biyu masu fada, shi ne hanya mafi
kyau wadda har yanzu wayon duniya bai kai ga yin aiki da shi ba. Da yanzu an zauna
lafiya, da Majalisar TDinkin Duniya na iya aiki da shi. Haka yake kuma ga sauran
hukunce-hukuncen mutanen duniya. Shan'ar Musulunci saboda adalcin da ke cikinta,
kuma wayon duniya bai kai ta ga ana iya zartar da shi ba, shine ya sa kasashen Musulunci
na kaucewa gare ta, domin son ran shugabanninsu. Allah Ya mayar da mu ga addininmu !
Dukan Musulmin da ya kauce wa shan'ar Musulunci, to, ya kauce ne domin ya sami
damar yin zalunci, kuma idan ya halatta kaucewar, ya zama ba Musulmi ba.
786
49 — Suratul Hujurat
&mm-*
ctan'uwansa yana matacce? To, kun
kl shi (cin naman). Kuma ku bi
Allah da takawa. Lalle Allah Mai
karbar tuba ne, Mai jin kai.
13. Ya ku mutane! (1) Lalle ne
Mu, Mun halitta ku daga namiji da
mace, kuma Muka sanya ku dango-
gi da kabiloli, domin ku san juna.
Lalle mafificinku daraja a wurin
Allah, (shi ne) wanda yake mafi-
ficinku a takawa. Lalle ne, Allah
Masani ne, Mai kididdigewa.
14. Kauyawa suka ce,J'Mun yi
Tmani." Ka ce, "Ba ku yilmani ba,
amma dai ku ce, 'Mun mlka wuya,'
Tmani bai gama shiga a cikin zuka-
tanku ba. Kuma idan kun yi da'a ga
Allah da ManzonSa, to, ba zai rage
muku kome daga ayyukanku ba.
Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin
kai."
15. Muminan gaskiya kawai, su
ne wadanda suka yi imani da Allah
da ManzonSa, sa'an nan ba su yi
shakka ba, kuma suka yi jihadi da
dukiyarsu da kuma rayukansu, ci-
kin tafarkin Allah. Wacfannan su ne
masu gaskiya.
16. Ka ce, "Kuna sanar da Allah
ne game da addininku, alhali kuwa
Allah Ya san abin da ke cikin sam-
mai da abin da ke cikin kasa, kuma
Allah Masani ne ga dukan kome?"
~fii\*5i'* *> ■■
4 ^^ *4<^y ' * t "* *'"'-* ' '" ' -'"'' ; >* ■*
>^ v rr^''t ^ -\\ ^ * **\t^4.
(1) Ya kirayi masu imani a cikin wannan sura sau biyar ga abin da ya ke6anta da su
na umurni da hani kamar yadda Lukman ya kirayi dansa wajen yi masa wasiyyoyi. Kuma
ya kirayi mutane a wannan aya ga abin da ya hada muminai da kaflrai wajen halitta, watau
alfahari da dangantaka. Dangantaka ba ta cfaukaka wanda takawarsa ba ta daukaka^shi
ba, kuma ba ta rage wanda takawarsa ta cfaukaka shi. FifTkon takawa, shT ne fTftko
tabbatacce.
787
50 - Suratu K
<&%&? — <>•
17. Suna yin gori a kanka wai
sun musulunta. Ka ce, "Kada ku yi
gorin kun musulunta a kaina. A 'a,
Allah ne ke yi muku gori domin Ya
shiryar da ku ga Imani, idan kun
kasance masu gaskiya.
18. "Lalle Allah Yana sanin gai-
bin sammai da icasa, kuma Allah
Mai gani ne ga abin da kuke aika-
tawa."
J9 u^LLjoU->j^^
Tana karantar da yadda mai wa'azi zai yi amfani da kalmomi
da kuma ma'anoni masu tasTri ga rai. Annabi yakan yi huduba da
ita a kan mimbarinsa.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
1. K. Ina rantsuwa da Alkur'ani
Mai girma.
2. A'a, sun yi mamaki, cewa mai
gargacfi, daga gare su, ya zo musu,
sai kafirai suka ce, "Wannan wani
abu ne mai ban mamaki."
3. "Shin, idan muka mutu, kuma
muka kasance tur6aya (za a komo
da mu)? Waccan komowa ce mai
nisa.
4. Lalle ne, Mun san abin da
Rasa ke ragewa daga gare su, kuma
wurinMu akwai wani littafi mai
tsarewa.
SjXa^
788
50 - Suratu K
5. A'a, sun karyata ne game da
gaskiyar a lokacin da ta je musu,
saboda haka suna a cikin wani
aramari mai raurawa.
6. Shin, to, ba su yi dubi ba zuwa
ga sama, a bisa gare su, yadda
Muka gina ta, kuma Muka kawace
ta, kuma ba ta da wacfansu tsa-
ogi?
7. Da kasa, Mun mike ta, kuma
Mun jefa kafaffun duwatsu a cikin-
ta, kuma Mun tsirar, a cikinta daga
kowane ma'auri mai ban sha'awa?
8. Domin wayar da ido da tuna-
tarwa ga dukan bawa mai tawak-
kali?
9. Kuma Mun sassaukar, daga
sama, ruwa mai albarka, sa'an nan
Muka tsirar game da shi (itacen)
lambuna da kwaya abin girbewa.
10. Da itacen dablno dogaye,
suna da 'ya'yan itace gunda masu
hauhawar juna.
77. Domin arziki ga bayi, kuma
Muka rayar da kasa matacciya
game da shi. Kamar wannan ne
fitar daga kabari kake.
12. Mutanen Nuhu sun karyata,
a gabaninsu (mutanen yanzu) da
ma'abuta Rassi, (1) da Samudawa.
13. Da Adawa da Fir'auna da
'yan'uwan Lucfu.
'-<--"'■ "-X&&&&
(1) Rassi sunan wata rijiya ce. Mutanenta na zaune a gefenta da dabbobinsu, suna
bauta wa gumaka, aka aika musu wani Annabi, ana ce da shi Hanzala bn Safwan ko kuma
waninsa.
789
50 - Suratu K
14. Da ma'abuta Runci (1) da mu-
tanen Tubba'u, (2) kowanensu ya
Raryata Manzanni, sai RyacewaTa
ta tabbata.
15. Shin, to, Mun kasa ne game
da halittar farko? A'a, su, suna a
cikin rikici daga halitta sabuwa.
16. Kuma lalle ne, hakiRa, Mun
halitta mutum, kuma Mun san abin
da ransa ke yin waswasi da shi,
kuma Mu ne mafi kusanta zuwa
gare shi daga lakar jannayensa.
17. A lokacin da masu haduwa
biyu suke haduwa daga dama,
kuma daga hagu akwai wani (ma-
la 'ika) zaunanne.
18. Ba ya lafazi da wata magana
face a like da shi akwai mai tsaro
halartacce.
19. Kuma mayen mutuwa ya je
da gaskiya. Wannan shi ne abin da
ka kasance daga gare shi kana biji-
rewa.
20. Kuma aka hura a cikin kaho.
Wancan yinin Ryacewar ne fa.
21. Kuma kowane rai ya zo, tare
da shi akwai mai kora da mai
shaida.
22. (Sai a ce masa), "Lalle ne,
hakika, ka kasance a cikin gafala
daga wannan. To, Mun kuranye
maka rufinka, saboda haka ganin-
ka a yau, mai kaifi ne."
** .y y* '*ys "y.yy *"
^i^v jp ' '* ■* yy S** y y*ys}**'Zss' »
EJ -W^JcH^^**u^ cPC^Wj
< f.y y y \'""'?0 ' ' » » "*' ' ^* 9 ' s
(1) Ma'abuta Runci, mutanen Shu'aibu ne na farko. Bayan an halaka su, sa'an nan ya
tafi Madayana.
(2) Tubba'u, Sarkin Himyar ne, a Yemen, ya musulunta amma mutanensa suka Ri bin
sa ga addini, aka halaka su, shi kuma ya tsTra. Shi ne sarki wanda ya sa6a wa ka'ida : ya
musulunta amma mabiyansa ba su musulunta ba.
790
50 - Suratu K
1 •- ***
23. Kuma abokin hacfinsa (1) ya
ce, "Wannan shi ne abin da ke tare
da ni halarce."
24. (A ce wa mala'iku) "Ku jefa,
a cikin Jahannama, dukan mai ya-
wan kafirci, mai tsaurin rai.
25. "Mai yawan hanawa ga alhe-
ri, mai zalunci, mai shakka.
26. "Wanda ya sanya, tare da
Allah, wani abin bautawa na da-
bam, saboda haka ku jefa shi a cikin
azaba mai tsanani."
27. Abokin hacfinsa (2) ya ce, "Ya
Ubangijinmu! Ban sanya shi gir-
man kai ba, kuma amma ya kasance
a cikin Bata mai nlsa."
28. Ya ce, "Kada ku yi husuma a
wuriNa, alhali Na gabatar da kyace-
wa zuwa gare ku.
29. "Ba a musanya magana a
wuriNa. Kuma Ban zama Mai za-
lunci ba ga bayiNa."
30. Ranar da Muke cewa ga
Jahannama, "Shin, kin cika?"
Kuma ta ce, "Ashe, (3) akwai wani
kari?"
31. Kuma a kusantar da Aljanna
ga masu takawa, ba da nlsa ba.
Mjl^i ji U \ JA,4^J Uj
rf^it " I?'" 'lift" . f "Jt
* ' ** *' *\\ I- *
(1) Mala'ika mai rubutun aikinsa. Ba ya rabuwa da shi sai a halaye uku, wurin jima'i
da saiga da wanka. Mala'ikan da aka hacfa shi da shi domin ya rubuta ayyukansa.
(2) Shaicfanin da ke tare da shi. A cikin Hadisi an ruwaito cewa kowa yana da
Shaidani tare da shi, sai dai idan ya rinjaye shi, da bin abin da Allah Ya aza masa, ko kuma
shi Shaidanin ya rinjaye shi da bin son zuciyarsa.
(3) Wannan jawabi na Jahannama yana daukar ma'anoni biyu. Ta farko tana nuna ta
cika kwarai, amma tana kukan a kara mata wani abu a cikinta. Wannan fassara ta yi
daidai da ayar da ta ce, "Lalle na cika Jahannama daga aljannu da mutane gaba daya."
Sura ta 32, aya ta 13. Fassara ta biyu, ita ce Jahannama na neman kari tana hushi saboda
masu sa6a wa umurnin Allah. Sura ta 67 ayoyi 6, 7 da 8.
791
50 - Suratu K
32. "Wannan shl ne abin da ake
yi muku wa'adi da shi ga dukan mai
yawan komawa ga Allah, mai tsare-
war (umurninSa).
33. "Wanda ya ji tsoron Mai
rahama a fake, (1) kuma ya zo da
wata irin zuciya mai tawakkali."
34. (A ce musu) "Ku shige ta da
aminci. (2) Waccan ita ce ranar
dawwama.
35. Suna da abin da suke so a
cikinta, kuma tare da Mu akwai
karin ni'ima.
36. Kuma da yawa Muka hala-
kar, a gabaninsu, (mutanen yanzu)
daga wacfansu al'ummomi, (wa-
tfanda suke) su ne mafi karfin
damka daga gare su, sa'an nan
suka yi bincike a cikin kasashe : 'K6
akwai wurin tslra? ,(3) (Babu).
37. Lalle ne a cikin wancan, ak-
wai tunatarwa ga wanda zuciyarsa
ta kasance gare shi, ko kuwa ya jefa
sauraro, alhali kuwa yana halarce
(da hankalinsa).
38. Kuma lalle ne, haklka, Mun
halitta sammai da kasa da abin da
ke a tsakaninsu, a cikin kwanaki
shida, alhali wata 'yar wahala ba ta
shafe Mu ba.
39. Saboda haka, ka yi hakuri a
kan abin da suke fada, kuma ka yi
^t » s <"'<
*p ju> &AjfyJ>ji&££
lUa> ~fA Ji^ bj>J* *-$ii l^===LbbllQ
ot^b*Jfc^}$y&
^ >/,/ <"
<iL; -^^ r~?r^-} ^^yjpy* uPJ^ »
(1) Tsoron Allah a fake, shT ne a bauta masa, ba da riya ba, bayyane da boye duka
cfaya.
(2) K6 kuma ku shiga da sallama.
(3) Sun nemi wurin tsTra, ba su samu ba, saboda haka kafiran yanzu ma ba su iya
samun wurin tsTra, sai dai idan sun koma ga Allah ta hanyar ManzonSa kawai, watau
takawa ga Allah ke nan. Ana kare azabarSa da ibadarSa kamar yadda Yake so.
792
50 - Suratu K
^&%£?-o*
tasblhi (1) game da gode wa Ubangi-
jinka (watau ka yi salla) a gabanin
fitowar rana da gabanin bacewarta.
4(1 Kuma daga dare, sai ka yi
tasblhi a gare Shi da bayan sujada.
41. Kuma ka saurara a ranar da
mai kira ke yin kira daga wuri (2)
makusanci.
42. Ranar da suke sauraron tsa-
wa da gaskiya. Wancan shine yinin
flta (daga kabari).
43. Lalle Mu ne hakikatan, Mu
ne ke rayarwa, kuma Mu ne ke
kashewa, kuma zuwa gare Mu ka-
wai ne makomar take.
44. Ranar da kasa ke tsattsage-
wa daga gare su, suna masu gagga-
wa. Wancan tarawar mutane ne,
mai sauki a gare Mu.
45. Mu ne mafi sani game da
abin da suke facfi, kuma ba za ka
zama mai tilasta su ba. Saboda
haka ka tunatar game da Alku-
r'ani, * ga wanda ke tsoron
kyacewaTa.
i tt
<M\^^j<&' ---*?-
(1) TasbThi game da gode wa Allah a gabanin fitar rana, shi ne sallar^asuba, na
gabanin 6acewarta, shi ne sallar Azahar da La'asar. Daga dare kuwa, shi ne ^allar
Magariba da Issha'i. Bayan sujada, shine salloli na nafila kuma ma'anarsa a nan tasbihi da
tahmldi da kabbarori a bayan salloli farillai talatin da uku kowace, sa'an nan a cika cfari da
addu'ar da aka ruwaito a nan.
(2) Mai kira shine Israfilu a cikin kaho a Baitil Makadis domin a nan kasa ta fi zama
kusa da sama.
(3) Wannan ya nuna ba a wa'azi da ilmin da ba daga Alkur'ani aka fitar da shi ba, sai
fa idan bai sa6a wa abin da ke cikin Alkur'ani ba.
793
51 - Suratudh Dhariyat
&M%&-*\
Tana karantar da gaggawar saukar azabar Allah ga wacfanda
suka ki bin umurninSa ko suka saba wa haninSa.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ina rantsuwa da iskoki masu
shekar abubuwa, shekewa.
2. Sa'an nan da giragizai masu
daukar nauyi (na ruwa).
J. Sa'an nan da jirage masu gu-
dana (a kan ruwa) da sauki.
4. Sa'an nan da mala'iku masu
rabon al'amari (bisa umurnin
Allah).
5. Lalle abin da ake >a muku
alkawari (da zuwansa), hakTka gas-
kiya ne.
6. Kuma lalle^ sakamako (ga
ayyukanku), hakTka, mai aukuwa
ne.
7. Ina rantsuwa da sama
ma'abuciyar hanyoyi (na tafiyar
taurari da sautin rediyo).
8. Lalle ku, hakTka, kuna cikin
magana mai saBa wa juna (game da
Alkur'ani).
9. Ana karkatar da wanda aka
juyar (daga gaskiya).
10. An la'ani masu kiri-facfi.
r^\ - \ \ ■ * -l -\
s ' s
33cJ^J*jd>Jl
794
51 — Suratudh Dhariyat
mum-os
11. Wacfanda suke shagala a ci-
kin zurfin jahilci.
12. Suna tambaya, "Yaushe ne
ranar sakamako za ta auku?"
13. Ranar da suke a kan wuta
ana fitinar su.
14. (A ce musu) "Ku cfancfani
fitinarku, wannan shT ne abin da
kuka kasance kuna neman zuwansa
da gaggawa."
15. Lalle masu takawa suna a
cikin lambunan itace da maremari.
16. Suna masu dibar abin da
Ubangijinsu Ya ba su. Lalle su, sun
kasance masu kyautatawa a gaba-
nin haka (a duniya).
17. Sun kasance a lokaci kacfan
na dare suke yin barci.
18. Kuma a lokutan asuba suna
ta yin istigfari.
19. Kuma a cikin dukiyarsu
akwai hakki ga (matalauci) mai
roko da wanda aka hana wa roko.
20. Kuma a cikin Rasa akwai
ayoyi ga masu yakTni.
21. Kuma a cikin rayukanku
(akwai ayoyi). To, ba za ku dubawa
ba?
22. Kuma a cikin sama arzikinku
(yake fitowa) da abin da ake yi
muku alkawari.
23. To, kuma Ina rantsuwa da
Ubangijin sama da Rasa, lalle ShT
(abin da ake yi muku alkawari),
hakika, gaskiya ne, kamar abin da
kuka zamo kuna karantawa na ma-
gana.
795
51 — Suratudh Dhariyat
<$&M%&-*\
24. Shin, labarin bakin Ibrahim,
wacfanda aka girmama, ya zo
maka?
25. A lokacin da suka shiga gare
shi, sai suka yi sallama; ya ce
"Aminci ya tabbata a gare ku, mu-
tane baki!"
26. Sai ya juya zuwa ga iyalinsa,
sa'an nan ya zo da maraki tutturna.
27. Sai ya kusantar da shi zuwa
gare su, ya ce, "Ba za ku ci ba?"
28. Sai ya ji tsoro daga gare su.
Suka ce, "Kada ka ji tsoro." Kuma
suka yi masa bushara da (haihuwar)
wani yaro mai ilmi.
29. Sai matarsa ta fuskanta cikin
kyallowa, har ta mari fuskarta,
kuma ta ce, "Tsohuwa bakarariya
(za ta haihu)!"
30. Suka ce, "Kamar haka
Ubangijinki Ya facfa. Lalle ShT, ShT
ne Mai hikima, Mai ilmi."
31. (Ibrahim) ya ce, "To, mene
ne babban al'amarinku, ya ku
Manzanni!"
32. Suka ce, "Lalle mu, an aike
mu zuwa ga wacfansu mutane, masu
laifi.
33. "Domin mu saka musu wa-
cfansu duwatsu na wani yumBu
(bom).
34. "Wacfanda aka yi wa alama
daga wajen Ubangijinka, domin
masu Barna."
35. Sa'an nan Muka fitar da
wanda ya kasance a cikinta daga
muminai.
^ f£r->Jf& y *J
^^^/y^i^3^i!jJK
^P cAJfc^ b^>- (i^tW^l
^^i^^^0^l^>^
796
51 — Suratudh Dhariyat
£)&W%&-os
36. Sai dai ba mu samu ba, a
cikinta, face gida guda na Musulmi.
37. Kuma Muka bar wata ay a, a
cikinta, ga wacfanda ke jin tsoron
azaba, mai radadi.
38. Kuma ga Musa, a lokacin da
Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da
wani dallli bayananne.
39. Sai ya juya baya tare da kar-
finsa, kuma ya ce, "Mai sihiri ne ko
kuwa mahaukaci!"
40. Saboda haka Muka kama shi
tare da rundunarsa, sa'an nan
Muka jefa su a cikin teku, alhali
kuwa yana wanda ake zargi.
41. Kuma ga Adawa, a lokacin
da Muka aika iska kekasasshiya a
kansu.
42. Ba ta barin kome da ta je a
kansa, face ta mayar da shi kamar
rududdugaggun kasusuwa.
43. Kuma ga Samudawa, a loka-
cin da aka ce musu, "Ku ji dan dadi
har wani dan lokaci!"
44. Sai suka yi girman kai ga
umurnin Ubangijinsu, saboda haka
tsawa ta kama su, alhali kuwa suna
kallo.
45. Ba su ko samu damar tsaya-
wa ba, kuma ba su kasance masu
neman agaji ba.
46. Da mutanen Nuhu a gabanin
haka, lalle sun kasance wadansu
irin mutane ne fasikai.
47. Kuma sama, mun gina ta da
wani irin karfi, alhali kuwa lalle Mu
ne Masu yalwatawa.
!|Mcfl-«L~J ^Cjt^^J^P l^dbJ^U?
797
51 — Suratudh Dhariyat
®&B$&-o\
48. Kuma Jcasa Mun shimficfa ta,
To, madalla da masu shimfidawa,
Mu.
49. Kuma daga kome Mun halit-
ta nau'i biyu, watakila za ku yi
tunani.
50. Saboda haka ku gudu zuwa
ga Allah, lalle nlmai gargadi kawai
ne a gare ku, mai bayyanannen
gargadi.
57. Kuma kada ku sanya, tare da
Allah, wani abin bautawa na da-
bam, lalle iiT, mai gargadi kawai ne a
gare ku, mai bayyanannen gargadi.
52. Kamar haka dai wani Manzo
bai je wa wadanda ke gabaninsu ba
face sun ce, "Mai sihiri ne ko mah-
aukaci."
53. Shin, suna yi wa juna wa-
siyya da shi ne? A'a, su dai mutane
ne masu girman kai.
54. Sai ka juya daga barinsu,
kuma kai ba abin zargi ba ne.
55. Kuma ka tunatar, domin tu-
natarwa tana amfanin muminai.
56. Kuma Ban halitta aljannu da
mutane ba sai domin su bauta Mini.
57. Ba Ni nufin (samun) wani
arziki daga gare su, Ba Ni nufin su
(yi Mini hidimar) ciyar da Ni. (1)
58. Lalle Allah Shine Mai arzut-
tawa, Mai ikon yi, Mai cikakken
Jcarfi.
59. To, lalle wadanda suka yi
zalunci suna da wasaki (na cfiban
zunubi) kamar wasakin abokansu,
<<£$> » *& •' t 9 "^^ ">\ '*i 'uk"*-'
fey o^yj»\*M
l^J^^y^^tj'^y^ cyU o£
(1) Ba Ni nufin su samo Mini abinci, kuma ba Ni nufin su dafa Mini abinci.
798
52 — Suratucf T)ur
j&m-«
saboda haka kada su yi Mini gag-
gawa.
60. Saboda haka bone ya tabba-
ta ga wacfanda suka kafirta, daga ra-
nar su wadda aka yi musu alkawari.
Tana karantar da yadda ake rumatar da abokin husuma da
hujjoji da kuma jan hankalinsa zuwa ga gaskiya.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ina rantsuwa da T)ur (Dutsen
Musa).
2. Da wani littafl rubutacce.
3. A cikin wata takardar fata
shimficfacfcfa.
4. Da Gidan da aka rayar da shi
(da ibada).
5. Da rufin nan da aka daukaka.
6. Da tekun nan da aka cika (da
ruwa).
J. Lalle azabar Ubangijinka, ha-
£i£a, mai aukuwa ce.
8. Ba ta da mai tunkudewa.
9. Ranar da sama ke yin motsi
tana kai kawo.
10. Kuma duwatsu na tafiya
suna shudewa.
9 1^ Jl>JI^a-^j
799
52 - Suratucf T>ur
m$&-<*
11. To, bone ya tabbata a ranar
nan ga masu karyatawa.
12. Wacfanda suke a cikin ku-
duddufi suna wasa.
13. Ranar da za a tunkuda su zu-
wa wutar Jahannama, tunkudawa.
14. (A ce musu) "Wannan ita ce
wutar da kuka kasance kuna karya-
tawa game da ita.
75. "To, shin, wannan sihiri ne
ko kuwa ku ne ba ku gani?
16. "Ku shige ta. To, ku yi haku-
ri ko kuma kada ku yi hakuri, dai-
dai ne a kanku, kawai ana yi muku
sakamakon abin da kuka kasance
kuna aikatawa."
17. Lalle masu takawa suna a
cikin gidajen Aljanna da wata
ni'ima.
18. Suna masu jin dacfi da abin
da Ubangijinsu Ya ba su, kuma
Ubangijinsu Ya tsare musu azabar
JahTm.
19. (A ce musu) "Ku ci, ku sha,
da ni'ima, domin abin da kuka
kasance kuna aikatawa."
20. Suna kishingicfe a kan kara-
gu wadanda ke cikin sahu, kuma
Muka aurar da su wadansu mata
masu farin idanu, masu girmansu.
21. Kuma wadanda suka yi ima-
ni kuma zuriyarsu (1) suka bi su ga
imanin, Mun riskar da zuriyarsu da
j^r ^ >i ^?> *r . ~* ' It
Pp oj!&[^j^^\^\3\*^
J lre*
l£jo
(v& ^iv^JOySllIl %\
( 1 ) Wannan aya tana nuna yadda wani ke ceton wani saboda kusanci domin a kara
daukaka mai ceton. Sharadin ceton, shT ne wanda ake ceton yana da nasa Imanin. Wanda
jinginarsa ta halaka babu mai cetonsa. Zuriya ta hada uwaye da almajiran malami salihi.
Suna shiga a cikin cetonsa.
800
52 - Suratud" T>ur
J»&-<*
su, alhali kuwa ba da Mun rage
musu kome ba daga aikinsu, kowa-
ne mutum jingina ne ga abin da ya
sana'anta.
22. Kuma Muka yalwata musu
'ya'yan itace da nama irin wanda
suke marmari.
23. Suna mlka wa junansu a ci-
kinta hinjalan giya, wadda babu
yasassar magana a cikinta, kuma
babu jin nauyin zunubi.
24. Kuma wadansu samari na
gewayawa a kansu, kamar dai su
lu'ulu'u ne wanda ke kulle.
25. Wadansunsu suka fuskanta
zuwa ga wacfansu, suna tambayar
juna.
26. Suka ce, "Lalle mu, mun
kasance a gabanin wannan (a du-
niya) a cikin iyalanmu muna jin
tsoro.
27. "To, Allah Ya yi mana kyau-
tar falala, kuma Ya tsare mana
azabar iskar zafi.
28. "Lalle mu, mun kasance, a
gabanin haka, muna kiran Sa. Lalle
Shi, Shi ne Mai kyautatawa, Mai
rahama."
29. To, ka tunatar, kai fa, sabo-
da ni'imar Ubangijinka, ba boka
kake ba, kuma ba mahaukaci ba.
30. Shin, za su ce, "Mawaki ne,
muna jiran maslfun mutuwa game
da shi"?
31. Kace, "Kuyijira, domin m
ma lalle ina a cikin masu jira tare
da ku."
fp 0^03)3!
fp j)juJ^ QVzi j5 &==> &\Q 6
pp ^Jj :.l\^\ J^bjjj iLjc 4S1
rA:>A\-<r"
©^»>4
b£L><ii>j
4 iT^ > ' » -^ ^^
^jjh fro ctbj c.« «^ ^ ^ —j ^--^ Jte
801
52 - Suratucf T>ur
m\%&-*
32. Shin, hankulansu ne ke
umarnin su da wannan, ko kuwa su
wasu mutane ne masu ketare haddi ?
33. Shin, cewa suke yi, "Shi ne ke
kaga fadarsa"? A'a ba su dai yi
Tmani ba.
34. Sai su zo da wani labari mai
misalinsa, idan sun kasance su masu
gaskiya ne.
35. Shin, an halitta su ne ba daga
kome ba, ko kuwa su ne masu yin
halitta?
36. Shin, sun halitta sammai da
kasa ne? A'a ba su dai yi Tmanin
yaklni ba.
37. Shin, taskokin Ubangijinka,
suna a wurinsu ne? Ko kuwa su ne
masu rinjaya?
38. Shin, suna da wani tsani ne
wanda suke (hawa suna) sauraron
(labarin sama) a cikinsa? Sai mai
sauraronsu ya zo da wani dalTli
bayyananne.
39. Shin, Yana (1) da'ya'ya mata
ne kuma ku, kuna da cfiya maza ne?
40. Shin, kana tambayar su wata
ijara ne, saboda haka suka zama
masu jin nauyin biyan tarar?
41. Shin, a wurinsu akwai ilmin
gaibi, saboda haka suna rubutawa?
42. Shin, suna nufin wani kaidi
ne? To, wadanda suka kafirta su ne
wadanda ake yi wa kaidi.
^>^i
in <<. \\<LZ\"-A . >i :•: : a\\*
gj b^y^&ji\jcJ^\\j^'^
A *. JLh» * Puis A& c ^ *-*"* " j^*** p* f '
™j c*J/iL[i>
$£^\&U^**$
(1) Wadansu Larabawa suna kiran mala'iku 'ya'yan Allah mata, suna kuma bauta
musu domin su cece su daga Allah, suna yin gumaka da sunansu.
802
52 - SuratucfDur
mt&-«
43. Shin, suna da wani abin bau-
tawa ne wanda ba Allah ba? Tsarki
ya tabbata ga Allah daga abin da
suke yi na shirki!
44. Kuma idan sun ga wani 6a6-
6ake daga sama yana faduwa, sai su
ce wani girgije ne, mai hauhawar
juna.
45. To, ka bar su, sai sun hacfu da
yinin nan da za a sumar da su a
cikinsa.
46. Ranar da kaidinsu ba ya wa-
datar masu da kome, kuma ba a
taimakon su.
47. Kuma lalle wadannan da
suka yi zaluncin, suna da azaba (a
nan duniya) banda waccan, kuma
mafi yawansu ba su sani ba.
48. Sai ka yi hakuri da hukuncin
Ubangijinka, lalle kai fa kana ida-
nunMu, kuma ka_ tsarkake (1)
Ubangijinka da (tasblhi) game da
gode Masa a lokacin da kake tashi
tsaye (domin salla ko wani abu).
49. Kuma daga dare, sai ka tsar-
kake Shi (da tasblhin) da lokacin
juyawar taurari.
\^> -* -"- > S> > " >
(1) Ma'anar ita ce tsarkakewa ko tasblhi, 'tsare salloli, farillai, ana cewa' facfin
"Subhanal Lahi wal Hamdu Lillahi" a bayan kowane mazauni, domin ya zama kaffarar
wannan mazaunin.
803
53 — Suratun Najm
&^ljg£-«r
Tana tsarkake Annabi da Manzancinsa daga kowane aibi.
Tana tabbatar da^shi daga Allah, sa'an nan tana 6ata dukan abin da
ba shi ba na addinai da aFadu.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ina rantsuwa da tauraron, a
lokacin da ya faku.
2. Ma'abucinku bai Bata ba,
kuma bai ketare haddi ba.
3. Kuma ba ya yin magana daga
son zuciyarsa.
4. (Maganarsa) ba ta zamo ba,
face wahayi ne da ake aikowa.
5. (Mala'ika) mai tsananin kar-
fi (1) ya sanar da shi.
6. Ma'abucin karfi da kwarjini,
sa'an nan ya daidaita.
7. Alhali kuwa yana a sararin
sama mafi daukaka.
8. Sa'an nan ya kusanta, kuma
ya matsa zurowa.
9. Har ya kasance gwargwadon
zira'i biyu, ko kuma abin da ya fi
kusa.
yy ' ^ 9 .
(1 ) Wahayin da ke zuwa ga Annabi babu 6ata a cikinsa domin Jibrilu mai kawo shi ga
Annabi, Mala'ika ne mai Icarfi kwarai, wani Shaidani ba ya iya taron sa domin ya musanya
wahayin, kuma Annabi ya san shi sosai, kuma idan ya kawo wahayin, sai ya sauko kusa
£warai da Annabi, sa'an nan shi kuma Annabi ba rikitacce ba ne, yana cikin hankalinsa.
804
53 — Suratun Najm
m$&-or
10. Sa'an nan ya yi wahayi zuwa
ga bawan Allah (Muhammadu) da
abin da ya facfa (masa).
11. Zuciyar(Annabi)batakarya-
ta abin da ya gani ba.
12. Shin, za ku yi masa musu a
kan abin da yake gani?
13. Kuma lalle ya gan shi, hakl-
katan, a wani lokacin saukarsa (1) .
14. A wurin da magaryar tuke-
wa take.
75. A inda taken, nan Aljannar
makoma take.
16. Lokacin da abin da yake rufe
magaryar tukewa ya rufe ta.
17. Ganinsa (2) bai karkata ba,
kuma bai ketare haddi ba.
18. Lalle, tabbas, (Annabinku)
ya ga wacfanda suka fi girma (3)
daga ayoyin Ubangijinsa.
19. Shin, kun ga Lata da
Uzza? (4)
20. Da (wani gunki wai shi) Ma-
nata, na ukunsu?
21. Ashe, ku ne da da namiji, Shi
(Allah) kuma da diya mace?
22. Wannan fa ya zama rabo
nakasasshe.
***** ' AT *' ft J* *\<
(1) Lamirin Mala'ika Jibrila ne.
(2) Lamirin Annabi Muhammadu ne.
(3) Watau dai Allcur'ani ya zo daga Allah ta hanya mafi aminci har ya sadu da
mutane domin su yi aiki da abin da ke cikinsa.
(4) Watau kun bar Alkur'ani kun koma wa surkullen da kuke hadawa game da
gumaka su Lata da Uzza da Manata. Kuna cewa su wakflan Mala'ikun da kuke bauta wa
ne kuma su 'ya'yan Allah mata ne. Suna ceton ku daga Allah.
805
53 — Suratun Najm
&A
-or
23. Wacfannan ba kome ba ne
face sunaye, wacfanda kuka ambace
su da su, ku da uwayenku. Allah bai
saukar da wani dalili game da su ba.
(Kafirai) ba su biyar kome face zato
da abin da rayukansu ke so, alhali
kuwa shiriyar, (1) ta daga wajen
Ubangijinsu, ta je musu (sai suka
bar ta suka koma wa zaton).
24. Ko (an facfi cewa) mutum zai
sami abin da yake guri?
25. To, Lahira da duniya na Al-
lah kawai ne (wanda ya neme su
daga wani, ya yi kuskure).
26. Akwai mala'iku da yawa a
cikin sammai, cetonsu ba ya wada-
tar da kome face bayan Allah Ya yi
izni (da shi) ga wanda Yake so,
kuma Yake yarda.
27. Lalle wadannan da ba su yin
Tmani da Lahira, hakika, suna kiran
mala'iku da sunan mace.
28. Kuma ba su da wani ilmi
game da shi, ba su bin kome face
zato, alhali kuwa lalle zato ba ya
amfanar da kome daga gaskiya.
29. Saboda haka sai ka kau da
kai daga wanda ya juya baya daga
ambatonMu, kuma bai yi nufin
kome ba face rayuwar kusa (du-
niya).
30. Wannan ita ce iyakar abin da
suke iya kai gare shi na ilmi. Lalle
Ubangijinka Shine Mafi sanin wan-
da ya Bace daga hanyarSa, kuma
Shi ne Mafi sani ga wanda ya nemi
shiriya.
"" ' " *■
^ 4"\' ' '• *»*t
^&%&%&&U$k
"i *y
MferM&t&Z
(jiJGjtf
(1) Watau Alkur'ani wanda Mala'ika JibrTla ya zo wa Annabi da shi. Sun bar shi sun
koma wa tatsuniyoyi da gurace-gurace.
806
53 — Suratun Najm
^4 -or
31. Kuma abin da ke cikin sam-
mai da abin da yake a cikin kasa na
Allah kawai ne, domin Ya saka wa
wadanda suka munana da abin da
suka aikata, kuma Ya saka wa wa-
danda suka kyautata da sakama-
kon da ya fi kyau.
32. Wadanda ke nisantar ma-
nyan zunubai da abubuwan alfas-
ha, face kananan laifuffuka, lalle
Ubangijinka Mai yalwatattar gafa-
ra ne, ShT ne Ya fi sani ga abin da ke
gare ku a lokacin da Ya kaga halit-
tarku daga kasa, kuma a lokacin da
kuke tayuna a cikin cikannan
uwayenku. Saboda haka, kada ku
tsarkake (1) kanku, ShTne Mafi sani
ga wanda ya yi takawa.
33. Shin, ka ga wannan da ya
juya baya?
34. Ya yi kyauta kadan, kuma
ya yi rowa?
35. Shin, akwai ilmin gaibi a wu-
rinsa, saboda haka yana ganin
gaibin?
36. Ko kuwa ba a ba shi labari ba
ga abin da yake a cikin Littafan
Musa?
37. Da Ibrahim wanda ya cika
alkawari?
38. Cewa wani rai mai kayan
laifi ba ya cfaukar kayan laifin wani.
39. Kuma mutum ba shi da
kome face abin da ya aikata.
40. Kuma lalle aikinsa za a gan
shi.
t&y
A>*^<\l*j\ZAil5l\
< s <if
m&j<£$\^s\j
EJ C££ c3>-^ » *->*-** o]j
(1) Wanda yake mutumin kirki, Allah Ya san shi. Kada ku dinga tsarkake kanku da
bakunanku domin neman girma, ko domin neman wani abu dabam.
807
53 — Suratun Najm
bM\%& - or
41. Sa'an nan a saka masa da
sakamako wanda yake mafi cikar
ma'auni?
42. Kuma lalle makomar zuwa
Ubangijinka kawai take?
43. Kuma lalle Shi, ShT ne Ya
sanya dariya, kuma Ya sanya kuka.
44. Kuma lalle ShT, ShT ne Ya
kashe, kuma Ya rayar.
45. Kuma lalle ShT neYayihalit-
ta nau'i-nau'i, namiji da mace.
46. Daga wani cfigon ruwa guda
a lokacin da ake jefa shi a cikin
mahaifa.
47. Kuma a kansa ne kaga halit-
ta ta biyu take.
48. Kuma lalle ShT, ShT ne Ya
arzuta, kuma Ya wadatar.
49. Kuma lalle Shi, Shi ne
Ubangijin Shi'ira (1) .
50. Kuma lalle ShT, Shi ne Ya
halaka Adawa na farko.
51. Da Sumudawa, sa'an nan bai
rage su ba.
52. Da mutanen Nuhu a gabanin
haka, lalle su, sun kasance mafi
zalunci kuma mafi girman kai.
53. Da wacfanda aka birkice (2)
kasarsu, Ya kayar da su.
54. Sa'an nan abin da ya rufe su,
ya rufe su.
fey L>-ijOuiyb»^->'j
*9<£<3kJ<uiw
(1) Sunan wasu taurari biyu ne suna fita a bayan taurarin Jauza'a suna tafiya daga
kudu zuwa arewa karkace. Kabilar Larabawa ta Khuza'a na bauta musu da umurnin Abu
Kabshah, (faya daga^cikin kakannin Annabi na wajen uwa domin haka ne FCuraishawa ke
ce wa Annabi Ibn ab! Kabshah, wanda ya kaga sabon addinln da ya sa6a wa na ubanninsa.
(2) Mutanen Ludu da aka birkice kasarsu da su.
808
53 — Suratun Najm
-or
55. To, da wace daga ni'imomin
Ubangijinka kake (1) yin shakka?
56. Wannan (Muhammadu) mai
gargatfi ne kamar irin masu gar-
gacfi na farko.
57. Makusanciya (2) fa, ta yi kusa.
58. Babu wani rai, banda Allah,
mai iya bayani gare ta.
59. Shin, kuma daga wannan (3)
labari kuke mamaki?
60. Kuma kuna yin dariya,
kuma ba ku yin kuka?
61. Alhali kuna masu wasa?
62. To, ku yi tawali , u (4) ga Al-
lah, kuma ku bauta (Masa).
*&>*'
Tana karantar da cewa wanda ya nemi wata mu'ujiza, to, ita za
ta zama sababin halakarsa.
j* -* . * v -*
Z>a .si/ftim Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
/. Sa'a ta yi kusa, kuma wata (5)
ya tsage.
(1) Kamar abokin magana ko mai karatu.
(2) Makusanciya, ita ce Kiyama.
(3) Alkur'ani.
(4) Ana yin sujadar karatu a nan, amma ba ta a cikin sujudai na tTlas.
(5) Kuraishawa suka nemi Annabi ya yi addifa domin wata ya tsage wani balgace
nasa ya facto a kasa ; ya yi addu'ar, wata ya tsage, wani abu daga gare shi ya facto kamar
yadda suka nema.
809
54 — Suratul FCamar
bm\m~*
2. Kuma idan sun ga wata aya,
sai su juya baya su ce, "Sihiri ne
mai dogewa!"
3. Kuma suka karyata, kuma
suka bi son zuciyarsu, alhali kuwa
kowane al'amari (wanda suke son
su ture daga Annabi) an tabbatar da
shi.
4. Kuma lalle, abin da yake ak-
wai tsawatarwa a cikinsa na labarai
ya zo musu.
5. Hikima cikakka! Sai dai abu-
buwan gargacfi ba su amfani.
6. Saboda haka, ka bar su! Ra-
nar da mai kiran zai yi kira zuwa ga
wani abu abin kyama.
7. Kaskantattu ga idanunsu za
su fito daga kaburburansu, kamar
dai su fari ne wadanda suka watse.
8. Suna gaggawar tafiya zuwa ga
mai kiran, kafirai na cewa, "Wan-
nan yini ne mai wuya!"
9. Mutanen Nuhu sun karyata, a
gabaninsu, sai suka karyata Ba-
wanMu, kuma suka ce, "Shi ma-
haukaci ne." Kuma aka tsawace
shi.
10. Saboda haka ya kira Ubangi-
jinsa (ya ce), "Lalle nl, an rinjaye ni,
sai Ka yi taimako."
77. Sai Muka bude kofofin sama
da ruwa mai zuba.
72. Kuma Muka BuBBugar da
kasa ta zama idanun ruwa, dada
ruwa ya harfu a kan wani umurni da
aka riga aka kaddara shi.
13. Kuma Muka dauke Nuhu a
kan (jirgi) na alluna da kusoshi.
sj* s -*»* ? \ >."• > *>ts K s
9 \\-'\ * 9 >Z'\'U" v'
e^Vto-^^l^oSlJ
£ / ^ T >
r *y±
±Js&
S
E|^^ U ^y^A <^\ y*b; l^-Xi
810
54 — Suratul Kamar
um\m-K
14. Tana gudana, a cikin kiyaye-
warMu, domin sakamako ga wan-
da aka yi wa kafircin.
15. Kuma lalle Mun bar ta ta
zama aya. To, shin, akwai mai tuna-
ni?
16. To, yaya azabaTa take da
gargacfiNa?
17. Kuma lalle ne, hakika, Mun
saukake Alkur'ani, domin tunawa.
To, shin, akwai mai tunawa?
18. Adawa sun karyata, to, yaya
azabaTa take, da gargacfiNa?
19. Lalle Mu, Mun aika da iska
mai tsananin sauti a kansu, a cikin
wani yinin nahisa mai dogewa.
20. Tana fizgar mutane kamar
dai su kututturan dablno
tumbukakku ne.
21. To, yaya azabaTa take da
gargacfiNa?
22. Kuma lalle ne, hakika Mun
saukake Alkur'ani, domin tunawa.
To, shin, akwai mai tunawa?
23. Samudawa sun karyata game
da gargacfin.
24. Sai suka ce, "Wani mutuin
daga cikinmu, shi kacfai, wai mu bl
shi! Lalle mu, a lokacin, hakika,
mun shiga wata 6ata da hauka.
25. "Shin, an jefa masa Manzan-
cin ne, a tsakaninmu? A'a shi dai
gawurtaccen makaryaci ne mai gir-
man kai!"
26. Za su sani a gobe, wane ne
gawurtaccen mai karyar, mai gir-
man kan?
>>/ ss s 'S '">
^^ > > ' 1 f '
811
54 — Suratul Kamar
ymm-K
27. Lalle Mu, masu aikawa da
rakumar (1) ne, ta zame musu fitina,
sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi
hakuri.
28. Kuma ka ba su labari, cewa
ruwa rababbe ne a tsakaninsu (da
rakumar), kowane sha, mai shi
yana halartar sa.
29. Sai suka kira abokinsu,
sai ya karBa, sa'an nan ya soke ta.
30. To, yaya azabaTa take da
gargacfiNa?
31. Lalle Mu, Mun aika tsawa
guda a kansu, sai suka kasance
kamar yayin mai shinge.
32. Kuma lalle ne, hakika, Mun
saukake Alkur'ani, domin tunawa.
To, shin, akwai mai tunawa?
33. Mutanen Ludu sun karyata,
game da gargadi.
34. Lalle Mun aika iskar tsaku-
wa a kansu, face mabiyan Ludu,
Mun tsirar da su a lokacin asuba.
35. Saboda wata ni'ima ta daga
gare Mu. Kamar haka Muke saka
wa wanda ya gode.
36. Kuma lalle, hakika, ya yi
musu gargadin damkarMu, sai
suka yi musu game da gargadin.
37. Kuma lalle, hakika, su, sun
neme shi ta wajen bakinsa, sai
Muka shafe idanunsu.'To, ku dan-
dani azabaTa da gargacfiNa."
IJpjU^^l^jkl^J 4^^l^[yL^lj>!
^j •S&rt-irtf.WK
Jr^t "Z ". < .""-T 9> ' \S\ »'S'.
^t **\f l*'l^ < | / ^ x \'' >''
jXib lL?Ul>3L\L*uJa)^jjG)jLa3j
f^ V' i<"
(1) Mutanen Saleh sun nemi mu'ujiza da rakuma, a fitar da ita daga dutse, sai aka
fitar da ita, kuma aka raba ruwan sha a tsakaninsu da ita.
812
54 — Suratul Kamar
£^)Ji&-<*
38. Kuma lalle, hakika, wata
azaba matabbaciya ta waye musu
gari da yaki, tun da safe.
39. To, ku dandani azabaTa da
gargacfiNa.
40. Kuma lalle ne, hakika, Mun
saukake Alkur'ani domin tunawa.
To, shin, akwai mai tunawa?
41. Kuma lalle, hakika, gargadin
ya je wa mabiyan Fir'auna.
42. Sun karyata game da ayoyin-
Mu, dukansu, sai Muka kama su,
irin kamun Mabuwayi, MaiTkon yi.
43. Shin, kafiranku ne mafi alhe-
ri daga wadancan, ko kuwa kuna da
wata bara'a a cikin littattafai?
44. K6 za su ce, "Mu duka masu
hada karfi ne domin cin nasara?"
45. Za a karya (1) taron, kuma su
juya baya domin gudu.
46. A'a, Sa'a ita ce lokacin
wa'adinsu, kuma Sa'ar ta fi tsana-
nin maslfa, kuma ta fi daci.
47. Lalle ne masu laifi suna a
cikin Bata da hauka.
48. Ranar da za a ja su a cikin
wuta a kan fuskokinsu. "Ku dan-
dani shafar wutar Sakar."
49. Lalle Mu, kowane irin abu
Mun halitta shi a kan tsari.
50. Kuma umurninMu bai zamo
ba face da kalma daya, kamar wal-
kawar ido.
|3| yJC^uJ* ^\^^^^r^>xl^> JjUJ
EJ j'^j o)^> \J>jj&
%^yi^ L y^
(1) Bushara ce ga Annabi, cewa zai yi yaki da Kuraishi kuma zai rinjaye su. Sa'an nan
yakin ya auku a Badar.
813
55 — Suratur Rahman
&&ym-oo
51. Kuma lalle ne, haklka, Mun
halaka irin gayyarku. To, shin, ak-
wai mai tunani?
52. Kuma kowane abu, da suka
aikata shi, yana a cikin littattafai.
53. Kuma dukan karami da bab-
ba, rubutacce ne.
54. Lalle masu takawa suna a
cikin gidajen Aljanna da koguna.
55. A cikin mazaunin gaskiya,
wurin Mai ikon yi, Mai iya zartas-
wa.
J43 ?&CjA U^JlaI aSl
&\ >V -M "- •* v^
Tana karantar da ni'imomin Allah nau'i-nau'i ga mutane da
aljannu a duniya da Lahira, kuma tana kwacfaitar da su ga gode wa
Allah Mai ni'imtar da su.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. (Allah) Mai rahama.
2. Ya sanar da Alkur'ani.
3. Ya halitta mutum.
4. Ya sanar da shi bayani
(magana).
5. Rana da wata a kan lissafi
suke.
o^*j-ii^jii
33oOUjb
[Jp cXJ^J^jj\) ^ I *Jl
814
55 — Suratur Rahman
£f^JiS£ - °°
6. Kuma tsirrai masu yacfo da
itace suna tawalu'i.
7. Kuma sama Ya cfaukaka ta,
kuma Ya aza sikeli.
8. Domin kada ku karkatar da
sikelin.
9. Kuma ku daidaita awo da
adalci, kuma kada ku rage sikelin.
10. Kuma kasa Ya aza ta domin
talikai.
11. A cikinta akwai 'ya'yan ita-
cen marmari da dabino mai kwasfa.
12. Da kwaya mai soshiya da
kamshi.
13. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku ( 1 } kuke
karyatawa?
14. Ya halitta mutum daga
kekasasshen yum6u kamar kasko.
75. Kuma ya halitta aljani daga
bira daga wuta.
16. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
17. Ubangijin mafita biyu na
rana, kuma Ubangijin mafada biyu
na rana.
18. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
19. Ya garwaya teku biyu (ru-
wan dadi da na zartsi) suna
hadiiwa.
Cp &*i lob jX^L, i^il^
tbe^^iiLi
£$ Qj^CvjcAs^ ^o
M ^C&(£j^£^
(1) Asalin lamiri "ku" yana nuni ne ga nau'i biyu, watau mutane da aljannu, sai dai
babu lamirin abu biyu kawai a cikin Hausa, sai na jama 'a. Janfi a luggar Hausa ya fara
daga biyu.
815
55 — Suratur Rahman
jliPI3£ - oo
20. A tsakaninsu akwai shama-
ki, ba za su ketare haddi ba.
21. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
22. Lu'ulu'u da murjani na fita
daga gare su.
23. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
24. Kuma Yana da manyan jira-
ge, wadanda ake kagawa a cikin
teku kamar manyan duwatsu.
25. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
26. Dukan wanda ke kanta (1)
mai karewa ne.
27. Kuma abin yardar Ubangi-
jinka^Mai girman Jalala da karim-
ci, shT ne yake wanzuwa.
28. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
29. Wanda ke a cikin sammai da
kasa yana rokon Sa (Allah), a kul-
lum Allah na a cikin wani sha'ani.
30. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
31. Za Mu dauki lokaci saboda
ku, ya ku (2) masu nauyin halitta
biyu!
EJ c) LjJj V r-j^i L^Jj
^oV&(&j £tf*!s\j
|p o^l ^\^ £yL~-
(1) Yana nufin Rasa.
(2) Mutane da aljannu.
816
55 — Suratur Rahman
&$)$&- °o
32. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
33. Yajama'ar aljannuda muta-
ne! Idan kuna iya zarcewa daga
sasannin sammai da kasa, to, ku
zarce. Ba zajcu iya zarcewa ba face
da wani dalili.
34. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke kar-
yatawa?
35. Ana sako wani harshe daga
wata wuta a kanku, da narkak-
kiyar tagulla. To, ba za ku nemi
taimako ba?
36. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa.
37. Sa'an nan idan sama ta tsage
kuma ta zama ja kamar jar fata.
38. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
39. To, a ran nan, ba za a tam-
bayi wani mutum laifinsa ba, kuma
haka aljani.
40. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
41. Za a iya sanin masu laifi da
alamarsu, saboda haka sai a kama
kwarkadarsu da sawayensu.
42. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
43. Wannan Jahannama ce wad-
da masu laifi ke karyatawa game da
ita.
S oC5^l^===uS^i^U
L-p£3U^L3
817
55 — Suratur Rahman
G$)£& - oo
44. Suna kewaya a tsakaninta da
ruwan cfimi mai tsananin tafasa.
45. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
46. Kuma wanda ya ji tsoron
tsayawa a gaba ga Ubangijinsa
yana da Aljanna biyu.
47. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
48. Masu rassan itace.
49. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
50. A cikinsu akwai maremari
biyu suna gudana.
51. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
52. A cikinsu akwai nau'i biyu
daga kowane 'ya'yan itacen mar-
mari.
53. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
54. Suna gincire a kan wadansu
shimfidu, cikinsu tufafin alharini
mai kauri ne, kuma nunannun
'ya'yan itacen Aljannar biyu kusa-
kusa suke.
55. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
56. A cikinsu akwai mata masu
takaita ganinsu, wani mutum, ga-
*s *s>s's
G^^", , i '}'T\'" ** <'
SoC^L^J^C^U
* k f > ^ < i
J^Zi ^l&fLhjl <y^ ^Ir^lyt?
818
55 — Suratur Rahman
£PJi3£ - oo
banin mazajensu, bai cfebe budur-
cinsu ba kuma haka wani aljani.
57. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
58. Kamar dai su yakutu ne da
murjani.
59. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
60. Shin, k^autatawa na da wani
sakamako? (A 'aha) Face kyauta-
tawa.
61. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
62. Kuma baicinsu akwai wa-
cfansu gidajen Aljanna biyu.
63. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
64. Masu duhun inuwa.
65. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
66. A cikinsu, akwai maremari
biyu masu kwararar ruwa.
67. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
68. A cikinsu akwai 'ya'yan ita-
cen marmari da dabino da rum-
mani.
69. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
&&tfj
j;^fC^U
ra oV^^l^vJ^/ C&U
fry o^J^L^v^^U^li
819
55 — Stiratur Rahman
^sat&v*.
-oc
70. A cikinsu, akwai wasu mata
masu kyaun halaye, masu kyaun
halitta.
71. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
72. Masu farin idanu da bakinsu
watfanda aka tsare a cikin haimomi.
73. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
74. Wani mutum, gabanin ma-
zajensu, bai debe budurcinsu ba,
kuma haka wani aljani.
75. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
76. Suna gincire a kan wasu ma-
tasai masu koren launi da katTfun
Abkara kyawawa.
77. To, saboda wane daga
ni'imomin Ubangijinku, kuke
karyatawa?
78. Sunan Ubangijinka, Mai gir-
man Jalala da Karimci, ya tsarkaka.
Muv^L^S t$ '*& V
' '*' ' s*<>*
^y^^^^y^^V-A^jp*^^
820
56 - Suratul Wa£i 4 a
$mm-<n
Tana karantar da kasuwar mutane uku, kowane kashi da
hanyarsa a rayuwarsa da mutuwarsa.
*)WA
Da sunan Allah, Mai raharna, Mai jin kai.
1. Idan mai aukuwa ta auku.
2. Babu wani (rai) mai karyata-
wa ga aukuwarta.
3. (Ita) mai kaskantawa ce, mai
daukakawa.
4. Idan aka girgiza kasa girgiz-
awa.
J. Kuma aka nike duwatsu,
nikewa.
6. Sai suka kasance kura da ake
watsarwa.
7. Kuma kun kasance nau'i uku.
8. Watau mazowa dama. (1)
Mene ne mazowa dama?
9. Da mazowa hagu. Mene ne
mazowa hagu?
10. Da wadanda suka tsere. Su
wadanda suka tseren nan,
//. Wadancan, su ne wadanda
aka kusantar.
12. A cikin Aljannar ni'ima.
'*' \\' Jt Z>'
amjl^jl
UJ uOiUbOulSsS
(1) Mazowa dama ko masu albarka wadanda za a bai wa takardunsu da dama.
Mazowa hagu ko masu shu'umci wadanda za a bai wa takardunsu da hagu.
821
56 - Suratul Wa£i'a
mmm-n
13. Jama'a ne daga mutanen
farko. (1)
14. Da kacfan daga mutanen
icarshe.
15. (Suna) a kan wasu gadaje
saicaicicu.
16. Suna gincire a kansu, suna
masu kallon juna.
17. Wasu yara samari na dindin-
din gewaya a kansu.
18. Da wasu kofuna da shantula
da hinjalai daga (giya) mai 6u66uga.
19. Ba a sanya musu ciwon jiri
saboda ita, kuma ba su buguwa.
20. Da wasu 'ya'yan itacen mar-
mari daga irin wacfanda suke za6e.
21. Da naman tsuntsaye daga
wanda suke ganin sha'awa.
22. Da wasu mata masu fararen
idanu da girmansu.
23. Kamar misalan lu'ulu'u wan-
da aka 66ye.
24. A kan sakamako, domin
abin da suka kasance suna aika-
tawa.
25. Ba su jin wata yasassar ma-
gana a cikinta, kuma ba su jin sun
yi laifi.
26. Sai dai wata magana (mai
dacfi): Salamun, salamun.
27. Da mazowa dama. Mene ne
mazowa dama?
ffa--: > »'* >> $'
^*S&&&j&
£&%ty\%£Z$
(1) Jama'a daga mutanen farko, su ne Annabawan farko da kacfan daga cikin
mutanen icarshe, shi ne Annabi Muhammadu, sallallahu alaihi wa sallama. Ba a shiga cikin
wannan kashi da aiki sai dai da zabin Allah. Kuma an rufe £6farsa. Babu sauran wani
annabi wanda zai zo da wani addini sabo a bayan Annabi Muhammadu, tsTra da amincin
Allah su tabbata a gare shi.
822
56 — Suratul Wa£i'a
mz&\m-n
28. (Suna) a cikin itacen maga-
rya maras kaya.
29. Da wata ayaba mai yawan
'ya'ya.
30. Da wata inuwa mlkakkiya.
31. Da wani ruwa mai gudana.
32. Da wasu 'ya'yan itacen mar-
mari masu yawa.
33. Ba su yankewa kuma ba a
hana su.
34. Da wasu shimficfu
macfaukaka.
35. Lalle Mix, Mun kaga halit-
tarsu kagawa.
36. Sa'an nan Muka sanya su
budurwai.
37. Masu son mazansu, a cikin
tsara cfaya.
38. Ga mazowa dama.
39. Wata kungiya ce daga muta-
nen farko.
40. Da wata kungiya daga muta-
nen karshe.
41. Mazowa hagu, Mene ne ma-
zowa hagu?
42. Suna a cikin wata iskar zafi
da wani ruwan zafi.
43. Da wata inuwa ta hayaki
mai baki.
44. Ba mai sanyi ba, kuma ba
mai wata ni'ima ba.
45. Lalle su, sun kasance a gaba-
nin wannan wacfanda aka jiyar dacQ.
46. Kuma sun kasance suna do-
gewa a kan mummunan zunubi mai
girma.
®G$S*
fa- . <t\-<»A*'
C|l ^Zj*& £&'S* ly^r i
823
56 - Suratul Waici'a
gi^li^-*
47. Kuma sun kasance suna
cewa, "Shin, idan mun mutu kuma
muka kasance tur6aya da kasu-
suwa, shin, lalle mu, wacfanda za a
koma rayarwa ne haklkatan?
48. "Shin, kuma da ubanninmu
na farko?"
49. Ka ce, "Lalle mutanen farko
da na karshe.
50. "Tabbas, wacfanda ake tara-
wa ne a cikin wani yini sananne.
51. "Sa'an nan lalle ku, ya ku
6atattu, masu karyatawa!
52. "Lalle masu cT ne daga wata
itaciya ta zakkum (danyen wuta).
53. "Har za ku zama masu cika
cikunna daga gare ta.
54. "Sa'an nan kuma masu sha
ne, a kan wannan abin cin, daga
ruwan zafi.
55. "Ku zama masu sha irin shan
rakuma masu kishirwa."
56. Wannan ita ce liyafarsu a
ranar sakamako.
57. Mu ne Muka halitta ku, to,
don me ba za ku gaskata ba?
58. Shin, kuma kun ga abin da
kuke fitarwa na maniyyi?
59. Shin, ku ne kuke halitta shi,
ko kuwa Mu ne Masu halitta wa?
60. Mu ne Muka kaddara mutu-
wa a tsakaninku, kuma ba Mu
zama Masu gajiyawa (1) ba,
(1) Aya ta 60 hade take da aya ta 61 watau, ba za Mu kasa musanya ku da wadansu
mutane ba su tsaya matsayinku, sa'an nan ku kuma Mu mayar da ku wata halitta.
824
56 - Suratul Waici'a
mmm-*\
61. A kan Mu musanya watfansu
(mutane) kamarku, kuma Mu
mayar da ku a cikin wata halitta da
ba ku sani ba.
62. Kuma lalle ne hakika, kun
san halittar farko, to, don me ba za
ku yi tunani ba?
63. Shin, kuma kun ga abin da
kuke nomawa?
64. Shin, ku ne ke tsirar da shi,
ko kuwa Mu ne Masu tsirarwa?
65. Da Muna so, lalle, da Mun
sanya shi busasshiyar ciyawa, sai ku
yini kuna mamakin bakin ciki.
66. (Kuna cewa) "Lalle hakika
an aza mana tara!
67. "A'a, mun dai zama wadan-
da aka hana wa!"
68. Shin, kuma kun ga ruwa
wannan da kuke sha?
69. Shin, ku ne kuke saukar da
shi daga girgije, ko kuwa Mu ne
Masu saukarwa?
70. Da Mun so, da Mun mayar
da shi ruwan zartsi. To, don me ba
ku godewa?
71. Shin, kuma kun ga wuta
wannan da kuke kyastawa?
72. Shin, ku ne kuke kaga halit-
tar itaciyarta, ko kuwa Mu ne Masu
kagawa?
73. Mu ne Muka sanya ta wata
abar wa'azi da jin dacfi ga matafiya
a cikin jeji.
74. Sai ka tsarkake sunan
Ubangijinka Mai girma.
^oy^y^^xy-jy^u
Sfc&£!lil
825
56 - Suratul Waki'a
%w\m-n
75. To, ba sai Na yi rantsuwa ba
da lokutan faduwar taurari.
76. Kuma lalle ne, hakika, rant-
suwa ce mai girma, da kun sani.
71. Lalle shi (wannan littafi),
hakika, abin karantawa ne mai
daraja.
78. A cikin wani littafi tsararre.
79. Babu mai shafa shi face wa-
cfanda aka tsarkake.
80. Wanda aka saukar ne daga
Ubangijin halitta.
81. Shin, to, wannan labarin ne
kuke masu wulakantawa?
82. Kuma kuna sanya arzikinku
(game da shi) lalle ku, ku karyata
(shi)?
83. To, don me idan rai ya kai ga
makoshi? (Kusa da mutuwa).
84. Alhali kuwa ku, a lokacin
nan, kuna kallo.
85. Kuma Mu ne mafi kusanta
gare shi daga gare ku, to, amma ku
ba ku gani.
86. To, don me in dai kun kasan-
ce ba wacfanda za a yi wa sakamako
ba?
87. Ku mayar da shi (cikin jikin-
sa) har idan kun kasance masu
gaskiya (1) .
88. To, amma idan (mai mutu-
war) ya kasance daga makusanta,
ISP ^y^v^^
ftp ojjv*^ \* \j*-~~ ^
9 S A'
'>\*X*x
(1) Idan kun kasance masu gaskiya ga da'awar rashin Tashin Kiyama, to, ku yi
kokarin hana mutuwa ga mutane domin ku hana cikar alkawarin tayarwa a bayan
mutuwa.
826
56 - Suratul Wa£i'a
&ffl\$&-*\
89. Sai hutawa da kyakkyawan
abinci da Aljannar ni'ima.
90. Kuma amma idan ya kasan-
ce daga mazowa dama,
91. Sai (a ce masa) aminci ya
tabbata a gare ka daga mazowa
dama.
92. Kuma amma idan ya kasan-
ce daga masu karyatawar, 6atattun,
93. Sai wata liyafa ta ruwan zafi.
94. Da konuwa da Jahlm,
95. Lalle wannan, haklka, ita ce
gaskiya ta yakini.
96. Saboda haka, ka tsarkake (1)
sunan Ubangijinka Mai karimci.
AVI ^aiCL^-iij^j
^p^V-t; <<
F^H^I
> • 2 » t -. rr; -^ :'»',* ^^S^M
Tana karantar da muhimmancin Jihadi da ciyar da dukiya
domin Jihadin cfaukaka kalmar Allah, a bayan Tmani da Allah da
ManzonSa.
* j*'^ s *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
I. Abin da ke cikin sammai da
kasa ya yi tasblhi ga Allah. Kuma
Shi ne Mabuwayi, Mai hikima.
* :\
Jeji \j C^yP \ ^U^ *xL-»
'^$JV
(1) A cikin ruku'i ana tasblhi da cewa "Subhana Rabbiyal Azlm wa Bihamdih" sau
uku. Ma'anarsa Tsarki ya tabbata ga Ubangijina Mai girma game da gode Masa.'
827
57 - Suratul Hacfid
&^&-*v
2. ShT ne da mulkin sammai da
kasa; Yana rayarwa kuma Yana
kashewa, kuma ShT Mai ikon yi ne a
kan kome.
3. ShT ne Na farko, Na karshe,
Bayyananne, *B6yayye, kuma ShT
Masani ne ga dukan kome.
4. ShTne Wanda Ya halitta sam-
mai da kasa a cikin wasu kwanuka
shida, sa'an nan Ya daidaitu a kan
Al'arshi, Yana sanin abin da ke
shiga cikin kasa da abin da ke fita
daga gare ta, da abin da ke sauka
daga sama da abin da ke hawa
cikinta, kuma ShT Yana tare da ku,
duk inda kuka kasance. Kuma Al-
lah Mai gani ne ga abin da kuke
aikatawa.
5. ShT ne da mulkin sammai da
kasa, kuma zuwa gare Shi (Allah)
kawai ake mayar da aFamura.
6. Yana shigar da dare a cikin
yini, kuma Yana shigar da yini a
cikin dare, kuma Shi Masani ne ga
abin da yake a cikin kiraza.
7. Kuyi Tmani da Allah da Man-
zonSa, kuma ku ciyar daga abin da
Allah Ya wakilta ku a cikinsa (na
dukiya). To, wacfannan da suka yi
Tmani daga cikinku, kuma suka
ciyar, suna da wani sakamako mai
girma.
8. Kuma me ya same ku, ba za
ku yi Tmani ba da Allah, alhali kuwa
ManzonSa na kiran ku domin ku yi
Tmani da Ubangijinku, kuma lalle
Allah Ya karBi alkawarinku (cewa
za ku bauta Masa)? (Ku bauta
3^£K^
S&j'j
myJ^yM's^
\jjy^>i.
WjWgj^W*^^^
828
57 - Suratul HadTd
MW&-*
Masa) idan kun kasance (1) masu
Imani.
9. Shi ne Wanda ke sassaukar
da ayoyi bayyanannu ga BawanSa,
domin Ya fitar da ku daga duffai zu-
wa ga haske, kuma lalle Allah hakika
Mai tausayi ne gare ku, Mai jin kai.
10. Kuma me ya same ku, ba za
ku ciyar ba domin rfaukaka kalmar
Allah, alhali kuwa gadon sammai
da kasa na Allah ne? Wanda ya
ciyar a gabanin cin nasara, kuma ya
yi yaki daga cikinku, ba ya zama
daidai (da wanda^bai yi haka ba).
Warfancan ne mafifita girman dara-
ja (2) bisa ga wadanda suka ciyar
daga baya kuma suka yi yaki.
Kuma dukansu Allah Ya yi musu
wa'adi da (sakamako) mai kyau,
kuma Allah Masani ne ga abin da
kuke aikatawa.
77. Wane ne wanda zai ranta wa
Allah ranee mai kyau domin Allah
Ya ninka masa shi (a duniya) kuma
yana da wani sakamako na karimci
(a Lahira)?
72. Ranar da za ka ga muminai
maza da muminai mata, haskensu
na tafiya a gaba gare su, da kuma
dama gare su. (Ana ce musu)
"Bushararku a yau, ita ce gidajen
Aljanna." Ruwa na gudana daga
karkashinsu, suna masu dawwama
a cikinsu. Wannan, shi ne babban
rabo mai girma.
> z>
\y /
(1) Wannan ya nuna bin umurnin Allah da nisantar abin haninSa shi ne bauta, domin
Ya ambaci ciyar da dukiya da yin jihadi bauta, ne.
(2) Wannan ya nuna cewa sahabban Annabi su ne suka fi kowane Musulmi a bayansu
daraja. Kuma akwai bambancin daraja a tsakanin sahabban farko da na baya.
829
57 - Stiratul HadTd
mm*-*
13. Ranar da munaflkai maza da
munafikai mata ke cewa watfanda
suka yi Tmani, "Ku dubo mu, mu yi
makamashi daga haskenku!" A ce
(musu), "Ku koma a bayanku, do-
min ku nemo wani haske." Sai a
danne a tsakaninsu da wani garu
yana da wani £yaure, a cikinsa nan
rahama take, kuma a bayansa daga
wajensa azaba take.
14. Suna kiran su, "Ashe, ba tare
muke da ku ba?" Su ce, "T, amma
ku, kun fitini kanku, kuma kun yi
jiran wata masTfa, kuma kun yi
shakka, kuma warfansu gurace-
-gurace sun rude ku, har umurnin
Allah ya je muku, kuma marucG ya
rude ku game da Allah.
75. "To, a yau ba za a kar6i
fansa daga gare ku ba. Kuma ba za
a kar6a daga wadanda suka kafirta
ba. Makomarku wuta ce, ita ce mai
dacewa da ku, kuma makomarku
din nan ta munana."
16. Shin, lokaci bai yi ba ga wa-
danda suka yiTmam (1) zukatansu su
yi tawalu'i ga ambaton Allah da
abin da ya sauka daga gaskiya?
Kada su kasance kamar wadanda
aka bai wa littafi a gabanin haka,
sai zamani ya yi tsawo a kansu,
saboda haka zukatansu suka £e£as-
he, kuma masu yawa daga cikinsu
fiasi£ai ne.
• "t ro \*\ > *'" ' *.\{*\ * 'ft
^^4>JUab A^j w<s*\ **-&>-
(1) Wanda ya yi Tmani da Allah amma bai bi umurninSa ba, sai zuciyarsa ta £e£ashe,
lmanin ya fita sa'an nan kuma ya zama fasi£i mai fita hanyar gaskiya. Barin ciyarwa da
dukiya domin jihadi yana niina £e£ashewar zuciya daga Tmani, saboda haka facfa da zuciya
domin tsaron imaninta shi ne jihadi mafi girma.
830
57 - Suratul HadTd
mm*-*
17. Ku sani cewa Allah Yana
rayar da kasa a bayan mutu-
warta. (1) Lalle Mun bayyana muku
ayoyi da fatan za ku yi hankali.
18. Lalle masu gaskatawa maza
da masu gaskatawa mata, kuma
suka ranta wa Allah ranee mai
kyau, ana riBanya musu, kuma su-
na da wani sakamako na karimci.
19. Kuma wacfanda suka yilma-
ni da Allah da ManzanninSa, wa-
dannan su ne masu kamalar gaska-
tawa, kuma su ne masu shahada a
wurin Ubangijinsu. Suna da
sakamakonsu da haskensu. Wa-
cfanda suka kafirta, kuma suka ka-
ryata game da ayoyinMu, wadan-
nan su ne 'yan Jahim.
20. Ku sani cewa rayuwar du-
niya wasa dai ce da shagala da kawa
da alfahari a tsakaninku da gasar
wadata ta dukiya da diya, kamar
misalin shuka wadda yabanyarta ta
bayar da sha'awa ga manoma, sa'an
nan ta kekashe, har ka gan ta ta
zama rawaya, sa'an nan ta koma
rauno. Kuma a Lahira akwai aza-
ba mai tsanani da gafara daga Al-
lah da yarda. Kuma rayuwar du-
niya ba ta zama ba face dan jin
dadin rudi kawai.
21. Ku yi tsere zuwa ga (neman)
gafara daga Ubangijinku, da Al-
janna, fadinta kamar fadin sama da
kasa ne, an yi tattalinta domin wa-
cfanda suka yi Itnani da Allah da
»\m *t ^frli^l-f
' **' 3s'*.'< 'UrtA
wp
'*>\<". - * 4>%tfi
>>?'> "
(1) Mai rayar da £asa a bayan mutuwarta da ruwa, yana rayar da zukata saboda
tawalu'i ga ambaton Allah da bin umurninSa. Watau tawalu'i daidai yake da ruwa wajen
rayarwa ga matattu, sai dai kowane da tasa hanya.
831
57 - Suratul Hacffd
M^-^Y
ManzanninSa. Wannan falalar Al-
lah ce, Yana bayar da ita ga wanda
Ya so. Kuma Allah Mai falala ne
Mai girma.
22. WatamasTfabazataaukuba
a cikin kasa ko a cikin rayukanku
face tana a cikin littafi a gabanin
Mu halitta ta. Lalle wannan, ga
Allah, mai sauki ne.
23. Domin kada ku yi bakin ciki
a kan abin da ya kubuce muku,
kuma kada ku yi murnar alfahari da
abin da Ya ba ku. Kuma Allah ba
Ya son dukan mai takama, mai
alfahari.
24. Watau wadanda ke yin rowa,
kuma suna umurnin mutane da yin
rowa. Kuma wanda ya juya baya,
to, lalle Allah, Shine kadai Mawa-
daci, Godadde.
25. Hakika, lalle, Mun aiko
ManzanninMu da hujjoji bayya-
nannu, kuma Muka saukar da Lit-
tafi da sikeli tare da su domin mu-
tane su tsayu da adalci, kuma Mun
saukar da bakin karfe, (1) a cikinsa
akwai cutarwa mai tsanani da am-
fani ga mutane, kuma domin Allah
Ya san mai taimakonSa da Man-
zanninSa a fake. Lalle ne Allah Mai
karfi ne, Mabuwayi.
26. Kuma hakika, lalle, Mun
aiki Nuhu da Ibrahim, kuma
> < t .s*> '&* **?iyi\' *>,
tJL
^k * A\t '&'> ^^ \< S'" "
* "^O^^Li^iJ^JaJ
rr *.<.^>^
5p J^<£jWO) ! £r~^ \
'"<* . x'X'"
'Stsv^-'A'
(1) Littafi a nan ana nufin dukan littattafan sama da aka bayar a bayan Nuhu da
Ibrahim. Ma'auni kuma, shi ne shan'ar da ke cikinsu. Bakin karfe kuwa domin kayan aiki
na amfanin sana'o'i da cutar da ke a cikinsa na makamai da kuma amfanin tsaron addini
da jihadi. Littafi da ma'auni ana aiki da su wajen awon ibadar Allah da mu'amaldi a
tsakanin mutane.
832
57 - Suratul HadTd
M^-^
Muka sanya Annabci da Littafi a
cikin zuriyarsu ; daga cikinsu akwai
mai neman shiryuwa, kuma masu
yawa daga cikinsu fasikai ne.
27. Sa'an nan Muka biyar a
bayansu {1) da ManzanninMu ;
kuma Muka biyar da Tsa dan Ma-
ryama, kuma Muka ba shi Linji-
la kuma Muka sanya tausayi da
rahama a cikin zukatan wadanda
suka bTshi, da ruhbananci (2) wan-
da suka kaga shi, ba Mu rubuta shi
ba a kansu, face dai (Mun rubuta
musu) neman yardar Allah, sa'an
nan ba su tsare shi hakkin tsare-
warsa ba, saboda haka Muka bai
wa wadanda suka yi imani daga
cikinsu sakamakonsu, kuma masu
yawa daga cikinsu fasikai ne.
28. Ya ku wadanda suka yi Ima-
ni! Ku bi Allah da takawa, ku yi
Imani da ManzonSa, (3) Ya ba ku
rabo biyu daga rahamarSa, kuma
Ya sanya muku wani haske wanda
kuke yin tafiya da shi, kuma Ya
gafarta muku. Kuma Allah Mai
gafara ne, Mai rahama.
29. Domin kada (4) mutanen Lit-
tafi su san cewa lalle ba su da ikon yi
\< * ?*>**»
OjA^^^j^j
U^^^M^^^M
(1) Nuhu da Ibrahim da Annabawan da ke bayansu zuwa ga Tsa dan Maryama.
(2) Ruhubananci a Kiristanci kamar tasawwufi ne a Musulunci. Hana bidi'a yana
cikin jihadi da tsaron addini, bidi'a kuma kashe addini ne. Ana kashe bidi'a idan ana awon
ayyuka da Littafi kamar yanda ake hana zalunci idan ana awo da sikeli ko mudu.
(3) Manzon Allah a nan, shi ne Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a
^are shi. Ana umarnin ma'abuta Littafi da su bTshi domin su sami rabo ninki biyu. Masu
imani a nan su ne Ahlul kitabi na kwarai.
(4) Rashin saninsu ya hana su su bi Muhammadu ga samun falalar Allah: rabo biyu.
Ga wata fassara, an ce harafin nafyi £ari ne, watau ma'anarsa ita ce Allah Ya bayar da
rabo biyu ga wadanda suka yi Tmani da ManzonSa, domin mutanen littafi su san ba za su
iya hana abin da Allah Ya nufa ba.
833
58 — Suratul Mujadala
%$m$&-*
ga kome na falalar Allah, kuma ita
falalar ga hannun Allah kawai take,
Yana bayar da ita ga wanda Ya so
(wannan jahilci ya hana su Tmani).
Kuma Allah Mai falala ne mai
girma.
E
Tana karantar da yadda tsarin Majalisar Annabi ta kasance a
lokacinsa, domin ta zama abar koyi ga sauran majalisun Shuga-
bannin Musulmi a bayansa.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Lalle Alia Ya ji maganar (1)
wadda ke yi maka jayayya game da
mijinta, tana kai kara ga Allah,
kuma Allah na jin muhawararku.
Lalle Allah Mai jT ne, Mai gani.
2. Wacfanda ke yin zihari daga
cikinku game da matansu, su matan
(1) Wannan Rissa tana nuna cewa a Majalisar Annabi kowa na da 'yancin shiga,
namiji da mace, kuma ya facfi abin da yake so, ko da ya saba wa abin da Annabi ya gani
kafin wani wahayi ya sauka. Ga wannan mace sunanta Khaulatu bnt Sa'alabah ta kai
Rarar mijinta Ausu bn Samit wanda ya yi zihari game da ita, watau ya ce idan ya kusance ta
kamar ya kwana da uwarsa ne. Ga aJ I'adar Larabawa wannan ba saki ba ne, kuma ba ya iya
kwana da ita har abada. Wannan shi ne ta kai Rara wurin Annabi har ta yi muhawara da
shi a kansa. Kuma wannan Rissa tana nuna gaskiyar Annabi, bai yi jawabi ba ga abin da
bai sami wahayi ba a kansa.
834
58 — Suratul Mujadala
®&mm-*
nan ba uwayensu ba ne, babu
uwayensu face wacfanda suka haife
su. Lalle su, suna facfar abin Ryama
na magana da karya, kuma lalle
Allah hakika Mai yafewa ne, Mai
gafara.
3. Wacfanda ke yin zihari game
da matansu, sa'an nan su koma wa
abin da suka fada, to, akwai 'yanta
wuya a gabanin su shafi juna. Wan-
nan ana yi muku wa'azi da shi.
Kuma Allah Ma kididdigewa ne ga
abin da kuke aikatawa.
4. To, wanda bai samu ba, sai
azumin wata biyu jere a gabanin su
shafi juna, sa'an nan wanda bai
sami^ikon yi ba, to, sai ciyar da
miskmai sittin. Wannan domin ku
yi Tmani da Allah da ManzonSa.
Kuma wadannan hukunce-hukun-
ce haddodin Allah ne. Kuma
kafirai, suna da azaba mai radadi.
5. Lalle wadanda ke saba wa
Allah da ManzonSa, an wulakanta
su kamar yadda aka wulakantar da
wadanda ke a gabaninsu, kuma
lalle Mun saukar da ayoyi bay-
yanannu, kuma kafirai na da azaba
mai wulakantawa.
5. Ranar da Allah zai tayar da su
gaba cfaya, sa'an nan ya ba su labari
game da abin da suka aikata, Allah
Ya lissafa shi, alhali kuwa su, sun
manta da shi, kuma a kan kome
Allah Halartacce ne.
7. Ashe, ba ka ga cewa lalle
Allah Yana sane da abin da yake a
cikin sammai da abin da ke cikin
/
."* *' *'*\S
±* 4*0
&\&l&^\$$Z8&jp\
<jf->
835
58 — Suratul Mujadala
feB^IM««A
Rasa ba? Wata ganawa (1) ta mutum
uku ba za ta kasance ba face Allah
ShT ne na hucfu cfinta, kuma babu
ta mutum biyar face ShT ne na shi-
da cfinta, kuma babu abin da ya
kasa wannan kuma babu abin da
yake mafi yawa face ShT Yana tare
da su duk inda suka kasance, sa'an
nan Ya ba su labari game da abin
da suka aikata a Ranar Kiyama.
Lalle Allah Masani ne ga dukan
kome.
8. Ashe, ba ka ga wadanda aka
hane su ba daga ganawar, sa'an nan
suna koma wa abin da aka hane su
daga gare shi, kuma suna ganawa
game da zunubi da zalunci da saBa
wa Manzon Allah, kuma idan sun
zo maka sai su gaishe ka da abin da
Allah bai gaishe ka da shi ba, kuma
suna cewa a cikin zukatansu, "Don
me Allah ba Ya yi mana azaba
saboda abin da muke fada ?" Jahan-
nama ita ce mai isarsu, za su shige
ta. Saboda haka makomarsu ta
munana.
9. Ya ku wadanda suka yilmani !
Idan za ku yi ganawa, to, kada ku
gana game da zunubi da zalunci da
sa6a wa Manzon Allah, kuma ku yi
ganawa game da alheri da takawa.
Ku bi Allah da takawa, Wanda za
a tattara ku zuwa gare Shi.
10. Ganawar daga Shaidan take
kawai domin ya munana wa wadan-
da suka yi Tmani, alhali kuwa ba zai
(1 ) A bayan kissar zihari, ya shiga maganar masu ganawa a cikin majalisa. Kuma ya
nuna cewa ba a sifanta Annabi ko a jingina wani abu zuwa gare shi sai idan abin nan ya fito
daga Allah a cikin harshen ManzonSa.
836
58 — Suratul Mujadala
m&m-**
iya cutar su da kome ba face da
iznin Allah. Kuma sai muminai su
dogara ga Allah.
//. Ya ku wadanda suka yi una-
ni! Idan an ce muku, (1) "Ku yalwa-
ta, a cikin majalisai," to, ku yalwa-
ta, sai Allah Ya yalwata muku,
kuma idan an ce muku, "Ku tashi"
to, ku tashi. Allah na tfaukaka wa-
danda suka yi Tmani daga cikinku
da wadanda aka bai wa ilmi, wasu
darajoji masu yawa, kuma Allah
Mai kididdigewa ne ga dukan kome.
12. Ya ku wadanda suka yi una-
ni! Idan za ku ganawa da Manzon
Allah, to, ku gabatar da 'yar sada-
ka (2) a gabanin ganawarku, wan-
nan ne mafi alheri a gare ku, kuma
mafi tsarki. Sai idan ba ku sami
(abin sadakar ba), to, lalle, Allah,
Mai gafara ne, Mai jin kai.
13. Ashe, kun ji tsoron ku gaba-
tar da sadakoki a gabanin gana-
warku? To, idan ba ku aikata ba,
kuma Allah Ya komo da ku zuwa ga
sauki, sai ku tsai da salla, kuma ku
bayar da zakka, kuma ku yi da'a
ga Allah da ManzonSa. Kuma Al-
lah ne Mai kididdigewa ga abin da
kuke aikatawa.
14. Ashe,bakagawadanda (3) suka
^f < // ^f *\ j\\ \* <
^k< V-K P* <
(1) Bayan £issar hukuncin ganawa cikin majalisa, sai kuma hukuncin zaunawa ko
tashi domin wani ya zauna. Kuma ana fifita masu ilmi da zama ga wurin da ya fi dacewa da
su.
(2) Hukuncin tayar da mutane domin a gana da Manzon Allah, ba ya halatta sai a
kan larura mai tsanani saboda haka aka sanya gabatar da sadaka, sa'an nan aka soke shi
da umurni da tsaron salla domin wa'azin da ke cikinta da kuma bayar da zakka.
(3) Bayan maganar masu tayar da mutane domin ganawa a cikin majalisa, sai kuma
munafikai masu mu'amala da kafirai, kuma su je su zauna cikin majalisar Musulmi domin
su cfauki rahotonsu zuwa ga ma£iyansu.
837
58 — Suratul Mujadala
t^^iM-OA
ji6inci wadansu mutane da Allah Ya
yi hushi a kansu ba, ba su cikinku,
kuma ba su a cikinsu, kuma suna
rantsuwa a kan karya, alhali kuwa
suna sane?
15. Allah Ya yi musu tattalin
azaba mai tsanani. Lalle su, abin da
suka kasance suna aikatawa ya
munana.
16. Sun riki rantsuwowinsu gar-
kuwa, saboda haka suka kange
(muminai) daga jihadin daukaka
tafarkin Allah. To, suna da azaba
mai wulakantawa.
17. Dukiyoyinsu ba su wadatar
musu kome ba daga Allah, haka
kuma cfiyansu. Wadannan 'yan
wuta ne. Su, masu dawwama ne a
cikinta.
18. Ranar da Allah ke tayar da
su gaba daya, sai su yi Masa rantsu-
wa kamar yadda suke yi muku rant-
suwa (a nan duniya) kuma suna
zaton cewa su a kan wani abu suke !
To, lalle su, su ne makaryata.
19. Shaidan ya rinjaya a kansu,
sai ya mantar da su ambaton Allah,
wadannan kungiyar Shaidan ne.
To, lalle kungiyar Shaidan, su ne
masu hasara.
20. Lalle wadanda ke sa6a wa
Allah da ManzonSa, wadannan
suna a cikin (mutane) mafi kas-
kanci.
21. Allah Ya rubuta cewa, "Lalle
zan rinjaya, NT da ManzanniNa."
Lalle Allah Mai karfi ne, Mabu-
wayi.
&\^\&j&d&^
1^4 * ' ' -
838
58 — Suratul Mujadala
t&l^ljgi-OA
22. Ba za ka sami mutane masu
yin Imani da Allah da Ranar Lahira
suna soyayya da wanda ya saBa wa
Allah da ManzonSa ba, ko da sun
kasance ubanninsu ne, ko diyansu
ko 'yan'uwansu, ko danginsu. Wa-
cfannan Allah Ya rubuta imani a
cikin zukatansu, kuma Ya karfafa
su da wani ruhi (1) daga gare Shi,
kuma zai shigar da su a gidajen
Aljanna, Koramu na gudana ka-
rkashinsu suna masu dawwama a
cikinsu. Allah Ya yarda da su,
kuma sun yarda da Shi. Wadannan
kungiyar Allah ne. To, lalle kun-
giyar Allah su ne masu babban
rabo.
*? > * ^ 4»t * ~ r > " »>r x **? / u"
Tana karantar da yadda Allah ke shirya yadda zai taimaki
wanda ya dogara a gare Shi ga bin umurninSa, da sauki, ta hanyar
da bai sani ba.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
I. Abin da ke cikin sammai da
abin da ke cikin kasa ya yi tasbihi
ga Allah, alhali kuwa, Shi ne Ma-
buwayi, Mai hikima.
>4dl\y£\%
(1) Wacfanda suka tsare dokokin Allah, Allah zai ba su karfm rai ga zartar da
aFamuransu dajcyau, kuma zai wadata su a duniya da Lahira. Asalin ruhi shi ne rai. Ana
nufin rayuwar imani da karfin halin fuskantar gaskiya.
839
59 - Suratul Hashr
\$&-o\
2. Shi ne Wanda Ya fitar da wa-
cfanda suka kafirta daga Mazowa
Littafi, (1) daga gidajensu da kora (2)
ta farko. Ba ku yi zaton suna fita ba,
kuma sun tabbata cewa ganuwo-
winsu masu tsare su ne daga Allah,
sai Allah Ya je musu daga wajen da
ba su yi zato ba, kuma ya jefa tsoro
a cikin zukatansu, suna rushe gida-
jensu da hannayensu da kuma han-
nayen muminai. To, ku lura fa, ya
masu baslrori.
3. Kuma ba domin Allah Ya ru-
buta musu korar ba, da Ya azabta
su a cikin duniya, kuma a Lahira
suna da azabar wuta.
4. Wannan, domin lalle su, sun
sa6a wa Allah da ManzonSa, alhali
kuwa wanda ya sa6a wa Allah, to,
lalle Allah, Mai tsananin ukuba ne.
5. Abin da kuka sare na dabT-
niya, ko kuka bar ta tsaye a kan
asallanta, to, da iznin Allah ne,
kuma domin Ya wulakanta fasikai.
6. Kuma abin da Allah Ya sanya
ya zama ganima ga ManzonSa,
daga gare su, to, ba ku yi hari a
kansa da dawaki ko rakuma ba,
amma Allah ne Ya rinjayar da Man-
zanninSa a kan wanda Yake so,
kuma Allah Mai Tkon yi ne a kan
kome.
7^ Abin da Allah Ya sanya shi
gamma ga ManzonSa daga muta-
nen kauyukan nan, to, na Allah ne,
f*rs
*^S£> > -" •• y ft
^J^J^<^^^ a 4^^^^W^
(1) Mazowa Littafi a nan, su ne Yahudun Madina, watau BanT NadTr,
(2) Korewa daga kasa, Annabi ya kore su zuwa Haibara a gargacfar farko, Umar ya
kore su daga Haibara zuwa Syria a gargacfa ta biyu.
840
59 - Suratul Hashr
-<*
kuma na ManzonSa ne, kuma na
masu dangantaka da marayu da
misklnai da dan hanya (1) (matafiyi)
ne, domin kada ya kasance abin
shawagi a tsakanin mawadata daga
cikinku, kuma abin da Manzo ya ba
ku, to, ku kama shi, kuma abin da
ya hane ku, to, ku bar shi. Kuma ku
bi Allah da taka wa. Lalle Allah, Mai
tsananin ukuba ne.
8. (Ku yi mamaki) Ga matalauta
masu hijira wadanda aka fltar daga
gidajensu da dukiyoyinsu, suna ne-
man falala daga Allah da kuma
yarda, kuma suna taimakon Allah
da ManzonSa! Wadannan su ne
masu gaskiya.
9. Da wadanda suka zaunar da
gidajensu ^ga Musulunci) kuma
(suka za6i) imani, a gabanin zuwan-
su, (2) suna son wanda ya yi hijira
zuwa gare su, kuma ba su tunanin
wata bukata a cikin kirazansu daga
abin da aka^bai wa muhajinna,
kuma suna fifita wadansu a kan
kawunansu, kuma ko da suna da
wata larura. Wanda ya sa6a wa
rowar ransa, to, wadannan su ne
masu babban rabo.
10. Kuma wadanda suka zo
daga bayansu, suna cewa, "Ya
Ubangijinmu! Ka yi gafara a gare
mu, kuma ga 'yan'uwanmu, wadan-
s£^. ' 9 " J- s -*' ' *t> ^'
^^ju «-u> <jy {jaj A^^Ua^/vf-: o ojij
^ ^ * \*>\t» ^4^
* >,
(1) T)an hanya, shi ne matafiyin da guzuri ya Rare masa, yana neman taimakon da zai
mayar da shi garinsa.
(2) Muhajinna sun yi hijira zuwa Madina daga Makka ko wadansu wurare. Ansar, su
ne mutanen MadTna. Wadannan su ne ya kamata a yi mamakin yadda suka taimaki addini
a lokacin tsanani. Muhajinna sun bar gidajensu da dukiyarsu sun yi hijira, Ansarai sun
raba dukiyarsu da gidajensu da iyalansu sun bai wa Muhajinna domin taimakon addini.
841
59 - Suratul Hashr
V&-o\
da suka riga mu yinTmani, kada Ka
sanya wani kulli a cikin zukatanmu
ga wadanda suka yi Tmani. Ya
Ubangijinmu ! Lalle Kai ne Mai
tausayi, Mai jin kai.
1 1 . Ashe, ba ka ga wadanda suka
yi munafinci (1) ba, suna cewa ga
'yan'uwansu, wadanda suka kafirta
daga Mazowa Littafi, "Lalle idan
an fitar da ku, lalle za mu fita tare
da ku, kuma ba za mu yi da'a ga
kowa ba game da ku, har abada,
kuma lalle idan an £ake ku, lalle za
mu taimake ku hakikatan?" Alhali
kuwa Allah na shaidar cewa lalle su,
tabbas, makaryata ne.
12. Lalle idan an fitar da su, ba
za su fita tare da su ba, kuma lalle
idan an yake su ba za su taimake su
ba, kuma lalle idan sun taimake su,
lalle ne, hakikatan, za su juyar da
bayansu domin gudu, sa'an nan
kuma ba za a taimake su ba.
13. Lalle ku ne kuka fi bayar da
firgita a cikin zukatansu bisa ga
Allah, wannan kuwa domin su lalle
wacfansu irin mutane ne da ba su
ganewa.
14. Ba su iya yakar ku gaba
daya, face a cikin garuruwa masu
ganuwa da garuna, ko kuma daga
bayan katangu. Yakinsu a tsaka-
ninsu mai tsanani ne, kana zaton su
a hade, alhali kuwa zukatansu
dabam-dabam suke. Wannan kuwa
domin su, lalle wasu irin mutane ne
da ba su hankalta.
^^isj^^J^^j^fv
'\ >'s
j*+>\> <iita cs-^^^^j ^h
( 1 ) Bayan ya nuna yadda Allah ke taimakon mai binSa da takawa. Kuma yana nuna
yadda Yake tabar da mai binSa da munafinci.
842
59 - Suratul Hashr
£&$£-<*
15. Kamar misalin wacfanda (1)
ke a gabaninsu, ba da dadewa ba,
sun cfancfani kucfar al'amarinsu,
kuma suna da wata azaba mai
racfacfi.
16. Kamar misalin Shaicfan a 16-
kacin da yake ce wa mutum, "Ka
kafirta". To, a lokacin da ya kafirta
din, ya ce (masa), "Lalle babu ruwa-
na da kai. Lalle ni ina tsoron Allah,
Ubangijin halitta!"
1 7. Sai akibarsu ta kasance cewa
su biyun duka suna a cikin wuta,
suna masu dawwama a cikinta.
Kuma wannan shl ne sakamakon
masu zalunci.
18. Ya ku wacfanda suka yi ima-
ni ! Ku bi Allah da takawa, kuma rai
ya dubi abin da ya gabatar domin
gobe, kuma ku bi Allah da takawa.
Lalle Allah, Mai kididdigewa ne ga
abin da kuke aikatawa. (2)
19. Kuma kada ku kasance ka-
mar wacfanda suka manta Allah,
Shi kuma Ya mantar da su rayu-
kansu. Wadannan su ne fasikai.
20. 'Yan wuta da 'yan Aljanna
ba su daidaita. 'Yan Aljanna, su ne
masu babban rabo.
21. Da Mun saukar da wannan
Alkur'ani a kan dutse, da lalle ka ga
dutsen yana mai tawali'u, mai tsat-
tsagewa saboda tsoron Allah, kuma
wadancan misalai Muna bayyana
(1) Kuraishawa da aka kashe a Badar.
(2) Daga wannan aya ta 18 zuwa karshen sura, yana bayanin hasilin darasin surar ne
dunkule, da kuma ambatar muhimman abubuwan da ta kunsa domin wa'azi da farkarwa
ga mai hankali.
843
59 - Suratul Hashr
uM%&-o\
su ne ga mutane, da fatan za su yi
tunani.
22. (Wanda Ya saukar da Alku-
r'ani) Shi ne Allah, Wanda babu
wani abin bautawa face Shi, Ma-
sanin fake da bayyane, ShT ne Mai
rahama, Mai jin kai.
23. ShT ne Allah, Wanda babu
abin bautawa face Shi, Mai mulki,
Mai tsarki, Aminci, Mai amintar-
wa, Mai Tsarewa, Mabuwayi, Mai
tilastawa, Mai kamun kai. Tsarki
ya tabbata a gare Shi daga abin da
suke yi na shirki da Shi.
24. ShT ne Allah, Mai halitta,
Mai ginawa, Mai surantawa. Yana
da sunaye masu kyau, abin da ke a
cikin sammai da kasa suna tsarkake
Shi, kuma ShT ne Mabuwayi, Mai
hikima.
Tana gargacfi ga Musulmi su tsintsintar da biyayyarsu ga Allah,
su yanke wata mu'amala da kafirai, ba da sun zalunce su ba.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rat
1. Ya ku wadanda suka yi Tmani !
Kada ku riki makiyiNa kuma maki-
iE^J^f^^^^-^-^l^-^^^L^^*^^*^^
844
60 — Suratul Mumtahana
- V
yinku masoyi, kuna jefa soyayya (1)
zuwa gare su, alhali kuwa hakika
sun kafirta da abin da ya zo muku,
na gaskiya, suna fitar da Manzon
Allah tare da kujdaga gidajenku)
domin kun yi imani da Allah,
Ubangijinku, idan kun fito domin
jihadi saboda cfaukaka kalmaTa da
neman yardaTa, kuna asirta
soyayya zuwa gare su alhali kuwa
Ni ne Mafi sani ga abin da kuka
66ye da abin da kuka bayyana,
kuma duk wanda ya aikata shi daga
cikinku, to, lalle ya 6ace daga tsakar
hanya.
2. Idan sun kama ku, za su ka-
sance makiya a gare ku, kuma su
shimficfa hannuwansu da harsunan-
su zuwa gare ku da cuta, kuma su yi
gurin ku kafirta.
3. Zumuntarku ba za ta amfane
ku ba, haka kuma diyanku, a Ranar
Kiyama. (Allah) zai (2) rarrabe
tsakaninku, kuma Allah Mai gani
ne ga abin da kuke aikatawa.
4. Lalle abin koyi mai kyau ya
kasance a gare ku game da Ibra-
him da wacfanda ke tare da shi a
lokacin da suka ce wa mutanensu,
"Lalle mu, babu ruwanmu da ku,
kuma da abin da kuke bautawa,
(1) Wani Sahabin Annabi da ake cewa Hatibu bn Abi Balta'a ya rubuta takarda zuwa
ga Kuraishawa yana sanar da su cewa Annabi na zuwa garinsu da yaki, sai Allah Ya sanar
da Annabi tun manzonsa bai isa ba ga Kuraishawa, sai aka mayar da takardar. Da aka
tambayi Hatibu dafllin yin ta, sai ya ce domin yana da dlya da dukiya ne a can, domin haka
ya so ya gaya musu zuwan Annabi ko da yake yana da cikakken Tmamin cewa Annabi
gaskiya ne, kuma zai rinjaye su duk yadda aka yi. Sai Annabi ya karbi uzurinsa, ba a yi
masa kome ba, sai dai abin da Allah Yajiana; kada Musulmi su sake wata ma'amala da
kaflrai a boye ko a bayyane saboda dalllan da aka fada a cikin surar.
(2) Ga wata kira'a za a fassara wurin da cewa 'za a rarrabe tsakaninku'.
845
60 — Suratul Mumtahana
5S2)«&-v
baicin Allah, mun fita batunku,
kuma kiyayya da jiyewa juna sun
bayyana a tsakaninmu, sai kun yi
Tmani da Allah Shi kacfai." Face
maganar Ibrahim ga ubansa (da ya
ce), "Lalle za ni nema maka gafara
kuma ban mallaki kome ba daga
Allah saboda kai." "Ya Ubangi-
jinmu! A gare Ka muka dogara,
kuma gare Ka muka mayar da
al'amuranmu, kuma zuwa gare Ka
makoma take."
5. "Ya Ubangijinmu ! Kada Ka
sanya mu fitina ga wacfanda suka
kafirta, kuma Ka yi gafara gare
Mu. Ya Ubangijinmu ! Kai ne Ma-
buwayi, Mai hikima!
6. Lalle, haklka, abin koyi mai
kyau ya kasance a gare ku daga
cikinsu, ga wanda ya kasance yana
fatan (rahamar) Allah da Ranar
Lahira, kuma wanda ya juya baya,
to, lalle Allah, Shi ne Wadatacce,
Godadde.
7. Ana tsammanin Allah Ya sa-
nya, a tsakaninku da tsakanin wa-
cfanda kuka yi kiyayya da su, wata
soya^ya daga gare su, kuma Allah
Mai ikon yi ne, kuma Allah Mai
gafara ne, Mai jin kai.
8. Allah ba Ya hana ku, daga
wadanda ba su yake ku ba saboda
addini kuma ba su fitar da ku ba
daga gidajenku, ga ku kyautata
musu kuma ku yi musu adalci. Lalle
Allah Yana son masu adalci.
9. Allah Yana hana ku kawai
daga wadanda suka yake ku saboda
addini kuma suka fitar da ku daga
gidajenku, kuma suka taimaki juna
•> *^ t *'<
1 ' '*' " IS+y' 4**1 *>*'', *'*-
846
60 — Suratul Mumtahana
•-V
ga fitar da ku, kar ku ji6ince su,
kuma wanda ya ji6ince su, to, wa-
tfannan su ne azzalumai.
10. Yaku wadandasuka yilma-
ni! Idan mata muminai suka zo
muku, suna masu hijira, to, ku jar-
raba su. Allah ShT ne Mafi sani ga
imaninsu. To, idan kun san su mu-
minai ne, kada ku mayar da su zuwa
ga kafirai. Su matan ba su halatta
ga aurensu, su kuma kafiran ba su
halatta ga auren matan. Ku ba su
abin da suka Batar na dukiya.
Kuma babu laifi a kanku ga ku aure
su idan kun ba su sadakokinsu.
Kuma kada ku rike auren mata
kafirai, kuma ku tambayi abin da
kuka 6atar daga dukiya, su kuma
kafirai su tambayi abin da suka
Batar na dukiya. Wannan hukuncin
Allah ne, Yana hukunci a tsaka-
ninku. Kuma Allah, Masani ne,
Mai hikima
11. Kuma idan wani abu ya ku-
6uce muku daga matanku zuwa ga
kafirai, sa'an nan kuma kuka rfauki
fansa, to, sai ku bai wa warfanda
matansu suka tafi kwatankwacin
abin da suka 6atar na dukiya.
Kuma ku yi biyayya da takawa ga
Allah Wanda kuke masu Tmani da
Shi, Shi Kadai.
12. Ya kai Annabi! Idan mata
muminai suka zo maka suna yi
maka mubaya'a a kan ba za su yi
shirki da Allah ba ga kome, kuma
-t..^
poj^p>mpz.^?>&3
^*Sl*&&&~a?<
Z££*£f*&M&\y&j
(1) A zamanin jahiliyya sun kashe 'ya'yansu mata ta hanya uku, cfaya saboda
bakance na addTni, na biyu saboda tsoron talauci ; suna turbude 'ya'ya mata a bayan sun
shekara shida, na uku saboda kunyar haihuwar mace sai uwa ta yi rami, idan ta haifi namiji
ta bar shi, idan kuma ta haifi mace, sai ta tura ta a cikin ramin ta turbude.
847
60 — Suratul Mumtahana
^ew»-v
ba su yin sata, kuma ba su yin zina,
kuma ba su kashe (1) 'ya'yansu,
kuma ba su zuwa da karya da suke
kirkirawa (1) a tsakanin hannu-
wansu da kafafunsu, kuma ba su
sa6a maka ga wani abu da aka sani
na shan'a, to, ka kar6i mubaya'ar-
su, kuma ka nemi Allah Ya gafarta
musu. Lalle Allah Mai gafara ne,
Mai jin kai.
13. Ya ku wadanda suka yi Ima-
ni! Kada ku ji6inci wadansu muta-
ne (2) da Allah Ya yi hushi a kansu.
Lalle sun yanke tsammani daga
(rahamar) Lahira, kamar yadda ka-
firai suka yanke tsammani daga
mazowa (3) kaburbura.
Tana karantar da gaskiyar maganar watau kada aikin mutum
ya sa6a wa maganarsa.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L Abin da ke cikin sammai da
abin da ke cikin kasa ya yi tasbihi ga
Allah, alhali kuwa, Shi ne Mabu-
wayi, Mai hikima.
i^ < ^^
(1) Suna tsintar yaro su mayar da shi cfansu, haka kuma maza na yin tabanni, watau
mutum ya mai da dan wani nasa kamar yadda har yanzu kafirai na yin sa.
(2) Allah Ya yi hushi ga duk wanda ya sani kuma ya ki aiki da saninsa kamar
Yahudawa da miyagun Malamai.
(3) Kafirai ba su yarda da Tashin ICiyama ba, saboda haka suke yanke kauna daga
wanda ya mutu.
848
61 - Suratus SafT
<Ua$&-it
2. Yakuwatfandasukayiimani!
Don me k uke fadin abin da ba ku
aikatawa?
J. Ya girma ga zama abin kyama
a wurin Allah, ku fadi abin da ba ku
aikatawa.
4. Lalle Allah Yana son wadanda
ke yin ya£i domin daukaka Kal-
marSa, a cikin safu kamar su gini ne
mai damfarar juna.
5. Kuma a lokacin da Musayace
wa mutanensa, " Ya mutanena ! Sa-
boda me kuke cutar da ni, alhali
kuwa lalle kun sani cewa lalle m
Manzon Allah ne zuwa gare ku?"
To, a lokacin da suka karkace,
Allah Ya karkatar da zukatansu.
Kuma Allah ba Ya shiryar da muta-
ne fasikai.
6. Kuma a lokacin da Isa dan
Maryama ya ce, "Ya Bam IsraTla!
Lalle m, Manzon Allah ne zuwa
gare ku, mai gaskata abin da ke
gaba gare ni na Attaura, kuma mai
bayar da bushara da wani Manzo
da ke zuwa a bayana, sunasa Ah-
mad (Mashayabo)." To, a lokacin
da ya je musu da hujjoji, suka ce,
"Wannan sihiri ne, bayyananne."
7. Kuma wane ne mafi zalunci
daga wanda ya kirkira karya ya
jingina ta ga Allah, alhali kuwa shl,
ana kiran sa zuwa ga Musulunci?
Kuma Allah ba Ya shiryar da muta-
ne azzalumai.
8. Suna nufin su bice hasken Al-
lah da bakunansu, alhali kuwa Al-
lah Mai kammala haskenSa ne,
kuma ko da kafirai sun £i.
££
849
61 - Suratus Saff
iU^III^-ll
9. Shi ne Wanda Ya aiko Man-
zonSa da Shiriya da addlnin gas-
kiya, domin Ya cfaukaka shi a kan
wani addlni dukansa, kuma ko da
mushirikai sun £i.
10. Yaku wadanda suka yiima-
ni ! Shin, in nuna muku wani fatauci
wanda zai tsarshe ku daga wata
azaba mai radadi?
11. Ku yi Tmani da Allah da
ManzonSa, kuma ku yi jihadi ga
daukaka kalmar Allah game da
dukiyoyinku da rayukanku. Wan-
nan shi ne alheri a gare ku idan kun
kasance kuna da sani.
12. Sai Allah Ya gafarta muku
zunubanku, kuma Ya shigar da ku
gidajen Aljanna, koramu na gudana
daga karkashinsu, da wadansu da-
kuna masu dadi a cikin gidajen
Aljannar zama. Wannan shi ne
babban rabo, mai girma.
13. Dawata(falala)dayakekuna
son ta: taimako daga Allah da cin
nasara wanda yake kusa. Kuma ka
yi bushara ga muminai.
14. Ya ku wadanda suka yi Tma-
ni ! Ku kasancemataimakan Allah,
kamar abin da Tsa (fan Maryama ya
ce ga Hawariyawa, "Wadknne ne
mataimakana zuwa ga (aikin)
Allah?" Sai wata kungiya daga
Bam IsraTla ta yi Tmani, kuma wata
kungiya ta kafirta. Sai Muka karfa-
fa wadanda suka yi Tmani a kan
makiyansu, saboda haka suka wayi
gari marinjaya.
850
62 — Suratul Jumu'a
«*7Ai*fiA
kBS&-v
Tana karantar da cewa cfaukar ilmi ba da yin aiki da shi ba, ba
shi da wani amfani sai wahalar banza.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Abin da yake a cikin sammai
da abin da yake a cikin kasa suna
tasblhi ga Allah, Mamallaki, Mai
tsarki, Mabuwayi, Mai hikima.
2. Shine Wanda Yaaika, a cikin
mabiya al'adu, (1) wani Manzo daga
gare su yana karanta ayoyinSa a
kansu, kuma yana tsarkake su,
kuma yana sanar da su Littafin da
hikimarsa ko da yake sun kasance
daga gabaninsa lalle suna a cikin
Bata bayyananna.
3. Da wacfansu mutane (2) daga
gare su, ba su i da riskuwa da su ba,
alhali kuwa Shine Mabuwayi, Mai
hikima.
£ • -* y ?>. ^<
(1) Larabawa su ne mabiya al'adu, watau ummiyyun daga ummu, watau uwa, watau
kamar yadda uwaye suka haife su domin ba su da wani littafi da suke bi, sai al'adunsu da
hukunce-hukuncen shaihunansu.
(2) Su ne Ajamawan da za su musulunta su bi Annabi, tsTra da amincin Allah su
tabbata a gare shi. K6 kuwa duk wanda ya musulunta a bayan Sahabban Annabi. Wannan
yana nuna falalar Sahabbai a kan wadansunsu.
851
62 — SuratuI Jumu'a
®m&-v
4. Waccan wata falalar Allah ce,
Yana bayar da ita ga wanda Yake
so. Kuma Allah ne Ma'abucin du-
kan falala mai girma.
5. Misalin wadanda aka dora wa
cfaukar Attaura sa'an nan ba su
dauke ta ba, kamar misalin jaki ne,
yana daukar littattafai. Tir da mi-
salin mutanen (1> nan da suka karya-
ta game da ayoyin Allah! Kuma
Allah ba Ya shiryar da mutane azza-
lumai.
6. Ka ce, "Ya ku wadanda suka
tuba (Yahudu)! Idan kun riya cewa
lalle ku ne zaBaBBun Allah ba sau-
ran mutane ba, sai ku yi gurin mu-
tuwa (2) idan kun kasance masu gas-
kiya."
7. Kuma ba za su yi gurinta ba
har abada saboda abin da han-
nayensu suka gabatar. Kuma Allah
ne Masani ga azzalumai.
8. Ka ce, "Lalle mutuwar nan da
kuke gudu daga gare ta, to, lalle ita
mai haduwa da ku ce sa'an nan
kuma ana mayar da ku zuwa ga
Masanin fake da bayyane, domin
Ya ba ku labari ga abin da kuka
kasance kuna aikatawa."
9. Ya ku wadanda suka yi imani !
Idan an yi kira zuwa ga salla daga
ranar Jumu'a, sai ku yi aiki zuwa ga
(1) Tir wanda ya yi siffa da inn sifrofm Yahudu daga Musulmi wajen cfaukar karatun
Alkur'ani amma kuma bai yi aiki da shi ba. Yahaya bn Yamani ya ce, "Suna rubuta HadTsi
ba su fahimtarsa, kuma ba su kula da ma'anarsa." Watau suna wahala wajen cfaukar ilmin
da aka dora musu daukarsa amma kuma ba su yin amfani da shi a wajen aikinsu da
mu'amaldlinsu.
(2) Ba a saduwa da Allah sai a bayan mutuwa. Masoyi na gurin saduwa da
masoyinsa, kuma ba zai yi gudun sababin saduwar ba.
852
62 — Suratul Jumu'a
&mi&-v
ambaton Allah, kuma ku bar (1)
ciniki. Wancan dinku ne mafi alheri
a gare ku idan kun kasance kuna
sani.
10. Sa'an nan idan an kare sal-
la, sai ku watsu a cikin kasa kuma
ku nema daga falalar Allah, kuma
ku ambaci sunan Allah da yawa
cfammaninku, ku sami babban
rabo.
11. Kuma idan suka ga wani
fatauci ko kuma wani wasan shaga-
la, sai su yi ruguguwar fita zuwa
gare su, kuma su bar ka kana tsaye.
Ka ce, "A bin da yake a wurin Allah
ne mafi alheri daga fataucin, alhali
kuwa Allah ne Mafi alherin masu
arzutawa."
^ •*
. »vM -X > .-.f X> < / ♦?
,>£-? *
(1) Ba a hana Musulmi aiki ba a kowace rana, sai dai an hana duk wanda Jumu'a ta
lazimta a kansa da ya yi wani aiki wanda ba na tattalin salla ba a ranar Jumma'a, a bayan
kiran salla. Ana nufi da kiran salla na biyu a bayan limami ya zauna a kan mumbarinsa,
domin wannan kiran aka sani a zamanin Annabi da Abubakar da Umar. Amma kira na
farko, Usman bn Affan ne ya fara shi domin farkar da mutane, a bayan sun yi yawa kuma
sun kama sana'o'i. Kuma a bayan an kare salla, sai a watse zuwa ga ayyuka da neman
abinci. Ba a tsayawa yin wata nafila a bayan sallar Jumu'a, sai dai an so yin raka'a biyu a
bayan fita daga masallaci kamar yadda Annabi ke yi.
A farko, ana yin hudubar sallar Jumma'a a bayan salla har a lokacin da ayarin
Duhayyah el Kalbi ya komo daga Sham (Syria) da abinci, ya sauka a Baki'a, suka buga
ganga, sai Sahabbai suka fita domin neman sayen abincin a gabanin a kare hudubar suka
bar mutum goma sha biyu tare da Annabi. Sai aka mayar da hudubar a gabanin salla.
Kuma an fahimci cewa ana yin huduba a tsaye. Kuma ba a kafa Jumu'a, sai a kafaffen gari,
amma Jumu'a na kulluwa da mutum goma sha biyu da Liman.
853
63 — Suratul Munafikun
mm&-v
Tana karantar da halayen munafukan MadTna a zamanin
Annabi da wa'azi ga barin yin hali irin nasu.
** j* s . *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Idan munafukai (1) suka je
maka suka ce, "Muna shaidar lalle
kai, haklka Manzon Allah ne,"
kuma Allah Yana sane da lalle kai,
haklka ManzonSa ne, Kuma Allah
Yana shaida lalle munafukan, hakl-
ka, makaryata ne.
2. Sun riki rantsuwowinsu
garkuwa, sai suka taushe daga ta-
farkin Allah. Lalle su, abin da suka
kasance suna aikatawa ya munana.
3. Wancan, domin lalle su, sun yi
Tmani, sa'an nan kuma suka kafirta,
sai aka yunke a kan zukatansu.
Saboda su, ba su fahimta.
4. Kuma idan ka gan su, sai jiku-
nansu su ba ka sha'awa, kuma idan
sun farfa, (2) za ka saurara ga maga-
narsu. Kamar dai su kyami ne wan-
(1) Munafuki, a zamanin Annabi, shi ne wanda ya yi kalmar shahada, ya bayyana
Musulunci, amma kuma a 66ye, shi kaflri ne. A bayan Annabi ana ce wa munafuki zindTki.
(2) Munafukai suna da kyaun surar jiki kuma sun iya magana da fasaha amma fa ba
su da hankali saboda karyar da suke a kanta, saboda haka suna tsoron kowane irin motsi
ya zama a kansu.
854
63 — Suratul MunaMiin
mm&-vr
da aka jingine. Suna zaton kowace
tsawa a kansu take. Su ne makiyan,
sai ka yi saunarsu. Allah Ya la'ane
su. Yaya ake karkatar da su?
5. Kuma idan aka ce musu, "Ku
zo Manzon Allah ya nema maku
gafara," sai su gyacfa kawunan-
su, kuma ka gan su suna kange-
wa, alhali kuwa suna masu girman
kai.
6. Daidai ne a kansu, ka nema
musu gafara ko ba ka nema musu
ba. Faufau Allah ba zai gafarta
musu ba. Lalle Allah, ba zai shiryar
da mutane fasikai ba.
7. Su ne wacfanda ke cewa,
"Kada ku ciyar a kan wanda ke
wurin Manzon Allah har su watse,"
alhali kuwa taskokin sammai da
kasa ga Allah suke, kuma amma
munafukai ba su fahimta.
8. Suna cewa, "Lalle ne idan
mun koma (1) zuwa MadTnar, hakT-
ka mafi rinjaya zai fitar da mafi
kaskanta daga gare ta, alhali kuwa
rinjayar ga Allah take kuma da
ManzonSa, kuma da muminai,
kuma amma munafikai ba su sani
ba.
9. Ya ku wacfanda suka yi Tmani !
Kada dukiyoyinku da cfiyanku su
shagaltar da ku daga ambaton Al-
lah. Kuma wanda ya yi haka, to,
wacfannan su ne masu hasara.
%1>*Y' tL *~ <9 t.Z*A'\» » £' -
as X.'SSs' ~.'>Wf\' .Aft'
(1) Abdullah bn Ubayyi bn Salul ya facfi cewa "Wallahi idan mun koma MadTna
wanda ya fl Rarfi, lalle zai fitar da wanda ya fl ^askanti." Yana nufin Ansarai mutanen
Madina za su kori Muhajirai. Ya fadi haka a cikin wata tafiya ta jihadi. Aka gaya wa
Annabi, sai ya yi musu. Allah Ya kunyata shi.
855
64 — Suratul Tagabun
am\%&-v
10. Kuma ku ciyar daga abin da
Muka arzuta ku daga gabanin mu-
tuwa ta je wa cfayanku har ya ce,
"Ya Ubangijina! Don me ba Ka yi
mini jinkiri ba zuwa ga wani ajali
makusanci domin in gaskata kuma
in kasance daga salihai?"
11. Kuma Allah ba zai jinkirta
wa wani rai ba idan ajalinsa ya je.
Kuma Allah Masani ne ga abin da
suke aikatawa.
Tana karantar da cewa wanda ya shagala da duniya ya bar
addini, ya yi hasara. Addini kuwa shi ne bin umurnin Allah da barin
haninSa ga kome.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Abin da yake a cikin sammai
da wanda yake a cikin kasa suna
tasbihi ga Allah. Gare Shi mulki
yake, kuma gare Shi godiya take.
Kuma Shi, a kan kome, Mai ikon yi
ne.
2. Shi ne Wanda Ya halitta ku.
Sa'an nan daga gare ku akwai kafiri
kuma daga gare ku akwai mumini.
Kuma Allah Mai gani ne ga abin da
kuke aikatawa.
856
64 — Suratul Tagabun
CW\$&-v
3. Ya halitta sammai da kasa da
abin da yake hakkinSa. Kuma Ya
suranta ku, sa'an nan Ya kyautata
surorinku. Kuma zuwa gare Shi
makoma take.
4. Yana sanin abin da ke a cikin
sammai da kasa. Kuma Yana sanin
abin da kuke Boyewa da abin da
kuke bayyanawa. Kuma Allah Ma-
sani ne ga abin da ke cikin kiraza.
5. Shin, babban labari bai je
muku ba na wadanda suka kafirta
daga gabani, sai suka dandani uku-
bar al'amarinsu kuma suna da wata
azaba mai radacfi?
6. Wancan, saboda lalle su Man-
zanninsu sun kasance suna je musu
da hujjoji bayyanannu, sai suka ce,
"Ashe, wasu mutane za su shiryar
da mu?" Sai suka kafirta kuma
suka juya baya, kuma Allah Ya
wadatu (daga gare su). Kuma Allah
Wadatacce ne, Godadde.
7. Wadanda suka kafirta sun
riya cewa ba za a tayar da su ba.JCa
ce, "Ni, ina rantsuwa da Ubangijlna.
Lalle za a tayar da ku hakTkatan,
sa'an nan kuma lalle ana ba ku
labari game da abin da kuka aikata.
Kuma wannan ga Allah mai sauki
ne."
8. Saboda haka ku yi Tmani da
Allah da ManzonSa da hasken nan
da Muka saukar. Kuma Allah, ga
abin da kuke aikatawa, Mai labar-
tawa ne.
9. A ranar da Yake tattara ku
domin ranar taruwa. Wancan ne
ranar kamunga. Kuma wanda ya yi
Tmani da Allah, kuma ya aikata
^>j4 Qfej ufjj\j vS^U^^s
9 ' *f *" * "t> i * y A y y y * ] y yy
857
64 — Suratul Tagabun
ffl®\%&-M
aikin kwarai, zai kankare masa mu-
nanan ayyukansa, kuma Ya shigar
da shi gidajen Aljanna, koramu
na gudana daga karkashinsu, suna
madawwama a cikinsu har abada.
Wannan ne babban rabo mai girma.
10. Kuma wadanda suka kafirta,
kuma suka karyata game da
ayoyinMu, wadannan su ne 'yan
wuta, suna madawwama a cikinta.
Kuma tir da makoma, ita.
11. Wata maslfa ba za ta samu
ba face da iznin Allah. Kuma wan-
da ya yi Tmani da Allah, Allah zai
shiryar da zuciyarsa. Kuma Allah,
ga dukan kome, Masani ne.
12. Kuma ku yi da'a ga Allah,
kuma ku yi da'a ga Manzo. Sa'an
nan idan kun juya baya, to, abin
sani kawai, akwai iyarwa bay-
yananna a kan ManzonMu.
13. Allah, babu wani abin bauta
wa face Shi. Kuma ga Allah, sai
muminai su dogara.
14. Ya ku wadanda suka yi Tma-
ni ! Lalle ne daga matanku da cfiyan-
ku akwai wani makiyi (1) a gare ku,
sai ku yi saunarsu. Kuma idan kuka
yafe, kuma kuka kau da kai, kuma
kuka gafarta, to, lalle Allah Mai
gafara ne, Mai jin kai.
75. Dukiyoyinku da diyanku fi-
tina (2) dai ne. Kuma Allah, a wurin-
Sa akwai wani sakamako mai girma.
•-*,-.
(1) Makiyi, shi ne mai hana mutumin da yake kiyayya da shi wani alheri ya sadu da
shi. Idan son dukiya ko mata ko cfiya ya hana mutum yin sadaka ko fita zuwa jihadi, to,
dukiyar da matan da cfiyan sun zama makiyansa ke nan.
(2) Fitina, ita ce duk abin da zai cuci mutum ta hanyar da yake amincewa, cutar ta
duniya ce ko ta Lahira. Cutar Lahira ta fi tsanani saboda girman hasarar da ke a cikinta.
858
64 — Suratut Tagabun
om\m-v
16. Sai ku bi Allah da takawa
^wargwadon abin da kuka sami
iko. Kuma ku saurara kuma ku yi
cfa'a, kuma ku ciyar, ya fi zama
alheri gare ku. Kuma wanda ya
saBa wa rowar ransa, to, wacfannan
su ne masu babban rabo.
17. Idan kun bai wa Allah ranee,
ranee mai kyau, (Allah) zai ninka
shi a gare ku kuma Ya gafarta
muku. Kuma Allah Mai yawan go-
diya ne, Mai hakuri.
18. Shi ne Masanin fake da
bayyane, Mabuwayi, Mai hikima.
Tana karantar da hukunce-hukuncen sakin matan aure da
hakkokin da ke ratayuwa ga ma'auran a bayan sakin.
*" J* -^ . **
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
/. Ya kai Annabi! Idan kun saki
mata, sai ku sake su ga iddarsu, (1)
(1) Saki, shi ne warware kullin halaccin saduwa da juna a tsakanin miji da mata.
Hakki ne wanda Allah Ya saka ga hannayen maza ban da mata. Saki ga idda, watau ya
sake ta saki guda a cikin tsarkin da bai shafe ta ba domin saukin idda. Yana haramta ga
mijin da matar ya fitar da ita ko ta fita daga dakinta a lokacin idda. Faruwar wani al'amari
shi ne soyayya a bayan kiyayya da mayarwa a bayan saki. Alfasha a nan, tana nufin facfa
da zage-zage a kan surukanta. Ana fitar da mai iddar saki saboda alfasha daga gidanta.
Akwai saki na sunna kuma akwai na bidi'a, amma saki na sunna cfaya ne, a cikin tsarkin da
ba a shafe ta ba, kuma kada a kara mata wani saki har ta kare idda. Sakin bidi'a kuwa shi
ne uku gaba daya ko a cikin idda guda, a cikin haila ko jinin blki. Sakin bidi'a yana
lazimta. Ana tilasta shi mayarwa ga wadda aka saki a cikin haila idan bai kai uku ba ga miji
'yanfacce, ko biyu ga miji bawa.
859
65 - Suratucf T>alak
&m\$&-v
kuma ku kididdige iddar. Kuma ku
bi Allah Ubangijinku da takawa.
Kada ku fitar da su daga gidajensu,
kuma kada su fita face idan suna
zuwa da wata alfasha bayyananna.
Kuma wacfancan iyakokin Allah
ne. Kuma wanda ya ketare iyako-
kin Allah, to, lalle ya zalunci kansa.
Ba ka sani ba cfammanin Allah zai
fitar da wani al'amari a bayan haka.
2. Sa'an nan idan sun isa ga aja-
linsu (na idda) sai ku rike su da abin
da aka sani ko ku rabu da su da abin
da aka sani kuma ku shaidar da
masu adalci biyu daga gare ku.
Kuma ku tsayar da shaidar domin
Allah. Wancan cfinku ana yin wa'azi
da shi ga wanda ya kasance yana yin
Tmani da Allah da Ranar Lahira.
Kuma wanda ya bi Allah da taka-
wa, Allah zai sanya masa mafita.
3. Kuma Ya arzuta shi daga inda
ba ya zato. Kuma wanda ya dogara
ga Allah, to, Allah ne Ma'ishinsa.
Lalle Allah Mai iyar da umurninSa
ne. Haklka Allah Ya sanya ma'auni
ga dukan kome.
4. Kuma wacfanda suka yanke ( * }
dammani daga haila daga matanku,
idan kun yi shakka, to, iddarsu
wata uku ce da wacfanda ba su yi
'*"'**$'< - ^f
f > fy f m K " •" \ > 9 ^y . > •'
^b-^^c^J?
(1) Muddar idda ga wadda ta yanke cfammanin haila saboda tsufa, watanni uku,
kuma ba za ta kara kome ba a kai. Wadda take akwai shakka a game da ita ga ko akwai
ciki ko babu shi, to, za ta yi iddar wattani uku kuma ta yi jiran watanni tara, watau ta yi
watannin shekara, uku na idda, saura na ta fid da shakka ne. Haka ne hukuncin mai
istihala, watau jinin ciwo. Amma yarinya mai shakkar ciki, sai ta zauna har shakka ta
gushe. Yarinyar da ba ta fara haila ba tana iddar wata uku. Babu bambanci a tsakanin cfiya
da baiwa ga idda da watanni, amma ga idda ta tsarki, to, baiwa tana yin rabin na diya ga
saki da mutuwa.
860
65 - Suratucf T>alak
m3\m~v
haila ba. Kuma ma'abuta cikinna,
ajalinsu, (shi ne) cewa su haifl
cikinnansu. Kuma wanda ya bi Al-
lah da takawa, (Allah) zai sanya
masa wani sauki daga al'amarinsa.
5. Wancan umurnin Allah ne, Ya
saukar da shi zuwa gare ku. Kuma
wanda ya bi Allah da takawa, Allah
zai kankare masa munanan ayyu-
kansa, kuma Ya girmama masa
sakamako.
6. Ku zaunar da su daga inda
kuka zauna (1) daga gwargwadon
samunku. Kuma kada ku cuce su
domin ku kuntata a kansu. Kuma
idan sun kasance ma'abuta ciki, sai
ku ciyar da su har su haifl cikinsu.
Sa'an nan idan sun shayar da mama
saboda ku, sai ku ba su tsadodinsu.
Kuma ku yi shawara a tsakaninku
bisa abin da aka sani. Kuma idan
kun nuna talauci, to, wata mace za
ta shayar da mama saboda shi
(mijin).
7. Sai mawadaci ya ciyar daga
wadatarsa kuma wanda aka kunta-
ta masa arzikinsa, to, sai ya ciyar
daga abin da Allah Ya ba shi. Allah
ba Ya kallafa wa wani rai face abin
da Ya ba shi. Allah zai sanya sauki
a bayan tsanani.
8. Kuma da yawa (2) daga alka-
rya wadda ta yi tsaurin kai daga
3 ^Jj>JLs> jjj 4ji\ ji>L^l^teU^
(1) Mijin zai fita ya bar wa matar da ya saki cfaki ta zauna a cfakinta har ta Rare idda.
Ana ciyar da mai sakin kome, amma ba a ciyar da mai sakin ba'ini sai idan tana da ciki.
Ijarar shayarwa tana a kan uba ga uwar da aka saki saki ba'ini ko ga watarta, bisa ga
yardar sassan biyu.
(2) A bayan da ya gama bayanin saki da hukunce-hukuncen da suka ratayu a gare shi,
sai kuma ya goya gargacfi ga wanda bai bi wadannan hukunce-hukuncen ba, ta hanyar
861
65 - Suratucf T>alak
®m$&-v
barin umurnin Ubangijinta da
ManzanninSa, sai Muka yi mata
hisabi, hisabi mai tsanani, kuma
Muka azabtar da ita, azaba abar
kyama.
9. Sa'an nan ta dandana maslfar
aPamarinta. Kuma karshen al'ama-
rinta ya kasance hasara,
10. Allah Ya yi musu tattalin
wata azaba mai tsanani. Saboda
haka ku bi Allah da takawa, ya
majabuta hankula, wadanda suka
yi Tmani ! Haklka Allah Ya saukar
da wata tunatarwa zuwa gare ku:
77. Manzo, yana karatun
ayoyin Allah bayyanannu a kanku
domin Ya fitar da wacfanda suka yi
imani kuma suka aikata ayyukan
kwarai daga duffai zuwa ga haske.
Kuma wanda ya yi Tmani da Allah
ya aikata aikin kwarai Allah zai
shigar da shi gidajen Aljanna, £o-
ramu na gudana daga karkashinsu,
suna masu dawwama a cikinsu har
abada. Hakika Allah Ya kyauta-
ta (1) masa arziki.
72. Allah, Wanda Ya halitta bak-
wai din sammai kuma daga kasa
kwatankwacinsu, umurninSa yana
ta sauka a tsakaninsu domin ku san
lalle Allah Mai Tkon yi ne a kan
M \J&\%C£)*j\j i ji* bl^>r
tsoratar da shi da cewa Allah Ya halaka alkaryu masu yawa saboda sa6a Masa ga
hukunce-hukuncenSa ga kananan abubuwa, balle mutum guda wanda ya sa6a masa ga
babban al'amari kamar aure da saki wacfanda rayuwar dan Adam ta dogara a kansu.
Kuma ya yi^bushara ga wanda ya b! Shi da takawa, ya fita daga duhun al'adu zuga ga
hasken Shan'arSa, kuma Ya yi wa'adi da ba shi saukin rayuwa daga WadatarSa mai yawa.
(1) Allah Ya kyautata wa wanda ya tsare shan'arsa da kyau, a wajen arzikinsa tun
daga duniya har ya zuwa Lahira, domin Ya ce, "Haklka Allah Ya kyautata masa (mai
tsare shari'ar) arziki" ba da Ya yi kaidin lokaci ko wuri ba.
862
66 — Suratut Tahrim
$m\m-^
dukan kome, kuma lalle Allah, ha-
£i£a Ya kewaye ga dukan kome da
sani.
M IX ^J>o iCJ j£ 3 olj
Tana karantar da yadda ake kyautata zamantakewa da iyali.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
1. Ya kai Annabi ! Don me kake
haramta abin da Allah Ya halatta
maka, (1) kana neman yardar ma-
tanka, alhali kuwa Allah Mai gafa-
ra ne, Mai jin £ai.
2. Haloica Allah ya faralta muku
warware (2) rantsuwoyinku, kuma
*£$*» '*»>' *'v\ <~k
^y^j {^luji ^^y^\j^y^
(1) A cikin littafin Buhari an ruwaito daga A'isha, matar Annabi, cewa Annabi, tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi, yakan ^i jinkiri a wurin Zainab bint Jahash domin
ya sha zuma a wurinta. Ta ce, "Sai na shirya, ni da Hafsah : Duka wadda Manzon Allah ya
shiga a gare ta daga gare mu, ta ce masa, ina jin warin tsimi daga gare ka ! Ka ci tsimi !' To,
sai Annabi ya shiga ga dayansu, ta ce masa, "Ka ci tsimi." Ya ce, "A 'aha! Na sha zuma dai
a wurin Zainab bint Jahash, kuma ba zan koma gare shi ba." Asalin abin, Annabi, tsTra da
amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana zagayawa a gidajen matansa a bayan
sallar la'asar domin ya gaishe su. To, sai ja shiga ga Hafsa a bayan ya shiga ga Zainab, ta
gaya masa haka. Kuma ya gaya mata nisantarsa ga zuman, kuma ya gaya mata labarin
cewa Abubukar da Umar, Allah Ya yarda da su, za su zama halifai a bayansa. To, sai ta
fadi wadannan labaru ga makwabciyarta A'isha. Wannan kissa tana koyar da saukin halin
Annabi a game da iyalinsa, da girmamawarsa a gare su.
(2) An rubuta yadda ake warware rantsuwa da kaffara^wadda aka ambata a cikin
sura ta 5, aya ta 89. Ana kaffarar rantsuwa da ciyar da miskinai goma daga matsakaicin
abinci, mudu biyu ga kowane, ko tufatar da su tufar da za ta ishe su salla, idan bai samu
ba, ya yi azumin kwana uku.
863
66 — Suratut Tahrim
WZ&WfcA
£^M£-T\
Allah ne Mataimakinku kuma Shi
ne Masani, Mai hikima.
3. Kuma a sa'ilin da Annabi ya
asirta wani labari zuwa ga sashen
matansa, to, a lokacin da ta ba da
labari da shi. Kuma Allah Ya
bayyana shi a gare shi, ya sanar da
sashensa kuma ya kau da kai daga
wani sashe. To, a lokacin da ya ba ta
labari da shi, ta ce, "Wane ne ya
gaya maka wannan?" Ya ce, "Ma-
sani, Mai labartawa, Ya gaya
mini."
4. Idan ku bijm kuka tuba zuwa
ga Allah, to, hakika zukatanku sun
karkata. Kuma idan kun taimaki
juna a kansa, to, lalle Allah Shi ne
Mataimakinsa, da Jibirilu da sali-
han muminai. Kuma mala'iku, a
bayan wancan, mataimaka ne.
5. Mai yiwuwa ne Ubangijinsa,
idan ya sake ku, Ya musanya masa
wacfansu matan aure mafiya alheri
daga gare ku, Musulmai, muminai,
masu tawali'u, masu tuba, masu
ibada, masu azumi, zawarori
da'yammata.
6. Ya ku wadanda suka yi Imani !
Ku kare wa kanku (1) da iyalinku
wata wuta makamashinta mutane
da duwatsu ne. A kanta akwai wa-
cfansu mala'iku masu kauri, masu
karfi. Ba su sa6a wa Allah ga abin
da Ya umurce su, kuma suna aikata
abin da ake umurnin su.
r<J^il3ir
\y>j
I^Jbl^cJlL*
• > < Tf >
ajojijLja
v#x *''<''
<' *' <' *'x' * {' % £*"?
(1) Tsare kai da iyali daga wuta yana samuwa da shiryar da su da karatu da nasiha a
kan addini. Wannan yana a cikin kyaun zamantakewa wanda surar ke karantarwa.
864
66 — Suratut Tahrim
lIU^-^
7. Ya ku wacfanda suka
kafirta (1) ! Kada ku kawo wani uzu-
ri a yau. Ana yi muku sakamakon
abin da kuka kasance kuna aikata-
wa kawai ne.
8. Ya ku wadanda suka yi imani !
Ku koma zuwa ga Allah komawar
gaskiya. Mai yiwuwa Ubangijinku
Ya kankare muku miyagun ayyu-
kanku kuma Ya shigar da ku a
gidajen Aljanna, koramu na gu-
dana daga karkashinsu a ranar da
Allah ba Ya kunyatar^da Annabi (2)
da wadanda suka yi imani tare da
shi. Haskensu yana tafiya a gaba
gare su da jihohin damansu, suna
cewa, "Ya Ubangijinmu! Ka cika
mana haskenmu, kuma Ka yi mana
gafara. Lalle Kai, a kan dukan
kdme, Mai ikon yi ne."
9. Ya kai Annabi ! Ka yaki kafi-
rai da munafikai. Kuma ka tsanan-
ta a kansu. Kuma matattararsu
Jahannama ce, kuma tir da mako
ma, ita.
10. Allah Ya buga wani misali
domin wacfanda suka kafirta (3) :
matar Nuhu da matar Lucfu, sun
»i ^ •
(1) Kafirai a nan, kafircinsu saboda kin bin umurnin Allah game da kyaun
zamantakewa da iyali yake. Laifinsu ya fi sauran laifuffuka domin yana sabbaba yamutsi a
gida T har abin ya shall zurriya da kasa gaba daya.
(2) Allah Ya yi alkawarin ba zai kunyatar da AnnabinSa ba, haka kuma wadanda
suka yi Imani tare da shi, watau Sahabbansa a Ranar Kiyama. Wannan shine dalllin da ya
sa Allah Ya tsare Annabi da Sahabbansa daga a bauta musu kamar yadda aka bauta wa
wadansu Annabawa da salihai wadanda Allah zai tambaye su ko su ne suka yi umurni da a
yi musu bautar, su kuma su fadi barrantarsu daga wadanda suka bauta musu.
(3) Wadannan misalai biyu, matar Nuhu da matar Ludu suna nuna kusanci ga salihai
ba ya isa ga addini sai kowa ya yi abin da Allah Ya yi umurni da shi. Kuma ana kallafa wa
mata da su kiyaye kyaun zamantakewa da mazansu. Kuma ana yi musu azaba saboda sa6a
wa Allah ga barin haka kamar yadda ake ga mazansu.
865
66 — Suratut Tahrim
&^M-Tl
kasance a karkashin wasu bayi
biyu daga BayinMu salihai, sai
suka yaudare su, saboda haka ba
su wadatar musu da kome daga
Allah ba. Kuma aka ce, "Ku shiga,
ku biyu, wuta tare da masu shiga."
77. Kuma Allah Ya buga wani
misali domin warfanda suka yilma-
ni : matar Fir'auna, (1) sa'ad da ta ce,
"Ya Ubangiji! Ka gina mini wani
gida a wurinKa a cikin Aljanna.
Kuma Ka tsirar da ni daga Fir'auna
da aikinsa. Kuma Ka tsirar da ni
daga mutanen nan azzalumai."
12. Da Maryama (2) cfiyar Imra-
na wadda ta tsare farjinta, sai Muka
hura a cikinsa daga RuhinMu.
Kuma ta gaskata game da ayoyin
Ubangijinta da LittattafanSa alhali
kuwa ta kasance daga masu tawa-
li'u.
^fe^^l^^U^^i
'\'*>\\>"'\''
^8^ ->v w ^ -^ -"> -^
(1) Wannan yana nuna cewa kusantar kafiri ba zai cuci muminai ba. Sai dai Allah Ya
hana aure a tsakanin Musulma da kafiri.
(2) Wannan yana nuna cewa rashin aure ga matar da ke iya tsare farjinta daga alfasha
kuma ta tsare addininta da ta£awa, ba zai cuce ta ba ga samun rahamar Allah a duniya da
Lahira.
866
67 - Suratul Mulk
mm-™
Tana karantar da tauhldi da kadaitar Allah ga mulki da
halittawa da ni'imtawa da cikakken iko wanda yake tare da rahama
da tausayi.
ANA SON KARATUNTA DARE DUKA DA KUMA HARD ACE TA DA KA.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. (Allah), Wanda gudanar da
mulki yake ga hannunSa (TkonSa),
Ya tsarkaka, kuma Shi Mai Tko ne a
kan kome.
2. Shi ne Wanda Ya halitta mu-
tuwa da rayuwa domin Ya jarraba
ku, Ya nuna waye daga cikinku ya fi
kyawon aiki, Shi ne Mabuwayi,
Mai gafara.
3. Shi ne Wanda Ya halitta sam-
mai bakawi, dabakoki a kan juna,
ba za ka ga goggociya ba a cikin
halittar (Allah) Mai rahama. Ka
sake dubawa, ko za ka ga wata
Baraka?
4. Sa'an nan ka sake maimaita,
dubawa, ganinka zai komo maka,
gajiyayye, ba da ganin wata nakasa
ba.
J. Kuma lalle Mun kawata sa-
mar farko da fitillu, kuma Muka
l &£^$&\&&$\'&$
y*y ''\' <*<*
\z+* 1^X1 \ tib \CJ&t $£/^&^f
m<,s •'<,
t&^jy^tiftiZtivj,^
867
67 - Suratul Mulk
OIBIi^-iv
sanya su abin jifa ga shaidanu,
kuma Muka yi musu tattalin aza-
bar Sa'Tr.
6. Kuma wadanda suka kafirce
wa Ubangijinsu na da azabar Ja-
hannama, ta munana ga zamanta
makdmarsu.
7. Idan an jefa su a cikinta, sai su
ji daga gare ta wata kara, tana
tafasa.
8. Tana kusa ta tsage domin hus-
hi, ko da yaushe aka jefa wani
6angaren jama'a a cikinta, matsa-
ranta na tambayar su da cewa,
"Wani mai gargacfi bai je muku
ba?"
9. Sai su ce, "I, lalle wani mai
gargadi ya je mana, sai muka £a-
ryata shi, muka ce, 'Allah bai sau-
kar da kome ba, ba ku cikin kome
sai 6ata babba'".
10. Kuma suka ce, "Da mun
zamo muna saurare, ko muna da
hankali^da ba mu kasance a cikin
'yan sa'Tr ba.".
11. Wato su yi ikrari da laifinsu.
Allah Ya la'ani 'yan sa'Tr!
12. Lalle wadanda ke tsoron
Ubangijinsu, a 6oye, suna da wata
gafara da wani sakamako mai-
girma.
13. Kuma ku asirta maganarku
ko ku bayyana ta, lalle Shi, (Allah),
Masani ne ga abin da ke cikin
kiraza.
14. Ashe, Wanda Ya yi halitta ba
zai iya saninta ba, alhali kuwa Shi
Mai tausasawa ne, kuma Mai
labartawa?
ptf&^a^&M
****4*M-
'.'?'.*'*'<+<<'*. 's *Zs *' 'sihs
;2^Ai'lfc~J&\&'
>£ ( l^Jli^IiLSjJly v^
foj&$&
(g&?^^^£f£tf
868
67 - Suratul Mulk
mm-™
15. Shi, (Allah), Ya sanya muku
kasa horarriya, sai ku tafi cikin
sasanninta, kuma ku ci daga arzi-
kinSa, kuma zuwa gare Shi ne tashin
yake.
16. Shin ko kun amince cewa
Wanda ke cikin sama, ba zai iya
shafe kasa tare da ku ba, sai ga
ta tana mai girgiza?
17. K6 kun amince cewa Wanda
ke cikin sama ba zai iya sako muku
iskar guguwa ba? To, za ku san
yadda (akibar) gargadiNa take.
18. Lalle, wadanda ke gabansu
sun karyata (manzanni). To, yaya
(akibar) gargadiNa ta kasance?
19. Ba za su yi dubi ba zuwa ga
tsuntsaye a kansu, masu sanwa,
kuma suna fiffikawa, babu mai rike
da su sai (Allah), Mai rahama? Lalle
Shi Mai gani ne ga dukan kome.
20. Wane ne wanda zai zame
muku mayakin da zai taimake ku,
wanda ba (Allah) ba, Mai rahama?
Kafirai ba su a cikin kome face
rutfu.
21. Wane ne wanda zai ciyar da
ku, idan (Allah) Ya like arzikinSa?
A'aha, sun yi zurfi cikin girman kai
da tashin hankali.
22. Shin wanda ke tafiya a kife a
kan fuskarsa ya fi zama a kan shi-
ryuwa, ko kuwa wanda ke tafiya
mike a kan hanya madaidaiciya?
23. Kace, "(Allah) Shine Wanda
Ya kaga halittarku, Ya sanya muku
ji da gani da tunani, amman katfan
ce kwarai godiyarku!"
[>&\g&^cA&^&4
^ Jj^^l^^JJOtl
ll«-^wix^j-u^o^ <^^\<Jo*fj^{
^j&^oo J&*4^o*iJ$<^&^j
869
67 - Suratul Mulk
mm-™
24. Kuma ka ce, "Shi ne Ya halit-
ta ku daga kasa, kuma zuwa gare
Shi ne ake tashe ku."
25. Kuma suna cewa, "Yaushe
ne wannan alkawarin zai tabbata,
in dai kun kasance masu gaskiya ne
ku?"
26. Ka ce, "Ilmin a wurin Allah
kawai yake, kuma ni mai gargacfi
kawai ne, mai bayyana (gargadin)."
27. To, lokacin da suka gan ta
(azabar) a kusa, fuskokin wadanda
suka kafirta suka munana, kuma
aka ce (musu) wannan shi ne abin
da kuka zamo kuna karyatawa.
28. Ka ce musu, "Idan Allah Ya
halaka ni, nlda wanda ke tare da ni,
ko kuma Ya yi mana rahama, to,
wane ne zai tserar da kafirai daga
wata azaba mai racfacfi?"
29. Ka ce, "Shi ne Mai rahama,
mun yi imani da Shi, gare Shi muka
dogara, saboda haka za ku san
wanda yake a cikin 6ata
bayyananniya."
30. Ka ce, "Ko kun gani, idan
ruwanku ya wayi gari fakakke, to,
wane ne zai zo muku da ruwa wani
mai 6u66uga?" (1)
(1) Ana so idan mai karatu ya kai £arshen wannan sura ya ce ^UJI <^j 4)1 wato
Allah Ubagijin halitta. An karanta wannan aya a gaban wani kafiri, sai ya ce za mu fito da
ruwan game da amfani da dundurusai da faretani, sai ruwan idanunsa ya fa£e.
870
68 — Suratul Kalam
^feSIM-lA
Tana yi wa Annabi bushara da cewa mutanensa na Makka za
su shiga Musulunci, su yi nadama a kan aikinsu na kafirci da cutar
da suka yi masa, kuma Allah zai kar6i tubarsu,
* J» s * s -*
;)\-&w
} J^
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
/. N. Na rantse da alkalami da
abin da (marubuta) suke rubutawa.
2. Kai, saboda ni'imar Ubangi-
jinka, ba mahaukaci kake ba.
3. Kuma, lalle, hakika kana da
ladar da ba ta yankewa.
4. Kuma, lalle, hakika kana a
kan halayen kirki, manya.
5. Don haka, za ka gani, su
kuma za su gani.
6. Ga wanenku hauka take.
7. Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi
sani ga wanda ya Bace daga tafar-
kinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga
masu shiryuwa.
8. Saboda haka kada ka bi masu
karyatawa.
9. Suna fatar ka sassauta, su
kuma su sassauta.
10. Kada ka bi dukan mai yawan
rantsuwa, walakantacce.
11. Mai zunde, mai yawo da
gulma.
> , ^ <* ' m ,
871
68 - Suratul Kalam
wJS?!li^-iA
12. Mai hana alheri, mai zalunci,
mai zunubi.
13. Mai girman kai, bayan haka
kuma laTmi (ba ya son alheri).
14. Saboda ya kasance mai du-
kiya da cfiya.
15. Idan ana karanta masa
ayoyinMu, sai ya ce, "Tatsuniyoyin
mutanen farko ne."
16. Za Mu yi masa alama a kan
hand.
17. Lalle Mun jarrabe su kamar
yadda Muka jarrabi masu gonar
lambu, a lokacin da suka yi rantsu-
wa, wai lalle za su girbe amfaninta,
suna masu asubanci.
18. Kuma (suka yi niyya), ba su
ko togewa.
19. Wani mai kewayawa daga
Ubangijinka ya kewaya a kanta, (ya
kone ta,) alhali suna barci.
20. Sai ta wayi gari (baka kirin)
kamar dare.
21. Sai suka kirayi juna, suna
masu yin asubanci.
22. Cewa ku yi sammako ga am-
fanin gonarku, idan kun kasance
masu girbewa.
23. Sai suka tafi, suna shawara a
Boye (suna cewa).
24. "Lalle kada wani miskini ya
shigar muku ita a yau!"
25. Kuma suka yi sammako a kan
(niyyar) rowa, matukar iyawarsu.
26. Lokacin da suka gan ta, sai
suka ce, "Lalle, mun saki hanya
(mun 6ace)!
*P '^y^jte &jJ^]^&<^&
(jp o^4>ib pjj 1 l^lt jb Vol
872
68 - Suratul Kalam
L$&$\%&-\*
27. "Ba haka ba, mu dai, an
hana mu ne."
28. Mafificinsu (hankali) ya ce ?
"Ban gaya muku ba, ya kamata ku
tsarkake Allah?"
29. Suka ce, "Tsarki ya tabbata
ga Ubangijinmu ! Lalle, mu mun
kasance azzalumai."
30. Sai suka fuskanci juna, suna
zargin kansu.
31. Suka ce, "Kaitonmu! Lalle,
mu ne muka kasance masu ketare
iyaka.
32. "Mai yiwuwa ne Ubangijin-
mu Ya musanya mana da wani abu
da ya fi ta. Lalle, mu (ba mu yanke
kauna ba) zuwa ga Ubangijinmu,
masu kwacfayi ne".
33. Haka dai azabar (1) take,
kuma lalle ne, azabar Lahira ta fi
girma, in da sun kasance za su iya
ganewa.
34. Lalle ne, masu takawa na da,
a wurin Ubangijinsu, gidajen Al-
janna na ni'ima.
35. Shin ko za Mu sanya wadan-
da ke bi da cfa'a kamar masu laifi ?
36. Me ya same ku, yaya kuke
yin hukunci (da haka)?
37. Ko kuna da wani littafi, wan-
da a cikinsa, kuke karantawa?
38. Cewa kuna da, a cikinsa lalle
(duk) abin da rayukanku suka za6a ?
$s^vj|3iyi^j1jii
Pvl^e^j^^ipli
tp ^S&J^&fr^. cM^
l$Q$i
$oj£#l^^
O0^J>x)U
>+'- " i-"*
^Sjj^li^Joi
(1) Irin wannan azaba ce za a yi wa Kuraishawa, dangin Annabi, kamar yadda aka yi
wa masu gonar lambu, wato da suka tuba aka musanya musu da abin da ya fi abin da suka
saba samu. Wato an gaya wa Annabi ne lokacin da danginsa suka kangare, suka £i shiga
Musulunci, aka yi musu azabar fari, da rashin ruwa shekara bakwai, Allah Ya gaya masa
cewa, za su musulunta, alheri ya koma musu. Ya kuwa koma, kamar yadda Allah Ya yi
alkawari.
873
68 - Suratul Kalam
i4S5lj^-iA
39. Ko kuna (rike) da wasu
rantsuwoyin alkawari a kanMu,
har ya zuwa Ranar Kiyama, cewa
lalle ne kuna da abin da kuke hu-
kunta wa kanku?
40. Ka tambaye su, wane, a ci-
kinsu, ke lamuncewa ga samun wan-
nan (hukuncin)?
41. Ko suna da abokan tarewa
(ga wannan ra'ayi)? To, sai su kawo
abokan tarayyarsu, idan sun kasan-
ce masu gaskiya.
42. Ranar da za a kuranye kwa-
bri, kuma a kira su zuwa ga yin
sujuda, sai ba za su iyawa ba.
43. Su fito da idanu kaskantat-
tu, wulakanci yana rufe su. Lalle ne
a da, sun kasance ana kiran su
zuwa yin sujudar, alhali kuwa suna
lafiya lau, (suka ki yi).
44. Saboda haka, ka bar Ni da
mai karyata wannan labari (Alku-
r'ani). Za Mu yi musu istidraji daga
inda ba su sani ba.
45. Ina jinkirta musu, lalle kai-
diNa mai karfi ne.
46. Ko kana tambayar su wata
la'ada ne, saboda haka su, daga
wannan tarar, suke jin an nauyaya
musu?
47. Ko kuma suna da ilmin gai-
bu ne, wato suna yin rubutun (abin
da suke facfa daga gare shi) ne?
48. Saboda haka, ka yi hakuri
da hukuncin Ubangijinka, kada ka
zama kamar Ma'abucin kTfi, a loka-
cin da ya yi kira, alhali yana cike da
hushi.
&o£*U;S&l
tMj*^j*4fe^S>W&ffl
M(J
»4^
4 >^*.
874
68 - Suratul Kalam
w^Uii^-iA
49. Ba domin ni'ima daga wajen
Ubangijinsa ta riske shi ba, lalle ne
da an jefa shi a cikin wofintacciyar
kasa, alhali yana abin zargi.
50. Sai Ubangijinsa Ya zabe shi,
sa'an nan Ya sanya shi a cikin
mutanen kirki.
51. Kuma lalle ne wacfanda suka
kafirta suna yin kamar su kayar da
kai saboda kallonsu (kallon mama-
ki), a lokacin da suke jin karatun
Alkur'ani, kuma suna cewa, "Lalle
ne shi mahaukaci ne!"
52. Shi (Alkur'ani) bai kasance
ba, face abin tunatarwa ne ga duka
duniya.
^*k" \<\\' <"'. *Z'>'<*1Z
^uJ^^^J^l^j
Tana bayanin kiran gaskiya zuwa ga Allah, Shi kacfai ne ga
sifofinSa da ikonSa, babu mai tsoma baki a cikin ikonSa.
>«i
'-£-
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Kiran gaskiya!
2. Mene ne kiran gaskiya?
3. Kuma me ya sanar da kai abin
da ake cewa kiran gaskiya?
4. Samudawa da Adawa sun ka-
ryatar da kiran gaskiya mai dukar
zuciya !
GSSOJ
UJ Af^LlJb jlfrj Jj^JC- JO
875
69 - Suratul Haicica
mm-*
5. To, amma Samudawa, to, an
halaka su da tsawa mai tsanani.
6. Kuma amma Adawa, to, an
halaka su da wata iska mai tsana-
nin sauti wadda ta ketare haddi.
7. (Allah) Ya hore ta a kansu, a
cikin dare bakwai da yini takwas,
biye da juna, saboda haka, kana
ganin mutane a cikinta kwance.
Kamar su kiraruwan dabino ne,
wacfanda suka facfi.
8. To, ko kana ganin abin da ya
yi saura daga cikinsu?
9. Kuma Fir'auna ya zo da
wacfanda ke gabaninsa, da wacfan-
nan da aka kife kasarsu, saboda laifi.
10. Domin sun saba wa manzon
Ubangijinsu, saboda haka ya kama
su da wani irin kamu mai karuwar
(tsanani).
11. Lalle ne Mu, a lokacin da
ruwa ya ketare haddi, Mun cfauke
ku a cikin jirgin ruwan nan.
12. Domin Mu sanya shi, gare
ku, abin tunawa, kuma wani kunne
mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
13. To, idan an yi busa a cikin
kaho, busa cfaya.
14. Kuma aka cfauki kasa da
duwatsu, kuma aka nika su nikawa
cfaya.
15. A ran nan, mai aukuwa za ta
auku.
16. Kuma sama za ta tsage, do-
min ita a ran nan, mai rauni ce.
17. Kuma mala'iku (su bayya-
na) a kan sasanninta, kuma wasu
Uii&t I^diu S£Si3i
876
69 - Suratul Ha££a
$&$&-*
(mala'iku) takwas na cfauke da
Al'arshin Ubangijinka, a sama da
su, a wannan ranar.
18. A ranar nan za a bijira ku
(domin hisabi), babu wani rai, mai
6oyewa, daga cikinku, wanda zai
iya boyewa.
19. To, amma wanda aka bai wa
littafinsa a damansa, sai ya ce wa
(makusantansa), "Ku karba, ku
karanta littafina.
20. "Lalle ne ni, na tabbata cewa
ni mai haduwa da hisabina ne."
21. Saboda haka, shi yana cikin
wata rayuwa yardadda.
22. A cikin Aljanna macfauka-
kiya.
23. Nunannun 'ya'yan itacenta
makusanta ne (ga mai son cfiba).
24. (Ana ce musu) "Ku ci, kuma
ku sha a cikin ni'ima, saboda abin
da kuka gabatar a cikin kwanukan
da suka shige."
25. Kuma wanda aka bai wa
littafinsa ga hagunsa, sai ya ce,
"Kaitona, ba a kawo mini littafina
ba!
26. "Kuma ban san abin da (ke
sakamakon) hisabina ba!
27. "In da dai ita, ta kasance mai
halaka ni gaba cfaya ce!
28. "Dukiyata ba ta wadatar da
ni ba!
29. "Tkona ya Bace mini!"
30. (Sai a ce wa mala'iku) "Ku
kama shi, sa'an nan ku sanya shi a
cikin kukumi.
^ "i . s"
6j*X. :
EJ XjI^. c^^js oiltji
RJi^fo
• or
>^b3-^*S4j^
EJ i_JL
y+ rr . »**
||p<uxikL-J^v*lU
877
69 - Suratul Ha££a
\%mm-*
31. "Sa'an nan, a cikin JahTm,
ku kona shi.
32. "Sa'an nan, a cikin sarka, tsa-
wonta zira'i saba'in, sai ku sanya shi.
33. ^Lalle ne shi ya kasance ba
ya yin Tmani da Allah, Mai girma !
34. "Kuma ba ya kwacfaitarwa
ga (bayar da) abincin matalauci!
35. "Saboda haka, a yau, a nan,
ba ya da masoyi.
36. "Kuma babu wani abinci, sai
daga (itacen) gislTn.
37. "Babu mai cin sa sai masu
ganganci."
38. To, ba sai Na yi rantsuwa da
abin da kuke iya gani ba,
39. Da abin da ba ku iya gani.
40. Lalle ne, shi (Alkur'ani) tab-
bas maganar wani manzo (Jibirilu)
mai daraja ne.
41. Kuma shi ba maganar wani
mawaki ba ne. Kadan kwarai za ku
gaskata.
42. Kuma ba maganar boka ba
ne. Kadan kwarai za ku iya tunawa.
43. Abin saukarwa ne daga
Ubangijin halitta duka.
44. Kuma da (Muhammadu) ya
facfi wata magana, ya jingina ta gare
Mu.
45. Da Mun kama shi da dama.
46. Sa'an nan, lalle ne, da Mun
katse masa laka.
47. Kuma daga cikinku babu
wasu masu iya kare (azabarMu)
daga gare shi.
&3 oysJL-ldtyS byLyuk^C-j* QJ^f&j*
.;»*.
'< i'
878
70 - Suratul Ma'arij
- V-
48. Kuma lalle ne shi (Alkur'ani)
tunatarwa ce ga masu takawa.
49. Kuma lalle ne Mu, wallahi,
Muna sane da cewa daga cikinku
akwai masu karyatawa.
50. Kuma lalle ne shi (Alkurani)
wallahi bakin ciki ne ga kafirai.
51. Kuma lalle ne shi gaskiya ce
ta yakini.
52. Saboda haka, ka tsarkake
sunan Ubangijinka, Mai girma.
Qpoj? jSsJfJ^J^O«>«y U]j
^^vr^r
Mu^»«3>tl4ji
»u
* <-• jf ,+*":
Q*J ^-JiJ li£i>j^J*b»c r «<£
Tana bayanin saukar azaba ga kafirai, babu makawa, kuma
tana bayanin cutar rai da maganin cutar.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Wani mai tambaya ya yi tam-
baya game da azaba, mai aukuwa.
2. Ga kafirai, ba ta da mai tun-
kudewa.
3. Daga Allah Mai matakala.
4. Mala'iku da Ruhi (Jibrila)
suna takawa zuwa gare Shi, a cikin
yini wanda gwargwadonsa, shekara
dubu hamsin ne.
5. Saboda haka, ka yi hakuri,
hakuri mai kyawo.
i^f^r-
^^ 4X^ vJu lOUj^j oj\ JUu
879
70 — Suratul Ma'arij
a^B^-v-
6. Lalle ne su, suna ganin ta mai
msa.
7. Kuma Mu, Muna ganin ta a
kusa.
#. Ranar da sama za ta kasance
kamar narkakkar azurfa.
9. Kuma duwatsu su zama ka-
mar sa&in sufi.
10. Kuma aboki ba ya tambayar
inda wani aboki yake.
1 1 . Ana sanya su, su ga juna, mai
laifi na gurin da zai iya yin fansa,
daga azabar ranar nan, da cfiyansa,
12. Da matarsa da cfan'uwansa.
13. Da danginsa, masu tattara
shi.
14. Da wanda ke a cikin duniya
duka gaba daya, sa'an nan fansar,
ta tsTrar da shi.
15. A'aha! Lalle ne fa, ita ce
Laza,
16. Mai twale fatar goshi.
17. Tana kiran wanda ya juya
baya (daga addini) kuma ya kau da
kai.
18. Ya tara (dukiya), kuma ya
sanya ta a cikin jaka.
19. Lalle ne mutum an halitta shi
mai ciwon kwadayi.
20. Idan sharri ya shafe shi, ya
kasa hakuri.
21. Kuma idan alheri ya shafe
shi, ya yi rowa.
22. Sai masu yin salla,
' f »" *y*
3 ol^ vSQ^oj^j
880
70 — Suratul Ma'arij
6»%£-v.
23. Wacfanda suke, a kan sallar-
su, su, masu dawwama ne.
24. Kuma wacfanda, a cikinduki-
yarsu, akwai wani hakki sananne.
25. Ga (matalauci) mai roko da
wanda aka hana wa rokon.
26. Da wacfannan da ke gaskata
ranar sakamako.
27. Da wacfannan, saboda aza-
bar Ubangijinsu, suna jin tsoro.
28. Lalle ne, azabar Ubangijinsu
ba wadda ake iya amincewa ba ce.
29. Da wacfanda suke, ga farjo-
jinsu, masu tsarewa ne.
30. Sai fa a kan matan aurensu
da abin da hannayensu na dama
suka mallaka. To, lalle ne su kam, ba
wacfanda ake zargi ba ne.
31. To, duk wanda ya nemi abin
da yake a bayan wannan, to, wa-
dancan su ne masu ketare iyaka.
32. Kuma da wadannan da suke,
ga amanoninsu da alkawarinsu,
masu tsarewa ne.
33. Kuma da wadanda suke, ga
shaidarsu, masu dagewa ne.
34. Kuma wacfanda suke, a kan
sallarsu, masu tsarewa ne.
35. Wadannan, a cikin gidajen
Aljanna, wacfanda ake girmamawa
ne.
36. Me ya sami wadanda suka
kafirta, a wajenka, suna gaugawar
(gudu).
<v»>^ *f
<£$* " k f *s 't*s*' ?L's
U*Jt'<
* *£ *' <<'•+*' \f'
^OjA^^J^J&{£f{£A\j
>v>*r » „^ '
IJ^Oi
p oy UjAPp^-j »-> l -*£oj.
' r. ' » »» >^ ^
®te\$tf$$fe&&&
881
70 — Suratul Ma'arij
- Y-
37. Daga barin jihar dama,
kuma daga barin jihar hagu,
jama'a-jama'a!
38. Shin kowane mutum daga
cikinsu yana neman a shigar da shi a
Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki
ba)?
39. A'aha! Lalle Mu, Mun halit-
ta su, daga abin da suka sani.
40. Saboda haka ba sai Na yi
rantsuwa da Ubangijin wuraren 6ul-
lowar rana da wuraren faduwarta
ba, lalle Mu, Masu iyawa ne.
41. Ga Mu musanya wadanda
suke mafi alheri, daga gare su.
Kuma ba Mu kasance wadanda ake
rinjaya ba.
42. Saboda haka, ka bar su, su
dulmuya, kuma su yi wasa, har su
hadu da ranarsu wadda ake yi
musu alkawari (da ita).
43. Ranar da suke fitowa daga
kaburbura da gaugawa, kamar su,
zuwa ga wata kafaffiyar (tuta),
suke yin gaugawa.
44. Maicaskanta ga idanunsu,
wani walakanci yana rufe su. Wan-
nan shi ne yinin da suka kasance
anan yi musa alkawari (a kansa.)
'* + SS »*
^S^JlP^Jc^^
' 'S.S 'S *> ■
r- ~ *\t> *'\A
> '"ItZ 'A"
pc^xal &yjilljj^!^pJi'S&
Epuji^r^ kJ^J T^i^J^o'd^
^^^^Ak^^j^^^aA^a:
Sp djJ&y\yo
882
71 - Suratu Nuh
M&A
- VN
Tana karantar da yadda Annabi Nuhu ya yi gargacfi ga
mutanensa har suka kai ga ya yi addu'a, suka halaka.
* j* s . * s *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Lalle ne Mun aiki Nuhu zuwa
ga mutanensa, cewa ka yi gargacfi
ga mutanenka gabanin wata azaba
mai racfacfi ta zo musu.
2. Ya ce, "Ya mutanena, ni, a
gare ku, mai gargacfi ne, mai bayya-
nawa.
3. "Cewa ku bauta wa Allah, ku
ji tsoronSa, kuma ku bi ni.
4. "Allah zai gafarta muku daga
zunubanku, kuma Ya jinkirta muku
zuwa ga ajalin da aka ambata. Lalle
ne ajalin Allah idan ya zo, ba za a
jinkirta shi ba, da kun kasance ma-
sana (ga abin da nake fada, da kun
bar kafirci)."
5. (Nuhu) ya ce, "Ya Uban-
gijina! Lalle ne, na kirayi mutane-
na, a cikin dare da yini.
6. "To, amma kirana bai kare su
ba sai da gudu (daga gare ni).
7. "Kumalalleneni,kodayaushe
na kiraye su domin Ka gafarta
3js^^j4y &$\& k
883
71 - Suratu Nuh
&- V>
musu, sai su sanya yatsunsu a cikin
kunnuwansu, su lullu5e da tufa-
finsu, su doge ga yin laifi. Sun yi
girman kai iyakar girman kai.
8. "Sa'an nan lalle ne ni, na kira
su, a bayyane.
9. "Sa'an nan lalle ne na yi yeku-
wa saboda su, kuma na gana da su a
cikin asm.
10. "Shi na ce, 'Ku nemi gafara
daga Ubangijinku, lalle ne Shi Ya
kasance Mai gafara ne.
11. "'Ya sako (girgijen) sama a
kanku da ruwa mai 6u66uga.
12. "'Kuma ya yalwata muku
game da dukiya da cfiya, Ya sanya
muku (albarka) ga gonaki, kuma
Ya sanya muku koguna.
13. "'Meya same ku,baku Star
samun natsuwa daga Allah,
14. '"Alhali kuwa, lalle ne, Ya
halitta ku, a cikin halaye?
75. '"Ba ku ga yadda Allah Ya
halitta^ wasu sammai bakwai cfa-
bakokT a kan juna ba?
16. "'Ya sanya wata a cikinsu,
yana mai haske, Ya sanya rana
babbar fitila?
17. "'Kuma Allah Yatsirardaku
daga kasa (kamar ganye) tsirarwa.
18. '"Sa'an nan Yamayar da ku
a cikinta, kuma Ya fitar da ku fitar-
wa.
19. "'Kuma Allah Ya sanya
muku Rasa shimfidadlcfiya.
20. "'Domin ku shiga a cikinta,
hanyoyi masu fadi.'"
J&
884
71 - Suratu Nuh
SSU^-V\
21. Nuhu ya ce, "Ya Ubangijina !
Lalle ne su, sun saBa mini, sun bi
wanda dukiyarsa da cfiyansa ba su
fare shi da kome ba sai da hasara.
22. "Kuma sun yi wani makirci,
makirci babba.
23. "Kuma suka ce, 'Faufau,
kada ku bar gumakanku, kuma
faufau, kada ku bar Wadda, kuma
kada ku bar Suwa, kuma kada ku
bar Yagusa da Ya'uka da Nasra.'
24. "Kuma lalle ne, sun Batar da
(mutane) masu yawa, kuma kada
Ka kara wa azzalumai (kome) sai
6ata."
25. Saboda laifukansu na gan-
ganci aka nutsar da su, sa'an nan
aka sanya su a wuta. Saboda haka
ba su sama wa kansu wani matai-
maki wanin Allah ba.
26. Kuma Nuhu ya ce, "Ya
Ubangijina! Kada Ka bari, a kan
£asa, daga cikin kafirai, wanda ke
zama a cikin gida.
27. "Lalle ne, Kai, idan Ka bar
su, za su Batar da bayinKa, kuma
ba za su haifi kowa ba face fajiri
mai yawan kafirci
28. " Ya Ubanginjina ! Ka yi mini
gafara (ni) da mahaifana biyu, da
wanda ya shiga gidana, yana mai
Tmani, da muminai maza da mumi-
nai mata, kuma kada Ka £ara wa
azzalumai kome sai halaka."
Jl>LO
!/£'
U^i£^^
©biU=»
'< <" ' S\' * ^4 ^|
885
72 — Suratul Jinn
vA - vr
Wa'azi ga masu bauta wa aljannu da mutane domin neman tsari ko
samu, da ladubban mai wa'azi da yadda ya kamata ya yi tawali'u.
Son girman shugabanni da jahilcin mabiya ne ke sanya ana bauta-
wa wanin Allah.
* J* ■* . * ** *
WU\
^r
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ka ce: An yi wahayi zuwa
gare ni cewa wasu jama 'a na aljan-
nu sun saurari (karatuna), sai suka
ce, 'Lalle ne mu, mun ji wani abin
karantawa (Alkur'ani), mai ban
mamaki.
2. 'Yana nuni zuwa ga hanyar
kwarai, saboda haka mun yi imani
da shi, ba za mu koma bauta wa
Ubangijinmu tare da kowa ba.
3. 'Kuma lalle ne shi, girman
Ubangijinmu, Ya cfaukaka, bai riki
mata ba, kuma bai riki da ba.
4. 'Kuma lalle ne shi, wawanmu
ya kasance yana fadar abin da ya
ketare haddi ga Allah.
5. 'Kuma lalle ne mu, mun yi
zaton mutum da aljani ba za su iya
fadar karya ba ga Allah.
6. 'Kuma lalle ne shi, wasu maza,
daga cikin mutane, sun kasance
suna neman tsari da wasu maza
//k ,<^i^ »><
3 UJ l^» ir^ ob-^^^Ul^r-
886
72 — Suratul Jinn
'sW.
-vr
daga cikin aljannu, saboda haka
suka kara musu girman kai.
7. 'Kuma lalle ne su, sun yi zato,
kamar yadda kuka yi zato, cewa
Allah ba zai aiko kowa ba.
8. 'Kuma lalle ne mu, mun nemi
(hawan) sama, sai muka same ta an
cika ta da tsaro mai tsanani, da
kuma yulaye.
9. "Kuma lalle ne mu, mun ka-
sance muna zama daga gareta, a
wuraren zama, domin saurare. To,
wanda ya yi saurare a yanzu, zai
sami yula, mai dako dominsa.
10. 'Kuma lalle ne mu, ba mu
sani ba, shin, sharri ne aka yi nufi ga
wacfanda ke cikin kasa, ko Ubangi-
jinsu Ya yi nufin shiriya a gare su
ne?
11. "Kuma lalle ne mu, akwai
salihai a cikinmu, kuma akwai a
cikinmu wacfanda ba haka ba, mun
kasance kungiyoyi dabam-dabam.
12. 'Kuma lalle ne mu, mun tab-
bata ba za mu buwayi Allah ba, a
cikin kasa, kuma ba za mu buwaye
Shi da gudu ba.
13. 'Kuma lalle ne mu, a lokacin
da muka ji shiriya, mun yijmani da
ita. To wanda ya yi imani da
Ubangijinsa, ba zai ji tsoron nakka-
sa ba, kuma ba zai ji tsoron zalunci
ba.
14. 'Kuma lalle ne mu^ akwai a
cikinmu, wacfanda suka mTka wuya,
kuma akwai, a cikinmu, karkatattu.
To, wanda ya mlka wuya wacfancan
kam sun nufi shiryuwa.
1r*\\- 9 * *\ -" (r "
r^^.fi^» x i,- -
»U ■■«» I L'^iiql ujj
^ u * ^ w ' '-'\'" ** *' ftvfi-
4 <-
„/ ^ *> ^-r ** i^-v- ^ftV* 'x'AtV
887
72 - Suratul Jinn
£&-vr
15. 'Kuma amma karkatattu,
sai suka kasance makamashi ga
Jahannama.'
16. "Kuma da sun tsayu (1) sosai
a kan hanya, da lalle Mun shayar
da su ruwa mai yawa.
17. "Domin Mu jarraba su a
ciki, kuma wanda ya kau da kai
daga tuna Ubangijinsa, Ubangi-
jinsa zai shigar da shi azaba mai
hauhawa.
18. "Kuma lalle ne wuraren su-
juda na Allah ne, saboda haka kada
ku kira kowa tare da Allah (da su, a
cikinsu).
19. "Kuma lalle ne shi, a lokacin
da bawan Allah (2) ke kiran Sa, sun
yi kusa su zama kamar shirgi a
kansa".
20. Ka ce, "Ina kiran Ubangijina
ne kawai, kuma ba zan tara kowa
da Shi ba."
21. Ka ce, "Lalle ne nl, ba ni
mallakar wata cuta gare ku, kuma
ba ni mallakar wani allien.' '
22. Ka ce, "Lalle ne ni, kowa ba
ya iya cetona daga Allah, kuma ba
zan iya samun mafaka ba daga gare
Shi.
23. "Face iyarwa, daga Allah, da
manzancinSa. To, wanda ya saba
wa Allah da ManzonSa, to, lalle
" '*" m-*ix* < t> ,<Tfrf'
^pU^vkl^J \y &S Qy±7>y~a\ \ [a\j
x ^ 2<m *&>*•" * \> 9 ' 'i-n *'*\'
ll^j^J^>)^V Jiji
(1) Tsayuwa sosai wato su bauta wa Allah kamar yadda Allah Ya umarce su, su yi
Masa cfa'a saboda Ya wadata su.
(2) Bawan Allah shi ne duk wani mai wa'azi yana kira zuwa ga Allah. Ba ya halatta a
gare shi ya bar wadanda yake yi wa wa'azi su kai fagen bauta masa shi kansa. Sai ya gaya
musu gaskiyar matsayinsa, kamar yadda Allah Ya fada wa AnnabinSa, kuma Ya umarce
shi da ya gaya wa wadanda yake yi wa wa'azi.
888
72 — Suratul Jinn
vai'tai.
-vv
yana da wutar Jahannama, suna
masu dawwama a cikinta, har
abada."
24. Har idan sun ga abin da ake
yi musu gargacfi da shi, to, za su san
wanda ya zama mafi raunin matai-
maki da mafi karancin adadi.
25. Ka ce, "Ban sani ba, a kusa
ne abin da ake yi muku gargacfi da
shi, ko Ubangijina Ya sanya masa
dogon ajali!
26. "Shi cfai ne Masanin fake,
saboda haka, ba Ya bayyana
gaibinSa ga kowa.
27. "Face ga wanda Ya yarda da
shi, wato wani manzo, sa'an nan,
lalle ne, zai sanya (1) gadi a gaba
gare shi da baya gare shi.
28. "Domin Ya san lalle, sun iyar
da sakonnin Ubangijinsu, kuma
(Shi Ubangijin) Ya kewaye su da
sani, kuma Ya lissafe dukan kome
da kididdiga."
&\\* A " *\
(!) Idan Allah Ya aiko wani manzonSa da wani umurni ko hani zuwa ga mutane, to,
zai sanya mala'iku gaba gare shi da baya gare shi suna gadin sa domin kada wani shaidani
ya kusance shi har ya sanya shi mantuwa ko kuskure, har ya iyar da manzancin nan kamar
yadda yake.
889
73 — Suratul Muzzammil
zmm-vr
^Sil
SURATUL MUZZAMMIL
Mum
v£|
Tana karantar da tarbiyya da juriya ga Musulmi, domin su
sami damar tsayuwa da umurnin Allah.
«* j* s . ** ^ ^
£>V#3U\
^»
Z)a sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
1. Ya wanda ya lulluBe!
2. Ka tsayu domin yin salla a
cikin dare (duka) face kadan.
3. Rabinsa, ko ka rage abu ka-
dan daga gare shi.
4. Ko ka kara kansa, kuma ka
kyautata karanta Alkur'ani, daki
daki.
5. Lalle ne Mu, za Mu jefa maka
magana mai nauyi.
6. Lalle ne tashin dare shi ne mafi
tsananin natsuwa, kuma mafi dai-
daituwa ga magana.
7. Lalle ne kana da, a cikin yini,
wani tasblhi mai tsawo.
8. Kuma ka ambaci sunan
Ubangijinka, kuma ka yanke (kau-
na daga kowa ka koma) zuwa gare
Shi, yankewa.
P. Shi ne Ubangijin mafitar rana
da mafadarta, babu abin bautawa
face Shi. Saboda haka ka rike Shi
Wakili.
3 ^SyoCj-it $jj& lj}
JS^jL^jgpsi
890
73 — Suratul Muzzammil
tmm-vr
10. Kuma ka yi kaloiri ga abin
da suke facfa, kuma ka kaurace
musu, kauracewa mai kyawo.
11. Kuma ka bar Ni da masu
karyatawa, mawadata, kuma ka
jinkirta musu kacfan.
12. Lalle ne, a wurinMu, akwai
wasu maruruwa masu nauyi da
Jahlm.
13. Da wani abinci mai makara
da azaba mai racfacfi.
14. Ranar da kasa ke raurawa,
da duwatsu, kuma duwatsu su ka-
sance tudun rairayi mai malala.
75. Lalle ne Mu; Mun aika,
zuwa gare ku, wani Manzo (1) mai
shaida a kanku, kamar yadda Muka
aika wani Manzo (2 } zuwa ga Fir 'auna,
16. SaiFir'aunayasaBawaMan-
zon, saboda haka Muka kama shi,
kamu mai tsanani.
17. To, yaya, idan kun kafirta,
za ku kare (azabar) wani yini mai
mayar da yara (tsofaffi) masu
hurhura.
18. Sama za ta tsage a cikinsa,
wa'adinsa ya kasance mai aukuwa.
19. Lalle ne wannan wata tuna-
tarwa ce, sai dai wanda ya so, ya
kama hanyar kwarai zuwa ga
Ubangijinsa.
20. Lalle ne Ubangijinka Ya sani
cewa, kai kana tsayuwa a kusan
kashi biyu daga uku na dare, da
rabinsa, da sulusinsa, tare da wani
3 ^^\A^c^r^ Jb ^ tiyy>y>^c> jy**\)
> f x >> 9 , s s, c ^*< .>>]><: \\
"l If > ■" '- % *4V G> V' ?\\' *t' ~\<' *'*£'
(i) Wato Annabi Muhammad, tsira da aminci su tabbata a gare shi.
(2) Wato Annabi Musa, aminci ya tabbata a gare shi.
891
73 — Suratul Muzzammil
m#$&-vr
6angare na wacfanda ke tare da kai.
Allah Yake iya kaddara dare da
yini, Ya san ba za ku iya lissafa shi
ba, saboda haka Ya kar6i tubarku,
sai ku karanta abin da ya saukaka
na Alkur'ani. Ya^san wasu daga
cikinku, za su yi ciwo, kuma wasu
za su yi tafiya cikin kasa suna ne-
man falalar Allah da fatauci, kuma
wasu za su yi yaki a cikin hanyar
Allah. Saboda haka ku karanta
abin da ya saukaka daga gare shi,
kuma ku tsai da salla, kuma ku
bayar da zakka, kuma ku bai wa
Allah ranee, ranee mai kyawo.
Kuma abin da kuka gabatar domin
kanku, na alheri, za ku same shi^a
wurin Allah, zai kasance mafTfici
(daga wanda kuka ajiye) kuma zai
fi girma ga sakamako, kuma ku
roki Allah gafara; lalle ne Allah
Mai gafara ne, Mai jin kai.
Tana karantar da fara yin wa'azi ga dangi na kusa ga mai
wa'azi kamin ya fita zuwa ga wasu mutane na nesa.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ya wanda ya lullu6a da
mayafi.
2. Ka tashi domin ka yi gargacQ.
4^j^lj
892
74 - Suratul Muddatthir
M\m-n
3. Kuma Ubangijinka, sai ka
girmama Shi,
4. Kuma tutafinka, sai ka tsar-
kake su,
5. Kuma gumaka, sai ka kaura-
ce musu.
6. Kada ka yi kyauta kana ne-
man kari
7. Kuma saboda Ubangijinka,
sai ka yi hakuri.
8. To, idan aka yi busa a cikin
kaho,
9. To, wannan, a ranar nan, yini
ne mai wuya
10. A kan kafirai, ba mai sauki
ba ne.
11. Ka bar Ni da wanda Na ha-
litta, yana shi kacfai,
12. Kuma Na sanya masa du-
kiya shimficfacfcfiya
13. Da cfiya halartattu,
14. Kuma Na shimficfa masa
kome shimficfawa.
15. Sa'an nan yana kwacfayin In
yi masa kari !
16. Faufau! Lalle ne shT, ya ka-
sance, ga ayoyinMu, mai tsaurin
kai.
17. Za Ni kallafa masa wahala
mai hauhawa.
18. Lalle ne shi, ya yi tunani,
kuma ya kaddara (abin da zai facfa
game da Alkur'ani)
19. Saboda haka aka la'ane shi,
kamar yadda ya kaddara.
%>j
' 'yi'? 'i'
>>
MjJdj(^3,4j\
J-M*
893
74 - Suratul Muddatthir
jmm-n
20. S'an nan aka la'ane shi ka-
mar yadda ya kaddara.
21. Sa'an nan ya yi tunani,
22. Sa'an nan ya gintse huska,
kuma ya yi murtuk.
23. Sa'an nan ya juya baya,
kuma ya bunkasa,
24. Sai ya ce, "Wannan abu dai
ba kome ba ne face wani sihiri,
wanda aka ruwaito.
25. "Wannan maganar mutum
dai ce."
26. Za Ni kona shi da Sakar.
27. Kuma me ya sanar da kai
abin da ake cewa Sakar!
28. Ba ta ragewa, kuma ba ta
bari.
29. Mai nacewa ga jiki ce (da
kuna).
30. A kanta akwai (matsara)
goma sha tara.
31. Kuma ba Mu sanya ma'abu-
ta wuta (wato matsaranta) ba, face
mala'iku, kuma ba Mu sanya ada-
dinsu (goma sha tara) ba, fSce do-
min fitina ga wadanda suka kafirta,
domin wadanda aka bai wa littafi su
sami yakini, kuma wacfanda suka yi
imani su kara imani, kuma wadan-
da aka bai wa littafi da muminai ba
za su yi shakka ba, kuma domin wa-
cfanda a cikin zukatansu akwai wa-
ta cuta da kafirai su ce, "Me Allah
Yake nufi da wannan ya kasance
misali?" Haka dai Allah ke 6atar da
wanda Ya so, kuma Ya shiryar da
wanda Ya so. Kuma babu wanda ya
[pjj^Ji*^
«*VS' .-1-
CHS Jilll
894
74 - Suratul Muddatthir
JSS]Jj&-yi
san mayakan Ubangijinka face Shi,
kuma ita (wutar) ba ta kasance ba
face wata tunatarwa ce ga mutum.
32. A'aha ! Ina rantsuwa da wata.
33. Dadarealokacindayajuyar
da baya.
34. Da safiya idan ta waye.
35. Ita (wutar) tfayan manyan
masifu ce.
36. Mai gargadi ce ga mutum.
37. Ga wanda ya so, daga cikin-
ku, ya gabata ko ya jinkirta.
38. Kowane rai ga abin da ya
aikata jingina ce.
39. Face mutanen dama.
40. A cikin Aljanna suna tam-
bayar juna.
41. Game da masu laifi.
42. (Su ce musu) "Me ya shigar
da ku a cikin Sakar?"
43. Suka ce, "Ba mu kasance
muna a cikin masu salla ba.
44. "Kuma ba mu kasance muna
ciyar da matalauta ba.
45. "Kuma mun kasance muna
kutsawa tare da masu kutsawa,
46. "Mun kasance muna karyata
ranar sakamako.
47. "Har gaskiya (wato mutuwa)
ta zo mana".
48. Saboda haka ceton masu
ceto ba zai amfane su ba.
49. Haba! Me ya same su, suka
zama masu bijirewa daga wa'azin
gaskiya.
*j*"
feists
&j$&$
^ "if ~ > '£*r£
895
74 - Suratul Muddatthir
i^l^-vt
50. Kamar dai su, jakuna firgi-
tattu ne.
57. Sun gudu daga zaki.
52. A 'aha ! Kowane mutum daga
cikinsu yana son a zo masa da
takardu (da sunansa) ana watsawa
53. A 'aha! Kai dai, ba su jin
tsoron Lahira.
54. A'aha! Lalle ne, shi (Alku-
r'ani) tunatarwa ce.
55. Domin wanda ya so, ya tuna.
56. Kuma ba za su tuna ba face
idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancan-
ta a bi Shi da takawa, kuma Ya
cancanta ga Ya yi gafara.
*?-. d»>> ->'*x
>**-*jr*»r*>
X
p3 6 jJlII
Tana karantar da bayanin yiwuwar Tashin Kiyama, da sifar
mumini ga saurin kama umurnin Allah, da sakamakon wanda ya bi
hanyar Allah, ko kuwa ya ki bin ta.
f^^Lf <-f
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
7. Ba sai Na yi rantsuwa (1) da
Ranar Kiyama ba.
> •!«
(1) Wasu na fassarawa: Ina rantsuwa da Ranar Kiyama. A ganina, da tabbatar da
rantsuwar da kuma kore ta duka daya ne, makasudi dai jan hankalin mai karatu ga abin da
yake a ciki, na hikimar Allah.
896
75 — Suratul Kiyama
t£t£)|j&-Yo
2. Ba sai Na yi rantsuwa da rai
mai yawan zargin (1) kansa ba.
3. Shin, mutum yana zaton cewa
ba za Mu tara kasusuwansa ba?
4. Na'am! Masu Ikon yi Muke a
kan Mu daidaita ga666in yatsunsa.
5. Ba haka ba ! Mutum so yake,
ya yi fajirci, ya karyata abin da
yake a gabansa.
6. Yana tambaya, "Yaushe ne
Ranar Kiyama?"
7. To, idan gani ya cfimauta (ya
yi kyalli).
8. Kuma wata ya yi husufi (has-
kensa ya dushe).
9. Aka tara rana da wata.
10. Mutum zai ce a ran nan,
"Ina wurin gudu?"
11. A'aha! Babu mafaka.
12. Zuwa ga Ubangijinka wurin
tabbata, a ranar nan, yake.
13. Ana gaya wa mutum, a ranar
nan, abin da ya gabatar da wanda
ya jinkirtar.
14. Ba haka ba! Mutum, ga
abin da ya shafi kansa, masani ne.
15. Kuma ko da ya jefa uzuro-
rinsa (ba za a saurare shi ba).
16. Kada ka motsar (2) da hars-
henka game da shi domin ka yi
gaugawar rike shi (Alkur'ani).
s~<
(1) Kowane rai na zargin kansa idan bai yi aikin alheri ba, ko kuma bai yi fiye da
wanda ya yi ba, ko kuma bai aikata wanda ya fi kyawo ba a lokacin aikinsa.
(2) Dangantakar wannan aya da ta sama da ita ita ce bambancin Annabi mai gaugawar
karBar umurnin Allah da kyamar kafiri ga karBarsa, da bayanin saukakewar Allah ga mai
bin umurninSa.
897
75 — Suratul Kiyama
t^iaili^-vo
17. Lalle ne wajibi ne a gare Mu,
Mu tara shi. Mu (tsare maka) kara-
tunsa.
18. To, idan Muka karanta shi,
sai ka bi karatunsa.
19. Sa'an nan lalle, wajibi ne, a
gare Mu, bayaninsa.
20. A'aha ! Ba haka ba, kuna son
mai gaugawar nan (duniya) ne.
21. Kuna barin ta karshen
(Lahira).
22. Wasu huskoki, a ranar nan,
masu annuri ne.
23. Zuwa ga Ubangijinsu masu
kallo ne.
24. Wasu huskoki, a ranar nan,
masu gintsewa ne.
_ 25. Suna zaton a sako musu ma-
slfa mai karya tsatso.
26. A'aha! Idan (rai) ya kai ga
karankarmai.
27. Kuma aka ce, 'Wane ne mai
tawada?"
28. Kuma ya tabbata cewa rabu-
wa dai ce.
29. Kuma kwabri ya lauye da
wani kwabri.
30. Zuwa ga Ubangijinka, a ra-
nar nan, magargada (1) take.
31. To, bai gaskata ba, kuma bai
yi salla ba!
32. Amma dai ya karyata, kuma
ya juya baya!
ivy 0^ b JU« •> o ^-%
v$$j5j2%
(1) Ranar kora mutane, kamar ana gargada tumaki, zuwa ga tsayi a gaba ga Allah,
domin hisabi.
898
75 — Suratul FCiyama
&t£*!lj&-vo
33. Sa'an nan ya tafi zuwa ga
mutanensa, yana takama.
34. Halaka ta tabbata a gare ka,
sa'an nan ita ce mafi dacewa.
35. Sa'an nan wata halaka ta
tabbata a gare ka domin ta fi dace-
wa.
36. Shin, mutum na zaton a bar
shi sagaga (wato babu nufin kome
game da shi)?
37. Bai kasance digo na maniyyi
ba, wanda ake jefarwa (a cikin
mahaifa),
38. Sa'an nan ya zama gudan
jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi,
sa'an nan Ya daidaita gabobinsa;
39. Sa'an nan Ya sanya, daga
gare shi, nau'i biyu.namiji da mace?
40. Ashe Wannan bai zama Mai
iko ba bisa ga rayar da matattu? (1)
0&&ttg-3%&
Tana, karantar da asalin mutum da yadda zai Rare, ko ya doge
idan ya bauta wa Allah.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Lalle ne wata mudda ta za-
mani ta zo a kan mutum, bai ka-
sance kome ba wanda ake ambata
1 c
(1) Ana son mai karatu a nan ya ce, a Boye jj-uUJI j. .ilJi J* UIj J,
899
76 — Suratul Insan
"<K\\i<*
-VI
2. Lalle ne Mu, Mun halitta mu-
tum daga digon ruwa garwayayye,
Muna jarraba shi, saboda haka
Muka sanya shi mai ji mai gani,
3. Lalle ne Mu, Mun shiryar da
shi ga hanyar kwarai, ko ya zama
mai godiya, kuma ko ya zama mai
kafirci.
4. Lalle ne Mu, Mun yi tattali,
domin kafirai, sarkoki da kukum-
ma da sa'ir.
J. Lalle ne mutanen kirki za su
sha daga finjalin giya, abin gaura-
yarta ya kasance kafur ne.
6. Wani marmaro ne, daga gare
shi bayin Allah suke sha, suna 6u6-
Bugar da shi 6u66ugarwa.
7. Suna cikawa da alwashin (da
suka bakanta), kuma suna tsoron
wani yini wanda sharrinsa ya ka-
sance mai tartsatsi ne.
8. Kuma suna ciyar da abinci, a
kan suna bukatarsa, ga matalauci
da maraya da kamamme.
9. (Suna cewa) "Muna ciyar da
ku ne domin neman yardar Allah
kawai, ba mu nufin samun wani
sakamako daga gare ku, kuma ba
mu nufin godiya.
10. "Lalle ne mu, muna tsoro,
daga Ubangijinmu, wani yini mai
gintsewa, mai murtukewa."
11. Saboda haka Allah Ya tsare
musu sharrin wannan yini, kuma Ya
hada su da annurin huska da farin
ciki,
4dUs^s 4-£2^lii \ Xklv^^S)! \ LiL~£}
EIV
f 'i*
■&&
\ ^iSTiij^r^ts ^J^^TiiSrj^d^
>^s$j&^>^^
\AJ\
$S *'\" >*'* *\>\' \' *'Y^s
^•^ y <
900
76 — Suratul Insan
&X\\£<u
-vn
12. Kuma Ya saka musu, saboda
hakurin da suka yi, da Aljanna da
tufafin alhanni.
13. Suna masu zaman ginciri (1) ,
a cikinta, a kan karagu, ba su ganin
rana a cikinta, kuma ba su ganin
jaura.
14. Kuma inuwoyinta suna kusa,
a kansu, an hdre nunannun 'ya'yan
itacenta, horewa.
15. Kuma ana kewayawa a kan-
su da finjalai na azurfa da kofuna
wadanda suka kasance na karau.
16. Karau na azurfa, sun kadda-
ra su kaddarawa, daidai bukata.
1 7. Ana shayarwa da su, a cikin-
ta, finjalan giya, wadda abin gaura-
yarta ya kasance zanjabil ne.
18. Wani marmaro ne, a cikinta,
ana kiran sa Salsabil.
19. Kuma wasu yara samarin
dindindin na kewayawa, a kansu,
idan ka gan su, za ka zaci su
lu'ulu'u ne wanda aka watsa.
20. Kuma idan ka ga wannan
wurin, to, ka ga wata irin ni'ima da
mulki babba.
21. Tufafinsu na sama na alhan-
ni ne, kore da mai walkiya, kuma
an kawace su da mundaye na wata
irin azurfa, kuma Ubangijinsu, Ya
shayar da su abin sha mai tsarka-
kewar (ciki).
(1) Kishingicfa.
901
76 — Suratul Insan
^i^-vn
22. (A ce musu) "Lalle ne wan-
nan ya kasance, a gare ku sakama-
ko, kuma aikinku ya kasance abin
godewa."
23. Lalle Mu ne, Muka saukar
da Alkur'ani a gare ka, saukarwa.
24. Saboda haka ka yi hakuri
ga hukuncin Ubangijinka, kuma
kada ka bi, daga cikinsu> mai zunu-
bi ko mai kafirci.
25. Kuma ka ambaci sunan
Ubangijinka, safe da maraice.
26. Daga dare, sai ka yi sujuda
gare Shi, kuma ka tsarkake Shi
dare mai tsawo.
27. Lalle ne wadannan suna son
mai gaugawa (duniya) kuma suna
bari, a bayansu, wani yini mai
nauyi.
28. Mu ne, Muka halitta su,
kuma Muka karfafa halittarsu,
kuma idan Mun so, za Mu musanya
su da wasu mutane, kwatan-
kwacinsu, musanyawa.
29. Lalle ne wannan wata tuna-
tarwa ce, saboda wanda ya so ya
rika hanyar kirki zuwa ga
Ubangijinsa,
30. Kuma ba za ku so ba, sai
Allah Ya so, lalle ne Allah Ya ka-
sance Masani, Mai hikima.
31. Yana shigar da wanda Ya so
a cikin rahamarSa, kuma azzalu-
mai, Ya yi musu tattalin wata aza-
ba mai radacfi.
'&&&S&&U
3w
902
77 — Suratul Mursalat
^gH^-W
Tana gargacfi domin neman a gaskata Alkur'ani da abin da
yake facfa game da Kiyama.
,»/.^ ,, *
v#3u\
J^
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ina rantsuwa da iskokin da
ake sakowa jere, suna bin juna.
2. Sa'an nan su zama iskoki
masu karfi suna kacfawa da Icarfi.
3. Kuma masu watsa rahama
watsawa.
4. Sa'an nan da ayoyi (1) masu
rarrabe gaskiya da karya rarra-
bewa.
5. Sa'an nan da mala'iku masu
jefa tunatarwa ga Manzanni.
6. Domin yanke hamzari ko do-
min gargacfi.
7. Lalle ne abin da ake yi muku
wa'adi da shi tabbas mai aukuwa
ne.
8. To, idan taurari aka shafe
haskensu.
9. Kuma, idan sama aka tsage ta.
c— *^t r^j 1 1 i^
(1) Ya kamanta manzanin Allah masu kawo ayoyinSa da iskoki masu kawo ruwa,
domin rahamar da ke cikin kowanensu.
903
77 — Suratul Mursalat
y -\\^>L\5^
S3g»lSi&-vv
10. Kuma idan duwatsu aka nike
su.
11. Kuma idan manzanni aka
kayyade lokacin tara su.
12. Domin babbar ranar da aka
yi wa ajali.
13. Domin ranar rarrabewa (1) .
14. Kuma me ya sanar da kai
ranar rarrabewa?
15. Bone ya tabbata, a ranar
nan, ga masu karyatawa!
16. Ashe, ba Mu halakar da
(masu karyatawa) na farko ba,
17. Sa'an nan kuma za Mu biyar
musu da na karshe?
18. Haka nan Muke aikatawa da
masu yin laifi.
19. Bone ya tabbata a ranar nan
ga masu karyatawa!
20. Ashe, ba Mu halitta ku daga
wani ruwa wulakantacce ba,
21. Sa'an nan Muka sanya shi a
cikin wani wurin natsuwa amintac-
ce,
22. Zuwa ga wani gwargwadon
mudda sananna,
23. Sa'an nan Muka nuna iya-
warMu? Madalla da Mu, Masu
nuna iyawa.
24. Bone ya tabbata a ranar nan
ga masu karyatawa!
25. Ashe, ba Mu sanya kasa ma-
tattara ba,
m J-^iJ tp>£ <ibp1 \j> j
^^^ "^t*" s''*j>»s
Eg <> JSc^ ju^Jm
(1) Yin hukunci a tsakanin talikai.
904
77 — Suratul Mursalat
^^y^-w
26. Ga rayayyu da matattu,
27. Kuma Muka sanya, a cikin-
ta, kafaffun duwatsu macfaukaka,
kuma Muka shayar da ku ruwa mai
dacfi?
28. Bone ya tabbata, a ranar
nan, ga masu karyatawa!
29. Ku tafi zuwa ga abin da kuka
kasance kuna karyatawa game da
shi!
30. Ku tafi zuwa ga wata inuwa
mai rassa uku.
31. Ita ba inuwar ba, kuma ba ta
wadatarwa daga harshen wuta.
32. Lalle ne ita, tana jifa da tar-
tsatsi kamar soraye.
33. Kamar dai su rakumma ne
bakake.
34. Bone ya tabbata, a ranar
nan, ga masu karyatawa!
35. Wannan yini ne da ba za su
iya yin magana ba.
36. Ba za a yi musu izni ba, balle
su kawo hanzari.
37. Bone ya tabbata, a ranar
nan, ga masu karyatawa!
38. Wannan ranar rarrabewa ce,
Mun tattara ku tare da mutanen
farko.
39. To, idan akwai wata dabara
gare ku, sai ku yi ma Ni ita.
40. Bone ya tabbata, a ranar
nan, ga masu karyatawa!
41. Lalle ne masu takawa suna a
cikin inuwowi da maremari.
42. Da wasu 'ya'yan itace irin
wadanda suke marmari.
*/ '* ^' >>
B3 <> jSsiU JL-4 \> \j
frrj
p^^bj^^e^pl^^
\»r> »'' y*\?
^c^^^y^j
&>?* '•**''«
Ip d?/i \J)g^£cA \(y\ Sa
P- r J 0>f^^U_4 4>y>j
905
77 - Suratul Mursalat
t^S^-vv
43. (A ce musu) "Ku ci ku sha
cikin ni'ima saboda abin da kuka
kasance kuna aikatawa."
44. Lalle ne Mu, haka Muke
saka wa masu kyautatawa.
45. Bone ya tabbata, a ranar
nan, ga masu karyatawa!
46. (Ana ce musu) "Ku ci ku ji
dan dacfi kadan, lalle ne dai ku masu
laifi ne."
47. Bone ya tabbata, a ranar
nan, ga masu karyatawa!
48. Kuma idan an ce musu, "Ku
yi ruku'i," ba za su yi ruku'in (sal-
la) ba.
49. Bone ya tabbata, a ranar
nan, ga masu karyatawa!
50. To, da wane labari (Littafi),
waninsa (Alkur'ani) za su yi imani?
'».'
SURATUN NABA'
JStftft
Tana nuna rikicewar mutane a farkon addini da yadda ake
jawo hankalinsu domin su koma ga hanya.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. A kan me suke tambayar
juna?
2. A kan muhimmin labari mai
girma (Alkur'ani)?
906
78 - Suratun Naba'
J^JM- - VA
3. Wanda suke sa6a wa juna a
cikinsa?
4. A'aha! Za su sani.
5. Kuma a'aha! Za su sani.
6. Ashe, ba Mu sanya kasa shim-
ficfa ba?
7. Da duwatsu turaku (ga rike
kasa)?
8. Kuma Mun halitta ku maza
da mata?
9. Kuma Muka sanya barcinku
hutawa?
10. Kuma Muka sanya dare (ya
zama) sutura?
11. Kuma Muka sanya yini (ya
zama) lokacin neman abinci?
12. Kuma Muka gina, a saman-
ku, sammai bakwai masu karfi?
13. Kuma Muka sanya fitila mai
tsanin haske (rana)?
14. Kuma Muka saukar daga
cikakkun giragizai, ruwa mai ya-
wan zuba?
75. Domin Mu fitar da kwaya
da tsiri game da shi?
16. Da itacen lambuna masu lil-
libniya?
17. Lalle ne ranar rarrabewa ta
kasance abin kayyade wa lokaci.
18. Ranar da za a yi busa a cikin
kaho, sai ku zo, jama'a jama'a.
19. Kuma aka bucfe sama, sai ta
kasance kofofi.
20. Kuma aka tafiyar da duwat-
su, sai suka kasance kura.
£\/ V'Y *A'' **\\ .>'>'•'
907
78 - Suratun Naba'
>mm-v*
21. Lalle ne Jahannama ta ka-
sance madakata.
22. Ga masu icetare iyakoki, ta
zama makoma
23. Suna masu zama a cikinta,
zamunna.
24. Ba su cfancfanawar wani sa-
nyi a cikinta, kuma ba su cfancfana
abin sha.
25. Face tafasasshen ruwa da
rubaBBen jini.
26. Sakamako mai dacewa.
27. Lalle ne su, sun kasance ba su
fatar sauicin wani hisabi.
28. Kuma suka icaryata game da
ayoyinMu, £aryatawa!
29. Alhali kowane abu Mun £i-
diddige shi, a rubuce.
30. Saboda haka ku dandana,
domin haka, ba za Mu icara muku
kome ba face azaba.
31. Lalle ne masu talcawa na da
wani wurin samun babban rabo.
32. Lambuna da inabobi.
33. Da cikakkun 'yammata, tsa-
rar juna.
34. Da hinjalan giya cikakku.
35. Ba su jin yasassar magana, a
cikinta, kuma ba su jin £aryatawa.
36. Domin sakamako daga
Ubangijinka, kyauta mai yawa.
37. Ubangijin sammai da icasa
da abin da yake a tsakaninsu, Mai
rahama, ba su da ikon yin wata
magana daga gare Shi.
%
fp b ' jS ^j \yj 1^3 j^t^liV
' ^-'v^* -tH^-'V • •Iff' - - "Zu - -
908
79 — Suratun Nazi'at
K\\-\Vi<A
®>w&*-^
38. Ranar da Ruhi da mala'iku
za su tsaya a cikin safu, ba su maga-
na, sai wanda Allah Ya yi masa izni,
kuma ya facfi abin da ke daidai.
39. Wancan shi ne yini na gas-
kiya; to, wanda ya so, ya rika ma-
koma zuwa ga Ubangijinsa.
40. Lalle ne Mu, Mun yi muku
gargacfin azaba makusanciya, ranar
da mutum ke dubi zuwa ga abin da
hannayensa suka aikata, kuma ka-
firi ya ce, "Kaitona, da dai na zama
tur&aya!"
M ^>,
*J-J \J&* j>j> ^r^y 3 bl -Xc-OslJ; Jbl u|
Tana karantar da cewa jinkirin saukar azaba ga mai laifi ba
kyale shi ba ne, ga Allah, istidraji ne.
«* j* s . «* ^ *
\&)\&\
} J^
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
1. Ina rantsuwa da mala'iku
masu fisgar rayuka (na kafirai) da
karfi.
2. Da masu cfibar rayuka (na
muminai) da sauki a cikin nishacfi.
3. Da masu sauka daga sama da
umurnin Allah kamar suna iyo.
4. Sa'an nan su zama masu gau-
gawa (da umurnin Allah) kamar
suna tsere.
909
79 — Suratun Nazi 'at
: &mm-n
5. Sa'an nan su kasance masu
shirya gudanar da umurni.
6. Ranar da mai girgiza abubu-
wa (busar farko) za ta kada.
7. Mai biyar ta (busa ta biyu) na
biye.
8. Wasu zukata, a ranar nan,
masu jin tsoro ne.
9. Alhali idanunsu na kaskan-
tattu.
10. Suna cewa,"Ashe, lalle za a
iya mayar da mu a kan sawunmu?
11. "Ashe,idanmukazamakasu-
suwa rududdugaggu?"
12. Suka ce, "Waccan kam ko-
mawa ce, ta6a66iya!"
13. To, ita kam, tsawa guda ka-
wai ce.
14. Sai kawai ga su a bayan kasa.
15. Shin, labarin Musa ya zo
maka?
16. A lokacin da Ubangijinsa Ya
kiraye shi, a cikin rafi mai tsarki,
wato T)uwa?
17. Ka tafi zuwa ga Fir'auna,
lalle ne shi, ya ketare haddi.
18. "Sai ka ce masa, 4 K6 za ka so
ka tsarkaka,
19. "'Kuma in shiryar da kai
zuwa ga Ubangijinka domin ka ji
tsoronSa?'"
20. Sai yanuna masa ayar (1) nan
mafi girma.
f^H- nix"'"
' \' si >S\
(&tf^i$T£>$
(1) Ayar Musa da ta fi girma ita ce sandarsa mai zama maciji ko hannunsa mai haske
kamar tocila idan ya sanya cikin hammata ya fitar.
910
79 — Suratun Nazi'at
r-'&m'i&L
$m$&-.v\
21. Sai ya karyata, kuma ya saba
(umurni),
22. Sa'an nan yajuyabaya, yana
tafiya da sauri.
23. Sai ya yi gayya, sa'an nan ya
yi kira.
24. Sai ya ce, "Nl ne Ubangijin-
ku mafi tfaudaka."
25. Saboda haka Allah Ya kama
shi, domin azabar maganar karshe
da ta farko
26. Lalle ne a cikin wannan
hakika akwai abin kula ga wanda
yake tsoron Allah.
27. Shin, ku ne mafi wuyar halit-
ta ko sama? Allah Ya gina ta,
28. Ya rfaukaka rufinta, sa'an
nan Ya daidaita ta,
29. Kuma Ya duhuntar da da-
renta, kuma Ya fitar da hantsinta,
30. Kuma kasa a bayan haka Ya
mulmula ta,
31. Ya fitar da ruwanta daga
gare ta da makiyayarta,
32. Da duwatsu, Ya kafe ta,
33. Domin jiyarwa dacfi a gare
ku, kuma ga dabbobinku.
34. To, idan uwar masifu, mafi
girma, ta zo,
35. Ranar da mutum zai yi tu-
nanin abin da ya aikata,
36. Kuma a bayyanaJahim ga
mai gani,
37. To, amma wanda ya yi gir-
man kai,
&t£s"£J^
&2&SsJJk «*U*S £>[
twCii'
911
79 — Suratun Nazi'at
l i<*
jj2»SS&-V*
38, Kuma ya zabi rayuwa ta
kusa, (wato duniya),
39, To, lalle ne Jahlm, ita ce
makoma.
40, Kuma amma wanda ya ji
tsoron tsayi a gaba ga Ubangijinsa,
kuma ya kange kansa daga son rai.
41, To, lalle ne Aljanna ita ce
makoma.
42, Suna tambayar ka game da
Sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
43, Me ya hacfa ka da amba-
tonta?
44, Zuwa ga Ubangijinka Icars-
hen al'amarinta yake
45, Kai mai gargadi kawai ne ga
mai tsoron ta.
46, Kamar su, a ranar da za su
gan ta, ba su zauna ba face a lokacin
marece ko hantsinsa.
'H'X?' ' 'Zi+S
^tet^oj^fe
(jp l^-i^<>» j A^ cd L^i
912
80 — Suratu 'Abasa
S^9J^- A#
Tana karantar da rashin bambanci a cikin Musulunci; ri£on
addini da gaskiya shi ne cfaukaka, ba samu ba.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ya game huska (1) kuma ya
juya baya.
2. Saboda makaho ya je masa.
3. To, me ya sanar da kai cewa
watakila shi ne zai tsarkaka,
4. Ko ya tuna, domin tuna war ta
amfane shi?
5. Amma wanda ya wadatu da
dukiya,
6. Sa'an nan kai kuma ka dora
bijira zuwa gare shi!
7. To, me zai cuce ka idan bai
tsarkaka ba?
^\ \"C' "'
^M ^*1m/ |j^ La I
®$y$£&Cj
(1) Wani makaho, Abdullahi bin Ummi Maktum ya je wurin Annabi domin ya
musulunta, sai ya iske a lokacin nan Annabi na ko£arin shiryar da wasu manyan mutane
na Kuraishawa, sai wannan makahon ya yanke maganar Annabi da su, ba da saninsa ba,
alhali Annabi na gurin su musulunta domin darajarsu ga idon mutanensu. Saboda haka
Annabi, (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), ya 6ata huska, ya tafi domin 6acin
ransa, saboda rashin musuluntarsu. Bayan haka Annabi na girmama Abdullahi £warai,
idan ya je wurinsa sai ya ce masa "Maraba da wanda Ubangijina Ya zarge ni saboda shi".
Kuma ya shimfida masa mayafinsa, idan ya fita tafiya, yakan sanya shi ri£on garin
MadTna,
Kissar tana nuna girmamawar Allah ga Annabi da Ya ce, "Ya game huska... " bai ce
masa, "Domin ka game huska"... ba sai ya fada a cikin hali mai sau£i.
913
80 — Suratu 'Abasa
^S2j^,- A*
8. Kuma amma wanda ya zo
maka yana gaugawa,
9. Alhali shl yana jin tsoron Al-
lah,
10. Kai kuma ka shagala ga
barinsa!
11. A'aha! Lalle ne wannan tu-
natarwa ce,
12. Saboda wanda ya so ya tuna
Shi (Allah).
13. (Tunatarwa ce) ta cikin lit-
tafai ababan girmamawa,
14. Ababan cfaukakawa, ababan
tsarkakewa,
15. A cikin hannayen mala'iku
marubuta,
16. Masu daraja, masu cfa'a ga
Allah.
17. An la'ani mutum (kafiri).
Me ya yi kafircinsa!
18. Daga wane abu, (Allah) Ya
halitta shi?
19. Daga digon maniyyi, Ya ha-
litta shi, sa'an nan Ya Raddara shi
(ga halaye).
20. Sa'an nan hanyarsa ta fita Ya
sau£a£e masa.
21. Sa'an nan Ya matar da shi,
sai Ya sanya shi a cikin kabari.
22. Sa'an nan idan Ya so, lalle ne,
zai tayar da shi.
23. Haioica, bai i da aikata abin
da Allah Ya umurce shi ba (lokacin
sanya shi a cikin kabari).
(3<yl^*u^Wj
914
80 — Suratu 'Abasa
^jS^j^i' — A*
24. To, mutum ya duba zuwa ga
abincinsa.
25. Lalle ne Mu, Mun zubo
ruwa, zubowa.
26. Sa'an nan Muka tsattsage
Rasa tsattsagewa.
27. Sa'an nan Muka tsirar da
kwaya, a cikinta.
28. Da inabi da ciyawa.
29. Da zaituni da itacen dabmo.
30. Da lambuna masu yawan ita-
ce.
31. Da 'ya'yan itacen marmari,
da makiyaya ta dabbobi.
32. Domin jin dacfi a gare ku, ku
da dabbobinku.
33. To, idan mai tsawa (busa ta
biyu) ta zo.
34. Ranar da mutum yake gudu
daga cfan'uwansa.
35. Da uwarsa da ubansa.
36. Da matarsa da diyansa.
37. Ga kowane mutum daga ci-
kinsu, a ranar nan, akwai wani
sha'ani da ya ishe shi.
38. Wasu huskoki, a ranar nan,
masu haske ne.
39. Masu dariya ne, masu busha-
ra.
40. Wasu huskoki, a ranar nan,
akwai kura a kansu,
41. Baki zai rufe su,
42. Wacfannan su ne kafirai faji-
rai (ga ayyukansu).
^^&&^^\j£&
© SlA^)Ul>*Oi&
•»-£.^
**/ . — >*
4jS^-Ly9
'/»>>'
915
81 — Suratut Takwir
$?»-A>
Tana karantar da Tashin Kiyama gaskiya ne, kuma Alkur'ani
gaskiya ne, daga Allah yake, babu ragi babu kari, ya taho ta hannun
aminci, daga Allah zuwa ga Annabi.
•+ J* ■* . *
y*m,
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
7. Idan rana aka shafe haskenta.
2. Kuma idan taurari suka gur-
Bace (wani ya shiga a cikin wani).
J. Kuma idan duwatsu aka ta-
fiyar da su.
4. Kuma idan rakuma masu ci-
kunna (1) aka sake su wawai, ba ga
kowa ba.
5. Kuma idan dabbobin daji aka
tattara su.
6. Kuma idan tekuna aka mayar
da su wuta.
7. Kuma idan rayuka aka
harfa (2) su da jikunkunansu.
8. Kuma idan wadda aka turbu-
tfe (3) ta da rai aka tambaye ta.
[3cJl^o>*^JI \'*[j
(1) Rakuma masu ciki dan wata goma.
(2) Ko kuma aka hacfa kowane mutum da inn mutanensa a Aljanna ko a wuta.
(3) A cikin zamanin jahiliyya Larabawa ba su son a haifa musu 'ya'ya mata domin
haka har sukan turbude 'ya'yansu domin kada su yi abin kunya ko kuma su talauce wajen
yi musu aure.
916
81 — Suratut Takwir
smm-n
9. "Saboda wane laifi ne aka
kashe ta?"
10. Idan takardun ayyuka aka
watsa su (ga masu su).
1 1 . Kuma idan sama aka fecfe ta.
12. Kuma idan Jahim aka hura
ta.
13. Kuma idan Aljanna aka ku-
santar da ita.
14. Rai ya san abin da ya halar-
tar (a ranar nan).
75. To, ba sai Na yi rantsuwa da
taurari matafa (1) ba.
16. Masu gudu suna 6uya.
17. Da dare idan ya bayar da
baya.
18. Da safiya idan ta yi lumfashi.
19. Lalle ne shi (Alkur'ani) hak-
kan, maganar wani manzon (Allah)
ne mai girma ga Allah.
20. Mai karfi, mai daraja a wurin
Mai AParshi.
21. Wanda ake yi wa da'a (wato
shugaban mala'iku) ne a can, amin-
tacce.
22. Kuma abokinku ba mahau-
kaci ba ne.
23. Kuma lalle ne ya gan shi (2) a
cikin sararin sama mabayyani.
A *>\
3 (I/^cJl^iihj
($p23y5P
M.^&dT;
^ s> "~* ' --
Js>r?~i
(1) Masu tafiya suna komawa baya.
(2) Annabi ya ga Mala'ika Jibirilu ya san shi. Saboda haka wani aljani ba zai yi kama
da shi ba balle ya kawo masa £arya.
917
81 — Suratul Takwir
^51^-a^
24. Kuma shi, ga gaibi (1) , ba mai
rowa ba ne.
25. Kuma shi (Alkur'ani) ba ma-
ganar shaicfani, wanda aka la'ana,
ba ce.
26. Shin, a ina za ku tafi?
27. Lalle ne shi (Alkur'ani) ba
kome ba ne face gargacfi ga talikai.
28. Ga wanda ya so, daga cikin-
ku, ya shiryu,
29. Kuma ba za ku so ba, sai
idan Allah Ubangijin halitta Ya
yarda.
i^;r^J>^ly>i>l
Tana karantar da gaskiyar Tashin Kiyama, kuma ayyukan
mutum na duniya ana tsare da su domin hisabi da sakamako. Akwai
mala'iku matsara na musumman.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Idan sama ta tsage,
2. Kuma idan taurari suka wa-
tse,
(1) Ma'anar gaibi a nan, ilmin da Allah Ya aiko Jibirilu da shi zuwa ga Annabi,
Annabi ba ya boye shi daga mutane. Ga wata kira'a, wanda ake tuhuma, wato ba a
tuhumar Annabi, ga gaibin da ya fada cewa daga Allah yake, wato Alkur'ani duka gaskiya
ne.
918
82 — Suratul Inficfar
*Mili8£-Ar
3. Kuma idan tekuna aka facce
su,
4. Kuma idan kaburbura aka
tone su,
5. Rai ya san abin da ya gabatar,
da abin da ya jinkirtar.
6. Ya kai mutum ! Me ya rude ka
game da Ubangijinka, Mai karim-
ci?
7. Wanda Ya halitta ka, sa'an
nan ya daidaita ka, Ya kuma tsakai-
ta ka.
8. A cikin kowace irin sura Ya so,
Ya gina ka a kanta.
9. A'aha, ba haka ba, kuna ka-
ryatawa game da sakamako!
10. Lalle ne, a kanku, hakika
akwai matsara,
77. Masu daraja, marubuta,
12. Suna sanin abin da kuke ai-
katawa.
13. Lalle ne masu cfa'a ga Allah,
dahir, suna cikin ni'ima.
14. Kuma lalle ne fajirai, dahir,
suna cikin Jahlm.
15. Za su shige ta a ranar saka-
mako.
16. Ba za su faku daga gare ta ba.
17. Kuma me ya sanar da kai
abin da ake ce wa ranar sakamako?
18. Sa'an nan me ya sanar da kai
abin da ake ce wa ranar sakamako?
19. Rana ce da wani rai ba ya iya
mallakar kome, domin wani rai,
al'amari, a ranar nan, ga Allah (cfai)
yake.
oij
Gp ^ Vji fe'A?
Q£J s^i! IfjjU <^bj^\ U Jr
919
83 - Suratul Mucfaffiffn
PAWU&A
- AT
Tana karantar da wajabcin tsare hakkokin mutane, tsakaninsu,
a ciniki da wasu mu'amalolin zamantakewa.
** J» *S * j, *
4W$^
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L Bone ya tabbata ga masu
nakkasawa.
2. Wacfanda suke idan suka auna
daga mutane suna cika mudu,
3. Kuma idan sun auna musu, da
zakka (1) ko da sikeli, suna ragewa
4. Ashe ! Wadancan ba su tabba-
ta cewa lalle su, ana tayar da su ba?
5. Domin yini mai girma,
6. Yinin da mutane ke tashi
zuwa ga Ubangijin halitta?
7. Haklka, lalle ne littafin fajirai,
dahir, yana a cikin Sijjln,
8. Kuma me ya^sanar da kai abin
da ake ce wa Sijjln?
P. Wani littafi ne rubutacce,
10. Bone ya tabbata a ranar nan
ga masu karyatawa,
//. Wadanda suke karyatawa
game da ranar sakamako,
^Oy_>*^j*-r'
* ^ "»^»? -» ^k > »*»?> -v
(1) Mudu.
920
83 - Suratul Mudaffifin
-^li^-Ar
12. Babu mai karyatawa gare shi
face dukan mai ketare haddi, mai
yawan zunubi,
13. Idan ana karatun ayoyinMu,
a kansa, sai ya ce, tatsuniyoyin
mutanen farko ne,
14. A'aha! Ba haka ba, abin da
suka kasance suna aikatawa dai, ya
yi tsatsa a cikin zukatansu.
75. A'aha! Hakika, lalle ne su,
daga Ubangijinsu, a ranar nan,
wadanda ake shamakacewa ne,
16. Sa'an nan, lalle ne su, masu
shiga cikin Jahlm ne.
17. Sa'an nan a ce, "Wannan shi
ne abin da kuka kasance kuna ka-
ryatawa game da shi."
18. A'aha! Hakika, lalle ne litta-
fin masu da'a yana a cikin
Illiyylna?
19. Kuma mene ne ya sanar da
kai abin da ake cewa Illiyyuna?
20. Wani littafi ne rubutacce,
21. Mukarrabai (1) suke halarta
shi.
22. Lalle ne masu da'a ga Allah
tabbas suna cikin ni'ima,
23. A kan karagu, suna ta kallo,
24. Kana sani, a cikin huskokin-
su, akwai kwarjinin ni'ima.
25. Ana shayar da su daga wata
giya wadda aka yunke a kan rufinta.
26. Karshen kur6inta miski ne.
To, a cikin wannan, masu gwagwar-
maya su yi ta gwagwarmayar nema.
(^ ^£\ x£ j^^'J&j
US^^^&£&$fy
m^M\^p\^
» ft
^^JkjtJJX^bV.
S3 oyJ^ u <^)oJ*\ Uj
•**->-iisr
C3 ^ lt ^lH\ f^ljbi JiJ> j j <&Z»a»
(1) Mala'iku masu daraja.
921
83 - Suratul Mudaffifm
*e"j&- A r
27. Kuma abinda ake gauraya ta
da shi, daga tasnlm yake,
28. (Wato) wani marmaro ne
wanda mukarrabai ke sha daga
gare shi.
29. Lalle ne wacfanda suka kafir-
ta sun kasance (a duniya) suna yi wa
wacfanda suka yi Imani dariya.
30. Kuma idan sun shucfe su, sai
su dinga yin zuncfe,
31. Kuma idan suka juya zuwa
ga iyalansu, sai su tafi suna kakaci,
32. Kuma idan sun gan su sai su
ce, "Lalle wacfannan batattu ne."
33. Alhali kuwa ba a aike su ba
domin su zama masu tsaro a kansu.
34. To, yau fa (a Lahira) wacfan-
da suka yi imani, su ke yi wa kafirai
dariya.
35. A kan karagu, suna ta kallo.
36. Shin, an saka ma kafirai abin
da suka kasance suna aikatawa? (1)
>-^>?fi/
^<^j>jij I L^. 4^i lllp
\p\+U&fr)jW*#<U&'k
&o
Tana karantar da tabbatar Tashin Kiyama, kuma duka abin da
ake aikatawa idan ba na tattalin Kiyamar ba ne, to, ya zama wahal
da kai, maras amfani, da 6ata lokaci.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Idan sama ta kece,
\&\1[
(1) Amsar tambaya '"na'am".
922
84 — Suratul Inshilcalc
i<A
-A£
2. Ta saurari Ubangijinta, kuma
aka wajabta mata yin sauraron,
3. Kuma idan kasa aka mike ta,
4. Kuma ta jefar da abin da yake
a cikinta, ta wofinta daga kome,
5. Kuma ta saurari Ubangijinta,
aka wajabta mata yin sauraren,
6. Ya kai mutum! Lalle ne kai
mai aikin wahal da kai ne zuwa ga
Ubangijinka, wahala mai tsanani,
To, kai mai haduwa da Shi ne.
7. To, amma wanda aka bai wa
littafinsa da damansa,
8. To, za a yi masa hisabi, hisabi
mai sauki
9. Kuma ya juya zuwa ga iyalin-
sa (a cikin Aljanna), yana mai raha.
10. Kuma, amma wanda aka bai
wa littafinsa daga wajen bayansa,
11. To, za shi dinga kiran
halaka!
12. Kuma ya shiga sa'Tr,
13. Lalle ne shi, ya kasance (a
duniya) cikin iyalinsa yana mai
raha.
14. Lalle ne ya yi zaton ba zai
komo ba.
15. Na'am! Lalle ne Ubangijin-
sa Ya kasance Mai gani gare shi.
16. To, ba sai Na rantse da sha-
faki ba,
17. Da dare, da abin da ya
kunsa,
18. Da wata idan (haskensa) ya
cika,
0aij
M r^ ly>Jb c3j~*3
El \ A~a>^Ai O^^Jc>lj^».
£j£&
i^J
923
84 - Suratul Insh£a£
&*m&?A
-A£
19. Lalle ne kuna hawan wani
hali daga wani hali.
20. To, me ya same su, ba su yin
Tmani?
21. Kuma idan an karanta Alku-
r'ani a kansu, ba su yin tawali'u?
22. Ba haka ba ! Wacfanda suka
kafirta, sai karyatawa suke yi.
23. Alhali, Allah ShT ne Mafi
sani ga abin da suke tarawa.
24. Saboda haka, ka yi musu
bushara da azaba mai radacfi,
25. Face wacfanda suka yi Tmani,
suka aikata ayyukan kwarai, suna
da wani sakamako wanda ba ya
yankewa.
> *>^*<\\^<
Tana bayanin mugunyar akibar masu wahal da muminai a kan
addininsu, ba da wata hujja ba ta shari'a.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
7. Ina rantsuwa da sama mai
taurarin lissafin shekara,
2. Da yinin da aka yi alkawarin
zuwansa, (1)
3 i^Vir!^
(1) Ranar Kiyama.
924
85 — Suratul Buruj
g$l£&-AO
3. Da yini mai shaidu, da yini da
ake halarta (1) a cikinsa
4. An la'ani mutanen rami (2) .
5. Wato wuta wadda aka hura
6. A lokacin da suke a kan (ge-
fen) ta a zazzaune.
7. Alhali su, bisa ga abin da suke
aikatawa ga muminai, suna halarce.
8. Kuma ba su tuhumce su ba,
face kawai domin sun yi imani da
Allah Mabuwayi, Wanda ake gode
wa,
9. Wanda Yake Shi ne da mulkin
sammai da Rasa, kuma Allah a kan
kome halarce Yake.
10. Lalle ne wadanda suka fitini
muminai maza da muminai mata,
sa'an nan ba su tuba ba, to, suna da
azabar Jahannama, kuma suna da
azabar gobara.
11. Lalle ne wadanda suka yi
Tmani, kuma suka aikata ayyukan
Rwarai, suna da gidajen Aljanna,
koramu na gudana daga Rarkashin
gidajen. Wancan abu fa shi ne rabo
babba.
12. Lalle ne damkar Ubangijin-
ka mai tsanani ce kwarai.
13. Lalle ne ShT, Shi ne Mai Raga
halitta, kuma Ya mayar da ita
(bayan mutuwa).
***' *>t »' t <>\\\\ is\>'\" fax
(1) Ranar Arafa.
(2) Mutanen Najiran ne suka yi rami suka hura wuta a ciki, domin su kone wanda ya
yi imani da addinin MasTh Tsa domin su hana yaduwarsa. Suka umurci kowane Musulmi
ya jefa kansa a ciki, su kuma suna zazzaune suna kallo.
925
85 - Suratul Buruj
g^jj&-AO
14. Kuma Shi ne Mai gafara,
Mai bayyana soyayya.
15. Mai Al'arshi mai girma
16. Mai aikatawa ga abin da
Yake nufi.
17. Ko labarin rundunoni ya zo
maka
18. Fir'auna da Samudawa?
19. A'aha ! Wacfanda suka kafir-
ta suna cikin Raryatawa.
20. Alhali, Allah daga bayansu,
Mai kewaye su ne (da saninSa).
21. A'aha! Shi Alkur'ani ne mai
girma.
22. A cikin Alio tsararre.
<&\> >Ai> t'Vy'* '
4»*
Tana karantar da tsaron Allah ga kome bisa ga tsari, kuma
kome asTrinSa ne, Alkur'ani gaskiya ne da asiri, Allah Ya tsare shi
daga mai son ya 6ata shi.
j*">" • -*
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jinkai.
1. Ina rantsuwa da sama da mai
aukowa da dare.
2. To, me ya sanar da kai abin da
ake cewa mai aukowa da dare?
fei&KPS
^ijlUf^Jbjsl'Cj
926
86 - Suratutf T>ari£
gm*&-n
3. Shi ne tauraron nan mai tsa-
nanin haske. (1)
4. Babu wani rai face a kansa
akwai wani mai tsaro.
5. To, mutum ya duba, daga me
aka halitta shi?
6. An halitta shi daga wani ruwa
mai tunkudar juna,
7. Yana fita daga tsakanin tsatso
da karankarman kirji.
8. Lalle ne Shi (Allah) ga mayar
da shi (mutum), tabbas Mai iyawa ne.
9. Ranar da ake jarrabawar asi-
rai
10. Saboda haka ba shi da wani
karfi, kuma ba shi da wani mai
taimako (da zai iya kare shi daga
azabar Allah).
11. Ina rantsuwa da sama
ma'abuciyar ruwa mai komawa
yana yankewa,
12. Da kasa ma'abuciyar tsage-
wa,
(2)
13. Lalle ne shi (Alkur'ani),
hakika magana ce daki-daki (s> ,
14. Kuma shi, ba bananci (4) ba
ne.
75. Lalle ne su, suna kulla kaidi
na sosai,
>„ * *>
&£&?*-
@^JblS^5
^-uOjJ^^
(1) Wannan ya yi kama da zuwan Annabi a cikin jahiliyya don ya haskaka duniya da
ilimi kamar yadda girgije ke ba da ruwa saboda tsiron kasa, hantsar uwa ta ba da nono
saboda jariri kuma maniyi ya zo lokacin jima'i.
(2) Domin fitar tsiro.
(3) Mai rabewa tsakanin karya da gaskiya.
(4) Kakaci.
927
87 - Suratul A'ala
mm*-"
16. Kuma Ni, Ina mayar da kai-
di (gare su) kamar yadda suke kulla
kaidi,
17. Saboda haka, ka yi wa kafi-
rai jinkiri, ka dakata musu, sannu-
sannu.
&<&&
"**>*> +\' . ^t^ ."X
©15W^J\#
Tana karantar da cewa rayarwa da matarwa ga hannun Allah
suke, su kuma nau'i-nau'i ne.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ka tsarkake sunan Ubangijin-
ka Mafi tfaukaka,
2. Wanda Ya yi halitta sa'an nan
Ya daidaita abin halittar,
3. Kuma Wanda Ya kaddara
(abin da Ya so) sannan Ya shiryar,
(da mutum ga hanyar alheri da ta
sharri),
4. Kuma Wanda Ya fitar da
makiyaya,
5. Sa'an nan Ya mayar da ita
kekasassa, baka.
6. Za mu karantar da kai (Al-
kur'ani) saboda haka ba za ka man-
ta (shi) ba.
\tey*\i\&!X*>&
928
87 - Suratul A'ala
$^S&-AV
7. Face abin da Allah Ya so, lalle
ne Shi (Allah) Ya san bayyane da
abin da yake Boye.
8. Kuma za Mu saukake maka
(aPamari) zuwa ga (Shari'a) mai
sauki.
9. Saboda baka, ka tunatar, idan
tunatarwa za ta yi amfani.
10. Wanda yake tsoron (Allah)
zai tuna.
11. Kuma shakiyyi, zai nisance
ta,
12. Wanda zai shiga wutar da ta
fi girma,
13. Sa'an nan ba zai mutu ba a
cikinta, kuma ba zai rayu ba,
14. Lalle ne wanda ya tsarkaka
(da imani) ya samu babban rabo.
75. Kuma ya ambaci sunan (1>
Ubangijinsa, sa'an nan ya yi salla.
16. Ba haka ba! Kuna zaBin
rayuwa ta kusa duniya (2>
17. Alhali Lahira ita ce mafi al-
heri kuma mafi wanzuwa,
18. Lalle ne wannan (3> yana a
cikin litaffan farko.
19. Littaffan Ibrahim da Musa.
r^j«\
^ >^
»
i^^Jf^U]^
(1) Ya ambaci sunan Allah ga ayyukansa duka, ya yi sallolin nan biyar da sauran
ibadodi duka.
(2) Rayuwa iri biyu ce, ta duniya da ta Lahira.
(3) Kamanta rayuwar ciyawa da rayar da ummiyyi da ilmi babu mantuwa, da rayar
da matattu cikin sa'ada ko cikin shakawa yana cikin litaffan farko.
929
88 - Suratul Ghashiya
(S^iaii^-AA
Tana karantar da yin hujja da abin da ake iya gani da ido
domin a fahimci abin da ake gani da hankali, gwargwadon tunanin
abokin magana.
. «*^*^ * ^ *
^
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin RaL
L Lalle ne labarin (Kiyama) mai
rufe mutane da tsoronta ya zo
maka?
2. Wasu huskoki a ranar nan
kaskantattu ne.
3. Masu aikin wahala ne, masu
gajiya,
4. Za su shiga wata wuta mai
zafi.
5. Ana shayar da su daga wani
marmaro mai zafin ruwa,
6. Ba su da wani abinci face dai
daga danyi.
7. Ba ya sanya £iba, kuma ba zai
wadatar daga yunwa ba.
8. Wasu huskoki a ranar nan
masu ni'ima ne.
9. Game da aikinsu, masu yarda
ne,
10. (Suna) a cikin Aljanna
madaukakiya.
//. Ba za su ji yasassar magana
ba, a cikinta.
3 A-^li) \£*J~.Sl5\ Ja
[53 ^U
930
88 - Suratul Ghashiya
62^Mi^-AA
12. A cikinta akwai marmaro
mai gudana.
13. A cikinta akwai gadaje
macfaukaka.
14. Da kofuna ar'aje.
15. Da filoli (1) jere,
16. Da katifu shimfide.
17. Ashe, to, ba za su dubawa ba
ga rakuma yadda aka halitta su?
18. Da zuwa ga sama yadda aka
daukaka ta?
19. Da zuwa ga duwatsu yadda
aka kafa su?
20. Da zuwa ga kasa yadda aka
shimfida ta?
21. Saboda haka, ka yi wa'azi,
kai mai yin wa'azi ne kawai.
22. Ba ka zama mai ikon tank-
wasawa a kansu ba.
23. Face dai duk wanda ya juya
baya, kuma ya kafirta,
24. To, Allah zai yi masa azaba,
azabar nan da take mafi girma.
25. Lalle ne, zuwa gare Mu ko-
mowarsu take,
26. Sa'an nan lalle ne aikinMu
ne Mu yi musu hisabi.
^^ "P t XT ' i''Y\>* \>** '>'
©3&IW&
^^i^ii^sr;*
*r
(1) Matasan kai.
931
89 - Suratul Fajr
i<A
&-K\
Tana karantar da cewa girmamawa da Tmani da takawa take,
ba da samun dukiya ko kyawon halitta ko mulki ba.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
L Ina rantsuwa da alfijiri,
2. Da daruruwa goma.
5. Da (adadi na) cika da (na)
mara.
4. Da dare idan yana shudewa,
5. Ko a cikin wadannan akwai
abin rantsuwa ga mai hankali (da
yake kange shi daga zunubi)?
6. Ba ka ga^yadda Ubangijinka
Ya aikata da Adawa ba?
7. Iramawa masu sakon (1) kTrar
jiki.
8. Wadanda ba a halitta kwa-
tankwacinsu ba, a cikin garuruwa
(na duniya).
9. Da Samudawa wadanda suka
fasa duwatsu a cikin wadi (2) (suka
yi gidaje)?
s^ssy sjZ"' '■£.
I^p *&&j &3§'j p\
fy&^^&$'&
(1) Tsawo mai ma'ana.
(2) Wadil fcura, sunan wuri ne kusa da Madina wajen Syria, wato Sham.
932
89 - Suratul Fajr
i^^fNiS^ — m
10. Da Fir'auna mai turaku,
11. Wacfanda suka ketare iya-
karsu, a cikin garuruwa?
12. Saboda haka, suka yawaita
yin 6arna a cikinsu.
13. Saboda haka Ubangijinka
Ya zuba musu bulalar azaba.
14. Lalle ne Ubangijinka Yana
nan a mafaka.
15. To, amma a mutum idan
Ubangijinsa Ya jarraba shi, wato
Ya girmama shi kuma Ya yi masa
ni'ima, sai ya ce, "Ubangijina Ya
girmama ni."
16. Kuma idan Ya jarraba shi,
wato Ya kuntata masa abincinsa,
sai ya ce "Ubangijina Ya walakanta
ni."
1 7. A'aha ! Bari wannan, ai ba ku
girmama maraya!
18. Ba ku kwadaita wa junanku
ga (tattalin) abincin matalauci!
19. Kuma kuna cin dukiyar
gado, ci na tarawa,
20. Kuma kuna son dukiya, so
mai yawa,
21. A'aha! Idan aka niJca kasa
nikewa sosai,
22. Kuma Ubangijinka Ya zo,
alhali mala'iku na jere, safu-safu,
23. Kuma a ranar nan aka zo da
Jahannama. A ranar nan mutum
zai yi tunani. To, ina fa tunani
yake a gare shi!
24. Yana dinga cewa, "Kaitona,
da na gabatar (da aikin kwarai)
domin rayuwata!"
&**X3>j
®'>M^ f *
>^ ^^ -£v > ft »-* '<^«. "" -^"V
933
89 - Suratul Fajr
r? — A^
25. To, a ranar nan babu wani
mai yin azaba irin azabar Allah.
26. Kuma babu wani mai cfauri
irin cfaurinSa.
27. Ya kai rai mai natsuwa!
28. Ka koma zuwa ga Ubangi-
jinka, alhali kana mai yarda (da
abin da Ya kaddara maka a duniya)
abar yardarwa (da sakamakon da
za a ba ka a Lahira).
29. Saboda haka, ka shiga cikin
bayiNa (masu bin umurni a
duniya).
30. Kuma ka shiga AljannaTa
(a Lahira).
»"£ >, 'S y *'* * m
^^^t^igfe
(sM^Jdra£
Tana karantar da cewa mutum an halitta shi cikin wahala, ko
mai amfanin sa idan ya bi umurnin Allah ko kuwa mai cutar sa idan
ya sa6a wa umurnin Allah.
** j* ■* . * s *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
1. Ba sai Na yi rantsuwa da wan
nan gari (1) ba.
(1) Allah Ya ce ba sai Ya yi rantsuwa da Makka ba sa'an nan za a san darajarta, a
lokacin da Annabi yake a cikinta, kuma shi yana da hakkin zama a cikinta mahaifansa da
zurriyarsa duka, ko da yake zai yi hijira saboda fitinar kafirai masu halaka dukiyarsu kan
adawa da shi. Da sun yi amfani da dukiyar ga ayyukan alheri, da ya fi musu.
934
90 - Suratul Balad
fc#&$&-V
2. Alhali kai kana mai sauka a
cikin wannan gari,
3. Da mahaifl da abin da ya
haifa,
4. Lalle ne, Mun halitta mutum
cikin wahala.
5. Ko yana zaton babu wani mai
iya samun iko, a kansa?
6. Yana cewa "Na (1) halakar da
dukiya mai yawa".
7. Shin, yana zaton cewa wani
bai gan shi ba?
8. Shin, ba Mu sanya masa idanu
biyu ba?
9. Da harshe, da le66a biyu,
10. Kuma ba Mu shiryar da shi
ga hanyoyi (2) biyu ba?
77. To, don me ne bai shiga Aka-
ba ba?
12. Kuma mene ne ya sanar da
kai abin da ake ce wa Akaba?
13. Ita ce fansar wuyan bawa,
14. Ko kuwa ciyarwa, a cikin
yini ma'abucin yunwa,
75. Ga maraya ma'abucin zu-
munta
16. Ko kuwa wani matalauci
ma'abucin tur6aya.
17. Sa'an nan kuma ya kasance
daga wacfanda suka yilmani, kuma
suka yi wa juna wasiyya da yin
hakuri, kuma suka yi wa juna wa-
siyya da tausayi.
ty JlS &i±S£i \ Lit Jul
^v *'* *^ ^ \ * ' »'\
l{jfC*jp>y.
.5 s ' '
*^n>
\* ' ('/ \> ' \" fa' ' \?'\
(1) Na halaka dukiya mai yawa domin fada da addini.
(2) Hanyar alheri da ta sharri.
935
91 — Suratush Shams
d§#,lj2&-u
18. Wacfannan ne ma'abuta
albarka (1)
19. Kuma wacfanda suka kafirta
da ayoyinMu, su ne ma'abuta shu'-
umci (2)
20. A kansu akwai wata wuta
abar kullewa.
Tana karantar da cewa idan azaba ta sauka a kan mutane,
takan shafi mai laifi da wanda ba shi da laifi daga cikinsu.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ina rantsuwa da rana, da
hantsinta,
2. Kuma da wata idan ya bi ta.
3. Da yini a lokacin da ya bayya-
na ta.
4. Da dare a lokacin da ya ke
rufe ta.
5. Da sama da abin da ya gina ta.
6. Da Rasa da abin da ya shim-
ficfa ta.
(1) Ko kuwa wacfanda ake bai wa takardunsu ga dama, a Lahira.
(2) Ko kuwa wadanda ake bai wa takardunsu ga hagu, a Lahira.
936
91 — Suratush Shams
&&$\$8? - ^
7. Da rai da abin da ya daidaita
shi,
8. Sa'an nan ya sanar da shi
fajircinsa da shiryuwarsa,
9. Lallene wanda ya tsarkake (1)
shi (rai) ya sami babban rabo.
10. Kuma lalle ne wanda ya tur-
bucfe (2) shi (da laifi) ya ta6e.
11. Samudawa sun karyata (An-
nabinsu), domin girman kansu.
12. A lokacin da mafi shakawar-
su ya tafi (wurin soke rakumar
Salihu),
13. Sai Manzon Allah ya gaya
musu cewa, "Ina tsoratar da ku ga
rakumar Allah da ruwan shanta!"
14. Sai suka karyata shi, sa'an
nan suka soke ta. Saboda haka
Ubangijinsu Ya darkake su, saboda
zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta
(azabar ga mai laifi da maras laifi).
75. Kuma ba ya tsoron akibarta
(ita halakawar).
(1) Kar6ar imani da aiki da abin da ya kunsa tsarkake rai ne.
(2) Kaflrci turbucfe rai ne da zunubi.
937
92 - Suratul Lail
ami^-w
Tana karantar da dangantaka tsakanin cfabi'a da halitta da
akibar mutum bisa aikinsa, da kuma kasuwar abubuwa tsakanin
alheri da sharri.
j* s . * ^ *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ina rantsuwa da dare a loka-
cin da yake rufewa.
2. Da yini a lokacin da yake
kuranyewa.
3. Da abin da ya halitta namiji
da mace.
4. Lalle ne ayyukanku, dabam-
dabam suke.
5. To amma wanda ya yi kyauta,
kuma ya yi takawa,
6. Kuma ya gaskata kalma (1)
mai kyawo,
7. To, za Mu saukake masa, har
ya kai ga sauki.
8. Kuma amma wanda ya yi
rowa, kuma ya wadatu da kansa,
9. Kuma ya karyatar da kalma
mai kyawo,
Ltl^ii
'^^•"S,
°l
bJ^tf;
(1) Kalma mai kyawo ita ce Kalmar shahada da abin da ta icunsa na addinin
Musulunci, wanda yake yinsa kamar yadda Allah Ya ce, ta hanyan Manzonsa, shi ne
taicawa.
938
92 - Suratul Lail
M&-v
10. To, za Mu saukakke masa,
har ya kai ga tsanani.
/ 1 . Kuma dukiyarsa ba ta wada-
tar masa da kome ba, a lokacin da
ya gangara (a wuta).
12. Lalle aikinMu ne, Mu bayya-
na shiriya,
13. Kuma lalle ne Lahira da du-
niya Namu ne.
14. Saboda haka Na yi maku
gargadi da wuta mai babbaka,
15. Babu mai shigarta sai mafi
shakawa,
16. Wanda ya karyata, kuma ya
juya baya.
17. Kuma mafi takawa (1) , zai
nisance ta,
18. Wanda yake bayar da du-
kiyarsa, alhali yana tsarkaka,
19. Alhali babu wani mai wata
ni'ima wurinsa wadda ake neman
sakamakonta.
20. Face dai neman yardar
Ubangijinsa Mafi daukaka.
21. To, lalle ne zai yarda (da
sakamakon da za a ba shi).
m^M^\^>ol
(1) Mafi ta£awa da Mafi shalcawa suna ma'anar mai ta£awa da shaiciyyi.
939
93 - Suratud Duha
$£S|lj&-*r
Tana karantar da ni'imomin da Allah Ya yi wa Annabi, tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi, a game da zatinSa, domin Ya
gina wasu hukunce-hukunce a kansu.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ina rantsuwa da hantsi
2. Da dare a lokacin da ya rufe
(da duhunsa).
3. Ubangijinka bai yi maka
bankwana ba, kuma bai ki ka ba.
4. Kuma lalle ta karshe (1) ce
mafi alheri a gare ka daga ta farko.
5. Kuma lalle ne Ubangijinka zai
yi ta ba ka kyauta sai ka yarda.
6. Ashe, bai same ka maraya ba,
sa'an nan Ya yi maka makoma?
7. Kuma Ya same ka ba ka da
shari'a, sai Ya shiryar da kai?
8. Kuma Ya same ka matalauci,
sai Ya wadata ka?
9. Saboda haka, amma maraya,
to, kada ka rinjaye shi,
10. Kuma amma mai tambaya,
kada ka yi masa tsawa,
77. Kuma amma ni'imar
Ubangijinka, sai ka fada (domin
godiya)
^5 ' *\i'
»■"< « <? fs.'Z'is
(1) Ta karshe, wato, Lahira; kuma ta farko, wato, duniya.
940
94 - Suratush Sharh
mm-\i
Tana karantar da ni'imomin da Allah Ya yi wa Annabi, tslra da
amincin Allah su tabbata a gare shi, game da sifofinsa, domin Ya
gina wasu hukunce-hukunce a kansu.
j*^** s> <*
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
1. Ashe, ba Mu bucfa maka zu-
ciyarka ba (domin daukar hakuri
da fahimta)?
2. Kuma Muka saryar maka da
nauyinka,
5. Wanda ya nauyayi bayanka?
4. Kuma Muka daukaka maka
ambatonka?
5. To, lalle ne tare da tsananin
nan akwai wani sauki,
6. Lalle ne tare da tsananin nan
akwai wani sauki.
7. Saboda haka idan ka kare
(ibada) sai ka kafu (kana rokon
Allah).
8. Kuma zuwa ga Ubangijinka
ka yi kwadayi.
941
95 - Suratut Tin
-V>
Tana karantar da cewa duka abin da ya shafi addini ba ya
halaka, sauran abubuwa suna halaka da shudewar zamaninsu.
•+ j* s . * ^ >*
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kal
1. Ina rantsuwa da Attinu da
Azzaitun. (1)
2. Da T>ur Sln7na. (2)
3. Da wannan gari (3) amintacce.
4. Lalle ne Mun halitta mutum a
cikin mafi kyawon tsayuwa
5. Sa'an nan Muka mayar da shi
mafi kaskantar masu rauni
6. Face wacfanda suka yi imani,
kuma suka aikata ayyukan kwarai,
saboda haka suna da sakamako
wanda ba ya yankewa.
7. To, bayan haka me ya sanya
ka ka karyata sakamako (wanda za
a yi a bayan Tashin Kiyama)?
8. Ashe, Allah ba Shi ne Mafi
masu hukunci kyawon hukunci
ba? (4)
|°| C{jJJtiui ( jJLi4U!o.>jj»j
ujy^il^^v^il^^i
(1) Ibn Abbas ya ce Attinu shi ne masallacin Nuhu a kan Judiyyi, Azzaitun Masallacin
Baitil Mukaddas.
(2) Dutsen da Allah Ya yi magana da Musa a kansa. Ma'anarsa dutse mai albarka
saboda itacen da ke kansa.
(3) Gari amintacce shi ne Makkah.
(4) Ana son wanda ya karanta surar har karshe ya ce J^ Wato na'am, Allah Ya fi
kowa kyawon hukunci.
942
96 - Suratul 'Ala£
&m&-*\
Tana karantar da cewa karatu shi ne gaba da kome, amma a
gama shi da sunan Allah, kuma a yi aiki da shi domin a sami
kiyayewar Allah daga dukan makiyin addini.
* ■* >. * s *
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ka yi karatu da sunan
Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.
2. Ya halitta mutum daga gudan
jini.
3. Ka yi karatu, kuma Ubangi-
jinka Shi ne Mafi karimci.
4. Wanda Ya sanar (da mutum)
game da alkalami
5. Ya sanar da mutum abin da
bai sani ba.
6. A'aha! Lalle,ne mutum, haki-
ka, yana girman kai (ya ki karatu).
7. Domin ya ga kansa, ya wada-
ta.
8. Lalle ne zuwa ga Ubangijinka
makoma take,
9. Shin, ka ga wanda ke hana,
10. Bawa idan ya yi salla?
11. Ashe, ka gani, idan (shi ba-
wan) ya kasance a kan shiriya?
12. Ko ya yi umurni da takawa?
943
96 - Suratul 4 Ala£
\m\m-\^
13. Ashe, ka gani, idan (shi mai
hanin) ya karyata, kuma ya juya
bay a?
14. Ashe, bai sani ba cewa Allah
Yana gani?
75. A'aha! Lalle ne idan bai
hanu ba, lalle ne za Mu ja gashin
makwarkwacfa
16. Makwarkwacfa makarya-
ciya, mai laifi.
17. Sai ya kirayi kungiyarsa.
18. Za Mu kirayi Zabaniyawa
(mala'iku masu girma).
19. A'aha, kada ka blshi. Kuma
ka yi tawali'u, (1) kuma ka nemi
kusanta (zuwa ga Ubangijinka).
Tana karantar da son Allah ga wannan aFumma ta Musulmi,
da Ya ba su Lailatul Kadari domin Ya yawaita ladar ayyukansu ko
da yake rayukansu ba su da tsawo kamar na aFummomin farko.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Lalle ne Mu, Mun saukar da
shi (Alkur'ani) a cikin Lailatul Ka-
dari (daren daraja)
3jISIi^4iJ>l!l
(1) Wato salla da sauran ibadodi.
944
97 - Suratul JCadr
i^j^-nv
2. To, me ya sanar da kai abin da
ake cewa Lailatul Kadari?
3. Lailatul Kadari mafi alheri ne
daga wasu watanni dubu.
4. Mala'iku da Ruhi suna sauka
a cikinsa da iznin Ubangijinsu sabo-
da kowane umurni.
5. Sallama ne shi daren, har fltar
alfijiri.
Tana karantar da halayen kafirai da mutanen Littafi, wato
Yahudu da Nasara game da Annabi, tslra da amincin Allah su
tabbata a gare shi, a gabanin da bayan bayyanarsa.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Warfanda suka kafirta daga
mutanen Littafi, da mushirikai, ba
su kasance masu gushewa daga gas-
kiya ba har hujja ta je musu.
2. Wani Manzo (1) daga Allah,
yana karatun wasu takardu masu
tsarki.
(1) Shi ne Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, domin babu
wanda ya dace da abin da ke cikin littafansu sai shi.
945
98 — Suratul Bayyina
&%$%&- AA
3. Ajrikinsu akwai wasu littafai
masu lama da daraja.
4. Kuma wadanda aka bai wa
Littafi ba su sa6a wa juna ba face
bayan hujjar ta je musu.
5. Kuma ba a umarce su da
kome ba, face bauta wa Allah, suna
masu tsarkake addinin gare Shi,
masu karkata zuwa ga addinin gas-
kiya, kuma su tsai da salla kuma su
bayar da zakka, kuma wannan shi
ne addinin wacfanda suke a kan
hanyar kwarai.
6. Lalle ne wadanda suka kafirta
daga mutanen Littafi da mushirikai
suna cikin wutar Jahannama, suna
madawwama a cikinta. Wadannan
su ne mafi ashararancin talikai.
7. Lalle ne wadanda suka yi ima-
ni, kuma suka aikata ayyukan kwa-
rai, wadannan su ne mafifita alherin
halitta.
8. Sakamakonsu, a wurin
Ubangijinsu, shi ne gidajen Aljan-
nar zama, koramu na gudana daga
karkashinsu, suna madawwama a
cikinta har abada. Allah Ya yarda
da su, kuma su, sun yarda da Shi.
Wannan sakamako ne ga wanda ya
ji tsoron Ubangijinsa.
946
99 — Suratuz Zalzala
m$&-\\
sCratuz zalzala
M»
J^
Tana karantar da yadda motsin Tashin Kiyama yake, da bai
wa mutane sakamakon ayyukansu.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Idan aka girgiza kasa, girgi-
zawarta.
2. Kuma kasa ta fitar da kayan-
ta, masu nauyi,
5. Kuma mutum ya ce "Me ne ya
same ta?"
4. A ranar nan, za ta facfi laba-
rinta,
5. Cewa Ubangijinka Ya yi
umurni zuwa gare ta.
6. A ranar nan, mutane za su fito
dabam-dabam domin a nuna musu
ayyukansu.
7. To, wanda ya aikata (wani
aiki) gwargwadon nauyin zarra, na
alheri, zai gan shi;
8. Kuma wanda ya aikata
gwargwadon nauyin zarra na shar-
ri, zai gan shi.
947
100 - Suratul 'Adiyat
^mm^-v
Tana karantar da yadda ake yin hari da lokacin da ake yakin
kafirai, da dalilin da ya sa a yake su.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
1. Ina rantsuwa da dawaki masu
gudu suna fitar da kukan ciki.
2. Masu kyasta wuta (da kofa-
tansu a kan duwatsu) kyastawa
3. Sa'an nan masu yin hari a
lokacin asuba,
4. Sai su motsar da kura game da
shi.
5. Sai su shiga, game da ita (ku-
rar), a tsakanin jama'ar makiya.
6. Lalle ne mutum mai tsananin
butulci ne ga Ubangijinsa.
7. Lalle ne shi mai shaida ne a
kan laiflnsa da haka.
8. Kuma lalle ne ga dukiya shi
mai tsananin so ne.
9. Shin, ba ya da sanin lokacin
da aka tone abin da yake cikin
kaburbura,
10. Aka bayyana abin da ke ci-
kin zukata,
11. Lalle ne Ubangijinsu, game
da su, a ranar nan, Mai
kididdigewa ne ?
948
101 - Suratul Kari'a
easa^-M
Tana bayanin Ranar Kiyama wajen halin fitar mutane daga
kaburbura da halayen kasa da rabuwar mutane bayan hisabi, wasu
zuwa Aljanna wasu zuwa wuta, a bayan busar kaho ta biyu.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
7. Mai kwankwasar (zukata da
tsoro) !
2. Me ne mai kawankwasa?
3. Kuma me ya sanar da kai abin
da ake ce wa mai kwankwasa?
4. Ranar da mutane za su kasan-
ce kamar 'ya'yan fari masu watsu-
wa.
5. Kuma duwatsu su kasance ka-
mar gashin sufin da aka sa6e.
6. To, amma wanda ma'aunansa
suka yi nauyi,
7. To, shi yana a cikin wata
rayuwa yardadda.
8. Kuma amma wanda ma'au-
nansa suka yi sauki (babu nauyi),
9. To, uwarsa Hawiya ce.
10. Kuma me ya sanar da kai me
ne ita?
77. Wata wuta ce mai zafi.
3^
949
102 - Suratut Takathur
$mm-\*
Tana bayanin hana alfahari, saboda dukiya ko dangi.
* j* s i * s **
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Alfahari da yawan dukiya da
dangi ya shagaltar da ku (daga
ibada mai amfaninku).
2. Har kuka ziyarci kaburbura.
5. A'aha! (Nan gaba) za ku sani.
4. Sa'an nan, tabbas, za ku sani.
5. Haklka, da kuna da sani, sani
na yakini.
6. Lalle ne da kuna ganin Jahim.
7. Sa'an nan lalle ne za ku gan ta,
da idanu, bayyane.
8. Sa'an nan lalle ne za a tam-
baye ku, a ranar nan, labarin
ni'imar (da aka yi muku).
Af.^-f^ '*&
,or* "
950
103 - Suratul 'Asr
fe^llM-vr
Tana bayanin cewa kome mutum ya yi a lokacinsa hasara ne da
6arnar zarafi, sai fa idan ibada ce yake yi.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ina rantsuwa da zamani. (1)
2. Lalle ne mutum yana a cikin
hasara,
3. Face wadanda suka yi Imani,
kuma suka aikata ayyukan kwarai,
kuma suka yi wa juna wasiyya da
bin gaskiya, kuma suka yi wa juna
wasiyya da yin hakuri (su kam, ba
su cikin hasara).
(1) Wasu suna fassarawa da wakatin sallar Asar da kuma marece. A kowane dai, an
bai wa wakati muhimmanci, zamani yana yanke wanda bai yanke shi ba. Ba ya halatta ga
mutum wata mudda ta zamani ta wuce shi bai san amfanin da ya sama wa kansa a cikinta
ba, kuma kome ya samu idan ba addini ba ne, to, hasara ce.
951
104 — Suratul Humaza
>i§2!l&&-vi
Tana bayani ga hana aibanta wasu mutane, da hana glba da
racfa a tsakanin Musulmi domin ginin al'umma ya tabbata, wanda
ya karya shi, a sanya shi wuta ta cikin ginin shika-shikai.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Bone ya tabbata ga duk mai
nune, mai zuncfe (mai racfa)
2. Wanda ya tara dukiya, kuma
ya mayar da ita abar tattalinsa.
3. Yana zaton cewa dukiyarsa za
ta dawwamar da shi.
4. A'aha! Lalle ne za a jefa shi a
cikin Hudama.
5. Kuma me ya sanar da kai abin
da ake ce wa Hudama?
6. Wutar Allah ce wadda ake
hurawa.
7. Wadda take lekawa a kan
zukata.
8. Lalle ne ita abar kullewa ce a
kansu.
9. A cikin wasu ginshikai
mlkakku.
> 1 > i *».
952
105 - Suratul Fil
£l^jjg£-V0
Tana nuna darajar Hurumin Makkah, yadda Allah Yake
halakar da mai nufinta da yaki ko wani sharri.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ashe, ba ka ga yadda Ubangi-
jinka Ya aikata ga mutanen giwa (1)
ba?
2 Ashe, bai sanya kaidinsu a
cikin 6ata ba?
3. Kuma Ya sako, a kansu, wasu
tsuntsaye, jama'a-jama'a.
4. Suna jifar su da wasu duwat-
su na yum6un wuta,
5. Sa'an nan Ya sanya su kamar
karmami wanda aka cinye?
JuJfvJ^l^JJ^J^JjJl
(I) An yi Yakin Giwa shekarar haifuwar Annabi, tsakanin halaka su da haifuwarsa
kwana hamsin. Bayan shekara arba'in Annabi ya fara karantar da mutane. Ya karantar da
su cikin shekara ashirin da uku, sa'an nan ya kaura. Bayansa da shekara hamsin wadanda
suka bi shi suka cinye duniya. Wannan yana nuna cewa mutane ba su samun daraja sai da
rikon addini da ilimi.
953
106 - Suratu Kuraish
$£?!&&- v"\
Tana bayyana darajar Kuraishawa da taimakon da Allah Yake
yi musu. Hade take da Surar Giwa, amma aka raba su da Basmala,
domin a bambanta darajar Hurumin garin Makkah da kuma ta
Kuraishawa kabilar Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Saboda sabon Kuraishawa,
2. Sabonsunatafiyarhunturuda
ta bazara,
3. Saboda haka, sai su bauta wa
Ubangijin wannan Gida (Ka'abah).
4. Wanda Ya ciyar da su (Ya
hana su) daga yunwa, kuma Ya
amintar da su daga wani tsoro.
*'*' 7>
4^J^
954
107 - Suratul Ma 4 un
£&£Uj&-vv
Tana bayanin yadda za a iya gane munafuki da halayensa a
tsakanin Musulmi.
•£*■
Z)a sunan Allah, Mai rahama, Mai jin Rai.
1. Shin, ka ga wanda ke Raryata-
wa game da sakamako?
2. To, wannan shi ne ke tunkude
maraya (daga hakkinsa).
3. Kuma ba ya kwadaitarwa bisa
bayar da abinci ga matalauci.
4. To, bone ya tabbata ga masal-
lata,
5. Wadanda suke masu shagala
daga sallarsu,
6. Wadanda suke yin riya (ga
ayyukansu)
7. Kuma suna hana taimako.
3 >^^^v4 j ^^^^y
+* * y y
Z$\ ' > i-^ff ^ *y*yy
1*1 Uj^LJl0>«^JJ
955
108 - Suratul Kauthar 109 - Suratul Kafirun
mm%&-" 0®m-^
Tana nuna darajar Annabi zuwa ga Allah, yadda Yake yi masa
kyauta kuma Ya yi masa facfa da makiyinsa.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Lalle ne Mu, Mun yi maka
kyauta mai yawa.
2. Saboda haka, ka yi salla do-
min Ubangijinka, kuma ka soke
(baiko, wato sukar rakumi).
3. Lalle mai aibanta ka, shi ne
mai yankakkiyar albarka.
*x^7>V S.*s <* ys
ljC%)J^i
Tana bayanin cewa ba a sassautawa ga gaskiya game da addini,
domin neman yardar wasu mutane ko wani mutum.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Kace, "Yakukafirai!
2. "Ba zan bauta wa abin da
kuke bauta wa ba.
y »<* ^>'fr ^ **
956
110 — Suratun Nasr
&gOJjg£_\\.
J. u Kuma ku, ba ku zama masu
bauta wa abin da nake bauta wa
ba.
4. "Kuma nTban zama mai bau-
ta wa abin da kuka bauta wa ba.
5. "Kuma ku, ba ku zama masu
bauta wa abin da nake (1) bauta wa
ba.
6. "Addininku na gare ku, kuma
addinina yana gare ni."
§jFj&Sfl3fy
SI JL^I La OjJLlP^I Vj
W&*Qjy&2jR
Tana nuna karewar aikin Annabi na Manzanci, kuma tana
nuna abin da tsoho zai kama yi idan aikin karfi ya buwaye shi.
-* >* ■ > • ** • -*
Z>a 5w«a« Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Idan taimakon Allah ya zo da
cin nasara.
2. Kuma ka ga mutane suna Shi-
ga addinin Allah, kungiya-kungiya.
3. To, ka yi tasbihi game da gode
wa Ubangijinka, kuma ka neme Shi
gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya
kasance Mai karbar tuba ne.
> »■ ^\f^ 4'\*' * "T ^"O^ i "T i
(1) Aya ta 4 da ta 5 sun nuna addinin icarya yakan canza amma na gaskiya ba ya
canzawa.
957
Ill — Suratul Masad
«gUj££-w
Tana nuna hushin Allah ga makiyin Annabi. Kuma ita da
surorin da suke bayanta suna nuna dogewar^ kiyayyar kafirai ga
addini bayan kaurar Annabi, da dogewar addini na gaskiya, kuma
Allah zai tsare Musulmin kwarai daga dukan sharrin masu camfe-
camfe da masu sanya dasisa a cikinsa.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Hannaye biyu na Abulahabi
sun halaka, kuma ya halaka.
2. Dukiyarsa ba ta tsare masa
kome ba, da abin da ya tara.
3. Za ya shiga wuta mai huruwa.
4. Tare da matarsa, mai daukar
itacen (wuta) {1) .
5. A cikin kyakkyawan wuyanta
akwai igiya ta kaba (Ranar
Kiyama).
'< S y ./' s
(0 Ana fassara shi da mai tsegumi, watau annamimanci ; da Larabci ana ce wa mai
annamimanci "mai daukar itacen wuta".
958
112 - Suratul Ikhlas 113 - Suratul Fala£
im)m-"r e^K^-w
Tana karantar da tauhidi, watau katfaita Allah Wanda ke kare
addininSa daga makiyansa.
4*33&&
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ka ce, "Shi ne Allah Maka-
cfaici,
2. "Allah Wanda ake nufin Sa
da bukata.
3. "Bai haifa ba, kuma ba a haife
Shi ba.
4. "Kuma babu daya da ya ka-
sance tamka a gare Shi."
*^> •*
CD jlC^tSiT^T
>,4)jK-?j»Jj
L- i...U B i.UJP.lU.lllM'
S^IJM
Tana karantar da yadda ake neman tsarin Allah daga sharri
duka, daga makiyi na bayyane.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
1. Ka ce "Ina neman tsari ga
Ubangijin safiya
jXiJ'C^^y^j*
959
114 — Suratun Nas
&?l3ti££-m
2. "Daga sharrin abin da Ya
halitta.
3. "Da sharrin dare, idan ya yi
duhu.
4. "Da sharrin mata masu tofi a
cikin kulle-kulle.
5. "Da sharrin mai hasada idan
ya yi hasada".
y^y . y - '
Tana karantar da yadda ake neman tsari daga sharrin Shaidan
na mutum da na aljani.
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.
j£\ .<*.; - - > > t 1-
/. Ka ce "Ina neman tsari ga
Ubangijin mutane.
2. "Mamallakin mutane.
J. "Abin bautawar mutane.
4. "Daga sharrin mai sanya wa-
suwasi, mai 6oyewa. (1)
5. "Wanda ke sanya wasuwasi a
cikin kirazan mutane.
6. "Daga aljannu da mutane."
./*^Tf -"<
JLxll
-11*11
(1) Shaicfan yakan boye idan ya ji an ambaci sunan Allah, domin haka aka yi masa
suna mai-66yewa, wato ba ya zama wurin da ake karatu da wa'azi, kamar yadda ba ya
zama cikin zuciyar mutum mai ibada da gaskiya. Ibada ta gaskiya ita ce wadda aka yi ta
kamar yadda Allah Ya ce a yi ta. Banda ibadar bidfa, ba ta korar Shaidan. Kuma da
sharadln a yi ibadar da kyakkyawar niyya, domin aikin da babu niyya mai kyawo game da
shi 6atacce ne.
960
. jJL-j aJp aDI J^
i
aJj£)Ij ^aJl Jl aj^ aDI ^j JUp j> j\£p JLil^Jl iiJiU l^
♦J^wd^j t ijjJiil J^-^^ aJU*- c£ JlJ! ^Lj>c^ailj t i-X*j *LiJ^
. J> % >b>-Nl JUP jUJl ^y-y £•
jL^Sfi ^ ^^Jji r L^5 ( (ji>i j^ jp jgju ^r j
961
Lft^pj t J^JAjJI ^L-»^J *j-*j^ i-Jj»U» ^l^T J i,jL. t^^o-
j* LgpLjIj jviJl 4_»l^lj oy*>Li)l 4_JI^>-I JJIjl jLrf Jl^
^L.^ «^-*>Jl i*Ji>U j . ^jj-iLLJI 4/5UIJ «*iJl d~i-» ^bT
t Jjjdl JL-*£ ^yiil « OLJI ^>~i£ » _j . W^J i-M^
^jS)) j «JIj£J( JL*P ^ JU^ ^ ^ ^U)l J[l c^llS")) j^
( -jJl l^LJb^ <j ks>JS\ <5)j \£ If Lv^U-j 4-ijSj jLj jl>-U
962
. &Lill oljil ^ ^ikJU W^ «-*>9 V^lr'J
UJOu <jJl Jj» ( • ) *-ft3l J.JT7.U..U ^aUM £-^JJ
d£j . AiSu£-H : y c li»>^ %^j V^j J* J-^J ^^^
*Jt>y *JUJ laJj C-iJj ^-^>} Jai^J L^l <J 3j>Cj» \j>Jj*j ^j\
' *
*-V~ <^' <^y (*) (^*^ ^-W) *£*** ft ^ t^b &*JJ
4PyL £~£ ^Ji* Ai\ Jpj .JyH ^JJi OjC J* Jjo
,> »> ^
J : yi c i.lT UUol jlsll J JjSfl r lPil J* jjb
* -J >,- ,*
^ *
963
*sp£3i-iP«- &*/-&
cr 1 ^ a* V^j (^ p**k» y> ^j OL~Ul 4PyL ^y>- ^Ji- yb *&
r L_p^vi jp ji jb JiJLu ? -£- '•&> W«isjj
J 5 Sj/dil <J>j/-l 01 — jp! Jp JJb" S^unJl <AbH?
964
^=*}ivliys : j£ c If- jkJl V^J <*-* V^-*^ OL>-Uail
^ *<\s ^Uall J dJUi jLjJ cj& 3 '^Ji\ ol^Jl u^
J jJUij ^1 iLsJU J — U^JI 01 Jp Ji jLaJl c^£ Oi- 51
•!• cjjJ Jp JJb «-y-l Jy ( ~ ) iJ^Ul dJL» ^i?jj
. UJOu
965
I 'j\ : j A c ijyJ\ j hy\ dU; ijp Jp \ fJ^j i»Nl
jbry N dliJOi «J» «#» J-i W-^j jj£ ^j 0^Vfi*
i *
. 5jl>w1JI v^>* J* J^i **^ <3j* Jr*-*' J 8 -^ *£~*33
£> r Jp JJL. 4-JT JOw ( f ) UM\ OJ-fc £->JJ
>C" l\"\
c^ ( ) J-£sJl <4^l ix-^Jl *JUM aJifclt ^jj
r i_^vi ^ ji . jijjjp^bJoifc; : ju ^ ^
ISJA d\ Jl SjLil i*^ jjaJl j^ ^ (OoUJl ^ yy)
966
. <jJ^fy S^J>I Ju (j\ j*>
oUlfll jiaju J j^ty d^» Jj» CfrJ» wJf £*jj
* 4_«UJi S,j_~o ^3\j jS^> iiyJ^JLi ijj— *> ^ bJ3/i 7
*UI Jb^ £. t JjNl *UI Jp OjOi i^U- ^ dUij t £*-j^
Owll ^ £>y i jLgJ^I Jp aMjOJ J*.uJl i,*>Vp ^ oUl
jjjj ijy~> «$L- IjjIp c-£~Jl Jp aSSjM ^ XjC^ ^ Jf
Sj^Lstf ftli jU-lj . J-M»j-N JU- J i-la^ £y. «UI «I* ilstf Jp JOj
967
UJOy j£> 1 li} ^it^Jall ail JJI j^ ^^4 <LaJl oSa Oj&j
If-ip **i*yb c ^ UJOu J^li[ Ju^aidl ail J~i j^ Oj&j
: ■**> > <!*> < 4 $$i
^JUJI :yLJJ j>w? *U JS^ Laj /%-m^Ip <jp U*ai>- Jl SapUllj
*l^l, Jji^Sfi J^ J ^4^1^ J*«J ^ *UI - (Y)
aJU t Jc 5 ! S,^ J ^ ^ ^ JiiJ ^ *UI - (r)
: JUj aJJ J 4*4-j)> Jii3 J Nl l*U^I
US"L- fl \ST^>«i« l^JLiL. Oisi *lj~- *UI oJla ju>U ^- ; SL. Ii| Ul
968
*e$^ 4Mf i^5C> ' <4&Jffi> : c>- V A
^O- ji — ^ y?\ i jr * j ^ -^3i; )> Ja — iJ J - (*)
• ^ , l^ ^^
j( — ^ oljVi s,^ j <^ SLJfc ^> Ji — aJ J> - (f)
~ 4 1 jii^ : I .^Uj 1 5^/1 oJNl oLJI : U*jl>-I
969
.« j^' ^A? j^' jj»" * or*-~^ **& J
jj^> jiljiU <_/a*J- ck/ s ?» JjkJl 1(8* <JJ^ ^1 £**!^J 4 '•**
Oj***. &cgj)l v^-y^l : y 1 - * £pU' «-a-»j" *-/** >
fi I yd c jvijaJl <j^ |)lj* J^4-I Jfijli V*P C
$> '- *■ i J? W & c ^ ^ *** *
z£$ -.y 1 4 J)' ^ Li J JI ^ £• >^ «- U J Jl ^^ ^
! * * t J
Oywyl ju>-I Jp <J*j I3J cL~£ <J£yl JiU; 3/>U * *
970
Alamun Dakatawa
Wacfannan su ne alamun da ake sawa bisa haruffa ko kalmomi don a
nuna inda ya kamata mai karatu ya tsaya ko kada ya tsaya
* Dakatawar tilas
V An hana dakatawa
C Cikakkiyar dakatawa ta ganin dama
i~ Dakatawa ta ganin dama, amma wucewa da karatu ya fi
& Dakatawa ta ganin dama, amma dakatawar ta fi
971
Kamus
Kamus
Adifa: Raunin hankali mai sa a yi hushi da
"Da'a: Hah" na gari
sauri ko a yarda da sauri, kamar han-
"Dabakoki: Hawa hawa da yawa irin na
kalin mata
bene
Aiwata: Aikata
Akiba: Sakamakon aFamarin da ake
Facce : T)ebe shamaki tsakanin ruwa biyu
aikatawa
masu karfi
AkTda: Kudurin zuciya game da imaninta
Fajirai: Masu saba wa shari'a da gangan,
ga wani abu
watau fasikai
Alaka: A bin da ya hada wasu abubuwa
Fajiri: Fasiki, mai saba wa shari'a da
biyu
gangan
Alharini: Tufa mai taushi ta siliki
Fakankani: Jam'in Fako
Fako : Wurin da ba ya jika da ruwa kuma
Badadayi: Masoyin da ake jin dadi da
ba ya fitar da tsiron ciyawa
ganinsa
Fasadi: "Barna da keta dokar shari'a
Ba'im: Sakin auren da ba a iya mayarwa
Fawwala : Mayar da dibara ga wani ko ga
sai an daura wani auren
Allah
Bakanta: Rantsuwar cika alkawari
Finjali: Kofi, tambulan
Bakarare: Wanda ba ya haihuwa
Furu'a: Mas'alolin da ake fahimta da
Bakarariya: Mace wadda ba ta haihuwa
Alkur'ani ko Hadisi, ko sanin Addinin
Bananci: Barkwanci, kakaci, wargi, wasa
Musulunci bisa ka'idodinsa
Bara'a: Yafewa daga laifi
Barranta: Tsira daga laifin da ake tuhu-
Gafala: Rashin kula har wani abin tsoro
mar mutum da shi
ya auku
Barrantacce: Wanda ya tsira daga laifin
Gafalallu: Marasa kula ga abin da zai
da ake tuhumar sa da shi
auku na wahala gare su
Bice: T)ebe haske; akan ce wuta ta bice,
Gamusa: Rantsuwar karya da gangan
idan haskenta ya 6ace
Giba: Yi da mutum
Biga: Hanya a karkashin kasa
Gincira: Kishingirfa amma ba da nufin
Bijira: ICi bin umurni
barci ba
Bijirewa: Kin bin umurni
Gislln: Mugun abinci mai kaya
Bira: Harshen wuta mara hayaki
Guna: Kankana
Bitattu: Wadanda ba su da basirar gane
Gunda: Dunkulen huren 'ya'yan dabino
gaskiya
tun bai yi huda ba
Gyada: Sunkuyar da kai a kan isharar an
Danyi: Kububawar makafi; wata ciyawa
yarda da maganar abokin hira
ce mai kaya da rakuma ke ci
Daranta: Sa wani ya yi dariya
Hanana: Kishi domin tsaron al'ada
Darbuka: Tanti a kan sirdin rakumi don
Hasili: Abin da ya tabbata daga wata
mata
mas'ala; sakamakon da aka samu
Darba: Zuman kudan rakuwa
bayan binciken wani al'amari
Darkaka: Ci gaba da tafiya kome wuya
Hinsi: Karya rantsuwa
Dasisa: Abin da yake a ido alheri ne,
Hiyaka: Aikata abin da ya fi dacewa ko
amma akwai sharri cikinsa
wanda ya fi tsanani
972
Kamus
Hul'i: Fansar igiyar aure domin miji ya
saki matarsa
Hususlyya: Abin da wani ya keftanta da
shi
Idiraki: Ji a jiki da fahimta
Ijtihadi : Tunani a binciken wata mas'ala
domin fitar da hukunci
Ikrari : Tabbatarwa da bakin mai magana
Ilhadi: Karkatar da hukunci domin wata
manufa
Ilhama: Fahimtarwa daga Allah
Illiyyina : Wurin da ake aje ayyuka nagari
Inabi: T)an itace mai kama da tsada
Inabobi: Jam'in Inabi
Isma: Tsarewar Allah ga annabawa don
kada su yi wani zunubi
Istidraji: Saurara wa mai zunubi har ya
aukar da kansa ga musifa
Istirja'i : Mayar da al'amari ga Allah tare
da neman taimakonSa
Jalala: Girma na Allah kawai, watau
daukaka
Jannaye: Hanyar abinci daga baki zuwa
ciki, ko jijiyar da ta hada kwakwalwa
da lakar kashin baya
Jizya: Kudln haraji
Kaidi: Mugun shiri
Kakaci: Ba'a, barkwanci, wargi, wasa
Kallafa: Lazamta; dora wa wani al'amari
ko hali tilas
Kamunga : A sayar wa mutum da abu da
tsada ko a saya daga gare shi da arha
don rashin saninsa ko wayonsa
Kankana: Guna
Karankarma: Kashin ban wargi, kashin
nan na tsakanin kirji, da kafada
Kinaya: Lakabi ga mutum domin girma-
ma shi
Kundukuki : Gefen goshi na dama ko na
hagu
Kwarkwada: Gashin goshi
Kindari: Dukiya mai yawa, kamar dinari
dubu goma sha biyu
Kisasi : Hukunci ga rama laifin yi wa wani
rauni
Kukumi : Marin wuya ; daure hannu a wuya
Kukumma: Jam'in Kukumi
Kyacewa: Kudurce laifin wani a cikin
zuciya domin ramawa
Kyami: Azara ta rufin daki
La'Tmi: Mara son alheri
Lallage: Shan ruwa da harshe irin na kare
Li'abi: T)an'uwa wanda aka hada uba
kawai da shi
Li'ani: Rantsuwar miji domin kore da ko
ganin zinar matarsa, da rantsuwar ma-
tar domin kare kanta
Li'ummai: 'Yan'uwan da aka hada uwa
kawai da su, uba kowa da nasa
Mahakama: T>akin Shari'a; kotu
Makai : Abin dibar ruwa, kamar kwarya
ko buta
Makkana: Mallaka, tabbata
Makwarkwada: Keya
Mannu: Dar6a, watau zuman kudan
rakuwa
Mara: Lamba kamar 1, 3, 5, 7 da sauransu
MaremarT: Jam'in Marmaro
Marmaro: Idon ruwa mai gudana
Mashi'a: Nufin Allah
Mubahala: Rantsuwa domin a tsine wa
mai karya
Mubaya'a: Nuna biyayya
Mudda: Lokaci iyakantacce
Mukarana: Auna abubuwa biyu ko gwa-
ma su domin a ga bambanci
Munazara: Hada karfi domin binciken
wata mas'ala
Murli: Nonon dabino
Mu'utumadi: Maganar da ake dogara a
kanta
Nafyi: Korewa ga magana, kamar a ce
"bai yi ba"
Rabbanta: Samun rabo
RakTki: Siriri kwarai
Rango: 'Yar hanya tsakanin duwatsu
Rauno: Ciyawa da aka daddage
Rububiyya : Siffar Allah ta mallakar kome
Ru6ushi: Hasara a Lahira
Ruhbanawa: Masu ibada daga cikin Ki-
rista wadanda suka yanke kansu daga
973
Kamus
jin dacfin duniya sabo da yin ibada.
Tasarrufi: Jujjuya abubuwa, kamar saye
Rumata: Tsare mutum ga magana da
da sayarwa
hujja
Tasawwufi: Kebance kai domin ibada irin
Rummani : 'Ya'yan wani itace wanda aka
ta Kirista
fi samunsa a kasashen Larabawa
Tasgaro: Abin da ba ya sayuwa sam
TasnTm : Suna ne na wani marmaro wanda
Sa'ada: Jin dacfin Lahira
zababbun 'yan Aljanna ke sha daga
Sakandami: Abin wuya; zanen riga ge-
gare shi
waye da wuyanta
Taukifiyyai: Abubuwan da za a tsaya a
Salladar: Bayar da iko a kan wani abu
kansu kamar yadda shari'a ta fada
Salsabll : Suna ne na idon ruwa a Aljanna
Tawada: A yi addu'a a tofa a kurji ko a
Salwa: 'Ya'yan shila
ruwa
Sansance : Ganewa a jika
Tawali'u: Kaskan da kai
Sanwa: Tsuntsaye su yi layi a sama da
Tawassuli: Neman hanya
fikafikansu bude
TawTli: Bai wa wata magana fassara
Saryar: A hutar da mutum daga daukar
Togewa: Kin yin abu, ko janye abin da
kaya
mutum ya ce
Sauma'a: Gidan ibadar mai halwa ta
Tsatso: Kugu
Kirista
Tsirfatawa : Sana'antawa
Sauna: Jin tsoro game da lura
Tsiwirwiri : Sana'a domin neman riba
Shafaki: Lokacin da rana ta yi ja bayan
Tunkuba: Rigyawa ko karikitan da ruwa
fadawarta
ke turawa
Shakawa: Rashin arzikin Lahira
Shibhohi : Abin da yake kama da gaskiya
Ukuba: Azaba domin wani laifi
a wani fanni, kuma ya yi kama da
Uluhiyya: Siffar Allah ta yin doka da
karya ta wani fannin
hukunci na halattawa ko haramtawa
Sijjlnu: Wurin da ake aje zunubai
Sofane : T)igon wani launi dabam a tsaka-
Wabili: Mamako, ruwan sama mai yawa
nin wani launin
WadT: Fili tsakanin duwatsu
Sufi : Abin yin tufa mai kama da wul
Wahami: Karkatattar fahimta
Wakkala: Dogara ga Allah
Ta'akibi: Karin bayani ga muhimman
Waraka : Warkewa daga jahilci
aFamurra ko kanun labaru
Wasaki: Babbar guga ta fata
Ta'aliki : Riskar da hukuncin abin da aka
Wasidar: Tsani, dalilin sadarwa
sani zuwa ga wani abu da sharhin
magana
Yakini : Sakankancewa ko imani mai karfi
Tabanni : Mayar da dan wani naka, kamar
Yula: Harshen wuta
dan hankaka
Yulaye: Jam'in Yula
Tadbiri: Tsara aKamaii gabanin a guda-
Yunke: A rufe a sa hatimi
nar da shi
Tafsili: Bayani filla-filla
Zambiyoyi: Filayen da ke tsakanin tako
Tahajjudi: Rashin barci domin yin ibada
da tako a tafiya
da dare
Zanjabil: Citta mai yatsu
Talakiya: Wani itace wanda ake asuwaki
Zihari : Haramta mata ta hanyar daidaita
da shi
ta da wadda ta haramta ba da niyyar
Talalabanta: Fadawa a santsi
saki ba sai da niyyar waharlarwa kawai
Tamani: Kimar abin sayarwa
Zira'i: Kamu guda, wato awon tsawo
Tambihi: Farkarwa; fadakarwa
daga guiwar hannu zuwa karshen yat-
sar tsakiya ta hannu
974
Fihirisa
Fihirisa
Lamba ta farko ta sura ce, wadda ke cikin baka kuwa ta aya ce. Misali: 5 (91) daidai
take da a ce Sura ta 5, aya ta 91. Game da sunan sura kuwa, lambar da ke biye da shi ta
shafin da surar ta fara ne.
Idan ba a sami kalmar da ake nema ba, a yi tunanin wata.
A'ala s. 928
Shaicfan ya yaudare shi, shi da Haw-
A'araf 7 (46)
wa'u 2 (36); 7 (20-22); 20 (120-121)
A'araf s. 219
Shaicfan ya yi jayayya 2 (34) ; 7 (1 1) ; 15
'Abasa s. 913
(30); 17(61); 18 (50); 20(116); 38
Abin sha mai sa maye
(73, 74)
dalilin haramtawa 5 (91)
shugaban dukan halitta 2 (34)
haramtawa 2 (219); 5 (90)
ya yi nadama 2 (37); 7 (23)
mataki na biyu ga haramtawa 4 (43)
Addini 2 (256); 4 (80); 50 (45)
mataki na farko ga haramtawa 2 (219)
bambance-bambancensa 2 (17)
mataki na £arshe ga haramtawa 5 (90)
na gaskiya ba ya canzawa 30 (30)
Abinci 2 (172); 5 (1, 3, 4, 96); 6 (119-121);
Dubi kuma Ibada
16 (114, 116-118); 22(34-36)
Addinin Kirista
cin abincin Ahlil Kitab 5 (5)
imani da Annabi Isa 4 (159)
ga Yahudawa 6 (146)
sukarsa ta farko 112 (3).
gidajen da aka halalta wa mutum cin
Addu'a
abinci 24 (61)
ta Ibrahim 2 (126-129); 9 (1 14); 26 (69-
haramtacce 2 (173); 5 (3); 6 (122, 146);
89)
16 (115)
ta Nuhu 71 (26-28)
£in cin halaltacce 5 (87, 88)
ta Sulaiman 27 (19)
AbuLahab 111 (1-3)
ta Yusuf 12 (101)
matarsa 111 (4, 5)
ta Zakariya 19 (4-6)
Abubakar
'Adiyat s. 948
sahibin Manzon Allah ne 9 (40)
Ahftaf s. 762
Adalci 4(105); 16 (90)
Ahzab s. 633
Adamu 2 (33, 35); 3 (33, 59); 20
Ai'bi
(123-127)
facfinsa 4 (148)
a Aljanna da Hawwa'u 2 (35); 7 (19);
Aiki mummuna
20(115-119)
horo ya yi daidai da shi 10 (27); 42 (40)
an hana shi da Hawwa'u kusantar itace
kore shi da aiki nagari 13 (22); 23 (96);
2 (35); 7 (19)
41 (34)
an kammala shi 15 (28); 38 (72)
£iyayyar mutum ga kansa 40 (10)
an zabe shi, shi da zuriyarsa 3 (32)
sakamakonsa 2 (81); 30 (9, 10)
halitta shi daga turbaya 3 (59); 15 (28);
sakayyarsa 4 (123)
38 (71)
A'isha
laifinsa don mantuwa ne 20 (115)
bata sunanta 24 (11-20)
mai mulkin duniya 2 (30)
Ajiya 4 (58)
mala'iku sun yi masa sujada 2 (34); 7
'Alafc s. 943
(11); 15 (28); 17 (61); 18 (50); 20
Al'arshi 40 (7)
(116); 38(72)
Alfahari 17 (37)
sakamakon cin (fan itace 7 (22); 20
Alfasha
(121)
a guje ta 6 (151)
sanar da shi sunaye 2 (31)
AHmrana s. 73
975
Fihirisa
Aljanna 2 (35, 36, 111); 13 (23); 18 (32,
canja ta 2 (142)
108); 19 (60, 61, 64); 22 (23, 24); 25 (15,
ra'ayoyin Yahudawa da Nasara 2 (145)
16); 36 (54, 55); 38 (49-54); 43 (70-73);
Alkur'ani
44 (51-57); 52 (17-28); 55 (46-78, 89);
a yi shiru a saurari karatunsa 7 (204)
56 (12-40); 76 (12-22)
Allah zai tsare shi 1 5 (9) ; 56 (77-80) ; 85
albarka madawwamiya 11 (108)
(21, 22)
albarka mara misaltuwa 32 (17)
ba a nasara ga 6ata shi 41 (41, 42)
aminci a cikinta 10 (10, 25); 19 (62, 63);
ba aikin Shaidan ne ba 26 (210-212)
36 (56-58)
ba mawaki ya yi shi ba 26 (224-226)
an ba Musulmi daularta 4 (54)
ba shi da wani kamansa 2 (23, 24); 10
an hana wa kafirai daularta 7 (40)
(37-40); 11 (13); 17 (88)
ba bakin ciki, wahala, gajiya 35 (34, 35)
ba shi da wata ilia 4 (82)
dandanonta a wannan duniyar 37 (41-
ba ya baki biyu 39 (23)
47); 89 (27-30)
ba ya tantama 11(1)
ganin Ubangiji cikinta 50 (35)
canjin da ya kawo 13 (31); 84 (1-5)
kama da ita 13 (35)
cikakken jagora 10 (37)
kyau da tsarkinta 37 (41-49)
cikansa ba gi6i 1 7 (89)
karin daukaka a cikinta 39 (20)
daukaka mabiyansa 21 (10); 43 (44)
maganar 'yan aljanna da 'yan wuta 37
dauke da labaru nagari 12 (1-3)
(51-60)
dauke da ra'ayoyi mafiya kyau 29 (49)
masu shiganta 2 (82, 123, 124); 9 (18);
fitar da mutane daga duhu 14 (1)
53 (52)
gargacfi ne ga duk duniya 6 (19); 25 (1)
mazaunin iyalan muminai 40 (8)
girma ga marubutansa 80 (13-16)
samun nasara 78 (31)
harhada shi 75 (17, 18)
tamkar lambu ne 47 (15)
harshensa 43 (3)
yadda take 15 (45-48)
jaddada wahayin farko 2 (41, 89, 101);
yalwarta 3 (132); 57 (21)
6 (93); 28 (51); 35 (31)
'ya'yan itatuwanta 2 (25); 69 (23)
kammalalle mai shiryarwa 5 (3) ; 1 8 (1 , 2)
Aljannu6(101, 113, 129, 130); 7 (38, 179);
kunsa dukan abubuwa masu kyau daga
27 (17, 39)
sauran littafai 98 (3)
ba su san gaibi ba 34 (14, 20)
maganin cututtuka 10(57); 17(82);41 (44)
halitta su daga wuta 7 (12); 15 (27); 32
mai bayanin abin da ya kamata 1 6 (89)
(13); 51 (56); 55 (15, 33, 39)
mai cika abin da aka fadi da can 17
Iblis ne ubansu 18 (50)
(105); 28 (52, 53); 46(12)
mushrikai sun ce aljannu ma tan Allah
mai kiyaye duk wahayoyi 5 (48)
ne 37 (158)
mai shiga zukata 26 (200)
mutane na bauta musu 34 (41); 72 (6)
mai tsarkakewa 29 (45)
Sulaiman ya mallake su 27 (1 7) ; 34 (12-
maye gurbin sauran littafai 16 (10)
14)
Musa ya gaskata shi 11 (17); 46 (10)
sun yi addini irin na Yahudawa 46 (30-
Musulmi na karanta shi a salloli 73 (20)
31)
raba gardama 16 (64)
suna musulunta su yi gargadi 46 (29-
rahama ce 29 (51)
32)
rubuta shi 98 (2)
suna sauraron Alkur'ani 46 (29); 72 (1-
saukar da shi a dare mai albarka 44 (3) ;
15)
97(1)
Alkawari 5 (1); 16 (90); 17 (34)
saukar da shi cikin watan Ramalan 2
Alkalami 96 (4); 3 (44); 68 (1)
(185)
Alkibla 2 (144, 146-150)
saukar da shi cikin zuciyar Annabi 2
an daukaka ta 2 (143)
(97); 26(193, 194)
976
Fihirisa
saukar da shi kacfan kacfan 25 (32)
Mahalicci Mai rayarwa 56 (58-74)
saukarsa nufin Allah ne 55 (1, 2)
Mahaliccin kome 13 (16)
saukaka shi cikin Larabci 44 (58)
Mai falala ga kowa 27 (73)
shiriya daga gare shi 2 (231); 3 (138); 6
Mai fararwa 2 (117)
(70,90,153,155, 157); 7 (40); 10 (1,
Mai gudanar da kome 4 (85)
58); 12(104, 111); 15(1); 16(89); 17
Mai halittawa, ginawa, surantawa 59
(9, 88); 18 (57); 25 (30); 29 (49); 32
(24)
(22); 36 (69, 70); 38 (29); 39 (17,
Mai karBar tuba da roko 42 (25, 26)
18); 41 (41, 44); 45 (20); 54 (17); 57
Mai nuna soyayya ne 11 (90); 85 (13,
(16); 58(5); 81 (27, 28)
14)
tarin koyarwa mafi kyau 39 (27)
Mai rahama ne ga masu zunubi 39 (53)
wahayi ya ba da tsarinsa 25 (32)
Mai raya kasa bayan mutuwarta 30
wasu Larabawa sun yarda da shi 72 (1-
(19)
9)
Mai rayar da kome 1 1 (6)
wulakanta ayoyinsa 4 (140)
Mai rayarwa, mai kashewa 53 (42-46)
ya kunshi hikima 10 (1)
Makusanci ga mutum 50 (16)
yana cfauke da amsoshin gardandami
mika wuya gare Shi 3 (82); 16 (48, 49)
25 (33)
Na hudu ga kowane uku 58 (7)
yana dauke da shiriya da bayanai 2
natsuwar zukata da ambatonSa take 1 3
(185)
(28)
zai yi nasara 20 (2-5)
rahamarSa ta rufe kome 6 (148); 7
Allah
(156); 40 (7)
a ji tsoronSa 3 ( 1 75)
Shi Kadai ne 3 (18); 112 (1-4)
a riki tsammanin rahamarSa 12 (87)
Shi ne Tabbatacce 31 (30)
ba a 6oye Masa 4 (108)
tabbatar samuwarSa 2 (164)
ba biyu ko uku ne ba 4 (171); 16 (51)
taimaka Masa 61 (14)
ba Shi da da 2 (116); 19 (35, 90-93);
tsayar da sammai ba ginshikai 1 3 (2, 3)
112(3)
wadanda ba Ya so 4 (116); 5 (64); 6
ba Ya bukatar hutawa 50 (38)
(141); 9 (19, 27); 10 (81); 16 (23); 39
ba Ya gajiya da halittawa 46 (33)
(3); 40 (28); 61 (5)
bauta Masa Shi Kadai 1 (4); 10 (105-
wadanda Yake so 2 (195, 232); 3 (71,
107); 36 (60, 61); 51 (51); 72 (18, 20)
146, 148, 160); 29 (69)
bin Allah da Ma'aikinSa 4 (59); 8 (1,
wasu daga sifofinSa 59 (23, 24)
13)
Ya halitta kome don rahama 11 (119)
dogara da Shi 3 (101-103, 160)
Ya san abin da ke zuciya 50 (16)
Daya ne 2 (163); 3 (17); 112 (1)
Ya san asiri mafi 6oyuwa 2 (115); 20
gamuwa da Shi 84 (6)
(7)
gode Masa 2 (152)
Ya san bayyananne da 6oyayye 13 (8-
hacfa wani da Shi 4 (26); 26 (213)
10)
halitta sammai da kasa a kwana shida
Ya san faduwar kowane ganye 6 (59)
50 (38)
Ya san kwatankwacin zarra 10 (61); 34
ikonSa ba iyaka 6 (104); 42 (11)
(2, 3); 57 (3, 4)
ilminSa na da yawa, bin shari'a ne tsira
Ya san Sa'a da abin da ke cikin mahai-
18 (109); 31 (27); 55 (15)
fa 41 (47)
ilminSa ya game sammai da kasa 2
Ya san shawara a asirce 58 (7)
(255)
Ya san tunani da furuci 6 (3)
kome na yi Masa sujada 13 (15)
Yana amsa addu'a 2 (186)
kowa ya yi murna da rahamarSa 10
Yana halitta abin da ba ku sani ba 16
(58)
(8)
977
Fihirisa
Yana son masu adalci 5 (42)
Ubangiji ke zaben su 22 (75); 28 (68)
Yana son masu ha£uri 3 (145)
Ansar9 (100, 117)
Yana son masu komawa gare Shi 2
Arafat 2 (198)
(222)
Arziki 13 (26); 17 (30); 53 (48)
Yana son masu kyautata wa wasu 2
masu arziki 3 (180); 4 (26, 27, 38); 24
(195); 3 (133, 147)
(22)
Yana son masu ta£awa 3 (76); 9 (4, 7)
'Asr s. 951
Al'ummoni
Attaura 3 (3, 48, 65, 93); 5 (43, 44, 66, 68,
daukakarsu 13 (11)
110); 7 (157); 9 (111); 48 (29); 61 (6);
halakarsu 7 (34); 17 (16
62(5)
Alwalla 4 (43); 5 (6)
Aure 4 (3, 4)
Amana
da Ahlil Kitab 5 (5)
cinta 3 (161); 4 (29, 30); 8 (27)
da kwarkwara 4 (25)
rikonta 4 (56)
da mushirika ko mushiriki 2 (221)
An'am s. 186
guje wa zina 70 (29-31)
Anbiya s. 484
haninsa 4 (22-25); 5 (5); 14 (32, 33)
Anfal s. 257
ma tan da aka haramta 2 (221); 4 (22-
'Ankabat s. 602
24); 60(10, 11)
Annabawa 2 (61, 91, 136, 177, 213); 3 (21);
mayar da shi 2 (228)
6(83-88, 113)
na bayi 2 (177); 4 (25, 36, 92); 24 (32,
alkawari da su 3 (80); 33 (7)
33); 58 (3); 90 (3)
an ba wasu littafai 6 (90)
na kamammu 60 (10, \\)
an kiyaye wahayin da suke samu 72
na Manzon Allah 35 (50-52)
(28)
sake aure ga mata 2 (232, 234, 235)
ana Bata koyarwarsu 19 (59)
saki na biyu 2 (229);
ba duka aka fadi a Alkur'ani ba 4
saki na uku 2 (230, 231)
(164); 40 (78)
tilas 24 (32, 33)
ba su munafunci 3 (160)
yarjejeniya ce 4 (21)
ba su yin zunubi 21 (25-28)
Dubi kuma Kashe aure
babu sauran annabci bayan Muham-
Mata
mad 21 (30)
Mat an aure
babu su daga aljannu 6 (131)
Miji da mata
bambanci a darajarsu 2 (253)
Zaman gida
daga dukan al'ummomi 10 (47); 13 (7);
Awo na gaskiya 17 (35); 26 (181-184); 55
16 (36); 35 (24)
(9); 83 (6)
duk sun gaskata Annabi 3 (80)
Ayuba 4 (163); 6 (85); 21 (83, 84); 38 (41-
farilla yarda da su 4 (150, 151)
44)
halakar makiyansu 14 (13); 77 (7)
Ayyuka
karbar asirai daga Ubangiji 72 (27)
Bacinsu 25 (23); 47 (1, 8,9)
makiya na zunden su 6 (10); 15 (10,
Ayyuka nagari
11); 36 (30)
awonsu 7 (8, 9)
mutane ne masu tin abinci 21 (7, 8); 25
masu wanzuwa 18 (46)
(20)
Azumi
na karya ba su yin nasara 69 (44-47)
farilta shi 2 (183)
rike gaskiyarsu 23 (51-56)
hakkokinsa 2 (187)
sun zo da bayanai da littafai 16 (43, 44)
jima'i da azumi 2 (187, 196)
suna da mata da 'ya'ya 13 (38)
masu ciwo da matafiya 2 (184, 185)
taimako daga Allah 12 (110); 14 (13-
20); 40 (51)
Badar 3 (123, 140, 165); 8 (18, 49-51); 25
978
Fihirisa
(25, 27); 33 (26); 44 (16); 54 (44-48); 64
sarrafa karfe 34 (10, 11)
(9, 10); 78 (18-20)
ya kashe Jaluta 2 (251)
abokan gaba na son hukunci 8 (19)
ya la' and Yahudawa saboda rashin yi
an karfafa Musulmi 8 (11)
wa juna wa'azi 5 (78)
aukuwarsa 34 (30)
Dhariyat s. 794
aya a kansa 3 (13)
Diyya (na jini) 4 (92)
gudunmawar Allah 3 (122); 8 (9, 17)
Duha s. 940
kafirai na murna 8 (47, 48)
Dukhan, s. 750
karya adawa 20 (129)
Dukiya
mai bayyanar da gaskiya 8 (6-8, 42)
a same ta ta hanyar halal 4 (29)
matsayin mayakan 8 (42)
don rayuwa 4 (5)
sakin fursunoni 8 (70)
girmama ta 2 (188)
Bakara s. 4
sarrafa ta 17 (26, 27, 29); 25 (67)
Balad s. 934
son dukiya 3 (180, 181); 4 (37); 9 (34,
Bani Kuraizah 33 (26)
35); 47 (38)
Bani Natir 59 (2)
ta mai rauni 4 (5)
Bara
Duniya
guje masa 2 (273)
farkonta da karshenta 46 (3)
Bashi 2 (280-284)
Dutsen Sinin 2 (63, 93); 4 (154); 7 (171);
Bashi da ruwa 2 (275-281); 3 (129, 130,
19 (52); 20 (80); 23 (20); 28 (44, 46); 52
230); 4(161); 30 (39)
(l); 95 (2)
Bauta wa wanin Allah 4 (48, 116-121)
Duwatsu
Bayar da hand 2 (188)
amsa girman Ubangiji 34 (10)
Bayi
halitta su 16 (15)
ana son a 'yanta su 47 (4); 90 (13)
hanyar abind 21 (31)
Bayi mata
icusoshin kasa 78 (7)
aurensu 4 (25)
wucewarsu 27 (88); 81 (3)
Bayyina s. 945
T>.H. s. 466
Biyayya 2 (170); 4 (69); 24 (51-54)
Dalafe s. 859
Bokaye 37 (7-10)
T>an fashi 5 (33)
Buruj s. 924
T)an hankaka Dubi Tabanni
Busa Kaho 6 (72, 74); 18 (100); 20
T>arife s. 926
(102); 23 (101); 27 (87); 36 (50); 39
T>arikoki 6 (159)
(68); 69 (13, 14); 74 (8); 78 (18-20);
T>ufanu 54 (11-15); 69 (11); 71 (25, 26); 7
79 (6-9)
(133)
*Bata mafi muni 22 (12)
Dubi kuma Nuhu
T>ur s. 799
Caca2 (219); 5 (90)
dalilin hanawa 5 (91)
Facfa2 (190); 4(30)
Camfi 2 (256, 257); 4 (60)
Fadir s. 656
Ceto 2 (225); 4 (85)
Fajr s. 932
Cewa "In Allah Ya yarda" 18 (22, 23)
Falafe s. 959
Cikamakin Annabawa 33 (40)
Fankama 31 (18); 57 (23)
Farauta 5 (4, 24, 95, 96)
Daraja duniya da lahira 70 (32-35)
Fassara
Dawud 2 (251); 4 (163); 5 (78); 6 (85); 17
dokarta 3 (6)
(55); 21 (78-80); 27 (15, 16); 34 (10-13);
Fat'h s. 776
38 (17-30)
Fatiha s. 3
an ba shi annabci da littafi 4 ( 1 63) ; 6 (85)
FT] s. 953
979
Fihirisa
Fir'auna 2 (49, 50); 3 (10); 7 (130-136); 8
Hajji 2 (158, 189); 3 (97); 22 (28-37)
(52, 54); 10 (75-78, 88-92); 11 (97, 99);
an jaddada maganarsa 22 (27)
17 (101-103); 20 (71-78); 26 (29); 28 (3-
halatta kamun kifi 5 (96); 9 (3)
40); 29 (39); 40 (24-46); 43 (46-56); 44
muhimmancinsa 2 (196-203); 5 (1, 2,
(24-27); 50 (13); 51 (38-40); 54 (41,42);
94-96); 9 (3)
69 (9, 10); 73 (15, 16); 79 (17-25); 85
plla .v. 875
(18); 89 (10-13)
Ha££in mutum 17 (15); 53 (38)
matarsa 28 (9); 66(11)
Halaye nagari
ruwa ya maido gangar jikinsa 10 (92)
dagewa 11 (112); 13(22); 30(43);41 (6,
Fur&an s. 542
30, 31)
Fussilat .v. 720
gaskiya 3 (60); 4 (135); 5 (1 19); 9 (1 19);
16(116); 17 (81); 22 (30); 25 (72); 33
Gado 2 (180-182, 240); 4 (13, 14); 5 (106,
(24, 35, 70); 39 (3, 32); 103 (23)
107)
godiya 2 (152, 172, 185, 243); 5 (6, 89);
dokarsa4(ll, 12, 177)
14 (7, 8); 28 (73); 39 (7, 66); 46 (15)
ga musakai in sun zo wurin rabo 4 (8)
guje wa zina 17 (32); 23 (5); 24 (30, 31,
ga 'ya'yan tabanni 33 (4, 5)
33); 25 (68); 33 (35); 70 (29, 35)
na mara iyaye ko 'ya'ya 4 (1 79)
ha£uri 2 (153-157, 177, 259); 3 (145,
rabon gado 4 (11, 12)
199); 11 (11); 16(126, 127); 28 (80);
wadanda za a ba 4 (7)
29 (58, 59); 39 (10); 42 (43); 103 (2)
Gafartawa 2 (263); 4(17, 18, 64, 106, 1 10);
jaruntaka 2 (38, 177); 3 (172-175); 6
5 (39); 9 (80)
(81-83); 9 (40); 20 (46); 33 (39)
Gaisuwa 4 (86); 24 (60)
mallakar zuciya 4 (135); 7 (201); 18
Ganima 7 (1, 41); 8 (41); 48 (20); 59 (6-8)
(28); 30 (29); 38 (26); 42 (37); 79
Ghafir s. 708
(40, 41)
Ghashiy a .v. 930
nagari na kawo ci gaba, miyagu na
Girma da tfaukaka 2 (269); 4 (32); 6 (83)
hanawa 2 (216), 6 (161); 10 (23); 1 1
12 (71); 39 (49)
(114); 14 (24-26); 16 (75, 76, 97); 25
Gumaka
(70); 53 (31, 39-41); 91 (9, 10); 92 (4-
caba musu ado 43 (18)
10)
masu bauta musu 2 (105, 135); 4 (48,
rashin munafunci 3 (166); 4 (107, 142,
51, 52, 76, 116); 5 (60, 82); 6 (138,
146); 39 (2, 3); 98 (5); 107 (4-6)
139); 9 (1-17, 28, 36, 113); 16 (75);
rashin son kai 2 (207, 262); 3 (91); 4
22 (17); 35 (14, 40); 48 (60)
(53); 6 (163); 11 (51); 59 (9); 64
na duwatsu 5 (3)
(16); 76 (8, 9); 92 (19, 20)
zaginsu 6 (108)
tawali'u 2 (45, 46); 6 (63); 7 (13, 55,
Gwamnati
146)
sai masu cancanta 4 (58)
tsarki 2 (222); 5 (6); 9 (103, 108); 24
da mijalisa 42 (38)
(21); 33 (33); 53 (32); 74 (4, 5); 87
(14); 91 (9, 10)
Hadaya 22 (37)
turakunsu 2 (207, 265); 4 (74, 1 14); 5
HadTd .v. 827
(16); 6 (163); 60(1); 92 (19-21)
Hada kai da taimakon juna 3 (103); 5 (2)
yafewa 2 (109); 3 (133, 158); 4 (149); 5
Haihuwa ga Allah
(13); 7 (199); 12 (92); 24 (22); 41
ba abu ne karbabbe ba 2 (1 16); 6 (102-
(34, 35); 42 (37-40)
104); 10 (68); 18 (4, 5); 19 (35, 91,
Halayya 3 (130-136); 4 (36, 59, 86); 9 (34,
92); 23 (91); 37(149, 159)
35); 17 (26-35); 24 (27, 28, 58, 59, 61);
Haila 2 (222)
25 (63-77); 31 (14-19); 33 (35, 36); 49
Hajj s. 499
(1-18); 60 (1-13)
980
Fihirisa
Halitta
addininsa Musulunci 3 (66)
bambantarta 13 (3, 4)
addu'a don mutanen Ludu 1 1 (74-76)
dabbobi 16 (5); 24(45)
addu'a tare da Isma'il 2 (129)
kama guda 67 (3, 4)
addu'arsa 2 (126-129); 9 (1 14); 1 1 (69);
mutum 4 (1); 6 (2); 7 (2); 15 (26-29); 16
12 (6, 38); 14 (35-41)
(4); 22 (5); 25 (57); 32 (7, 8); 35
aje Isma'il kusa da Ka'aba 14 (37)
(11); 40 (67); 51 (56); 86(6)
an ba shi annabci 2 (124, 131); 3 (66); 4
Haman 28 (6, 8, 38); 29 (39, 40); 40 (24,
(125); 16 (119); 37 (83, 84)
36)
an ba zuriyarsa annabci 29 (27); 37
Hankali
(113); 58 (26)
aiki da shi 2 (44, 73, 242); 5 (58); 6
an masa alkawari 2 (124)
(152); 17 (26); 25 (44); 36 (62); 45
bakinsa 15 (51-60)
(5); 67 (10)
bushara da Isma'il 37 (101)
hana bi ido rufe 2 (170, 171); 5 (104); 7
bushara da samun da 15 (53-56); 51
(129, 179); 43 (22, 23)
(24, 25)
Hanya kyakkyawa 6 (155)
bushara da samun jika 6 (85); 11 (71);
Haruna 2 (248); 4 (163); 7 (122); 20 (29-
19 (49); 21 (72); 29 (27); 37 (112)
35); 28 (34, 35); 37 (114-122)
da fadi-tashin al'ummomi 2 (260)
bauta wa dan maraki na zinari 7 (148);
da mai bautar rana 2 (258)
20 (90, 95)
da manzanni 11 (69, 70); 15 (51, 52); 51
bayaninsa 7 (15)
(24, 25)
da Musa 20 (30); 26 (12); 28 (34, 35)
dangantaka ta kusa da Annabi 3 (67)
ya rika wa Musa shugabanci 7 (142)
hanyar karantarwarsa 6 (75-82)
ya zama Annabi 4 (161); 6 (85); 10
horo da hada kai 2 (132); 43 (28)
(75); 19 (53); 21 (48); 23 (45); 25
Isma'il ya sake gina Ka'aba 2 (127)
(35, 36)
jefa shi wuta 21 (68); 29 (24); 37 (97)
Hashr s. 839
kawar da gumaka daga T)aki Mai
Hijira 9 (40); 25 (54)
Tsarki 2 (125); 22 (26)
Hijr s. 381
littafansa 87 (19)
Hud 7 (65-72); 11 (50-60, 89); 26 (123-
mafarkin yanka dansa 37 (102)
140); 46 (21-26)
mahaifinsa 19 (41-48)
Hud s. 319
Makama Ibrahim 2 (125); 3 (96)
Hudahuda 27 (20)
neman a sami masu ibada 2 ( 1 28) ; 1 4 (40)
Hudaibiya
uban Larabawa 90 (3)
nasara 48 (1)
ya karya gumaka 21 (57, 58); 47 (91-93)
sulhu don Musulmi a Makka 48 (25)
ya roki da nagari 37 (100)
Hujurat s. 784
ya roki gafara don mahaifinsa 9 (114)
Humaza s. 952
ya roki mayar da Makka amintacciya 2
(126)
Ibada 2 (43-46, 125, 149, 150, 238, 239); 4
ya soki bautar gumaka 6 (75); 19 (42-
(43, 101-103); 5 (2, 6, 95); 11 (114); 17
48); 21 (52-56, 62-65); 26 (69, 82);
(78-80); 24 (56); 29 (45); 62 (9, 10)
29 (16, 17); 37 (85-96); 43 (26, 27)
Iblis Dubi Shaidan
ya soki bautar taurari 6 (76-84); 38 (88)
Ibrahim 2 (133-140); 3 (33, 55, 68, 84, 95,
ya tsira daga wuta 21 (69-71); 29 (24-
97); 4 (54, 163); 21 (59-61, 66, 67); 22
26); 37 (98, 99)
(43); 26 (70-81, 83-89); 29 (31); 42 (13);
ya yi addu'a don Makka 14 (37, 38)
51 (26-37)
ya yi imani da Allah 2 (124, 131); 3
abin misali 16 (120); 60 (40)
(66); 4(125); 16(119); 37 (83, 84)
abin tunawa ga al'unima 37 (108-111)
yanke hulda da kafirai 60 (4, 5)
981
Fihirisa
Ibrahim .v. 371
ba Allah ne ba 5 (72, 116); 19 (89-92)
Idanu da kunnuwa
bai mutu a tsire ba 4 (157)
bayar da shaidarsu 41 (20-23)
bai wulakanta uwarsa ba 19 (32)
Idda 2 (228)
gaskata Taurat 3 (50)
Idda (ta rasuwar miji) 2 (234)
girmamawar Musulmi gare shi 43 (59)
auren mai idda 2 (235)
haifuwarsa 19 (22, 23)
Rare idda 65 (2, 3)
halifansa 3 (51, 52); 61 (14)
lissafin lokacin 65 (1, 4)
ishara ga Yahudawa 43 (61)
Idris 19 (56, 57); 21 (85); 29 (56)
kafirai sun ki yarda da shi 43 (57, 58)
I'itikafi 2 (187)
kiyaye shi daga makiya 5 (1 10)
Ikhlas s. 959
koya masa Taurat da Injil 3 (48); 5
Ilmi
(110)
an ba Adam ilmin sunayen abubuwa 2
magana a tsumma da kuma girmansa 3
(31)
(46); 5 (110)
an ba annabawa 21 (79)
manzo ne 4 (171)
an umurci Annabi ya roki karinsa 20
mutum ne kurum 3 (58); 19 (30-33)
(114)
mutuwarsa 5 (117)
Annabi Dawud ya zama Malami 2
nasara ga mabiyansa 3 (55)
051)
rayar da matattu 3 (49); 5 (110)
don kariya a yaki 21 (80)
shi ishara ne 23 (50)
don sarrafa abubuwa 2 (30, 34); 7
shirin kashe shi 3 (54)
(140); 14 (32-34); 16 (12, 14); 17
tsarkake shi daga zargi 3 (55)
(70); 21 (79, 81, 82); 22 (3, 65); 31
warkar da mara lafiya 3 (49); 5 (110)
(20); 45 (12, 13)
ya dan canja dokar Musa 3 (50)
tfaukaka darajar mutum 39 (9)
ya la'anci Yahudawa saboda rashin yin
iri uku 102 (5-8)
wa'azi 5 (78)
matakin hikima 2 (269)
ya yi nasara 61 (14)
nazarin halayen kasashe 16 (4); 17 (21);
yana cin abinci 5 (75)
22 (46); 29 (20); 35 (27, 28)
yin surar tsuntsaye 3 (49); 5 (110)
nazarin halitta 3 (189, 190); 10 (5, 6);
zuwansa cikon wahayi ne 4 (171)
13 (3, 4); 17 (12); 43 (3-5)
Is'hak 2 (133-140); 3 (84); 4 (163); 6 (85);
nazarin tarihin kasashe 3 (116); 12
11 (71); 12(6); 14(39); 19 (49); 21 (72);
(111); 14 (5); 30 (9); 33 (62); 35 (43,
37 (112, 113); 38 (45-47)
44); 40 (21)
Isharori
nemansa ta karatu da rubutu 96 (1-5)
kafirai sun roka 17 (90-93)
tafiya don nemansa 18 (65, 66)
wadanda aka hana 6 (110); 17 (59)
Imran 3 (32-35); 66 (12)
Isma'il 2 (125-140); 4 (163); 6 (87); 14
Infidar s. 918
(39); 21 (85); 38 (48)
Insan .v. 899
annabci 19 (54, 55)
Inshifcafc .v. 922
sake gina Ka'aba da Ibrahim 2 (127)
Isa 2 (253); 4 (172); 5 (46); 19 (16-21); 42
ya zauna a Arabiya 14 (37)
(13); 57 (27)
Isra' s. 414
addu'a don saukar abinci 5 (114)
lyaye4(2); 6(152); 46(13, 14)
alkawarin cetonsa 3 (55)
ba a bin su ga zunubi 6 (74); 9 (23, 24,
ambaton zuwan Annabi 36 (14); 61
113, 114); 17 (25); 19 (41-50); 29
(16)
(8); 31 (15)
an aiko shi ga Yahudawa kawai 3 (49)
cudanya da su 2 (83); 17 (23-25); 31
an ba shi hujjoji 2 (87); 5(111)
(15)
an halitta shi da tur6aya 3 (59)
kyautata musu 17 (23, 24); 29 (8); 31
982
Fihirisa
(14, 15); 46 (15)
Kahf s. 433
yaye yara 31 (14)
Kalmar Allah 31 (27)
Karuwanci 24 (2-3)
Jafa'i 4 (112); 24 (4-9, 23); 33 (57, 58); 49
Kashe aure 2 (226, 227, 234, 235, 238-241);
(12)
4 (25); 33 (4)
Jahannama 2 (24); 3 (12); 4 (93); 6 (129); 7
ana iya yi sau biyu 2 (229)
(38); 11 (106, 107); 15 (43, 44); 17 (8);
banda lokacin haila 65 (1)
22 (19-22); 25 (11-14); 32 (13); 38 (57-
dadada wa matan da aka saki 2 (236)
64); 40 (46-50); 43 (74-78); 55 (43, 44);
hana wa mace sake aure 2 (233)
56 (41-45); 73 (26-31)
in an wulakanta ko an guji mata 4 (128)
masu tsaronta 40 (49); 67 (8); 74 (31)
kafin tarawa da mata 2 (236, 237); 4
Jaluta 2 (250)
(4); 33 (49)
Jarirai
karbe kyauta daga mata 4 (19, 129)
shayar da su 2 (223); 65 (7)
korar mace daga gidan miji 65 (1)
Dubi kuma 'Ya'ya
kulawa da mata 65 (6)
Jassasa (Ra£uma) 27 (82)
kyautata wa mata 65 (1, 2 6, 7)
Jathiya s. 756
kyautatawa 2 (231)
Jayayya 16 (125); 29 (46)
mayar da aure 2 (228)
Jibril 2 (87, 97, 98); 53 (5-14); 66 (4)
nacfa masu sulhu a tsakanin ma 'aura 4
Jihadi
(35)
a Makka 29 (6)
sake auren miji na farko 2 (232)
a yi ta yin ya£i muddin akwai kuntata-
saki na uku 2 (230, 231)
wa 8 (39)
sakin mai goyo 2 (233)
azaba ga masu fitina 2 (191)
tabbatarwa 2 (230)
bayar da Mni 2 (90); 22 (39)
tilas in mata na cutuwa 2 (231)
da Ahlil Kitab 9 (29)
tsawon idda 2 (228); 65 (4)
da masu bauta wa gumaka 9 (5)
Dubi kuma Aure
da mutanen Makka 100 (1-6)
Kasuwanci 2 (198, 275)
dainawa da kafuwar addini 2 (193)
Kauthar 108 (1)
don kafa 'yancin addini 22 (40)
Kauthar .v. 956
don tsaron kai 3 (166); 22 (39)
Khaibar48 (18)
ganimar jihadi 8 (41)
Kibau
har sai an karbi Makka 2 (191)
na caca 5 (3)
kafiran da za a yi da su 9 (123)
na kuri'a 5 (90)
wahayi na farko-farko 79 (1-9)
Kirista Dubi Nasara
ya£i a cikin hurumin Makka 2 (191)
Kisan kai 4 (29); 5 (32); 6 (151); 17 (33)
Jinginar gida 2 (283)
sakamkonsa 4 (92, 93)
Jinn s. 886
Kishi 4 (32)
Jumu'a s. 851
Kulle 24 (30, 31)
Kushe 24 (4, 27); 49 (12); 104 (1)
Ka'aba2(149, 150); 9 (17, 18)
Kwanukan Allah 45 (14)
cibiyar Musulunci 2 (144, 148)
Kyautatawa 2 (263); 4 (36); 16 (90); 17
T)akin Allah 2 (125)
. (23)
kada kafirai su je 9 (28)
K. s. 788
madogarar mutane 5 (97)
Kabila da HabTla 5 (27-31)
wuri na mutane 5 (125)
Kabilu 49 (13)
yanka dabbobi a wurin 22 (33)
Kadr s. 944
Kafirai da munafukai 2 ( 1 77) ; 4 (1 50, 1 5 1 )
Kalam s. 871
Kafiran s. 956
Kamar s. 809
983
Fihirisa
Kari'a s. 949
na tsuntasaya da ake kira 2 (260)
Kasa
na turuniwa 2 (26)
halittata41 (9, 10); 79(30)
na wanda darajarsa ta fadi 22 (31)
Kasas s. 586
na wanda mamaki ya rufe 6 (71)
FCaskan da kai 31 (18, 19)
na wutar da aka kunna 2 (17, 18)
FCaura 2 (218); 4 (97, 100, 101)
Labaru
Kaurace wa iyali 58 (2-4)
a tabbatar da su 49 (6)
FCauyawa 9 (97, 99); 49 (14-17)
Laifl
Kawa 7 (32)
aza shi ga wani 4 (1 12)
Kazafi 24 (33); 24 (4-9)
horon masu laifl 83 (4-10)
Kin bin umurnin Allah
kowa ya dauki nasa 29 (12, 1 3); 35 (18)
sakamakonsa 47 (38)
masu laifi 83 (1-3)
Kisasi 2 (178)
Lail s. 938
Kjyama s. 896
Lailatul ICadr 97 (1-5)
ICuraish s. 954
La£abobi49(ll)
ICuraishawa 106 (1)
Larabawa
falalar da suka samu 106 (4)
auren uwaye 4 (23)
halakar kafiransu 53 (57)
gadon mata 4 (19)
samun galaba a kansu 70 (40)
hana gado ga mata da yara 89 (59)
izgili ga Annabi 21 (36, 37)
Labari 2 (26)
jinkirta hajji 9 (36)
na banzantattun mutane 13 (17)
kafln isowar Musulunci 3 (102)
na bawa da ubangijinsa 16 (75); 30 (28)
madauka sakon Annabi 16 (89)
na bawan mutane da yawa 39 (29)
masu mulkin manyan dauloli 18 (13)
na bebe 16 (76)
rantsuwoyi na yaudara 16 (92)
na duhu mai tsanani 24 (40)
sun dauki haihuwar diya masifa ce 16
na gari amintacce 16 (1 12)
(58); 47 (17)
na ginshikin haske 24 (35)
sun fi Yahudu da Nasara bin gaskiya 6
na giya 1 6 (67)
(157)
na gizo-gizo 29 (41)
turbude 'ya'ya da rai 6 (138); 16 (59)
na inn da aka shuka a kan dutse 2 (264)
'yanta dabbobi don gumaka 6 (139,
na irin da ke 'ya'ya da yawa 2 (261)
140)
na itace mai kyau 14 (24, 25)
Lat 53 (19)
na itace mara kyau 14 (26)
Leken asiri 49 (12)
na jaki 62 (5)
Li'an 24 (6-10)
na kare 7 (176)
Linjila 3 (3, 48, 65); 5 (66, 1 10); 7 (157); 48
na kawalwalniya 24 (39)
(29)
na kuda 22 (73)
alkawarin alheri 9 (111)
na kudan zuma 16 (68, 69)
gurbata ta 2 (75); 3 (76, 77); 4 (46); 5
na lambu 2 (265, 266)
(13, 44-47, 68)
na lambu mai rafukan madara 47 (15)
saukarta 3 (3)
na madara 16 (66)
Littafin Ayyuka 45 (28); 81 (10); 84 (7-15)
na mai arziki da matalauci 18 (32-44)
Ludu 6 (86-87); 11 (89)
na mai kin sakonni 7 (175, 176)
an halaka mutanensa 7 (83, 84); 1 1 (82)
na mai warware labari 16 (92)
hana shi kare bakinsa 15 (70)
na masu lambu 68 (17-33)
kin yarda da kiransa 7 (80-84)
na mutanen gari 36 (13)
manzanni sun zo masa 11 (77-83); 15
na ruwa da walkiya 2 (19, 20)
(58-76)
na ruwan sama da tsiro 18 (45)
matarsa 66 (10)
984
Fihirisa
mutanensa 50 (13)
ibada dai suke yi 21 (19, 20)
mutanensa sun nemi bakinsa 1 5 (67-69)
kafirai na neman saukarsu domin kure-
neman musanya da 'ya'yansa (watau
wa 7 (94, 95); 25 (21, 22)
matansu) 11 (78)
kawo sako 16 (2)
ya bar alkaryar 11 (81); 15 (65, 66)
kawo wa Annabi wahayi 19 (64)
ya gargadi mutanensa 26 (160-173); 27
marubuta ayyukan mutum 82 (10-12)
(54); 29 (28-35); 37 (133-137); 54
matsaran mutum 13 (11)
(33-39)
sauka ga muminai 41 (30)
Lukman 31 (12)
sun yi sujuda ga Adamu 2 (34) ; 7 (1 1);
tarbiyarsa ga dansa 31 (13-19)
15 (31); 17 (61); 18 (50); 20 (116)
Lukman s. 622
suna barranta daga masu bauta musu
34 (40, 41)
Ma'arij s. 879
suna karfafa wa mutane muminai zu-
Mabaraci 2 (263); 93, (10)
kata 8 (12)
Mace da namiji
suna roka wa mutane gafara 40 (7-9);
bambancinsu a ayyuka 3 (195); 4 (32)
42(5)
damarsu daya ce 2 (228)
taimakawarsu 3 (122, 123); 8 (10); 33
fifikon namiji 2 (228)
(9)
gadon mace 4 (18)
zuwansu 16 (33)
mace mai tsaurin kai 4 (24)
Maliki (mala'ika) 43 (77)
Madina 9 (101, 120); 63 (8)
Manat 53 (20)
sunanta cikin jahiliyya 33 (13)
Maraki na zinari 2 (51); 7 (148); 20 (90)
Mafarki 12 (4, 36, 43)
Marayu 2 (177); 4 (3-5, 7-9); 93 (9)
Magana 31 (19)
a ba su ilmi a gwada su 4 (6)
mummuna 4 (148)
hana cin dukiyarsu 4 (10)
Mai gaskiya 9 (119)
kar a barnata dukiyarsu 4 (2); 6 (153);
Ma'ida s. 155
17(34)
Makka 2 (144, 149); 3 (96); 17 (40), 48 (24)
kulawa da su 2 (220)
abu uku game da kasancewarta 3 (96)
yi musu adalci 4 (127)
addu'ar Ibrahim don kare ta 2 (126); 14
Marubuta ayyuka 82 (10-12)
(35)
Marwah 2 (158)
an tsarkake ta 27 (67, 91)
Maryam 2 (87, 253); 3 (43)
Annabi ya yi gargadi 47 (13); 65 (8-10)
an ba ta mafaka 23 (50)
azaba don kin Annabi 16 (1 12)
an zabe ta 3 (41)
ba a yi gargadi ba da 32 (3); 36 (6)
bayar da renonta ga Zakariya 3 (36)
ba ta tabuwa 2 (191, 194)
haihuwarta 3 (35)
ba ta 'y a 'y an itatuwa 14 (37)
ibadarta 3 (42)
jagora ga sauran kasashe 3 (95)
imaninta da Allah 3 (36)
Musulmi za su kame ta 1 7 (76)
Nasara sun dauke ta abar bautawa 5
za ta zama amintacciya 28 (57)
(116)
Malaya 5 (33)
labarin haihuwarta ga Isa 19 (17-21)
Mala'iku 2 (30-33, 177, 210, 248, 285)
labarin samun da 3 (44)
ba su laifi 21 (27)
mace mai gaskatawa 5 (75)
ba su saba wa Allah 66 (6)
misali ga muminai 66 (12)
ba su zama manzanni ga mutane 6 (8,
mutuwarta 5 (17)
9)
'yar'uwar Harun 19 (28)
daukarsu 'ya'ya mata 37 (149-157); 43
zarginta da zina 4 (156); 19 (27, 28)
(19); 53 (27, 28)
Maryam s. 453
fikafikansu 35 (1)
Masad s. 958
985
Fihirisa
Masar
Mubaya'a 48 (10, 18)
Annabi Yusuf ya fassara mafarki 12
ta mata muminai 60 (12)
(47, 49)
ta maza muminai 9 (111, 112)
bala'i ya sauka wa mutanenta 7 (133-
Muddatthir s. 892
135)
Mudaffffin s. 920
rayar da ita 29 (63)
Muhajirin 9 (100, 117)
rushe kasashe makwabtanta 46 (27, 28)
Muhammad 3 (144); 33 (40); 47 (1); 48
yadda sarki ya gan ta 12 (43)
(29)
Masu hali nagari 41 (25)
abin misali 33 (21)
Masu wa'azi 3 (104)
adalci tsakanin makiya 5 (42, 43)
Mata 4 (15, 19, 34); 5 (5); 60 (10-12)
adalci tsakanin Musulmi da wasunsu 4
lulluBi 33 (59)
(105)
tsofaffi 24 (60)
addu'ar Ibrahim da Isma'il 2 (129)
yin tafiya 24 (31)
al-Amin 6 (33)
Mata 4 (18)
alkawari ga annabawa kan zuwansa 33
bayar da shaida 2 (282)
(7)
cfauke wa tsofuwa lullu6i 24 (60)
Allah Ya kiyaye shi 3 (144)
hakkokinta na aure 2 (228); 4 (34)
amsar wai shi mahaukaci ne 68 (1-7)
jin tsoron zaluncin miji 4 (128)
an hore shi da yin gargacfi 74 (1, 2)
mai renon 'y a 'y a 2 (223)
an kira shi mawaki, mai sihiri da sau-
matan da aka hana aure 4 (23)
ransu 21 (3, 5); 74 (18-25)
rike fiye da cfaya 4 (3, 129)
an tsarkake sahabbansa 24 (21); 98 (7,
ta farko da ta biyu 4 (20)
8)
tana iya neman saki 2 (229)
an umurce shi da yin ibada 20 (130)
tana iya sa babbar riga 33 (59)
annabawa duka sun gaskata shi 3 (80)
tilas a ba ta sadakinta 4 (4)
Annabi Isa ya ambaci zuwansa 7 (157);
yin lulluBi 24 (31)
61 (6)
Dubi kuma Miji da mata
Annabi Musa ya ambaci zuwansa 7
Mata masu takaba
(157)
an yarda su sake aure 2 (235)
annabin karshe 33 (40)
kula da su garni da ba su gado 2 (240)
auratayyarsa 33 (50)
tsawon lokacin takaba 2 (234)
ba shi hakuri 20 (1-8)
Matalauta 69 (34); 90 (11-16); 107 (1-3)
ba ya kuskure 53 (2)
Matan aure 4 (12, 20-25), 33 (4, 37)
ba ya mance wahayi 87 (6, 7)
adalci tsakanin matan 4 (129)
ba ya neman wata lada sai daga Allah
na Manzon Allah 33 (6, 28-34, 50-55)
42 (23)
Matattu
ba ya sha'awar dukiya 20 (131)
ba su komowa wannan duniya 2 1 (95) ;
ba ya shiryar da wanda ya so 28 (56)
23 (100); 39 (42)
ba ya son kawa ta duniya 15 (88)
tayar da su 6 (36, 123); 75 (40)
bayyanarsa daidai da sanarwa 26 (195,
Ma'un s. 955
196); 28 (43-46); 37 (37)
Mawaka 26 (224-227)
dagewa don tsayar da gaskiya 9 (88)
Mayar da al'amura ga Allah 4 (59)
daidaitacce 53 (6, 7)
Mazowa kogo 15 (80); 18 (9-29)
damu warsa don 'yan Adam 9 ( 1 28), 1 8
Miji da mata
(6); 26 (3); 94 (3)
rantsuwar guje wa mata 2 (226, 227)
darajarsa 94 (4) ; 96 (3)
sulhunta su 4 (35, 130)
dawo warsa Makka bayan hijira 28 (85)
Mi'raj 17(1)
dogara ga Allah don tsari daga zargi 7
Mizani 7 (8, 9); 23 (102); 42 (17); 55 (7-9)
(200)
986
Fihirisa
duk arummomi su bi shi 22 (67)
mafi cancanta bisa muminai kansu 33
daukakarsa 81 (19-21)
(6)
fitar da mutane daga duffai zuwa haske
mafificin annabawa 2 (253)
65(11)
mai bin Alkur'ani tsintsa 10 (15); 11
fitila ga matafiya 33 (46)
(12)
ganawa da shi 58 (12, 13)
mai gargadi 6 (50)
gaskiyarsa za ta bayyana a hankali 93
mai karfin hali a wa'azi 42 (15)
(1-5)
mai mayar da mabiyansa malamai 62
haRuri da al'amura 46 (35)
(1-4)
halakar makiyansa 7 (182-187); 18
mai rarrabewa 98 (1, 2)
(59); 38 (67); 51 (59, 60); 69 (1-3);
mai sasanta arummomi 2 (213)
77 (12-40)
manzo, mai tsarkakewa 2(1 29, 151); 3
halattaccen Makka 90 (2)
(163); 62 (2, 3)
halin sahabbansa 49 (7)
maraya 93 (6)
hasara gaba da shi 18 (47); 22 (49-54);
matansa su tsarkaka 33 (30-32)
23 (62-67, 93-95); 52 (35-43); 68 (17-
matansa su zama masu saukin kai 33
33); 75 (10-13); 79 (7-9); 84 (16, 17)
(28, 29)
haske ne ga duniya 5 (15, 16)
matansa uwayen muminai ne 33 (6)
haskensa 81 (23)
matsalar makaho da Annabi 80 (1-10)
hijira zuwa Madina 9 (40)
miyagun ayyuka gabanin bayyanarsa
himmarsa 10 (99)
30 (41)
horon makiyansa 20 (129)
Musulmin farko 6 (164)
hukfa da kangararru 3 (158)
nasararsa 14 (14)
isar da sa£o 5 (67)
neman kashe shi 5 (1 1)
isowa bayan sauran annabawa 5 (19);
neman tsari daga kurakurai 40 (55)
21 (30)
neman yaudararsa 17 (73)
jaruntarsa 43 (88)
rahama ga mabiyansa 7 (156)
jin dadi da isowar wahayi 94 (1-8)
rahama ne ga duk duniya 21 (107)
kada matansa su nuna adonsu 33 (33,
rantsuwar goyon bayansa 48 (10)
34)
rayuwarsa sassauka ce 25 (7)
kama da Musa 46 (10); 52 (1-7); 73 (15)
rayuwarsa ta shaidar gaskiya ce 10 (16)
kar a sake auren matansa 33 (53)
rokon gafara ga masu fitinarsa 1 10 (3)
kar ya karkata 10 (105)
rufe zuciyarsa daga kushe-kushen mu-
kar ya saki matansa 33 (52)
tane 42 (24)
kar ya yi da 'a ga kafirai da munafukai
sabunta imani 17 (51, 52)
33(1)
sakonsa ga duk duniya ne 6 (91); 7
karbar wahayi daga Jibril 2 (97)
(158); 25 (1, 2); 42 (7); 68 (52); 81
kare shi daga dukan makiya 5 (67)
(27)
kawo canji 14 (48); 25 (63-75)
shari'a da wahayi 5 (49)
kira ga Nasara 3 (61)
shi ba mawaki ne ba 69 (38-43)
kusantarsa da Mala'ika Jibril 53 (8, 9)
shi fa Annabi ne 46 (9)
kasaitar halayensa 43 (32)
shi Manzo ne 72 (21-23)
kaunar muminai 9 (128)
shi mutum ne 7 (188)
kiyayyarsa ga gumaka 109 (1-5)
sunansa a cikin Attaura 7 (157, 158)
kulle-kullen Kuraishawa 8 (30); 16 (26)
sunansa a cikin Injila 61 (6)
ladabi da biyayya gare shi 49 (1-5); 58
taimako daga Allah 22 (15)
01)
tauraro mai zuwa da dare 86 (1-4)
mafarkinsa 48 (27)
tausaya wa mabiyansa 15 (88)
1
tsarkinsa da kamalarsa 33 (45-46)
987
Fihirisa
wahalce-wahalcensa 14 (13)
ba su da gaskiya 2 (8-16)
wai ya koyo Alkur'ani daga wasu 16
ba su kaunar yaki 47 (20)
(103)
ba su yin nasara 5 (53)
wajibi ne a yi masa biyayya 4 (64, 65) ;
ba su zuwa Tabuka 9 (42-45, 47)
24 (62, 63)
bin makiyan Musulunci 47 (25-28)
walakanta makiyansa 27 (87) ; 42 (45) ;
dalilan karya 9 (90, 94)
73 (10-14)
damun Annabi 9 (61)
ya bi hanyar Ibrahim 16 (123)
dole a raba su 3 (178); 29 (11); 47 (29-
ya raunana yarda da gumaka 25 (42)
31)
yadda ake kintatar sa 52 (29-34)
dukiyarsu da 'ya'yansu 9 (55, 85)
yafe wa makiya 15 (85)
gabarsu 9 (63)
Yahudawa sun jira bayyanarsa 2 (89)
gina masallatai don raba Musulmi 9
yaki da kafirai da munafukai 66 (9)
(107-110)
yi masa taron munakisha 2 (102)
gudun shan wahala 9 (49)
yin salla cikin dare farilla ne gare shi
gwajinsu 9 (126)
73 (1-9)
hasara gaba da Annabi 4(115)
za a daukaka mabiyansa 95 (6)
horo matsananci 48 (6)
zarginsa 33 (56, 57)
horonsu 4 (137-139, 141, 145)
zarginsa da kagowa 25 (4)
horonsu sau biyu 9 (101)
Muhammad s. 769
hukfa da su 4 (88-91)
Mujadala s. 834
jihadi da su 66 (9)
Mulk s. 867
juyawar zukatansu 9 (127)
Mulkin kasa
kar a yi abuta da su 4 (144)
biyayya ga hukuma 4 (59)
kar a yi musu addu'a 9 (84)
dangantaka da sauran kasashe 16 (92,
kar su je yaki da Musulmi 9 (83)
94); 60 (8)
kar su raka kungiyoyin Musulmi 48
dangantakar jama'a 3 (185); 60 (8, 9)
(15)
lokacin da yaki ya zama dole 2 (190-
karya alkawarinsu ga Yahudawa 59
193, 246, 251); 4 (75); 8 (39); 9 (29);
(11-14)
22 (39, 40)
kira ga zunubi 9 (67)
tsaregaskiya4(58, 105-107, 135); 5 (8);
kushe-kushensu 9 (58, 59)
6 (153); 16 (90); 38 (26); 42 (15)
kin karbar hukuncin Annabi 4 (60-64) ;
wanda ya kamata ya yi mulki 2 (247) ; 4
24 (47-50)
(53, 58); 10 (14); 12 (55); 22 (41); 24
kulle-kullensu 9 (48)
(55); 38 (17-20)
makircinsu ga Musulmi 63 (3-8)
yanayin gwamnati 3 (158); 42 (38)
masu amsa laiflnsu 9 (102, 103)
zaman salama 8 (56-58, 61, 62)
matsorata a yaki 33 (12-20)
Mu'minun s. 514
mummunan rashin kirkinsu 9 (76)
Mumtahana s. 844
murnar rashin zuwa yaki 9 (81, 86, 87,
Munafi&un s. 854
93)
Munafukai 2 (17-20); 3 (168)
rantsuwar karya 9 (56, 62, 74); 58 (14-
abuta da makiyan Musulunci 5 (52)
19); 63 (1, 2)
alkawarinsu 9 (75)
rashin gaskiyarsu 4 (106-112)
an gafarta wa wasunsu 9 (66)
rashin tsarkinsu 9 (125)
an nana musu haske 57 (13-15)
shawara a asirce 4 (81, 82, 114)
an la'ance su 9 (68)
son gudu daga wurin alheri 9 (57)
an la'anci aikinsu 9 (69)
sun ki Musulmi 9 (50-52)
Annabi ya yi tsaye kansu 9 (73)
sun ki yaki 3 (166, 167); 4 (77-80)
ba a yafe musu zuncfen muminai 9 (80)
suna zamba 4 (142, 143)
988
Fihirisa
tsokalarsu 9 (65)
sa 2 (87)
tsoronsu 8 (49); 9 (64, 74)
masu yarda da shi 10 (83); 40 (28-45)
Ubangiji bai karbar aikinsu 9 (53-55)
mutanen Fir'auna sun tsince shi 20 (39)
watsa labarun £arya 4 (83); 33 (60, 61 )
mutanensa na bauta wa maraki 7 ( 1 50) ;
yafe musu in sun daina munafunci 4
20 (86-90)
(146, 147)
neman Haruna ya taimake shi 20 (25-
yunkurin la'antar Musulmi 4 (113)
35); 26 (12-14); 28 (33, 34)
'yan leken asiri 5 (41)
nuna wa Fir'auna alamu 7 (107, 108);
za a karbi tubarsu 33 (24)
26 (32, 33); 79 (20)
zuncfen muminai 9 (79)
ratsa teku 7 (138); 10 (90); 20 (78); 26
Mursalat s. 903
(53-66)
Musa 2 (54-59, 61, 108, 136); 5 (22-29); 32
rokon ruwan sha 2 (60)
(23)
rokon wa mutanensa gafara 7 (155,
a Masar 7 (103-137)
156)
aSinai 7(138-157); 17(101, 102); 27 (7,
tafiyarsa mahacfar tekuna biyu don
8); 79 (15, 16)
neman ilmi 18 (6-82)
alkawari ga jama'ansa 7 (129)
tafiyarsa zuwa ga Fir'auna 7 (103), 10
an ba shi Attaura 2 (53); 6 (92, 155); 7
(75); 11 (96, 97); 20 (24); 23 (45,
(142-145)
46); 26 (15-17); 27 (12); 40 (23, 24);
an fifita shi 2 (53); 21 (48)
51 (38); 79 (17)
an kira shi 19 (52); 20 (1 1-14); 27 (8, 9);
umurnin tafiya Kasa Mai Tsarki 5 (21)
28 (30); 79 (16)
wa'adin dare arba'in 2 (51); 7 (142)
Annabi 19 (51, 52)
wahala a hannun mutanensa 61 (5)
da masu sihiri 7 (113-126); 10 (80-82);
ya bugi dutse 2 (60, 61)
20 (60-73)' 26 (38-51)
ya fadi zuwan Annabi Muhammad 28
da tsaurin kan Bani Isra'ila 2 (67-73,
(44); 36 (14)
92)
ya ga wuta a lokacin komowarsa daga
Fir'auna ya gana da mutanensa 7 (109-
Madyana 20 (10); 27 (7); 28 (29)
112); 10 (76-79); 20 (56-59); 26 (34-
ya kashe mutumin Misra, Bakibde 20
37)
(40); 26 (14, 19-21); 28 (15-21, 33)
ganin sandarsa da hannunsa sun canja
ya £ona dan maraki 20 (97)
20 (17-23); 27 (10-12); 28 (31, 32)
ya sami marmaro sha biyu 2 (60)
gardama da Fir'auna 20 (49-55); 26
ya so ganin Ubangiji 7 (143)
(18-31)
ya tafi Madyana 20 (40); 28 (22-28)
hijira da dare 20 (77); 26 (52); 44 (23, 24)
ya yi umurni a yanka sanuwa 2 (67-71)
hushinsa da Haruna 7 (1 50); 20 (92-94)
ya zo da doka 7 (150)
isharorinsa tara 17 (101)
zamansa a dutse 7 (143-145); 20 (83, 84)
jefa shi rafi 20 (39); 28 (7)
zargi na karya 33 (69)
kira a yi hakuri da yin addu'a 7 (128);
Musulmi
10 (84, 87)
abuta da wadanda ba Musulmi ba 60
kiran a saki Yahudawa 7 (104, 105); 20
(8,9)
(46-48); 26 (15-17); 44 (18)
abuta da Yahudu da Nasara makiya 5
ketare doka na Yahudawa 7 (146, 147)
(51)
Littafansa 87 (19)
adalci ga abokan gaba 5 (2, 8)
littafinsa yana shaida Alkur'ani 11(17)
adalci tsakanin juna 4 (135)
mafarkin mahaifiyarsa 20 (38); 28 (7)
Allah ba Ya zaluntar su 4 (40); 10 (44)
maido shi ga mahaifiyarsa 20 (40); 28
al'uraraa mail daraja 2 (143); 3 (109,
(12, 13)
110); 22 (65, 66)
manzannin Yahudawa sun biyo bayan-
amsa gaisuwa irin ta Musulunci 4 (94)
989
Fihirisa
an ba su babbar daula 4 (54)
39 (22); 42 (30); 49 (14); 53 (29, 30);
an matsa musu 3 (194); 16 (41, 42)
58 (20); 59 (19); 65 (8, 9)
bayar da mafaka ga kafirai 9 (6)
sako gare su ta hannun Jibril 16 (102)
biyayya ga hukuma 4 (59)
samun galaba 29 (58, 59, 69)
biyayya ga kafirai 33 (1)
sasanta su 8 (46, 49); 49 (9, 10)
dangantaka da wasun da ba Musulmi
sauki cikin matsuwa 29 (60)
ba 5 (5)
shugabannin jama'a 22 (78)
dangantakarsu da makiya 48 (29)
su bi tsaka-tsaki a rayuwarsu 57 (27-29)
facfa ko an nunka su goma 8 (65, 66)
su kafa kungiya 3 (103)
fifiko a kan kafirai 83 (34, 35)
su rike alkawura 2 (177); 5 (1); 16 (91)
gaisuwarsu ga juna 4 (86)
su riki halayya nagari 16 (90)
hakuri da makiya 9 (28); 16 (126, 127);
su yafe wa masu matsa musu 22 (60)
73 (10)
su zama masu gaskiya 6 (153)
hana su abuta da makiya 3 (27, 1 17-
sulhu da wacfanda ba Musulmi ba 8
119); 60(1-3)
(61)
haske a gidjensu 24 (36)
sun fi kaunar Allah 2 (165)
hukfa da Ahlil Kitab 29 (46)
sun yarda da duk annabawa 2 (136)
hulcfa da makiyan Musulunci 16 (126);
taimakon juna a alheri 5 (2)
17 (53)
taimakon juna a sha'anin addini 8 (73)
jin tausayinsu 4 (36)
wadansu dokokin rayuwa 3 (16); 6
kar su bi Yahudu da Nasara ga canza
(152-154); 13 (19-22); 23 (57-61); 25
addini 3 (99, 100)
(63-75); 51 (15-19); 61 (2, 3); 64 (11-
kar su damu in an matsa musu 29 (10)
18); 70 (22-35); 74 (4, 5)
kar su juya baya ga abokan gaba 8 (15,
wanda ya kaflrta tilas 16 (106)
16)
yarjejeniya da kafirai 9 (4)
kar su kashe juna da gangan 4 (92)
yi musu alkawarin nasarori 2 (115)
kar su rarrabu 3 (102, 104); 6 (160)
yi musu bushara ta kwarai 10 (63, 64)
kare kansu daga 6ata 2 (288); 39 (53,
za a ba su daula 3 (25, 26)
55)
za a cfaukaka su 2 (152)
kare masu bin gumaka har su ji Alku-
Musulunci 2 (84, 131, 132); 3 (19, 20); 4
r'ani 9 (6)
(125); 6 (14, 126, 164); 10(73); 16(81);
kashe dukiyarsu domin Allah 2 (195)
22 (78); 33 (35); 39 (22, 54); 49 (17)
kashi uku na Musulmi masu karatun
addini kammalalle 5 (3)
Alkur'ani 35 (32)
addinin annabawa 42 (13)
kyautata wa kafirai 17 (53)
addinin kowa 3 (82); 30 (30)
karfafa su 9 (124)
alamun ci gaba 7 (57, 58)
mala'iku na ba su bushara 41 (30, 31)
ba matsi a addini 2 (256)
mamallanka Kasa Mai Tsarki 21 (105)
ba shi daraja babba 6 (163)
masu T>akin Allah 22 (25)
babu bambance-bambance 6 (52)
masu mulkin duniya 24 (45); 27 (62)
ci gabansa kome kiyayya 41 (53)
mulkin kasashen Larabawa 70 (40-44)
gaba da shi hasara 61 (8)
mutunta juna 49 (11, 12)
haskaka 24 (35-38)
nasara har bayan kasashen Larabawa
kafuwar daular Musulunci 24 (55) ; 28
33 (27)
(58)
nazarin facfi-tashin arummdmi 3 (136,
kafuwarsa 32 (5)
137)
kare ci gabansa 32 (5)
sadaukar da kai don gaskiya 2 (154-
kare kai 42 (41)
156, 177); 3 (185, 199); 9 (24, 88)
kawar da camfe-camfe 6 (137-140, 144,
sakamakon ayyukansu 2 (286) ; 10 (23) ;
145)
990
Fihirisa
kowace al'umma na da doka 5 (48)
Nas s. 960
matsanancin hakurinsa 29 (40, 67)
Nasara
muhimmancinsa 2 (112, 156)
hanyar samunta 3 (200)
nasararsa48 (28); 61 (10-13)
Nasara (Kirista) 2 (111, 113, 120, 135,
sabuwar ma'anar hadaya 22 (36, 37)
140); 5 (18, 50, 69, 84, 85); 9 (30); 22
shikashikansa 2 (3, 4, 15, 16, 18, 19)
(17)
sukar kaurace wa aure 24 (32)
alkawari da su 5 (14)
taimaka masa 22 (40); 47 (7)
an kira su zuwa ga addini sahihi 3 (64)
tamkar an yi shuka 80 (24-32)
an kalubalance su da addu'a 3 (61)
tausayawa a shari'a 5 (34)
imani da Musulunci 5 (83)
ya soki fasikanci 6 (121)
kwadayin duniya 2 (96)
ya yarda da duk annabawa 2 (4)
makusanta addinin Musulunci 5 (82)
yacfa shi farilla ne 9 (122)
mayar da mutum tamakar Allah 4
yacfuwarsa 9 (33); 48 (28); 61 (8)
(171); 5 (77); 18 (102)
'yan'uwantaka 49 (13)
samun tsira 2 (262)
Mutum 40 (67)
Nasr 71 (23)
ayyukansa uku 5 (93)
Nasr s. 957
bukatunsa na ruhi 6 (38)
Nazi'at s. 909
dalilin halitta shi 11 (7); 51 (56-58); 75
Nisa' s. 112
(36)
Niih s. 883
girmansa 30 (54, 55)
Nuhu 3 (32); 6 (85); 7 (59-64); 9 (163); 10
guje wa Allah cikin ni'ima 7 (189-192);
(71-73); 14 (9); 25 (37); 51 (46); 53
17 (67)
(52); 57(26); 66 (10); 69 (11, 12)
halifan Allah 2 (30)
addu'a don cfansa 1 1 (45-48)
halitta shi daga laka 15 (26); 23 (12)
da T>ufanu 54 (9-15); 71 (1-28)
halitta shi daga tur6aya 3 (59); 6 (2); 7
da jirgin ruwa 1 1 (26-48); 17 (3); 21 (76,
(11, 12); 22(5); 32(7); 35 (11); 55
77); 22 (42); 23 (23-29); 26 (106-
(14)
120); 29 (14, 15); 33 (7); 37 (75-82);
hasararsa 2 (35-39); 20 (120)
42 (13)
ikon Allah ne 32 (9)
matarsa 66 (10)
jama'a guda 2 (213); 10 (19); 21 (92, 93)
ruwa ya cinye cfansa 1 1 (42, 43)
kadaicewarsa 24 (58, 59)
tarihinsa gargacfi ne 11 (35)
koya masa harshe 55 (3, 4)
Nur s. 527
matakan girmansa 22 (5); 23 (14)
mulkin duniya 14 (32-34); 16 (10-19);
Ra'ad s. 361
31 (20); 45 (12, 13)
Rahman s. 814
rashin gode wa Allah 41 (49, 51)
Rai na mutum
rashin rike amana 33 (72)
dogara ga Ubangiji 2 (67); 7 (200); 23
rayuwa da mutuwa a duniya 7 (25)
(97, 98); 113 (1, 2); 114(1-3)
sakamakon aikinsa 4 (79); 53 (29)
fa'idar addu'a 9 (103); 10 (87); 1 1 (52);
tsarkake kai ne tufarsa 7 (26)
19 (4, 48); 25 (77); 29 (45); 52 (27);
Muzzammil s. 890
71 (10-12)
gamuwa da Ubangiji 2 (45, 46, 223); 6
Naba' s. 906
(31); 32(10); 53 (42); 84(6)
Nagarta
gaskata Ubangiji 9 (129); 11 (88); 12
sakamakonta 10 (26)
(67); 13 (30); 14 (12); 25 (58); 60
Nahl s. 391
(4); 65 (3)
Najm s. 804
godiya ga Ubangiji 13 (28); 89 (27, 28)
Nam] s. 572
991
Fihirisa
hura masa ruhi 15 (28, 29); 17 (85); 32
Rarrabar addini 6 (159)
(7-9)
Rashin biyayya 4 (14)
karbar addu'a 2 (186); 14 (39); 27 (62);
Rayuwa
40 (60)
ba wasa ba ce 29 (64); 57 (20)
kaunar Ubangiji 2 (165,177); 3 (30); 5
fama da wahaloli 90 (4)
(54); 76 (8, 9)
halittawa bibbiyu 36 (36)
tsarkinsa 7 (122); 14 (22); 15 (42); 30
makasudinta 23 (115-118)
(30); 95 (4)
muhimmancinta 30 (7, 8)
Ubangiji Sahibin mutum ne 2 (257); 3
mutum daga kasa 18 (37); 23 (12-14);
(67); 4 (45); 6 (14); 42 (9); 45 (19)
40(67); 53 (32); 71 (13-17)
wanda Ubangiji ba Ya so 2 (190) ; 3 (56,
Rayuwa a duniya 3 (135); 7 (28, 29); 31
139); 5 (64); 6 (142); 8 (58); 16 (22);
(17)
28 (76); 57 (23)
Rayuwar mutum
wanda Ubangiji ke so 2 (195, 222); 3
an soki tara dukiya 9 (34)
(75, 145, 147, 158); 5 (42); 9 (7)
ba a watsi da aikinsa 3 (194)
yadda ake addu'a 1 (Al-Fatiha) ; 2 (20 1 ,
ba a dukiya don Allah 2 (177)
250, 286); 3 (7, 192, 193); 12 (101); 14
ba da dukiya ga dangi, marayu, mata-
(40, 41); 17 (80); 18 (10); 20 (25-28); 25
lauta, da matafiya 2 (215)
(74); 40(7-9); 46 (15); 71 (28)
bashi, jingina, yarjejeniya 2 (280, 282,
yarda da Ubangiji 2 (256, 257); 10 (9);
283)
19 (96); 33 (47); 48 (4, 18); 49 (7); 57
ciyar da dukiya na kawo karuwa 2
(12, 19); 58 (22)
(268)
yinaddu'al(4);10(12,22);22(12);39
dangantaka da mutane 5 (2, 5)
(8, 49); 41 (51)
dukiya daga duwatsu 16 (15-18)
Rakumar Salihu 17 (59); 26 (155-158); 54
dukiya daga shanu 16 (5-7)
(27-30); 91 (13-15)
dukiya daga teku 16 (14); 17 (66); 34
Rakumi 7 (73); 22 (27)
(18)
Rama cuta 2 (179, 194); 4 (149); 17 (33);
dukiya na rucfin mutum 102 (1, 2)
41 (34); 42 (29, 30, 43)
duniya cike take da dukiya 4 (100)
a kisan kai 2 (178)
kar a yi dukiya da damfara 2 (188); 4
dokar a Attaura 5 (45)
(100)
dokarta 2 (178)
kira zuwa ga muhimman mas'aloli 3
Ramalan 2 (186, 187)
(13); 18(46, 105); 63(9)
farilla azuminsa gaba cfaya 2 (185)
kokarin saduwa da Ubangiji 84 (6)
saukar da Alkur'ani cikinsa 2 (185)
mai nema zai samu 53 (39-41)
Rana
maza da mata na gadon dukiya 4 (7,
hanyarta 36 (38)
29-33)
nacfe ta 81 (1)
neman dukiya 4 (32); 67 (15); 34 (18)
tare da wata 75 (9)
rike gaskiya a cikin hukfa 7 (85); 17
Ranar FCiyama
(35); 83 (1-6)
Dubi
sakamakon masu aiki 3 (135)
Tashin Kiyama
sarrafa dukiya daidai 17 (26-29); 25
Rantsuwa 2 (225); 9 (42); 16 (93, 95); 60
(67)
(12); 66 (2)
saye da sayarwa 4 (29)
da barin yin abu nagari 2 (224)
shaida 2 (140, 282, 283); 4 (15); 5 (8,
kaffararta 5 (89)
106,107); 12 (26,27); 24 (4,5); 65(2)
kar a karya ta 16 (91)
son dukiya 89 (17-20); 100 (6-8)
kar a yi ta don zamba 16 (92, 94)
yin aiki 39 (39); 53 (39-41); 79 (34-35);
kiyaye ta 5 (89)
92(4)
992
Fihirisa
Riba Dubi Bashi da ruwa
fa'idarta9(103); 10(87); 1 1 (52); 19(4,
Ridda 2 (117); 5 (54)
48); 25 (77); 29 (45); 52 (27, 28); 71
Rowa 3 (179); 4(37)
(10-12)
Rubuta ayyuka 17 (13)
kar6ata 2 (186); 14 (39); 27 (62); 40
Rum s. 613
(60)
Ruwa
kariya daga zunubai 29 (45)
tushen rayuwa 11 (7)
mafi cancantar addu'a 1 (1-7)
mutum ya gaje ta 1 (4); 10 (12, 22); 22
§. s. 686
(12); 39(8, 49); 41 (51)
Saba' s. 647
rage ta cikin tafiya 4 (101)
Sadaki
rashin mayar da hankali cikinta 107 (4,
ba a kar&ewa 4 (19)
5)
ba shi da iyaka 4 (20)
sau biyar a rana 17 (78); 30 (17, 18)
dole a ba mata 4 (4)
ta tahajjud 17 (79)
fansarsa 2 (229)
tsakatsaki 17 (110)
ga wanda aka saki 2 (236)
Ubangiji Ya kar&a 40 (60)
maido da rabi 2 (237)
yadda ake yin ta Sura ta 1 ; 2 (201, 250,
Sadaka don gina addini 2 (219, 270, 272,
286); 3 (7, 192, 193); 12 (101); 14
291); 3 (92, 134); 4 (114); 9 (60, 79,
(40,41); 17(80): 18 (10); 20 (25-28);
103); 24(56); 58 (12, 13)
25 (74); 40 (7-9); 46 (15)); 71 (28)
a asirce da a bayyane (2, 271)
Sallar Jumu'a 62 (11)
a bayanne 2 (264); 4 (38)
ciniki a ranarta 62 (9, 10)
abin yinta 2 (267)
Salsabil 76 (18)
banda gori 2 (262-264, 266)
Sama
domin neman yardar Allah 2 (265)
an tsare sama 72 (8-9)
fa'idarta 8 (60); 57 (18); 64 (17)
arziki daga sama 40 (13)
in ba abin yinta 17 (28)
bakwai 2 (29); 17 (44); 23 (17, 86); 61
ladarta 2 (261)
(12); 65 (12); 67 (3, 4); 71 (15); 78
masu cancanta a ba su zakka 2 (273); 9
(12)
(60)
cike da hanyoyi 51 (7)
matakin nasara 2 (274)
daga sama ba ginshikai 13 (2); 31 (10)
Safa 2 (158)
fecfe ta 81 (11)
Saff s. 848
halitta ta 7 (54); 10(3); 32 (4)
Saffat s. 673
hayaki 41 (11)
Sajda s. 628
nacfe ta 21 (104)
Saki Dubi Kashe aure
Sama da Kasa 37 (5)
Salihu da Samudawa 7 (73-79) ; 1 1 (61-68) ;
tsagewarta 25 (25)
14 (9); 15 (80-84); 25 (38); 26 (141-
Samiri
159); 27 (45-53); 29 (38); 41 (13, 14, 17,
Musa ya hore shi 20 (97)
18); 51 (43-45); 53 (51); 54 (23-31); 69
ya amsa laifi 20 (96)
(4, 5); 85 (18); 89 (9); 91 (11-15)
ya 6atar da Yahudawa 20 (85)
Dubi kuma Samudawa
ya yi dan maraki 20 (87, 88)
Salla
Samudawa 7 (73); 9 (70); 1 1 (61); 14 (9);
a fagen yaki 4 (102)
17 (59); 22 (42); 25 (38); 26 (141-158);
a kan doki 2 (239)
27 (45, 46); 29 (38); 41 (13, 14, 17-19);
a lokuta ajiyayyu 4 (103)
51 (43-45); 54 (23-29); 85 (17); 89 (9);
ado dominta 7 (31)
91 (11, 12)
cikin tsoro ko hacfari 2 (239)
Sata
dalilan yinta 2 (45); 29 (45)
sakamakonta 5 (38)
993
Fihirisa
yafe wa 6arawo 5 (39)
matasa su nemi izini 24 (59)
Shaida 2 (41, 283); 3 (135); 4(6, 15, 41); 5
Shirka
(106); 24 (4-9); 33 (70, 71); 65 (2)
ba ta da tushe 30 (35)
kar shaidu su yi hasara 2 (282)
mafl munin zunubi 4 (48, 116)
yin rantsuwa 5 (107)
Shiryuwa 17 (15); 29 (7)
Shaicfan 2 (14); 4 (116-1 18); 7 (18, 19, 21-
Shu'aibu 7 (85-93); 1 1 (84-95); 15 (78, 79);
26); 15 (30, 38-41); 17 (63, 64); 18 (51);
26 (176-191); 29 (36, 37)
20 (117); 26 (95); 38 (75-85); 55 (14)
Shu'ara' s. 553
a mutum 3 (174); 8 (48); 22 (3)
Shura s. 729
an kaskanta shi 7 (13)
Sulaiman
ba shi da iko kan mutum 15 (42); 17
an ba shi dukiya 27 (16)
(65)
bai yi sihiri ba 2 (102)
ba zai yi nasara ba 4 (76)
da dawakansa 38 (31, 32)
bai sami biyan bukata ba 7 (16)
da Dawud 21 (78-80); 27 (15, 16)
6atar da muminai 41 (36)
fahimtar maganar tsuntsaye 27 (16)
gaba da annabawa 22 (52, 53)
fakuwarsa 34 (14); 38 (35)
halitta shi daga wuta 7 (12)
mayakansa na ruwa 34 (12)
iko a kan mabiyansa 16 (99)
nazarin tsuntsaye 27 (20)
kiyayewa daga shafarsa 7 (201)
ya roki wata daular 38 (35)
kawata fasadi 16 (43)
yi masa karairayi 2 (102)
kin sujuda ga Adam 2 (34); 7(11, 12);
Sulhuntawa 4 (35)
15 (31-37); 17 (61); 18 (50); 20 (116)
Sunaye miyagu 49 (11)
mabiyansa 58 (18-20)
Surori na Alkur'ani 2 (23); 9 (64, 86, 124,
mai ishara ga miyagun al'adu 4 (119,
127); 11 (13); 24 (1); 47 (20)
120)
mayaudari 7 (17)
Tabanni
rade-racfensa 114 (1-6)
hana shi da aiki 33 (36-38)
rantsuwar halaka mutane 17 (62)
hana shi da doka 33 (4)
sauka ga masu zunubi 26 (221-223)
Tabuka
tsira daga makircinsa 15 (36)
an umurci Musulmi su je 9 (41)
wakilin mugayen shawarwari 23 (97,
tsawon tafiyar 9 (42)
98)
Tagabun .v. 856
ya nemi jinkiri 7 (14, 15)
Tahrfm s. 863
yarucfi Adam 2 (36); 7(20)
Taimama 4 (43); 5 (6)
yana alkawari na karya 14 (12)
Takathur s. 950
yana cikin jinn 1 8 (50)
Takawa
yana ganin mutum, shi ba a ganin sa 7
yadda ya kamata a yi ta 1 7 (37) ; 3 1 ( 1 9)
(27)
Takwfr s. 916
yana satar saurare 15 (16-18)
Taron asiri 58 (7-10)
yana zuga kafirai 19 (83)
Tashin Kiyama 51 (12-14); 82 (17-19)
Shams s. 936
tanadar ayyukan mutane 50 (4)
Shanu 5 (103), 6 (137); 16 (5)
tona asirai 24 (24); 50 (22); 69 (18); 86
don dan Adam 6 (143-145); 39 (6)
(9)
Sharh s. 941
Tauba s. 272
Shari'ar gaskiya
Taurari
a Musulunci 6 (153)
6acewarsu 77 (8)
tsakanin Musulmi da wasunsu 4 (105)
masu nazarinsu 67 (5)
Shawara 3 (159); 42 (38)
watsewarsu 82 (2)
Shiga gidajen wasu 24 (27, 28, 58)
yinduhu 81 (2)
994
Fihirisa
Tm s. 942
4 (164); 5 (48); 10 (47); 13 (7); 16
Toshiyar baki 2 (188)
(36); 22 (67); 35 (24); 40 (78)
Tsafta 2 (222)
sauka ta zuciya 2 (97) ; 26 ( 1 92- 1 94) ; 53
Tsarki4(43); 5 (6); 24 (21)
(10, 11)
Tsegumi
sifa ce ta Ubangiji 6 (92)
garkuwarsa 24 (58, 59)
tushen gmin halin mutum 6 (152-154);
Tsira 91 (9)
17 (23-39); 25 (63-75); 70 (23-35)
Tsuntsaye
yin aiki don jama'a 2 (112, 117, 195,
Sulaiman ya mallake su 27 (17)
261, 262, 267, 271, 272); 3 (91, 133);
Tuba 5 (39); 16(119)
4 (36-38) ; 7 (55) ; 1 6 (90) ; 29 (69) ; 39
lokacin da ba a kar6a 3 (89); 4 (17, 18)
(34); 51 (19); 76 (8, 9); 89 (17, 18)
zuwa ga Annabawa 4 (163)
Uhudu 3 (121-125, 127-129)
zuwa ga mahaifiyar Annabi Musa 28
an karya makiya 3 (126)
(7)
dalilan hasara 3 (151, 152)
zuwa ga sahabban Annabi Isa 5 (111)
gafarta wa masu laifi 3 (154)
Wsiki'a s. 821
gudummawar mala'iku 3 (183)
Waliyyai
gunagunin munafukai 3 (153)
bauta musu 17 (57)
mai rarrabewa 3 (139-142, 153-167)
Waliyyin maraya 4 (6)
matsayin abokan gaba 3 (152)
Wasan banza 25 (72)
Musulmi sun zo ga Annabi 3 (153)
Wasiyya 2 (180, 182); 4 (11, 12); 5 (106)
samun nasara 3 (151)
Wata
yadda Annabi ya yi 3 (158)
tsagewarsa 54 (1)
yin duhu 75 (8)
Wahayi
Watanni masu alfarma 2 (189); 9 (36)
an amshe a duk duniya 8 (12); 16 (68,
jinkirta su kafirci 9 (37)
69); 41 (12); 99 (4, 5)
ya£i cikinsu tilas 2 (194)
daukaka dan Adam 2 (1-5); 10 (2); 11
Wuta
(2, 3); 14 (27); 20 (75); 23 (1-4); 24
ba a dawwama ciki 6 (129); 11 (107)
(55); 28 (67); 38 (2, 28, 67, 68, 87);
ba mutuwa ko rayuwa ce ba 20 (74) ; 87
58 (11); 68 (52); 92 (4-7)
(12, 13)
hada kan arummomi 2 (213); 4 (1); 10
ci gaba da horo 4 (56)
(19); 23 (52); 30 (22); 48 (13)
don fasikai ce kawai 19 (68-72)
hada kan kasa 7 (34); 10 (49); 13 (11);
horo daidai da laifi 78 (21-30)
15 (4, 5); 45 (28); 49 (13)
horo ga wannan rayuwar 29 (54)
hanyoyin saukarsa uku 42 (51)
kofofinta bakwai 15 (44)
kare mutum daga mugun aiki 2 (38); 4
muminai ba su shiga 21 (101, 102)
(31); 5 (12, 65); 7 (35); 8 (29); 14
nadamar masu shigarta 101 (8-11)
(1); 17 (82); 25 (70); 29 (7); 41 (44);
sakamako da Hudama 104 (4-9)
47 (2); 48 (5); 62 (2)
wanke zunubi 57 (15)
Musulmi dole su yarda da duk annaba-
'yan wuta na kiran 'yan aljanna 7 (50)
wa 2 (4, 136, 285); 4 (152)
ni'ima ga dan Adam 4 (164); 10 (47);
Y.S. s. 664
35 (24); 40 (78)
Ya'akub 2 (134-140); 3 (84, 92); 4 (163); 6
mini ga rayuwa mafi daukaka 2 (4); 17
(85); 11 (71); 12(38,68); 19(49, 50);21
(21); 23 (15, 16, 115); 32 (10); 36
(72); 38 (45-47)
(78, 79); 50 (3, 4); 56 (60, 61); 71
a gadon mutuwarsa 2 (133); 12 (6)
(17, 18); 75 (36-40)
kiran hadin kai ga zuriyarsa 2 (132)
samun annabawa a dukan arummomi
ya tafi Masar 12 (99)
995
Fihirisa
Yafewa 2 (263); 3 (134); 4 (17, 18) ; 24 (22);
rokon a cece su 10 (85, 86)
42(40)
sabuwar fitina daga Fir'auna 7 (127)
Yahudawa 2 (143-147); 3 (193); 5 (14-19,
sake zaunar da su 17 (6, 104)
21, 23, 25); 10 (91, 94); 17 (2-7, 101,
Samiri ya batar da su 20 (85)
102); 26 (10-66, 197); 32 (23, 24); 40
shugabanninsu sha biyu 5 (12)
(53); 44 (30-32); 45 (16, 17); 61 (5, 6)
sun £i shiga Kasa Mai Tsarki 5 (22, 24)
a alkarya 2 (58)
sun rabu kabilu sha biyu 7 (160)
a cikin daji 5 (26)
sun rarrabu gida-gida 7 (168)
abutar masu bauta wa gumaka 5 (80,
sun ro£i abinci 2 (61)
81)
sun ro£i ruwa 2 (60); 7 (160)
an ba su sarauta da annabci 5 (20)
sun sami darba da tantabaru 2 (57)
an ba su sarautar Kasa Mai Tsarki 7
suna bin abubuwan bautawa na karya
(137)
7 (138)
an zabi manyansu saba'in 7 (155)
taurin zuciyarsa 2 (74)
ba su dama da zuwan Annabi 17 (8)
tsagerancinsu 2 (67-142)
baiwa gare su 2 (122)
tsallake Bahar Maliya 2 (50); 10 (90);
bauta wa dan maraki 2 (51, 54); 4
20 (77); 42 (24)
(153); 7(148, 149, 152, 153)
wai ba a azabta su 2 (80)
bauta wa gumakan Larabawa 4 (51)
wai sun kashe Annabi Isa 4 (157)
6ata littafai 2 (75)
wulakanta su 2 (61)
cikakkiyar kiyayya ga Musulunci 5 (82)
yarjejeniyarsu 2 (63, 93); 4 (154, 155)
dole su ba wasu jama'a wuri 17 (107)
yi wa Annabi Isa kaidi 3 (53)
fatansu ga annabci 2 (89)
yi wa Annabi kulle-kulle 2 (87); 3 (20,
Fir'auna ya yi musu azaba 2 (49); 7
21)
(167); 40 (25)
yi wa Maryam kagen zina 4 (156)
girgizar kasa ta shafe su 4 ( 1 53) ; 7 (171)
yi wa Musulmi dariya kan tsaron kasa
haramta musu abinci 6 (147)
5(64)
horonsu da bala'i 2 (59); 7 (161, 162)
yin cuta sau biyu 17 (4)
inuwa daga girgije 2 (57); 7 (160)
yunkoron kashe Annabi Isa 2 (7, 2)
jahilcinsu 2 (78)
'yan leken asiri 5 (41)
karbar riba 4 (160)
zalunci a dukiya 4 (161)
kashe annabawa 2 (61, 91); 3 (20)
zukatansu sun kekashe 5 (13)
kira su yarda da Annabi 2 (40)
Yahya 3 (38); 6 (85); 19 (7-15); 21 (90)
kaunar rayuwa 2 (96)
Yajuju da Majuju 18 (94-99)
ketare haddi cikin Asabar 2 (65)
mamaye duniya 21 (96)
kin Annabi don ba Bayahude ne ba 2
Yaki 2 (190-195, 216, 217, 246); 4 (74-84,
(89-91)
91, 94, 104); 9 (5, 29, 36, 41-47, 122,
kin gaskiya sau biyu 5 (71)
123); 22 (39, 40); 47 (4)
kin yarda da Annabi 2 (101)
Yakin Ahzab (a Madina) 33 (9, 22)
kiyayya ga Annabi 2 (104)
gudummawar mala'iku 3 (124)
la'anta daga Dawud da Isa 5 (78)
labarin yakin 38 (11)
mayar da su birai 2 (65); 5 (60); 7 (165,
Yakin Badar Dubi Badar
166)
Yakin Hunain 9 (25-27)
munafukai 5 (61)
Yakin Uhudu Dubi Uhudu
munafunci tsakaninsu 2 (76)
Yarjejeniya
mutuwar shekara dari 2 (259)
cika ta 5 (1); 16 (91, 92)
neman ganin Ubangiji 2 (55); 4 (153)
matan Annabi 33 (27-34, 50-59)
nuna kiyayya ga Jibril 2 (97)
soke ta 8 (58)
raya su daga mutuwa 2 (243)
Yi da wani 32 (58); 49 (11, 12); 104 (1)
996
Fihirisa
Yi wa wani hanya 4 (85)
Zainab
Yin daidai 2 (177)
aurenta da Annabi 33 (36-38)
Yin kyashi 4 (32)
Zakariya 3 (36); 6 (86); 19 (2-15); 21 (89,
Yini
90)
a wurin Allah daidai yake da shekara
an ba shi ishara 3 (40)
dubu 22 (47); 32 (5)
labarin haihuwar Yahya 3 (38)
na Kiyama daidai da shekara dubu
ya roki a ba shi da 3 (37)
hamsin ne 70 (40)
Zakka 2 (43); 9 (60)
Yunus s. 300
Zakkum 17 (60); 37 (62); 44 (43)
Yunusa 4 (163); 6 (85); 10 (98); 37 (139-
Zalzala s. 947
149); 68 (48-50)
Zama cikin jama'a 58 (11); 74 (4)
Yusha'u da Kabilu 5 (23)
Zaman gida
Yusuf
asirtawa 24 (27, 28)
adduarsa 12 (101)
cudanyar maza da mata 24 (30, 3 1 , 60) ;
an ba shi hikima 12 (22)
33 (59)
bayyana kansa ga yayyinsa 12 (80-91)
duk kyauta ga mata tata ce 4 (19-21,
tfaukaka shi 12 (54-56)
24)
fitar da shi daga rami 12 (19, 20)
kyautata wa 'yan'uwa 2 (177); 4 (1, 36);
jefa shi kurkuku 12 (35)
16 (90); 17 (26); 24 (22); 25 (54)
karamin kaninsu 12 (63-69)
kauna da girmama iyaye da 'ya'ya 4
kulle-kullen 'yan'uwansa 12 (7-18)
(11); 17 (23, 24); 25 (74); 31 (14,
matsalar ma'auni 12 (70-77)
15); 46 (15)
sayar da shi a Masar 12 (21)
matsayin mata 3 (41, 194); 4 (4, 7, 32,
shi da fursunoni biyu 12 (36)
124); 16 (97); 28 (7); 40 (40)
tabbatar da rashin laifinsa 12 (26-29)
maza su ciyar da mata 4 (34)
warware shi daga zargin karya 12 (50-
miji da mata: dadadawa 7 (189)
53)
miji da mata: karimci 2 (228, 229, 231)
wasu yaudare-yaudaren 12 (30-34)
miji da mata: tufa ga juna 2 (187)
ya daure yaudarar mata 12 (23-35)
miji da mata: yin kyauta 2 (237)
ya fassara mafarkin fursunoni 12 (41)
rike mata gwargwadon iko 65 (6)
ya fassara mafarkin sarki 12 (43-49)
sadaki kyauta ce 4 (4)
ya taimaki yayyinsa 12 (58-62)
Zariyat s. Dubi Dhariyat
ya yafe wa 'yan'uwansa 12 (92)
Zato 49 (12)
ya yi mafarki 12 (4-6)
Zihar 33 (4); 58 (1-4)
yi wa fursunoni biyu wa'azi 12 (37-40)
Zina 25 (68)
Yusuf s. 340
alfasha ce 17 (32)
'Yan Adam 7 (26-36, 172); 17 (70)
haninta 24 (3)
'Yan'uwantaka 3 (102-105)
horo dominta 24 (1, 2)
'Yan'uwantakar dan Adam 49 (13)
hukuncinta 24 (1-5)
'Ya'ya
kubutar mace daga zargin zina 24 (8-
hana kashe su 6 (152); 17 (31)
10)
mata 16 (58, 59)
makaranta 24 (27, 30, 31)
na tabanni 33 (4, 5, 37)
shaidar yinta 24 (4, 6, 7, 13)
renonsu 2 (233); 4(11)
Zukhruf s. 739
rufe su da rai 81 (8, 9)
Zul-Karnain 18 (83, 94)
'Ya'yan hankaka Dubi Tabanni
Zumunta 4 (1)
Zunubi
Zaidu
mafi muni 4(116)
ya saki Zainab 33 (37)
sakamakonsa 4 (110, 111); 6 (164)
997
A^mimmWfa*
Suna
Sura ta
Shafi
Wuri
&tA*a}\
«ft
5j^»Jl
Fatiha
1
1
Makka
£>sj»
\
\
£jliJI
Ba£ara
2
2
Madina
iJJl«
Y
Y
Sy3l
Al-'Imrana
3
73
Madina
oJL«
vr
r
ji^p JT
Nisa'
4
112
Madina
iJJl*
m
i
•ILJI
Ma'ida
5
155
Madina
<Jju»
\00
SaJtJl
An'am
6
186
Makka
4^*
U*\
1
f liSfl
A'araf
7
219
Makka
&>>*
y\i
V
<J>l>Sll
Anfal
8
257
Madina
iJj£
YoV
A
jiiSfi
Tauba
9
272
Madina
iJJl*
YVY
^
4^11
Yunus
10
300
Makka
££l*
r» •
^
crl*
Hud
11
319
Makka
Zj>~»
m
\\
>
^
Yusuf
12
340
Makka
4%l»
n«
H
Ra'ad
13
361
Madina
iJJL*
n\
\r
Jp^I
Ibrahim
14
371
Makka
££v«
nn
u
e*W
Hijr
15
381
Makka
£>**
rA\
^
j>^\
Nahl
16
391
Makka
<&*
rM
H
>ji
Isra'
17
414
Makka
££L*
t\t
W
J»!
Kahf
18
433
Makka
t!SsA
trr
\A
Jiffll
Maryam
19
453
Makka
££L*
tor
\*
^
T>.H.
20
466
Makka
££j»
m
Y*
a]*
Anbiya'
21
484
Makka
££*
tAt
Y^
*C&i
HajJ
22
499
Madina
aJX»
t^
YY
g^JI
Mu'minun
23
514
Makka
4&J*
*U
Yr
Oj^jll
Nur
24
527
Madina
aJx*
oYV
Yt
J^ll
Furkan
25
542
Makka
*ux*
oiY
Yo
j\iji\
Shu'ara'
26
553
Makka
4^*4
oor
Yn
j^Iji
Naml
27
572
Makka
£!£•
oVY
YV
J-JI
Kasas
28
586
Makka
aIx*
oAn
YA
^^-a-iiJI
'Ankabut
29
602
Makka
<lSv«
VY
Y^
o«*>^*Jl
Rum
30
613
Makka
<fsjk
■nr
r»
>
Lukman
31
622
Makka
4^*
1YY
n
jlli)
Sajda
32
628
Makka
4ISC4
nYA
rY
so>*!ji
Ahzab
33
633
Madina
iJx«
nrr
rr
v i>Sfi
Saba'
34
647
Makka
4^V4
ntv
rt
C
Facfir
35
656
Makka
££v«
no
ro
j,u
Y.S.
36
664
Makka
££a
nit
ri
cTi
Saffat
37
673
Makka
£>sA
nvr
rv
OliliJI
?.
38
686
Makka
<£**
iai
ta
W*
998
i
{ &<£
S53I&3 JDii
&»
>
Suna
Sura ta
Shall
Wuri
A^jJail
&J
Ojj^j\
Zumar
39
696
Makka
4^Sv4
*\^n
r<\
&
Ghafir
40
708
Makka
^u£«
V«A
t»
j*
Fussilat
41
720
Makka
££*
VY«
n
cii*
Shura
42
729
Makka
4^X*
VY^
tY
Ujjlil
Zukhruf
43
739
Makka
4^Sv«
vr\
IT
0>>
Dukhan
44
750
Makka
£>**
v««
tl
0U3
Jathiya
45
756
Makka
££*
von
to
oWl
AMaf
46
762
Makka
aIx*
V1Y
tn
«j»u>-Su
Muhammad
47
769
Madina
OJL«
vn^
tv
Si -
Fat'h
Hujurat
48
49
776
784
Madina
Madina
vvn
VAi
1A
i^
K.
50
788
Makka
£>j*
VAA
0*
J
Dhariyat
51
794
Makka
£!x*
VM
o^
oCjIjUI
T>ur
52
799
Makka
A^X*
VM
oY
Jdl
Najm
[Camar
53
54
804
809
Makka
Makka
A«t
A^
or
Rahman
Wafi'a
55
56
814
821
Madina
Makka
if.
AU
AY^
00
on
Hadid
57
827
Madina
4JJl«
AYV
oV
JuJ^}\
Mujadala
58
834
Madina
aJ£*
Art
oA
^GJLI
Hashr
59
839
Madina
iJJU«
An
o<\
y£JI
Mumtahana
60
844
Madina
aJj£
Ait
n*
<CJ>W>W<JJ
Saff
61
848
Madina
iJJL*
AtA
n^
OWill
Jumu'a
62
851
Madina
4JJL«
ho\
nY
iiliJl
Munafilcun
63
854
Madina
OJU
A*l
nr
j^iULi
Tagabun
64
856
Madina
iJJl«
Aon
nt
i^>
Dalak
65
859
Madina
4JJL*
Ao^
no
J&Jl
Tahrim
Mulk
66
67
863
867
Madina
Makka
Anr
A1V
nn
nv
Kalam
Ha££a
68
69
871
875
Makka
Makka
AV^
AVo
nA
n^
r^ 1
3&JI
Ma'arij
Nuh
70
71
879
883
Makka
Makka
AV^
AAr
V*
v^
Jinn
72
886
Makka
4*X«
AAn
VY
:*»
Muzzammil
73
890
Makka
£x^
AV
vr
J*>
Muddatthir
74
892
Makka
£lx*
A^Y
vt
/all
Kiyama
75
896
Makka
i;^
A^n
Vo
oigji
lnsan
76
899
Madina
iJJL-
AM
vn
OCjVI
999
ivmm& mM$&>
Suna
Sura ta
Shafi
Wuri
&<A^\
&J
Mursalat
77
903
Makka
ZSsA
vr
vv
o^^lJI
Naba'
78
906
Makka
££L»
vn
VA
j3l
Nazi'at
79
909
Makka
aIx*
v^
V*
O^jLJI
'Abasa
80
913
Makka
<ux«
\\r
A»
J^
Takwir
81
916
Makka
ilx*
*n
A^
JJJ&I
Infidar
82
918
Makka
X&j*
MA
AY
jUaiJVI
Mucfaffifm
83
920
Makka
<IX«
*Y*
Ar
t jyLilail
Inshilcak
84
922
Makka
Al£v4
^YY
At
JliiJVI
Buruj
85
924
Makka
iIX4
Ml
Ao
^?
T>ari£
86
926
Makka
aISv*
m
An
jjiyi
A'ala
87
928
Makka
aIx*
^YA
AV
>Sll
Ghashiya
88
930
Makka
££**
^r»
AA
Cilij!
Fajr
89
932
Makka
Lp^»
^n
A<\
yjjjl
Balad
90
934
Makka
£&**
M-t
V
jdbi
Shams
91
936
Makka
£>•*»
*n
M
^^JlH
Lail
92
938
Makka
Z^A
^rA
M
J^»
Dnha
93
940
Makka
*J&J*
m>
<\r
^
Sharh
94
941
Makka
££L»
M\
m
c^ 1
TTn
95
942
Makka
^Sv4
My
m
^
4 Alak
96
943
Makka
££a
Mr
M
Jfll
ICadr
97
944
Makka
£!£w4
Ml
M
jOiJ!
Bayyina
98
945
Madina
iJwU
Mo
M
O
Zalzala
99
947
Madina
iSjC*
MV
M
^>
'Adiyat
100
948
Makka
Z>^»
MA
\ • •
ol>&l
Kari'a
101
949
Makka
A^V4
M*
^ \
ie-jUJi
Takathur
102
950
Makka
4%l»
^o *
W
'Asr
103
951
Makka
40v«
\o\
\>r
^1
Humaza
104
952
Makka
<LSv^
MY
w
s>4ji
FTl
105
953
Makka
£&*
Mr
^ •«
J^J
Kuraish
106
954
Makka
aIx*
Mt
^ «i
cr#
Ma'un
107
955
Makka
aI>w«
^00
^ »v
jjpllli
Kauthar
108
956
Makka
aIx«
Mn
W
i£)l
Kafirun
109
956
Makka
^L>v«
Mn
\>\
jjjlSCil
Nasr
110
957
Madina
iJwU
mv
\\>
^1
Masad
111
958
Makka
k£**
MA
\\\
jLIII
Ikhlas
112
959
Makka
4lSv4
M^
UY
^5U>I
FaM
113
959
Makka
££*•
M^
> \r
JU!I
Nas
114
960
Makka
<U>w4
M»
m
^Ull
1000
rr
(♦l)U) (J»T^-{..»)
ALKUR'ANI
MAIGIRMA
Da Kuma Tar jaman
Ma'anoninsa
Zuwa Ga
Harshen HAUSA